BOYAYYEN YARIMA

5-6

by @autarmama

🌈🌈BOYAYYEN YARIMA (MUTANEN DAJI)🌈🌈




BY.


ƳAT LELEN ROYAL STAR.



*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*

    {R.S.W.A}


***

 *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*

_(ROSWA) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*




P. 3-4.




Yana da Tsawo da Ƙiba , da Wani irin Faffadan Jiki irin na Manyan Sadaukan Jarumai masu Jini a Jika,, yana da cika Ido da Kwarjini na Musamman, ta yarda Duk wanda ya kalli Tsakiyar Idanunshi ko ya kallesa ba zai iya furta komai ba Saboda Mutuƙar Ƙwarjin da ya kasance yana da shi, Yana dai Baiwa sosai, Ya iya Sihiri kala-kala, Yana bayar da ko wani Kalar magani, Yana da Ilimi sosai, Wanda duk a cikin Kauyen bb mai iliminshi, gashi da Hikima da Kimiyar haɗa Abubuwa, yana Ƙoƙari gurin ganin ya haɗa Abubuwan da zai taimaki Rayuwar Danginsa na cikin Ƙasar.



Yana Ƙarasawa Gurin Aka basa guri, chan kusa da Sarki akan wata Kimtsatsiyar Kujera mai kyawun gaske, Ya Zauna, tare da Nannaɗe Ƙafafunsa, kamar yarda Al`ada ta tanadar, bayan gama dukkan kalolin Bukukunan da suka dace da Al`adarsu, Aka fara Bukin Zaɓen Mata, a Ƙa'idance Kwamanda ake fara bawa Damar Bude ido ya Zaɓi Macen da yake so, sai dai shi hakan baya cikin lissafin Tsarin Rayuwarsa, bashi da wani haɗi da Mata, baya shiga dukkan wata Sabga tasu, hakan yasa ko kallo basu ishesa ba.



Haka Aka shiga Zaɓe, kowa na zaɓar wadda ta Masa a cikin Matan da suke gurin, Yawancinsu an daukesu, Sai wata guda da take Gefe daya ta Cure jikinta guri daya ta haɗa kanta da Guiwa kamar mai jin sanyi, Gaba daya jikinta a Suturce yake, har gashin kanta baya buɗe, sai hannayenta da Ƙafafunta, sai kuma Bayanta da Suturar bata samu ta gama rufewa ba.



    Haka aka gama aka watse Amma ita babu wanda ya je gareta balle a Dauketa a matsayin mai Hidima, haka taro ya shiga Watsewa, Wata Yar Yarinya ce ta zo ta riƙe hannunta, tare da mata magana a hankali, maganar da taji ne yasa ta laluɓi Sandarta , A hankali ta miƙe , hannunta daya na riƙe da Sanda dayan hannun kuma na Dafe da Kafaɗar Yarinyar da tazo gareta, Tafiya suka fara yi a hankali , har suka ɓacewa gurin hasken Wutar.



A hankali shima ya miƙe daga gurin ya nufi hanyar da ya fito, Cikin Izza yake takawa, yana kallon sama da idanuwanshi, har ya ƙarasa bakin Bukkarsa, shiga ya yi tare da turo Ƙofar bukkar ya rufe.

Inda ya tashi ya koma ya kwanta, tare da dan Sanya hannunsa a gefen Zuciyarsa, ya lumshe idanu yana jin yarda take Bugawa da sauri-sauri.



     WASHE GARI.


Da sassafe ya fito Saboda Aikan Sarki da yace zasu Fita, hakan yasa Hasken Alfijir na ketowa, ya miƙe shirinshi ya yi cikin Sulkesa , ya fita, yana takawa cikin Taƙama, duk hanyar da ya nufa ana faɗuwa tare da gaisheshi, har ya isa Bukkar Sarki.

A waje ya tsaya Jakadiyarsa ta shiga , bayan mintuna ta fito tare da mishi iso ciki.



Zaune ya samu Sarkin yana Cin Gasasshen Nama, da akawa Gashin Ruwa-ruwa, mai dadin gaske sai kamshi yake.

Zama ya yi tare da gaisheshi, bayan ya Amsa ne ya mishi Umarnin yazo su ci, A ƙa'idar Mutanen Dajin bb mai yiwa Sarki musu, hakan yasa ya matsa suka dan taɓa, bai ci da yawa ba ya tsame hannunsa tare da matsawa baya.

Yana zaune a gefe har ya gama, A tare suka fito gari suka fara zazzagayawa, daga nan kuma suka shiga cikin Jeji, sune basu dawo ba sai da gari ya dan fara Alamar yin duhu.



Tafe suke,akan Dawakansu, wanda da Alama tafiyarsu tayi, nisa kasancewar yarda su kansu Dawakan suke tafiya cike da gajiyawa.



Zaune take a ta chan bayan gari, Gefenta Wasu Yan mata ne, suna Irin Taɗinsu na Tsakankaninsu, Sai wasa da dariya suke, Saɓanin ita.

 Fuskarta a Buɗe, Kyakyawace sosai , Launin Fatarta ba za'a kirasa baƙi ba sanan kuma ita ba fara ba, Sai dai ace mata Chocolate calour, tana da dogon hanci da Dan ƙaramin baki, mai dauke da Siraran Ƙananan Fararan Haƙora, Idanunta kalar Gold ,wanda suka ƙara mata kyau, suka kara fitar da kyawun Fuskarta, 

Tsurawa Zara-zaran yatsun Hannayenta idanu tayi, wanda idan baka santa ba, ko kuma ka mata kallo daya zaka dauka Tana gani da Idanuwan nata, sai dai ko kaɗan bata gani da su, Amma kuma suna da kyawu sosai

.



 Zaune take gefe daya, ta nannaɗe ƙafafuwanta, shiru ita kaɗai, kallo daya zaka mata, kasan cewar ba wai taji dadin zaman gurin bane, ko kuma tana zaman gurin ne cikin jin dadi a'a, Zamanta gurin yafi kama da zaman wanda yake cikin matsananciyar Damuwa da Begen wani Abu da kayi Rashi Zama ne irin na wanda yake Mararin samun Wani Abu, zama ne na irin wanda ya miƙa gaba daya Ragamarsa da Aqalar Rayuwarsa, Zama ne irin na Tsammani.



     Jin Ƙarar Takun Dawakai yasa ta kara Rabewa A bayan bukkar da take, ta lafe sosai, jikinta na dan karkarwa, Har sai da ta ji Takun Dawakan ya sihirta Alamar sun bar gurin kafin ta sauke Nannauyar Ajiyar Zuciya, Sandarta wadda take mata Jagora ta Laluɓa . har Allah yasa ta ji inda take, cikin sauri ta dauka, tare da miƙewa, gyara Tufar jikinta tayi, tare da fara Ɗaddogara Sandar tana laɗuɓe har tayi nisa sosai, Gurin Wani Bukka ta tsaya, tare da zama tana goge zufar da ta tsatsafo mata a goshi.



"Bul-bul!", ta ji an kirata, a dan zabure ta Amsa tana mai kama jikinta guri daya, Cikin Yarensu ta fara zaginta, da watsa mata wasu Suturu irin nasu , ta bata Umarnin ta je ta wanke mata su yanzu ta kawo mata, Dauka tayi, ta nufi Rafinsu inda suke yi wanki, Babu kowa a gurin, Haka ta fara Wankin , Cike da Tsoro Jikinta na Rawa, haka take yin Wankin, tana dan wawwaga Kudu,da Yammanta, sai kace Mai neman wani Abu, Wanda a Baɗini kuma Zallar Tsoron da Ya mamaye mata Rayuwarta ne yasa take hakan.

Magana taji a bayanta da Sauri ta waiga, ta ma Manta da tana gaban Ruwa, juyawar kuma da tayi ne yasa ta ƙara kusanci da Ruwan Sosai, Wata gigitacciyar Magana da ta tsoratar da ita ta ji, baya tayi cikin wani irin tsoro.



Bata Ankara ba ta ji ta faɗa cikin Babban Rafin da yake Bayanta, mai zurfi da Faɗi, facal-facal ta shiga yi cikin ruwan tana neman Hanyar da zata bi ta fito daga cikin ruwan, Ita ba Idanu ba, balle ta taƙala wani gurin ko ta kama wani abun ta fita, gashi gurin babu mai ceto, gashi ko ruwan bata iya ba, ta Riga da ta gama Ruɗuwa, ta Sadaƙas, Sai ƙoƙarin Fiddo kanta take.



Hakan yasa ta fara nutsewa cikin ruwan, ta shiga yin Ƙasa, dai-dai lokacin da ya ƙaraso Gurin Rafin domin shayar da Dokinshi, kaya ya gani a Gefe, bai kawo komai a ransa ba ya fara bawa Dokinshi ruwa, kamar An ce ya daga kanshi ya kalli Cikin ruwan ya fara hango Kwayayen Numfashi, dan ware ido ya yi, dubawa ya ƙara yi da kyau, Tabbas mutum ne a cikin ruwan, Cikin wani irin sauri ya nutsa cikin Ruwan.



Nemanta ya shiga yi, Ya dade sosai yana nemanta kafin ya sameta, Fiddo kanshi ya yi daga ciki, haka ya ɗagota fa ha gigitacciyar Magana da ta tsoratar da ita ta ji, baya tayi cikin wani irin tsoro.



Bata Ankara ba ta ji ta faɗa cikin Babban Rafin da yake garin, mai zurfi da Faɗi, facal-facal ta shiga yi cikin ruwan tana neman Hanyar da zata bi ta fito daga cikin ruwan, Ita ba Idanu ba, balle ta taƙala wani gurin ko ta kama wani abun ta fita, gashi gurin babu mai ceto, gashi ko ruwan bata iya ba.



Hakan yasa ta fara nutsewa cikin ruwan, ta shiga yin Ƙasa, dai-dai lokacin da ya ƙaraso Gurin Rafin domin shayar da Dokinshi, kaya ya gani a Gefe, bai kawo komai a ransa ba ya fara bawa Dokinshi ruwa, kamar An ce ya daga kanshi ya kalli Cikin ruwan ya fara hango Kwayayen Numfashi, dan ware ido ya yi, dubawa ya ƙara yi da kyau, Tabbas mutum ne a cikin ruwan, Cikin wani irin sauri ya nutsa cikin Ruwan.



Nemanta ya shiga yi, Ya dade sosai yana nemanta kafin ya sameta, Fiddo kanshi ya yi daga ciki, haka ya ɗagota da hannu daya zuwa Gabar Rafin.



    A sume ya daukota ,Ajiyeta ya yi a Gaɓar Ruwan, tare da sanya gaba daya hannayensa ya danna cikinta, Da karfi ya ƙara danna cikinta, Tari ta fara yi da Aman Ruwa, jikinta na rawa sosai ta riƙe hannunsa, tana jin wani mashahurin sanyi mai shiga cikin bargon jiki, Numfashi ta shiga fesarwa, tana zazzare manya-manyan idanuwanta wanda in ka kalleta zaka rantse da Allah tana gani da su.



Hannunsa da ta riƙe ya zame daga cikin nata ba tare da ya kalleta ba ya ja Dokinsa suka bar gurin, Kuka ta shiga yi tana laluɓen inda zata ga sandarta, Amma bata ganta ba, Sai wani dan Icce da ta gani a gefen inda ta ajiye kayan wankin da take, jikinta na rawa ta dauki sandarta , ta fara tafiya tana tafiya tana cin tuntuɓe saboda tsananin Tsoro da rawar da jikinta Ya ke.



      A haka ta nufi gida tana laluɓen hanya, Har ta ƙarasa gida bata haɗu da kowa ba, Sakamakon Haɗarin da Hanyar Babban Rafin yake da shi, Yasa aka Haramtawa Dukkan Wani wanda yake Garin bin Hanyar da dare, gashi ita kuma Daren ya Risketa akan hanyar, shi yasa take a Matuƙar Tsorace.

Haka har ta ƙarasa gida.




Bayan Kwana biyu ne kuma, Gaba Daya Ɓoyayyen Yareema Yay Ƙaura daga cikin Garin Fur, Ya tafi izuwa Darfur Chan Tsakankanin Dutsin Jebel Sî Da Jebel Mara, Inda Mafi Akasarin Lokutta Anan ya fiye yin Rayuwarsa, bai fiye son Takura ba, hakan yasa yake zamansa a cikin Kaɗaici don ya fiye masa Ciki gari Wani lokacin.



     Zaune yake a Gefen Ruwan da ya Ratsa Tsakiyar Manyan Duwatsun na Jebel Sî da Jebel Mara,Manyan duwatsu Masu Ɗumbin tarihi da Asali, sun kasance suna da girmzn gaske, girma irin na wuce Misali, A tsakankaninsu Akwai Wani ruwa Mai Ƙawanya da Yawan Gaske, Kaɗan daga cikin Wani Yanki na Ruwan ma Yana zubowa ne daga Yankin Dutsen Jebel Sî.



    Gaba daya gurin Yana dauke da Korayen Tsirrai masu ban sha'awa da kyau, Akwai dukkan Wani Nau'in Ittace wanda ake Buƙata domin Ci, Haka kuma dajin Na dauke da Manyan Namun Dawa, wanda suke Rayuwa ba tare da Cutar Wani ba, Suna zaune tsayin Shekaru, basa da Cutar wa sai idan ka nemi Cutar da su Shine suke Cutar da kai.


  

     Abin cin Kifi ne a gefensa, ya zura Ƙafafunsa a cikin ruwan yana yi yana jefa musu Abin cinsu, Su kuwa Abin cin da suke gani ne yasa suke ta facalniyar ci, suna Tasowa sama,har suna watsa masa ruwa, Duk da bashi sha'awar Wasu Abubuwan Amma hakan na Matuƙat basa Sha'awa, hakan yasa yafi kaunar kasancewa a gurin.



       Iska ce mai ƙarfi ta Fara Kaɗawa a Filin Gurin, yana yin yarda Iskar ke kaɗawa ne yasa sa dan Curw jikinsa, yana yin Ƙasa da zara-zaran Gashin idanunshi, tare da shaƙar daddadar iska mai kaɗawa.



      A hankali Aka fara Yayyafi, cikin nishaɗin da yaji ya zo masa, ya kwanta yana kallon Sama, tare da lumshe idanunshi.

Ƙarfin Ruwan da yaji yana ƙaruwa ne ya tilasta masa tashi daga gurin , ya nufi babban Bukkarsa da yake Rayuwa a ciki, yana shiga ya kulle,kamar kuma jiran shigarsa ake aka fara Ruwa sosai.



       ****



   Zaune take A faffaɗan tsakar gidansu, ta tsarw guri daya da idanu tana kallo, in ka ganta taka dauka tana gani ne da idanuwanta.



   A zabure ta ƙanƙame jikinta jin saukar ruwa masu sanyin gaske a jikinta, Cikin faɗa, ta fara Mata magana da zaginta, Da sauri ta tashi daga inda take, da Lalube ta Laluɓi Kwaryar da take chan Nesa da ita.



     Kasantuwar tasan komai a inda yake yasa ta fara Lalaɓa, cikin sa'a komai a inda tasan yake anan ta samesa, dandanan ta Fara Abun da aka sanyata, daga inda take tana jiyo yarda take zaginta da Mata Faɗa, Ita dai bata ce komai ba, sai Aikinta take kanta A ƙasa.



    Cikin Ƙanƙanin lokaci ta Gama Aikin da ta sanyata, duk da Tsananin Yunwar da take ji, Haka ta yi Abin cin kuma ta barshi a inda yake Sakamakon Hanata cinsa da tayi Ƴar ƙaramar Bukarta Mai kama da Aƙurƙin kaji ta shiga.



    Zama tayi a gefe, don ita ko Arzikin Taburma bata samu ba, Wasu Tsibirin kaya ta jawo ta daura kanta a Sama, ta ƙasan kayan ta zaro wasu Yan Abubuwa Ƙwara biyu ta rugumesu a Kirjinta, tare da fara rera kuka.



     Kukan da taken ma Cikin tsari take yinsa, babu wata Hayaniya a cikinsa, sai Yar shasheƙa, da haka barci mai nauyin gaske ya dauketa, tana rungume da Abubuwan a Kirjinta.




     Cikin Natsuwarsa yake tafiya Akan lafiyayyen Ƙosasshen Dokinsa, Shi kansa Dokin yana da wani irin Cika ido na Musamman.



     Tun daga nesa A`lamar zuwansa ta shelantawa Gaba ki daya Yan garin, Ko da ya shigo cikin .......


#400.


1499884120

UMMA SALMA SANI

ACCESS BANK.



***



P.R.O SALMAH🤙🏽SALMAH🤙🏽