ƊAURIN ƁOYE

Page 01 to 05

by @huguma

DAURIN BOYE

PAGE 01




 Sake gyara tsaiwarshi yayi jikin machine din nasa samfurin lifan kirar MOTO B,agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yana sake qiyasta mintocin daya kashe tsaye a qofar gidan,tabbas banda wani babban dalili babu abinda zaya sanyashi zaman jira har kamar haka,babu abinda ya tsana a rayuwarshi kaman jira,mutum ne shi mai kiyaye qa'ida wanda bai yarda da samfurin wannan maganar da hausawa ke bawa lokaci ba na african time.



   Sauke hannun nashi yayi ya maida dubansa ga madaidaicin get din dake maqale da katangar gaban gidan wanda ya kasance shine kofar da zai sadaka da ainihin cikin gidan,kaman jiran hakan kuwa ake qofar ta soma yunkurin budewa,cikin sakannin kadan matashiyar dake yunqurin bude qofar ta bayyana.



   A hankali take takowa zuwa inda yake,sanye cikin dinkin atamfa riga fitted da skert wanda ya zaunawa jikinta das,ta lullube jikinta da mayafi wanda baikai matsayin medium ba,a hankali yayi kokarin mamaye fuskarshi da murmushi duk da yadda fuskarta take kadaran kadaham hakan bai dameshi ba duk da yana ankare,ba fara'a sannan ba kuma a daure take can ba,kallo take kare masa tun daga nesa kaman yadda ta saba masa duk sa'ilin da ya ziyarceta,shirt ce jikinsa ruwan makuba da bakin wando jeans mai matsakaicin kudi,kafafunsa saye da takalmi budadde dinkin hannu na kasuwar kofar wambai,fes yake hakanan kayan sun masa kyau babu laifi,sumarshi kanshi zuwa sajensa a gyare a taje wanda hakan ya sake bayyana sirrin kyan da Allah ya bashi,ba shakka banda wani abu guda tak muhammad ya cika mijin aure wanda za'a iya nuna shi a ko ina,saidai wannan abun daya rasa din ya sanya ta cireshi daga tsarin mutumin daya cancanci aurenta.



"Barka da fitowa gimbiya zulaiha" ya fada cikin sassanyar muryarsa wadda na daya daga cikin abinda ke burge zulaihan tare da shi,duk da bata jin zata iya bashi damar kasancewa cikin rayuwarta,yana ci gaba da nazarin yanayin fuskarta a fakaice sanda ta amsa masa

"Barkan ka" ta fada cikin wani salon shan qamshi da basarwa

"Har na fidda rai ai,na tsammaci yau bazan samu ganinki ba"

"Kusan da hakan ce ta kusa faruwa,saboda zamu fita ne da maama,sannan ma kuma bansan zaka zo din ba,yanzun ma zuwa nayi na gaya maka.....don Allah ya kamata ace duk sanda zaka zo ka fara sanarmin tukunna kafin kazo din"ta fada kanta tsaye tana yamutsa fuska murmushi ya saki gami da dan duqar da kanshi qasa yana wasa da duwatsun dake shimfide a qofar gidan,baice komai ba sai murmushin da yaci gaba da fitarwa yana tattaunawa shi da zuciyarsa,tabbas yasan wannan rana na nan tafe,fiye da haka kuma na nan zuwa nan gaba kadan,wannan ba baqon lamari bane a gareshi,zulaiha ba itace mace ta farko da makamancin hakan ta faru tsakaninsu ba,saidai bazai yanke mata hanzari ba,zai jirata har zuwa ranar da zai zata furta kota yanke alaqar dake tsakaninsu da bakinta,sai bayan daya kammala wannan tunanin sannan ya dago ya dubeta

"Shikenan....babu damuwa...kiyi hakuri" ba tare data tanka ba ta juya tana niyyar komawa cikin gidan nasu

"Ki gaida maaman idan kin shiga"

"Zata ji" ta fada gami da jan qaramin tsaki can qasa ta shige gidan gami da rufe qofar gidan garam.



   Kai ya girgiza bayan shigewarta cikin gidan yana sakin murmushi tare da cije lebansa na qasa,cikin qwarewa ya haye saman babur din bayan ya tadashi ya figeshi cikin gudu ya fice daga layin,zuciyarsa cike fal da tunani da mamaki,mamakin da har yau yaqi barinsa,tsahon shekaru kenan wannan abu na daure masa kai,da gaske haka rayuwa ta koma?,ya gode Allah da baiyi gaggawar yiwa hukunci wa rayuwarsa ba.



   Titi ya hau ba tare da yayi wata doguwar tafiya ba ya soma sauka daga kan kwaltar zuwa gangaren titin,daf da wasu jeran baqaqen motoci da farare a qalla guda biyar ya soma qoqarin tsaiwa,wanda tun kafin ya kai ga tsaiwar wasu matasa kimanin su bakwai sanye da coat baqi da fari suka doso shi,kowanne fuskarshi manne da baqin gilashi wanda hakan ya sanya baka iya ganin qwayar idanunsa,ya kuma qara musu kwarjini qwarai,daya daga cikinsu shi ya riqe babur din sanda ya sauka,yayin da dayan ya matso kusa da shi yana bude masa qofar daya daga cikin motocin wadda duka ta fisu kyau da girma,sai da yaga ya shiga sannan ya rufe masa qofar,sauran suka zagaya suka shige ragowar motocin nasu,yayin da daya daga cikinsu shi kuma ya haye babur din ya bisu a baya.



   "Ya dai,akwai wani sauyi ko ci gaba kuwa yau?" Wani kyakkyawan matashi wanda aqalla zaiyi shekara talatin da hudu dake zaune daga corner motar riqe da magazine ya fada yana dubanshi,fuskarshi na nuna alamun dariya yakeson yi,takalman qafarsa ya soma yunkurin cirewa gami da agogon hannunshi ba tare daya dubeshi ko ya amsa masa ba,ya dannan wani madanni dake gaban sit dinshi,wani qaramin akwati ne ya fito ya zuba agogon takalmin harda wayar dake hannunshi qirar VIVO bayan ya kasheta,ya maida akwakwun muhallinsa ya jingina da makarin kujerar sannan ya waiwaya ya dubeshi

"Me kake tunani mahmoud?,ita dinma kaman sauran,abun ma kamar yana sake lalacewa ne" ya qarashe maganar yana lumshe idanunsa tare da sauke numfashi



  "Duk inda xaka je ka dawo dai shawarata ce kan hanya,na sha gaya maka ka sauqaqewa kanka walaha,ka laluba cikin familynka,akwai gomayyar 'yammatan dake sonka ka zabi daya cikinsu ka huta,kaga wannan babu wani fargaba tattare da kai,duka ana tare". Kansa yaci gaba da girgizawa ba tare daya bude ido ya kalli mahmoud ba,tsahon sakanni tamkar bazai amsa mishi ba sannan ya ware idanunsa yana duban sit din dake gabansa

"kana tunanin qaramin abu ne ya sanya na guje musu dukkaninsu na xabi inbiyo ta wannan hanyar?,su dinma kusan duka abu guda ne,babu wani banbanci,halayyar daya ce dai kaman yadda sunansu yake daya,abu guda dukkaninsu suke wa,manufarsu guda ce......" Maganar tashi ta katse sakamakon shigowar kira wayar tasa,ya maida qwayar idanunsa ahankali kan wayoyin dake zube a gefansa,kusan lokaci guda idanunsu shida mahmoud suka sauka kan wayar RAMLA sunan dake yawo kenan bisa screen din,murmushi mahmoud ya saki ganin ya kau da kanshi tamkar ba cikin wayarshi kiran ya shigo ba

"Yallabai ka daga mana?"

"Qyaleta kawai" ya bashi amsa kai tsaye gami da danna wani madanni,wani dan qaramin abu mai kama da fridge ya bayyana,cikinsa nau'ikan abubuwan sha ne masu sanyi da duka duka basu wuce gwangwanaye da kwalba goma sha biyu ba,daya a ciki ya dauka hadi da cup ya maida abun muhallinsa ya koma ya jingina da kujera ya tsiyaya yana kaiwa bakinsa ba tare da yabi ta kan qorafin daga waya da mahmoud ke masa ba,a maimakon hakan ma sai ya maye gurbin qorafin nasa da tambaya

"Jirgin qarfe nawa zamu bi ne?" Tunda ya masa hakan yasan bai bukatar xancan,saboda haka shima ya tayashi

"Yanzun airphort din muka nufa ai,tunda duka duka awa guda da 'yan mintuna ya rage lokacin tashin jirgin ya cika"

"Ok,kafin nan mu biya na sauya kayan jikina"

"Ba matsala" ya fadi yana gayawa driver inda zasu fara zuwa kafin su isa airphort din.



      🧣🧣🧣🧣



   A nutse ta miqe daga saman abun sallar tana sakin 'yar qaramar hamma tare da furta "a'uzu billahi minash shaidanir rajim" gami da ninke daddumar ta mata ma'ajiya a muhallinta,zare hijabin jikinta tayi tanayi tana duba agogon dake maqale a bango saboda gudun makara,qarfe shida na safiya ya nuna mata,hakan ya mata dadi ta tabbatar kafin lokacin tafiyarsu makaranta ta kammala dukkan abinda zata yi din,gyara dankwalin kanta tayi wanda ke niyyar zamewa saboda santsinsa da kuma santsin sumar kanta,sannan ta zura slippers ta bude qofar dakin nata ta fita a hankali.



    Makekan falon nasu shiru yake tamkar babu halittar kowa cikin gidan,bugu da qari mamaye yake da dan sauran duhun asuba da bai gama yayewa ba,babu motsin kowa,don hatta da masu aikin gidan basu tashi ba,kunna qwayayen falon tayi take haske ya game ko ina ya kuma bayyana asirin kyan da falon ke da shi,sannan taci gaba da takawa a hankali ta doshi wani corridor wanda a nan kitchen dinsu yake.



   Kitchen ne na alfarma wanda ya mallaki dukkan wani nau'in kayan amfani da kitchen ka iya buqata,kai tsaye ta nufi jikin wani dan qaramin Allo wanda ke dauke da timetable na abincin da gimbiyar gidan ke buqata kowacce rana,alhamis ce saboda haka ta sauke idanunta kan THURSDAY dake rubuce baro baro,ta kuma karanta abincin dake qarqashin ranar,kanta ta jinjina saboda yau aikin nata kaman mai yawa ne,gashi a jiya bata samu ta duba me zata girka ba yau sakamakon bacci fa yayi nasarar saceta tana tsaka da karatun test da zasuyi a safiyar yau,cikin hanzari ta bude freezer ta fiddo dukkan abinda zata buqata,sannan ta wuce store dake cikin kitchen din ta fiddo kayan amfani,sannan ta soma aikinta cikin hanzari da qwarewa.



   A qalla ta shafe kusan mintina talatin sannan ta jiyo motsi alamun ana niyyar shigowa kitchen din,fuskarta qunshe da murmushi wanda ya sanya dimple dinta dake dukka kumatunta lonawa,tunkan ta qaraso tasan wacece,ita kadai ke tashi ta kama mata aiki,ita daya ce matar da hakanan Allah ya hada jininsu take qaunarta,ita daya ce take ganin qauna daga idanunta,irin qaunar data rasa,irin qaunar da take buri da fata ta ganta daga wajen wadda tayi silar kawota duniya saidai har yau abu yaci tura,a wajenta ne kawai take ganin kulawa qauna da kuma sassauci.



    Ita dince kuwa,daya daga cikin masu aikin gidan ce inna laraba,fuskarta fadade da fara'a tace

"Yanzu inna laraba yau dinma ba zaki kwanta ki huta ba?,ina cewa jiya da qyar kika samu ciwon qafar nan ya barki?" Itama fuskarta qunshe da fara'ar tace

"Banda abinki shatu ai kema kinsan ban saba da wannan baccin bayan sallar asubar ba,kuma na tabbatar kina nan ke daya kina fama da kacaniya" ta fada tana qarasowa kusa da ita,murmushi ta saki sannan cike da girmamawa ta gaida innar kaman yadda take kiranta tare da tambayarta ya qafar tata,amsa mata tayi itama cikin kulawa kafin ta matso da niyyar kama mata aikin,duk yadda taso hanata amma innan sam taqi,haka ta sakar mata suka ci gaba da aikin tare suna hira.



   Bata ankara ba taga lokaci ya ja,har qarfe tara saura na safiya,idanu ta zaro don tun jiyan da daddare anty asma'u ta ja mata kunne cewar qarfe tara zata fita,kuma driver ba tsayawa jiranta zaiyi ba,ruwanta ta shirya da wuri ruwanta karta shirya ta samu mai ajjiyeta makaranta"hakan ya sanya ta tattare komai a gurguje ta soma shiryawa saman qawataccen teburin cin abincin dake sashe na musamman dake cikin falon.



    Plates da spoons suka rage suta dauko ta dawo da niyyar ajewa daga nan ta shiga ciki ta shirya itama,duk da cewa ita sai goma zata fita,amma dole ta shirya tabi asma'un koda qarfe bakwai asma'un zata fita,tsaye ta tadda ta shirya tsaf cikin wata doguwar rigar material,ta zuba makeup sosai,hannunta maqale da 'yar madaidaiciyar hand bag mai azabar kyau,kafadarta rataye da mayafinta wanda wanda haka qa'idar saka mayafinta yake,qwayar idanunta saye da tafkeken sun glasses wanda ya kusan cinye rabin fuskarta,table din take qarewa kallo har sanda aysha ta qaraso wajen tana dora plates din saman teburin gami da gaida asma'un.



   Bata damu da amsa gaisuwar da take mata ba saima tambayar data jefo mata

"Waima baki shirya ba?" Ta fada cikin bacin rai tana zare glass din fuskarta kasancewarta mace wadda qanqanin abu sai ya bata mata rai ko ya tunzurata

"Yanzun zan shirya in sha Allahu" ta fada a tausashe,cikin hasala asma'un tace

"Kada ma ki shirya wannan ya rage naki,ni dama na soma gajiya da tafiya dake gaskiya,ya kamata daddy ya barni haka nan ya raba mana tafiya tunda babu dole.....ina cewa tun jiya na sanarmiki lokacin da zan fita,amma saboda tsabar raini da salon ki jawa mutum fada baki tashi kin gama komai a kan lokaci ba"

"Kai...kai me yake faruwa haka da sassafen nan kuma lafiya?" Cikin bacin rai asma'u ta juya tana kallon mahaifiyarta dake saukowa daga stairs,shirye cikin tsadajjen lace na alfarma,hannayenta da wuyanya duka sanye da jewels da banguls masu tsada

"Mommy nida yarinyar nan ne mana,wai ki duba fa jiya gabanki na gaya mata when zan fita shine wai har yanzu bata shirya ba"

"Garin yaya ke ayshatu?...." Jin tambayar tayi banbarakwai,tunda dukkaninsu sunsan me ya tsaidata,hidimar abincin safen asma'un ne,wanda dukkansu sun kwana da sanin cewa don ta itama a soke abincin safe,totally ma ba damuwarta bane abinci

"Ya kuma kika tsaya,jeki ki shirya,idan kuma har ta gama baki fito ba sai ki samu napep ya kaiki" ta fada itama tana jan daya daga cikin kujerun dining din da alama karyawa zatayi akwai muhimmiyar fita kenan.



    Juyawa tayi a hankali ta doshi corridor din da dakunansu suke,sam batayi mamaki ba tunda ba yau bane farau,hajiya sa'adatu irin matan nan ne da basu cika ganin aibu ko laifin dansu ba,bugu da qari tana da attitude na idont care kan lamuran da ba nata ba,tayi ma rawar gani yau data tanka,idan da taso Allah ya kyauta kawai zata ce tayi zamanta ta hau hidimar gabanta ya tasu koma ya zasu qarke ohon mata,indai hakan bazai shafi shalelen tata ba ko kuma ita bazai kawo mata wani cikas ba.



    Duk da cewa a gurguje ta shirya amma hakan bai sata ta samu nasarar tadda asma'un ba,saima hajiya sa'adatu data samu tana yunqurin bude murfin mota zasu fita ita da drivanta,kallo daya tayi mata tace

"Gashi har asma'un ta wuce tun dazun,saidai ki qarasa titi kibi ta haya" ta qarashe maganar tana shigewa motar tare da yunqurin rufewa

"Ba komai zan qarasa din mommy,a dawo lafiya"

"Allah yasa" ta masa sanda drivern ya fara jan motar suna niyyar ficewa daga gidan ba tare data damu da yadda ayshan zata kai kanta makarantar ba.



   Tana nan tsaye har motar mommy ta fice sa'annan ta soma takawa a hankali cike da nutsuwar data zama tambarinta tabi bayan qurar motar ta fice daga gidan ta 'yar qaramar qofar dake maqale jikin get din.



   Duk da yake akwai 'yar tazara kadan tsakanin gidan nasu da bakin titi amma sam bata ji tafiyar ba,hakan ya faru ne sakamakon yadda qwaqwalwa da zuciyarta baki daya sukayi zurfin tare da nisan kiwo wajen tunani,tunani qwaya daya da ko yaushe bata gajiya da shi,hakanan batasan randa babin tarihin rayuwarta zai rufe ba,hakan batasan meye qarshen nasa ba,yaya qarshen nasa zai kasance?,wata iriyar cukurkudaddiyar rayuwa da tayi take kuma kanyi ita ke mata kai kawo cikin qwaqwalwarta.



   Sam ta sha'afa sai data tsaida mai napep sukayi cinikin nawa zai kaita sannan ta laluba jakarta cikin fargabar ta fito da kudi?,Allah ya taimaketa jakar a ciki ta sanya kudaden da daddy ya bata sanda zaiyi tafiya,ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana hamdala cikin zuciyarta.



   Kusan babu wanda ta tarar cikin ajin,sakamakon akwai tazarar awa guda daga lokacin da za'a shiga lacture din da sanda tazo,guri ta samu na musamman inda tafi sha'awar zama ta zauna,sa'an nan ta zaro handout dinta taci gaba da dubawa kafin lokacin da zasu zana test din ya cika.


   

*mrs muhammad ce*👑



*DAURIN BOYE



     *NA*


*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*





     0⃣2⃣






 Kusan rabi da rabi take karatun,fiye da rabin hankalinta ya ta'allaqa ne akan wayarta,wadda ba komai take kalla ba sai wasu numbers wanda ke rubuce da sunan MAMA NA,ta kallesu yafi sau shurin masaki,ta kwatanta kira fiye da irgen yatsun hannunta saidai ta kasa hakan,ba wani abu bane ya jawo haka ba illa tsoro da fargabar abinda kiran zai biyo baya,taji ance bata ji dadi ba,tana so ta kirata ta mata sannu da jiki,saidai bata da wannan damar,ba qaramin qunar baqin wake take ba duk sanda tayi jarumtar kiranta,wanda hakan daga qarshe baya haifar mata da d'a mai idanu.


  

   "Qawata sarkin sammako" taji an ambata ta gefanta,wayar ta rufe ya dago kai fuskarta qunshe da murmushi tana duban Aliya dake sauke jakarta daga kafada kana ta yiwa kanta mazauni kusa da ayshan itama tana murmushi

"To ya za'ayi" ayshan ta maida mata amsa tana gyara zamanta

"Hala yauma uwar masu gidan zata fito da wuri ne kika kwaso qafa kika biyota?" A maimakon ta bata masa murmushi ayshan ta saki,tasan halin rigima sarai irin na Aliya.


   'Yar tsama suke qwarai da asma'u,basa hada hanya da ita,saboda banbancin halaye qwarai dake tsakaninsu,bugu da qari tana jin haushin yadda take mu'amalantar ayshan wadda ta zame mata qawa kuma aminiya a dui fadin makarantar,sosai Aliya keson aysha sabo managartan halayenta,nutsuwa haquri gami da kunya,uwa uba ayshan na daya daga cikin daliban da sukayi fice a duk fadin department dinsu,kai bama iya tsangayar tasu kadai ba a duka makarantar ma.


   Kai Aliya ta kada cikin takaici,saidai ayshan bata bata damar cewa komai ba ta tareta

"Kinso yau ki makara qawata,ya akai haka?"

"Hmmm,wlh yau mama ta tsaidani sai dana hadawa ya khalil breakfast,Allah ne ya soni na masa sharp sharp na fece,da Allah ne kadai ya san makarar da zanyi" duka tana zancan ne sanda take ciro handout dinta daga jaka,kafin su sake cewa komai lacturer din ya shigo ajin.



   Qarfe uku na rana ta kammala duk abinda zatayi cikin makarantar,hakan ya sanya ta tattara komai nata ta fito don ta qarasa inda zata samu asma'u,saidai koda taje wayam taga wurin babu alamun motarta,hakan ke nuna bata cikin makarantar,bata wani damu ba ta soma takawa da qafa don zuwa bakin get din makarantar don ta sami abun hawa,don yau Aliya ta rigata tafiya gida,ita ta tsaya ta dudduba wasu karatuttuka.



   Jin qarar mota a bayanta ya sanyata sake rabewa don bawa motar damar wucewa,a sannan idonsu ya hadu da drivern,asma'u ce,ita da wasu mutum biyu a motar,da alama qawayenta ne,dauke kai asma'un tayi tamkar bata ganta ba,sai tama qarawa motar wuta tayi hanzarin wuce ayshan,sam hakan bai dameta ba,saboda ba yau farau ba,babu abinda asma'un ta tsana nan gidan duniya irin alaqar da zata bayyanar da cewa ayshan jininta ce,gida daya suka fito ko suna da dangantaka,tunda ayshan ta fahimci hakan sai itama take baya baya da duk wata alaqa da zata hadata da asma'u cikin bainar jama'a.



   Kai ta jinjina kawai taci gaba da takawa zuwa qofar makaranta,wannan abun na asma'u zata iya cewa bai bata ranta ko kadan,idan ma ya bata din bai wuce digo daya cikin dari ba,a yanzu qyamatar da take fuskanta take kuma bata mamaki ta shafe ko wacce iriyar qyama da qiyayya da dukkan wata halitta zata nuna mata a doron duniya,dukkan wata tsana saidai ta biyo bayan waccar,da wannan tunanin ta tsaida wani dan sahu dake niyyar gifatata ta masa kwatance inda zata ta fada ciki.



   Kamar kullum yauma a qalla ya kusa shafe mintuna ashirin yana tsaye yana jiranta,har sai data kaishi ga qosawa ya haye saman babur din da yazo da shi ya zauna,saboda rashin sabo saura kadan babur din ya tuntsira da shi Allah ya taimaka cikin zafin nama yayo gaba ya dawo ya zauna dai dai,mahmoud dake zaune cikin motarsu dake fake a wani layi ya tuntsire da dariya harda duqawa,ba don ba dabanba da ya fito ya masa vedio ya ajjiye saboda tarihi,saidai yana tsoron tashin balli tilas ya zauna cikin motar kamar yadda yayi masa umarni.


   Sake duba agogonsa yayi yana qissimawa ranshi mintinan da zai qara wanda matuqar bata fito ba zai qara gaba,a gajiye yake,daga airphort yake ko gida bai isa ba ya sauya kaya ya canza akalar tafiyar tasa zuwa gidansu,bayan ya yiwa daya daga cikin yaranshi waya ya kawo masa babur din,kwanaki goma ya kwashe a qasar da yaje,bai kuma samu damar kiranta ba tunda ya tafi saboda gudun tonuwar asiri,don kada ta tsammaci ya janye hakan ne ya sanyashi tahowa kai tsaye gidansu.



   Kamar ko yaushe yauma haka fuskarta take,ta qaraso inda yake saidai a yau waya take amsawa,ganin ta iso gareshi yasa ta bada uzurin zata sake kira ta kashe wayar ta lanqwasheta a hannunta yauma tana sake qare masa kallo a kaikaice

"Allah ya baka kyau na nunawa sa'a,saidai hakan ba zaiyi tasiri a raina ba saboda kana da babban naqasu na rashin hatimin nasara" duka take wannan maganar a ranta,sama sama suka gaisa tamkar baqin juna,shi kansa yana jin wani irin cikin ranshi,duk yadda yaso kawo sabo da shaquwa tsakaninsu zulaihat taqi bashi dama.



   Shiru ya ratsa tsakaninsu bayan ya gama iya maganganun da yaga sun kamata,saidai rashin samun gamsashshiyar amsa yasa maganganun nashi basuyu tsaho ba

"Ammm...dama akwai abinda nakeson gaya maka" ta fada tana gyara yafen mayafinta

"Uhmmm...babu damuwa,yi maganarki"

"Cewa nayi don Allah daga yau ina son ka janye daga zuwa wajena da kake....saboda ina da buqatar space"qaramin murmushi ne ya subucewa fuskarsa,abinda yake zato yau zai tabbata kenan

"Amma wani laifi na aikata ne haka" kai ta kada tana dan tabe baki

"Ko daya,kawai na gaji da alaqarmu ne haka.....har yau jiya iyau,kai ba qaruwa ake da kai ba" ta qarashe furucin qarshe can qasan maqoshinta,saidai abinda bata sani ba shine,yana daga cikin jinsin mutanen da Allah ya musu kaifin ji matuqa,murmushi ya kuma saki mai dan sauti,ga mamakinta taji yace

"Shikenan....in sha Allahu daga yau din zan janye....amma" ya fadi yana sanya hannunsa cikin aljihun trouser dinsa,american dollers ya ciro daga aljihun nasa wanda baisan ko na nawa bane,takawa yayi a hankali har ya isa inda take jingune rungume da hannayenta ya soka mata su tsakanin hannayenta yana ci gaba da jifanta da murmushi

"Na gode da lokutanki na baya da kika aramin.....sai wara rana" ya fadi yana juyawa,binsa tayi da kallo galala,duk wata tasha ta tunaninta ta dauke tsaf,har ya isa bakin wata baqar mota wadda bataji sanda ta iso inda suke ba,gidan baya ya bude ya shige kana ya rufe,sai data ga motar ta bar layin nasu sannan hankalinta ya dawo jikinta,tabi dollers din dake liqe a jikinta da kallo,sabbi kar suna fidda wani irin qamshi dake cakude da sassanyan qamshin turarensa da har rana irin ta yau ta rasa gane wanne irin turare yake amfani da shi,cikin sauri kaman wadda aka yiwa allura ta juya cikin hanzarinta shige gidan su,bata tsaya ko ina ba sai parlourn gidansu,inda tabar qawarta barratu na jiranta

"Ya akayi,kin sallami dan anacen naki" maimakon ta amsa mata saita miqa mata dalolin dake hannunta

"Wadannan fa daga ina?" Barratu ta fada tana zakudawa gami da gyara zamanta tare da tattara dukkan hankalinta kan zulaiha,mayafinta ta yage sannan ta zauna hannun kujera tana baiwa barratu labarin abinda ya faru,ta rufe da cewa

"Tsoro na daya barratu,kada ya kasance irin mijin da nake muradi ne na koreshi da kaina,kinga irin motar daya shiga kuwa" ta fada fargabarta na fitowa fili qarara,murmushi barratu ta saki tana karkada kudaden

"Kinga malama....kwantar da hankalinki....tundan yau kin gano haka ai baki makara ba,waskewa zakiyi,ai kiransa zakiyi kawai ki nuna ke bakison kudinsa yazo ya amshi abinsa,ke gwadashi dama kike yi" bata tsaya ta gama jinma qarshen zancan ba ta zaro wayarta cikin hanzari ta soma laluba inda ta jefa lambar tasa,can cikin black list ta ganota,cikin hanzari ta cireta daga black list din sannan ta soma kiransa.



    Dai dai lokacin yana lafe a bayan motar suna tafe, mahmoud nata tambayar sa ya akayi a gefe guda kuma yana sheqa masa dariya,qarar wayar ita ta sanyashi bude manyan idanunshi da suke a rufe,waya ce da ita daya keda number,wadda dama dominta ya siya wayar da layin,hannunshi ya kai ya daga wayar ya kara a kunnensa ba tare da yace komai ba

"Ka dawo ka amshi kudinka,ni basu nake so ba,gwadaka dama nake,kuma alamu sun nuna kaci wannan jarrabawar" irin maganganun data ringa jerowa kenan duk a niyyarta nason amintar da shi da gamsar da shi,murmushi kawai ya sake mata wanda ya ratsa kunne da qwaqwalwarta

"Am sorry to say,ida na wuce aji bana maimaita shi.....sai wata rana" ya qarashe fada yana cire wayar daga kunneshi,bai tsaya a nan ba sai daya cire layin ya karyashi gida biyu,ya sauke glass din motar qasa kadan ya watsar ta window sannan ya maidashi yadda yake ya koma jikin kujerar motar ya sake lafewa ba tare daya bi ta kan dariyar mahmoud ba,hannayensa ya saka ya rufe kunnuwansa saboda yadda mahmoud din ya hanashi sakat,daga bisani da yaga baida niyyar barinshi ya huta ya shammaceshi ya kai masa naushi,Allah ya taimakeshi ya kauce yana cewa

"A'ah,karka lahantani,haka kawai bani na kar zomon ba ai,danma ka samu wai ina rakoka,tunda an kasaka ba shikenan ba sai ka sake sabon lale....amma fa ka riqr a ranka,'yammatan zamani indai zaka ci gaba da zuwa musu a haka za'a dade ana kasaka" dariya ce ta subucewa khalipha ba tare saya shirya ba,suka dan dara tare da mahmoud din,shi kansa lamarin na bashi mamaki gamibda daure masa kai,karo na uku?,karo na uku duk tafiyar ta kasance iri guda?,sai yaushe?,sai yaushe zaiga sauyi,zaya so yaga wannan rana qwarai.



*_HUGUMA_*




     0⃣3⃣


   Tsaye yake cikin tafkekan dakin taron a gaban wani hamshaqin teburi wanda yake dauke da aqalla ma'aikata kimanin mutuk arba'in,hannunsa guda dafe yake da gaban teburin yayin da daya hannun yaketa wulwulgashi cike da gwanancewa duk da baisan yana yi ba,da alama bayanin da yakewa ma'aikatan da suka bashi dukkan nutsuwarsu ya dauki zafi,lokaci lokaci yana daga daya hannun nasa dake dafe da teburin yana duba agogon hannunsa,wannan kadai ya isa ya nuna maka mutum ne mai kiyaye lokaci da kuma alfanunsa.



   "Is there any problem?...." Ya qarashe jimlar tasa ta qarshe yana duban fuskokin ma'aikatan,saidai kowanne ya gamsu girgiza kai suka dinga yi daya bayan daya,ganin haka ya sanya shi ya soma tattare kayanshi dake saman teburin tare da bada umarnin a rufe taron da addu'a kaman yadda yake a qa'idarsa.



   Shine mutum na farko da ya soma fita,shahid ya rufa masa baya suna magana qasa qasa,a bakin hall din daya daga cikin mutanen dake tsaye a wajen ya karbi kayan hannunsa sannan yabi bayansa har cikin elevetor wadda bata saukesu ko ina ba sai hawan qarshe na kamfanin inda office dinsa yake.



   Mahmoud ne kawai zaune cikin office din ya tasa computer a gaba da alamu wani aiki yake ragewa mai muhimmanci Hannu mahmoud ya baiwa shahid suka gaisa cike da alamun cikakkiyar sanayya a tsakaninsu bayan security din dake riqe da kayan khaliphan ya aje ya fice,yayin da khalipha ya wuce kai tsaye bakin freezer ya dauki ruwa ya sha bayan ya rage suit din jikinsa kana ya shige toilet,alwala ya daura sannan ya dawo cikin office din ya tadda shahid da mahmoud suna hira,wadda fiye da rabinta abinda ya shafi kasuwancinsu ne,daya daga cikin wayayoyinshi wadda ke dauke da lambobin dukkan mutanen daya baiwa muhimmanci a rayuwarsa lambarsu ke ciki,kai tsaye ya nufi bakin daya daga cikin windows din dake cikin dakin office din wanda kai tsaye zaka iya kiransu da qofa saboda kadan ne ya rage basu kai girman qofar ba,saidai glass ne zalla a jiki wanda hakan zai baka damar gano ainihin farfajiyar companyn daga sama har qasa.



   Bugu biyu aka daga wayar,ya sauke ajiyar zuciya sallamar matar na ratsa kunnensa,cikin sanyin murya kaman yadda halittar muryarshi take ya amsa sallamar sannan yace"Anni...barka da warhaka"

"Barka kadai khalipha,kun fito daga taron ne?"

"Mun fito ammi,saidai aci gaba da yi mana addu'a Allah yasa mu dace"

"Ubangiji ya dafa,ya shiga lamarinku,ya zama jagora a gareku,ya albarkaci rayuwarku". Cike da jin dadi yaketa amsawa da ameen,idanunsa lumshe yana shafa qirjinsa yana jin zuciyaraa wasai

"Ya jikin anni?,kinsha maganinki na rana,naga lokaci yayi"murmushi ta saki cike da qaunar yaron nata

"Khalipha kenan baka gajiya?,kaman ba awannin da suka shude muka gama waya da kai ba,jiki alhamdulillah,magani kuma ina gama sha kiranka ya shigo"cikin murmushi ya amsa

"Ya za'ayi na gaji da jinki anni....Allah ya qara miki lafiya mai dorewa"

"Allahumma amin khalipha,Allah yayi albarka"

"Ameen anni...sai na dawo"

"Allah ya tsare" ta sake ambata cikin nuna kulawa da qauna,ya amsa sannan ya kashe wayar yana murmushi,abubuwa da yawa na dawowa cikin kwanyarsa game da annin tasa,zai iya cewa baiga uwa irin tashi ba,kuma baya zaton za'a samu,anninsa da taban ce ko cikin halittun ubangiji,da wannan zancan zucin ya qaraso inda su mahmoud suke.



     🧶🧶🧶



  Zaune yake gaban annin tashi cikin shigar qananun kaya na t shirt da trouser,qafafunshi tanqwashe gabanshi kuma plate ne wanda ke dauke da tuwon shinkafa miyar water leaf da ogu wadda ta wadata da ganda busashshen kifi da kuma tsokar nama,a nutse yake cin abinci gefe guda suna hira da anni,hirar dake nuna tsantsar shaquwa dake tsakaninsu,kallo daya zaka yi musu ka tabbatarwa kanka lallai akwai saboda da shaquwa mai qafi tsakaninsu

"Khalipha..." Ta ambata a hankali wanda hakan yasa ya dago kanshi yana dubanta sannan ya amsa

"Wai sau yaushe zan daina jiran ganin zuwam surukata?" Murmushi ne ya subuce masa,sai ya aje cokalin hannunsa ya fasa kai lomar da yayi niya,cikin kulawa da qauna yake dubanta sannan yace

"Kwanan nan anni,karki damu....addu'arki nake buqata kawai...ina son na kawo miki surukar da zata kulamin dake,surukar da zata daukeki a matsayin uwa....surukar da zakiji dadin zama da ita fiye dani yadda zanji" murmushi ya subuce mata,sai ta kada kai tana dubanshi

"Allah ya baka mace ya gari wadda zata zame maka majingina.....amma banda abin khalipha kana tunanin akwai irin wannan surukan yanzu?" Ta qarashe managanar tana dariya qasa qasa,don har ga Allah bata dauki burinta ta cillashi har haka ba,kullum dai addu'arta Allah ya bashi wadda zata soshi tsakani da Allah,nagartacciyar matar aure,dan marairaicewa yayi kadan sannan yace

"Anni,kin sha gayamin ba'a fidda rai da rahamar Allah"

Kai ta jinjina cike da gamsuwa tace"wannan haka yake,ubangiji ya maka zabi ja gari"

"Ameen" ya amsa yana daukar cokalinsa dinci gaba da cin abincinsa sannan yace

"Cikin sati na gaba haidar zai dawo gida hutu" murmushi tayi kaman ko yaushe

"Sun kammala jarabawar kenan"

"Eh sun samu hutu na wata biyu"

"Allah ya kai mana rai"

"Ameen" ya amsa yana daukar cup din daya cika da ruwa ya soma sha.


     🧶🧶🧶



   Da sauri sauri take tafiya hadi da duba agogon hannunta,qarfe tara da rabi na safe dai dai,mintuna talatin zata qara ta makara wanda hakan dai dai yake da rasa lacture dinta har na tsahon awa biyu.


   Turus tayi gabanta na dan dokawa ganin asma'u zaune dafa'an cikin falon sanye da kayan barci wanda hakan ke nuna ko wanka bata yi ba bare a kai ga shirin fita,hannunta daya riqe da cup na tea tana kurba a hankali,daya hannun kuma wayarta ce samfurin iphone 8 take latsawa,jikinta sanyaye ta qaraso gefanta ta tsaya

"Ashe baki shirya ba anty asma'u?" Sai data shaqi iska kafin ta amsa

"Eh....sai eleven"

"Gashi goma lacturer din yake shiga..." Ta fada adamuwance,saboda daddy yana gidan,kusan yasan lokutan fita lactures dinsu daya ne,tare suke fita su kuma dawo tare a iya saninsa kenan,idanu ta daga ta kalleta ta watsa mata wani kallo

"Naga alamun raini na son soma shiga tsakaninmu aysha duk don saboda sharing abun hawa da muke ko...to ki shiga taitayinki,ke kanki kinsan wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,banda game game irin ja daddy da sunan zumunci saidai ki dinga hangoni ta cikin glass,to banson zura kai in zaki wuce kije ki hau abun hawa na haya ki wuce,dama dashi kika fi dacewa kuma dashi kika saba" tana kaiwa nan ta maqala earpiece a kunnenta da alama kira ne ya shigo mata zata amsa.



   A kasalance take takawa a harabar gidan,zuciyarta cike fal da tunani,tana tsammanin kyautatawa na sanyawa kaso mutum koda baka sonshi,saidai ta gefan asma'u sam ba haka bane,mommy kuwa har yau ta kasa fahimtar a wanne aji take?,banbancin rayuwar data baro da wannan baya wuce sauyin muhalli,sutura da ilimi data samu ba,amma baya ga haka zata iya kiran yanayin da SAMMAKAL a wajenta

"A'ah,ina zaki a qafa aishatu?" Ta tsinkayi muryar daddy dake fitowa daga babban falonshi da yake ganawa da baqinsa,wanda sam bata lura da shi ba saboda zurfin tunanin da tayi,cikin hikima tayi qoqarin saisaita yanayinta,ta qaraso cike da girmamawa

"Ina kwana daddy..." Ta soma da gaisheshi,don yau duka basu samu damar haduwa ba,kasancewar jiya wajen goma na dare ya dawo qasar,ya kuma buqaci mommy ta tasota saidai tanajin sa'adda da tace masa ai ayshan tayi bacci,bayan idanunta biyu a sannan litattafanta ne a gabanta take dubawa,har lokacin data shiga dakin asma'u ta tadata kan ta fito daddynsu ya dawo amma asma'un tayi qememe tace ta gaji sa gaisa gobe,haka mommyn ta fito tace masa itama din tayi bacci

"Ina zaki aysha?" Ya sake jeho mata tambayar bayan sun gama gaisawa,bata da wata qarya da zata masa don kare asma'un wannan karon,saboda haka kai tsaye tace

"Makaranta" agogon wayarsa ya duba sannan yace

"Ina asma'un.....ina kuma drivern naku?"kanta ta duqar qasa sannan tace

" yau akwai banbancin lokacin fitar namu ne"

Kai ya jinjina,tun da can shi ba mutum bane mai yawan sanya ido da takura ba,hakan ya sanya abubuwa da dama kan gudana cikin gidan ayi musu kwaskwarima a sauya musu salo a bashi a haka ya karba ba tare da ya sani ba.



   Dai dai sannan usama drivansa ya turo get din gidan ya shigo,saboda ga tsammaninsa a sannan zasu tafin,hakan ya sanya daddyn ya sallameta bayan ya miqa mata sabbin 'yan dubu dubu guda biyar da sukayi saura a hannunsa wanda da alama ya gama sallamar masu neman taimako ne wadan nan suka rage,tasan baya kyauta a dawo masa da ita hakan ya sanya tasa hannu biyu ta amsa tana jero masa godiya.



   Ko cikin motar tunanin karamci irin na daddyn take,har abada kuma har ta mutu ba zata taba manta alkhairinsa da karamcinsa gareta ba,qarar wayar usama ta dawo da ita hayyacinta,daga jin yadda yake amsa wayar cikin daburcewa tasan akwai magana

"Kiyi haquri ranki ya dade,yanzu zan ajeta na dawo,na dauka yau bazaki fita bane...kiyi haquri" kalmar yayita maimaitawa,saidai hakan bai hana asma'u yi masa tas ba harda alakoron zagi ta kuma katse wayar

"Kaga....ajjiyeni usama kaje ka daukota saina qarasa wani abun hawan" yana bala'in ganin qimar ayshan saboda yadda take girmamashi tamkar yayanta,hakan ya sanya yace

"Barshi kawai na qarasa dake aishatu,koda na ajekin ma na koma daukota ba tsira zanyi ba" kai ta kada

"Ka ajenin babu komai...laifin ai zai ragu idan kace mata ajjiyeni kayi ba kamar ka kaini ka dawo ba" haka ya gangara gefan titi bada son ransa ba ya ajeta ya juya ya koma,ta tsaida adaidaita sahu ya qarasa da ita,idan da sabo ta jima da sabawa da halayen asma'u,ta haddacesu tsaf,shi yasa ba komai ke bata ranta ba.



*mrs muhammad ce*👑






🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣



     *NA*


*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*






      0⃣4⃣




   Qarfe daya ta fito daga library dake cikin makarantar don ta qarasa masallaci tayi sallah,tattaunawa suka sakeyi da sauran dalibai 'yan uwanta kan lacuture din da suka gama yi,qoqarinta da yadda kanta keja yasa yawa yawan dalibai ke maqale mata saboda ta sake ganar da su abinda basu fahimta ba,ta kammala alwalar tana gab da shiga masallacin wayarta tayi tsuwwa,dakatawa tayi ta ciro tana duba mai kiran,gwaggwo asabe ce take kiranta qanwa ga mahaifiyarta,mace daya tak da ko a baya tayi qoqari wajen ganin ta taimaki rayuwarta,tana daya daga cikin jerin jama'ar da bazata mance da su ba cikin rayuwarta,gefe ta samu ta jingina da wata bishiya dake wajen bayan ta katse kiran ta kirata da kanta don kada ta cinye mata kudi,gaisawa sukayi bayan 'yan tambaye tambayen lafiyar juna da suka biyo baya tace da ita

"Indo hala bakisan malam baida lafiya ba ko?"

"Kai haba?,tun yaushe gwaggwo?"

"Sati kusan biyu kenan,har a asibitin cikin gari ya kwanta,amma alhamdulillahi yanzu jikin nasa da sauqi an sallamoshi yau kwana uku yana gida ma"

"Ayyah,Allah ya sawwaqe ya bashi lafiya,in sha Allah zan shigo garim cikin qarshen satin nan,kiyi masa sannu kafin na iso"

"Zaiji,saikinzo Allah ya kawoki lafiya"

"Ameen gwaggo na gode,ki gaishemin da su lami"

"Zasuji" daga haka ta kashe wayar ta maidata cikin jakarta tana sauke ajiyar zuciya,ta tabbata ba don gwaggwo asaben ba babu lallai tasan da rashin lafiyar malam din,ta rasa wanne irin baqin abu ta aika har baqin jini yake bibiyarta wajen danginta na uwa da uba?,me tayi musu haka da kowa ma bai damu da rayuwarta ba?,a hakan ma takan iya cewa alhamdulillah da yadda ta tsinci kanta a yanzu akan shekaru kusan bakwai zuwa goma baya da suka shude,wanda abun yayi tsananin da har bata marmarin tunawa?,saidai har yau akwai wawakeken tabo da gibi cikin rayuwarta wanda batasan ranar da wannan gibin zai cike ba,batasan randa wannan babban jigon zai rabeta ba,batasan yaushe zai waiwayo ya dubi rayuwarta duba irin na idon rahama ba kaman yadda sauran 'ya'ya ke samu daga wajen uwayensu,da wannan tunanin ta qarasa cikin masallacin ta tada sallarta.


   🧶🧶🧶🧶



   Cikin nutsuwa ya kammala sanya maballan t.shirt dinsa wadda kudinta ya kama naira dubu biyu ita da wandon jeans dake jikinsa,har ya dauki turarensa zai fesa sai ya tuna,maidashi yayi wajensa,ya sake miqa hannu ya dauko wani daban wanda kallo daya zaka masa ka qiyasta kudinsa bazai wuce naira dubu guda ba idan yayi wuta ya fesa a jikinsa,duk da qarancin kudin turaren kuma bai cikin jinsin irin turarukan da yake mu'amala da su amma hakan bai hanashi jin dadin qamshinsa ba,saboda turare ne sanyi dake fita a hankali ba tare da ya daga hankalin wanda yake shaqa ba.



   Gaban mudubi ya qarasa yana duban kansa,sai murmushi ya subucewa fuskaraa,duk da arhar kayan amma sun masa kyau

"Gwanjo" ya fada yana shafa gaban rigar dake jikin nasa zuwa saman cikinsa,yana tuna can wani lokaci baya daya shude,wani zamani da yayi tafiyar ruwa da dukkan farincikin rayuwarsu,wani qarni wanda basu taba tsammanin zaya wuce babinsa ya shafe kaman bai taba wanzuwa ba cikin littafin qaddararsu ba,tunanin ya saka ya zarce da sake gyara sumarshi da tayi matuqar yi masa kyau.



   Kafin ya kai ga aje comb din hannunsa aka turo qofar dakin hade da sallama,mahmoud ne ya shigo idanunsa na kan khalipha,daga gani tambayoyi ne fal cikin qwaqwalwarsa wanda tun kafin ya zauna ya jefo masa daya

"Me haka ne malam?,ban fahimceka ba" juyawa yayi yana ci gaba da gyara kansa kafin ya bashi amsa

"Na zaci shigata kawai ta isa ta baka amsar abinda yake faruwa ko?"

"Wai har yau baka haqura ba?,baka kuma daina ba?" Ajjiye comb din yayi ta tako kusa da mahmoud din ya dauki qaramar vivo din dake aje kusa da shi ya bude bayanta ya soma qoqarin sanya mata layi

"Na sake haduwa da wata,kuma na fuskanci kaman wannan karon ina tare da nasara" dariya sosai mahmoud din ya bushe da ita harda kwantar da gadon bayansa saman gadon khaliphan,san dariyar mahmoud din bata dameshi ba saima yunqurin kunna wayar da yake bayan ya kashe nashi tsadaddun guda uku ya jefa cikin wata 'yar kyakkyawar briefcase dake nuna alamun da ita zai fita

"Me yasa kake wahalar da kanka ne babu gaira babu dalili my man.....ka saki kudi kawai ka auri duk kalar macen da kakeso kada ba jinsinka bace ba 'yar qasarka ba,kowa ya sani cewa mata yanzu kudi kawai suke so,mai kudi suke nema koda baida hali koda bai cancanta,koda ba saurayi bane koda ba kyakkyawa bane,koda jahili ne,to bare kai da babu abinda Allah bai baka ba,c'mon muhammad khalipha ka aje wannan game din a gefe ka fuskanci reality,ba irin matan da kaketa serching a yanzu,baka gani duk inda ka soma farauta daga qarshe sai kaga no signal?".



   Hannu yasa ya dauki briefcase dinsa tamkar bada shi mahmoud ke magaba ba ya doshi qofar fita ba tare da yace masa ci kanka ba,hakan ya sanya shi miqewa da dan tsallensa ya biyo bayansa,saidai bai sake biyo ta kan wancan maganar ba ya sauya topic,yasan ko yaci gaba ma ba amsa zai samu daga gun khaliphan ba

"ka rakani mu shiga na gida anni"

"Daga nan ni sai inda na nufa,idan ka fito daga wajenta ka kwashe su jibril duka ku wuce kamfani na tadda ku a can,ni da mota daya zan fita,bana buqatar gayya" ya fada yana gaba yana ci gaba da dubo lambar sabuwar budurwar tashi don ya sanar mata da tahowarshi.



   Yana fita duka suka taso inda yake,da hannu ya tsaidasu kafin ya daga kai ya dubesu

"Mota daya ta isheni da driver,zaku jira mahmoud tare zaku tafi,zan taho daga baya" kai auka jinjina suna janyewa,yayin daya bude motar da kanshi ya shige gidan baya,drivan motar ya shiga ya tasheta suka bar harabar makeken gidan.



  Layuka biyu suka rage kafin ya qarasa layin gidan nasu ya bashi umarnin ya saukeshi ya kuma jirashi a nan,ba musu ya tsaya kaman yadda ya umarceshi,ya bude ya fice.


   Sannu a hankali yake takawa,shi kansa yana jin dadin takawar da yake,saboda ko banza ya motsa gabbansa,ba kamar baya ba da motar ita ta zame masa qafafunsa,sauqin abun daya bai da lalaci,duk safiyar duniya sai ya shiga dakin dake bangarensa,wanda ke cike sa nau'in qarafuna da na'urori na motsa jiki da qara lafiya.


   Plashing yayi bugu biyu ya katse,shi kansa sai da dariya ta subuce masa

"Shame on you khalipha,wai yau kaine da yin plashing,Allahu yahdik" ya furta a zuciyarsa yana sakin murmushi gami da ranqwashin tsakiyar kansa,fitowarta ita yasa ya maida hankalinsa ga qofar gidan,tayi kwalliya sosai cikin atamfarta

"Sannu da zuwa" ta furta tana wuwwulga ido kaman mai neman wani abu,amma sai ta basar saboda jin kanta da take a mace mai aji

"Yauwa barka da fitowa"

"Ina kuma abun hawan yau?" Ta tambaya kai tsaye tana dubanshi,wani abu mai kama da mamaki yaso mamayarsa amma sai yayi hanzari kau da shi yace

"Kinsan qarfen nasara bashi da tabbas,yau yaqi tashi kawai sai na yanke na taho a na haya"

"Kan bala'i,ana wata ga wata" ta furta qasa qasa,sarai ya jita amma sai yace

"Na'am,me kika ce?" 

"Babu komai,shigo daga ciki" ta fada ranta a alamun bace,bai musa ba yabi bayanta har setting room din gidan,duk da cewa ba baqonsa bane gidan da zuwanshi kusan na uku kenan,kallon farko zuwa na biyu zaka yankewa maxauna gidan ajin rayuwar da suke ciki,ba alamun suna cikin talauci,dukkan wata alama ta rufin asiri akwaita a gidan,kaman yadda ya tsammaci akwai tarbiyya gwargwado gidansu khadijan.



  Nan ta masa sauki ta gabatar masa da abun motsa baki kamar kullum,saidai abinda ya fuskanta abinda aka kawo masa jiya idan ya sake zuwa yawansu da tsadarsu kan ragu,idan cake da doghnout da lemo yaci to zuwa na gaba doughnout da lemo kawai zai samu,yasan bai taba baiwa khadijan komai ba,haka itama bata taba roqarsa ba,saidai amma ya lura duk sanda sukayi sallama zai tafi ba tare da ya miqo komai ba yakanga bacin rai qarara a fuskarta,har idan ya koma gida ya kirata da zummar gaya mata ya iso bata dagawa,saidai duk ya share wannan bai sanyashi a babin komai ba.



   Tun kafin aci talata da laraba a hirar tasu ta gyara zamanta tare da sake lanqwashe murya

"Ammm....dama muhammad akwai maganar da nakeso muyi"

"Ina saurarenki" ya fada yana harde qafafunshi waje guda tare da zuba mata idanunsa,haka nan taji ya mata kwarjini,abinda take yawan tunani kenan,me yasa yake yawan cika mata ido,wanda wannan dalilin yasa tun zuwansa na farko dana biyu data fuskanci ba kalar wanda take lalube bane ta kasa masa bayani,janye qwayar idanunta tayi cikin dakiya tace

"Dama.....biki zamuyi na wata qawata,so an fidda anko nakeso ka yimin" janye yatsansa dake saman lebansa yayi ya dan motsa jikinsa kadan sannan yace

"Kaman nawa ne kudin how much?" Sai da tayi rolling qwayar idanunta sannan tace

"Dubu talatinma is enought,idan son samu ne kuma 40k" murmushi ya qwace masa saidai iya shi da zuciyarsa,ba kudin data tambaya bane suka bashi mamaki don ba matsalarsa bane,don a yanzun haka akwai ninkinsu a wajensa,wanda ya fito da su ne yau dan ya mata kyauta matuqar ta sake tsallake yau din bata nemi komai daga wajensa ba,mamakinsa shine yadda yarinya budurwa da bata rasa ci sha da sutura daga gidansu ba take iya duban qwayar idon namiji ajnabinta ta roqeshi kudin da zata dinka suturawa jikinta haka kanta tsaye ba kunya,tamkar ta bashi ajiya ne,kai yake kadawa a hankai zuciyarsa na gaya masa bata gama cin jarabawa ba ba shakka

"Ya naji kayi shiru ne?" Ta tambayeshi tana dan bata rai gami da fiddo ido waje

"A'ah babu komai,kawai....gani nayi kudin basuyi yawa ba?" Tsaf ta dinke girar sama da qasa

"Just 30 to 40k dinne sukai yawa?,ko iyawa ne ba zaka yi ba?,thank god da ba'a gaban qawayena bane da nake cika musu kanka da naji kunya" murmushi ya saki yana miqewa tsaye

"Ba zakiji kunya ba in sha Allahu zan shiga na fita,amma sai kin danmin haquri kadan kinsam abinka da almajiri mai nema"

"Ba damuwa indai zasu samun,amma kar su wuce nan da one week don Allah" ta qarashe maganar a shagwabe,kai kawai ya iya jinjinawa mamaki na kasheshi,haka tayi masa rakiya har qofar gida yau cike da kulawa sannan ta juya ta koma,shi kuma yaci gaba takawa yana juya abinda ya faru tsakaninsa da khadijan har ya isa bakin motar,wanda tuni driver ya bude masa ya shige shi kuma ya maidata ya rufe sannan ya shiga mazauninsa ya tada motar suka bar unguwar.


  "Ashe duk kanwar jaa ce?" Ya fada qasa qasa cikin sigar tambayar kansa da kansa bayan ya ciro sabbin kudaden dake aljihunsa ya qare musu kallo ya watsasu cikin wata ma'ajiyar dake motar ya maidata ya kulle yana sauke ajiyar zuciya,kansa ya shafa sau biyu yana kiran sunan Allah sannan ya maida idanunsa ya lumshe yana aje numfashi

*DAURIN BOYE*



     *NA*


*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*




     0⃣5⃣




   A hankali take takowa bayan fitowarta daga kitchen dauke da babban tray data shiryo abincin daddy a kai zuwa inda yake zaune yana faman rubuce rubuce cikin wasu takardu,yayin da gimbiyar tasa hajiya sa'adatu mommy ke zaune gefanshi cikin kwalliya tana aikin duba tashar da zata dace da kallonta.



   Duk da yawan ma'aikatan dake gidan hakan sam bai damu ayshatu ba ko ya tsone mata idanu,takan bata lokaci aduk sadda take da dama tayi girkin da zata ciyar da mutanen gidan,musamman daddy mutumin dake da qima a idanunta,mutumin da take masa kallon mahaifi,kai tana iya cewa abinda yayi mata ko mahaifin da yayi silar kawota duniya baiyi mata shi ba,don ba zata iya cewa yau ga dadin da mahaifi yake da shi ba.



   Gabansa ta aje tray din cikin nutsuwa a ladabce,ya dan daga kansa ya dubeta fuskarshi washe da fara'a

"Sannu indon baffale" murmushi ta saki saboda kiranta da wani suna daya shude can baya cikin tarihin rayuwarta,sai ta duqad da kanta ta koma can baya ta rabe daura da momy,tana jira ya bata dama ta sanar masa tafiyarta qauye da takeso tayi gobe asabar ta dawo litinin tunda bata da makaranta ranar litinin din.



   Asma'u ce ta fito daga dakinta sanye da dogon wando da riga 'yar qarama mai gajeran hannu,sai ta dora top wadda takai har saman gwiwarta,kunnenta sanye da earpiece kaman yadda yake kusan al'adarta kenan ko da yaushe,kanta babu dankwali sai yalwataccen gashinta mai tsaho dake fake cikin ribbom,a shagwabe ta qaraso gaban iyayen nata ta zube a gaban daddyn 

"Daddy....tun shekaran jiya ka dawo har yau zuwa fa banga alqawari na ba" 

"Hmmm,bake kadai ba,nima shiru nake ji har yau ba'a cemin komai ba,safina ma tayo waya tana jira amma duk daddy ka mana shiru"inji mummy sa'adatu ta fada tana ci gaba da sauya tasha,takaddun ya tattara gefe daya kana daga bisani ya cire gilashin idanunsa yana murmushi

" kowa sai daya min qorafin saqonsa shiru,ayshatu ce har yau banji ta fadi komai ba"murmushi aysha tayi tana sadda kanta qasa,ita awa?,wanne saqo ma ta baiwa daddyn?,iya alfarmar da ya yiwa rayuwarta kadai ta isheta har abada,ta gefan asma'u kuwa fuska ta kwabe tana dan bata rai,ta tsani daddy ya dinga hada yarinyar da su sam,tana ganin bata cancanci jerawa da su ba,yayin da hajiya sa'adatu ta dan tabe baki gami da dauke kai a fakaice,wanda ba kowa bane zai kula da hakan,bai sake cewa komai ba ya kira waya ya bayar da umarni,cikin mintina biyu daya daga cikin amintattun yaran gidan ya shigo jaye da akwati da kuma wata babbar jaka ya dire a falon ya juya ya fice.

   


   Saukowa yayi qasa carfet din ya janyo jakar ya soma kici kicin zugeta hadi da fadin

"Ai gwara na sallameku na huta kada ku cinyeni danye" dukkansu sai da sukayi dariya,kasancewarsa mutum mai barkwanci a wasu lokutan,amma fa idan ya murde sam bashi da dadin sha'ani.



   Wayoyi ya fito da su guda biyu irin wanda asma'un ta zaba tace tana so iri daya sak komai da komai,wayace sabuwar shigowa mai dan karen tsada da kyau ya miqawa asma'un,cike da murna da zumudi ta amsa tana jujjuyata ranta fari qal,saidai tuni murnarta ta koma ciki sanda taga ya miqawa aysha irin tata wayar sak,farincikin dake kan fuskarta ya koma bacin rai,ya sake fito da wasu dogayen riguna masu azabar kyau guda shida ya raba musu uku uku,cikin sanyin jiki da fargaba aysha ta miqa hannu zata amsa,yayin da idanunta ya sauka kan mommy da asma'u,mommyn dai ta share kaman bata gani ba,yayin da asma'u idanunta ke kan ayshan,haka ta amsa cikin sanyin jiki tana jerama daddyn godiya da addu'ar Allah ya qaro budi,wasu kayan ya sake fitarwa ya turawa mommyn yana cewa

"Ga kayan su safina nan,saiki san yadda zaki gobe ki aika musu da saqonsu nima na huta"

"Tohm" ta amsa wanda ga duk wanda yai tsai da hankalinsa zai fuskanci ranta a bace yake,muqullin mota sabuwa dal ya ciro ya miqa mata yana fadin

"Ga taki tsarabar saiki barni na sarara" sai a sannan fuskarta ta washe ta koma kaman da,cike da murna tasa hannu biyu ta karba tana masa godiya

"Ta wajenki saiki barwa su asma'u da aysha su ajje tasun ko?"

"Kan uba" kalmar data subuce daga bakin asma'u,motar data jima da ciwa burin daddyn nata yasa mommy ta bar mata shine yanzun zaice wani wai ita da aysha?,wallahi ko sama da qasa zasu hadu ba zata yi sharing motar nan da ita ba

"Me kike fada asma'u?" Daddyn ya tambayeta yana mai zuba mata ido don yaso yaji kalmarta ta farko

"A'ah mamaki nake daddy,mun gode Allah ya qara budi"

"Ameen" ya fada yana rufe jakarsa,aysha na gefe baki daya a takure

"Alla ya qaro arziqi daddy mun gode,Allah ya saka da alkhairinsa" ta furta a sanyaye

"Amin aisha....amin" ya fada cikin jin dadi,a tajure take,saboda ji take kaman idanun mommy da asma'u na kanta har yanzu,hakan ya sanya ta miqe tare da fakewa da cewa zata duba farfesun naman kan ragon da takewa mommy a kitchen tayi shigewarta kitchen din,zamanta tayi a can tana duba farfesun tare da sake gyara freezer din da suke zuzzuba kayan girke girke da suke da saurin lalacewa har naman ya nuna,zuwa sannan bata jiyo muryar kowa a falon,hakan ya tabbatar mata sun bar gurin kenan,don haka ta juye naman a warmer ta gyara wajen ta baro kitchen din.



  Asma'u kadai ta taras ta nutse cikin kujera,idanunta saman t.v saidai ba ita take kallo ba,ta cika tayi fam,ta soma gajiya da yadda daddyn ke dai daita da 'yar qauyen yarinyar a komai nata,da kafin zuwanta duka batasan irin wannan ba,ita kadai ta rage a gabansu sai abinda ta zaba ake mata,komai nata daban yake ba tare da an hadata da kowa ba,kallon baqin ciki tabi aysha da shi wadda ta giftata ta nufi dining ta dora warmer din.



   Tana saukowa daga wajen mommy na shigowa falon,cikin hanzari asma'u ta miqe ta gyara zamanta sosai cikin bacin rai ta soma fada kaman zata saki kuka

"Yanzu fisabillilahi mommy ni an kyauta min kenan?,babu dama nace ina son abu sai daddy ya hadani da yarinyar nan,yanzu kaman ni ace in saka kaya iri daya da nata,na riqe waya irin tata,mu shiga mota daya tayi driving nayi,mu shiga makaranta a gani ai wallahi sai friends dina su rainani" mommyn dake shirin zama nan wajen tace

"To ya zakiyi husna,sarai kinsan halin mahaifinku,idan yayi niyyar abu babu kai hanashi" ta sake narkewa kaman mai shirin fidda qwalla tace

"Ni wallahi na fahimci kawai daddy ya shurya zubda min mutunci na da ajina,ke ba sai kiyiwa tufkar hanci ba mommy,gaskiya bazan yarda ba nidai kawai ki karbi wayar kya siya mata wata,koni na saka hamid ya kawo mata dai dai ita daga kamfaninsu tunda sun fara qananun wayoyi daga 50k zuwa sama"

"To ai shikenan indai kinsan zaki kawo mata watan,banson ne daddynku ya fuskanci bata hannunta ya daga ma mutane hankali....aysha" mommy ta qwala mata kira wadda ita tuni har ta isa dakinta ma tana shirin daura alwala tayi shafa'i da wutiri,sai ta fasa ta fita kiran mommyn

"Wayar da daddynku ya baku dazu zaki kawomin na ajjiye miki wajena,za'a kawo miki wata wannan bai kamata ki fara amfani da irinta ba tun yanzu" cike da rashin damuwa ta nunawa mommyn inda kayan suke,don tunda aka soma dramer tasan akwai abinda zai biyo baya shinyasa ma bata debe kayan ba,asma'un ita taje ta birkita kayan ta dauko wayar tana jifan ayshan da harara kamar ita ta cewa daddyn ya aikata hakan ko tana da masaniyar zai aikata din

"A'ah dawo ki debi sauran kayan mana ya zaki barsu nan?" Mommy tace da aysha wadda take niyyar komawa dakinta,bata ce komai ba ta dawo ta kwashesu tana fadin

"An gode".

" ke kawo....zonan mu ga"asma'u ta fada cikin hargagi,ba musu ta dawo da baya ta sake zube kayan a gabanta,hannu ta saka ta bibbirkita ta ciro doguwar riga guda daya wadda bata da kalarta cikin wadda daddyn ya raba musu,gefanta ta jefa tana cewa

"Jeki wannan ta yimin,kamar ma tafi tawa tsada,ina da wata idan na shiga daki zan dauko miki a amadadinta" Tsaki asma'u taja bayan ayshan ta shiga dakin

"Rigima ce fa kawai irin ta daddynku,ita kanta yarinyar na fuskanci rayuwa bata dameta ba,yarinyar data taso a qauye saika dinga siyan kaya na manyan kudi kana bata,harda abinda batasan darajarsa ba ma....miqo min wayar" mommy ta fada tana miqawa asma'u hannu,saita noqe 

"Namecy zan bawa ita mommy please" dan zare ido mommy tayi

"Ke bana son sakarci bani nace" cikin shagwaba tace

"Habba mana mommy,kinsan 'yar waye ne cikin garin nan?,wallahi nasan na bata wannan wayar as a gift ba qaramin daga min aji kyautar zatayi ba" harara mommyn ta watsa mata

"Yar banza,sai shegen son suna da tara qawaye"

"Thank you my mommy,i love you so much" ta fada tana tsalle hadi da faduwa saman kujerar cikin farinciki,ta tabbata gobe zatayi abunda kowacce saita kalleta cikin qawaye,haka nan husna zata sake ganin darajarta da yadda da irin kudin nasu gidan,duk da qawaye ne amma gasa ce sosai a tsakaminsu,kowacce so take tayi abinda zata burge daga,kowacce so take 'yar uwarta taga ta fita,kowacce so take ta ganta itace a gaba ta baro daya a baya,su kansu basu san cewa abota suke mara ma'ana ba,har hassada da qyashi da kishi ya shigo cikin tarayyarsu yayi kane kane ba tare da sun sani ba,abu daya ne ya hana mommy amshe wayar jin cewa 'yar wani za'a bawa,kasancewarta mace mai son mu'amala da manyan mutane,tana son a ganta tana mu'amala da wani,wanin ma da yayi suna ya kuma shahara,haka dabi'arta take a jininta take,kusan ba'a qasa yaranta suka dauki wannan dabi'a,za'a iya cewa duk cikinsu mutum daya ce ta banbanta da su,halayenta kusan irin na mahaifinta ne,hakan ya sanya babu jituwa ko alaqa mai qarfi tsakaninta da asma'u,saboda banbancin ra'ayi da hali.


   A hankali yake kurbar lemon dake cikin tambulan din qarau na glass sake gabanshi,yayi kyau cikin shigar da yafiyi shigar suit musamman idan ranakun aiki ne,yanayin zamanshi a wajen da yadda yake kai lemon bakinsa lokaci lokaci kadai ya isa ya gaya maka nutsuwar da yake sa ita uwa uba aji da kyau da Allah ya bashi,kusan babu budurwar da zata shigo wajen bata kalleshi ba,masu rawar kan cikinsu kanyi sha'awar dosar sa su taya hajarsu saboda alamun malasa da suke hangowa tattare da shi,saidai basu iya qarasawa saboda kwarjinin da yake da shi suke karya kwana su sauya hanya.



   Agogonsa ya sake dubawa ya yarfar da hannu gami da jan tsaki,banda haduwarsu da mas'ood yau ta zama dole baiga abinda zai sashi zaman wajen ba,sam wajen baiyi masa ba,akwai yawaitar cakudedeniyar maza da mata abinda yafi tsana,yana da kishi qwarai duk da cewa kuwa baida qanwa mace,a zahiri zaka ce bai damu da motsin dake faruwa a wajen ba,saidai a badini yana zaune ne yana sake.nazarta da karatun halayyar 'yammatan zamani,abubuwa da yawa sun faru da suka bashi mamaki suka kuma sake sa mishi tsanar zaman wajen,yana mamakin yadda yammatan ke shigowa,wata tsakiyar maza biyu wata namiji daya,ba wani kunya ko takatsantsan da aka san diya mace da ita,ta zauna cikinsu suci abinci ko abinsha suna hira kaman zasu tafa,wasunsu ma sukan kebe can baya suje susha shisha,wanda shi a wajenshi bata da maraba da taba wiwi da sholisho,hakan take ko a wajen malaman lafiya,zuqa daya ta shishar dai dai yake da ka zauna kasha karan taba sigari guda dari biyu,yana da yaqinin mafi yawansu ba nan suka cewa iyayensu zasu ba,suna iya qarya da sunan mabanbantan wurare da sunan cewa can suka nufa,su binne iyayen har su zo su koma basu fuskanci komai ba.



   Dogon tsaki ya kuma ja yana niyyar dauke kanshi wata mota ta shigo wajen,hakanan yaji ta dauki hankalinsa,bawai don kyanta ko bai taba ganin irinta ba,a'ah,hasalima shekararsa uku da hawanta,duk da ba ita yake kallo kai tsaye ba amma hankalinshi na wajen.


  kaman a mafarki yaga khadija na fitowa daga gaban motar bayan matashin dake tuqa motar ya zagayo ya bude mata,yana iya ganin sanda ta sauya hijabin jikinta da mayafi sannan ta fito,tare suka jero har zuwa kan daya daga cikin kujeru da teburan dake wajen suna wa juna magana.



   Sosai mamaki ya kamashi,don bai tsammaci ganinta a ire iren guraren nan ba tare da wani namiji,da kuma shiga irin ta jikinta,aljihunsa ya laluba sai yaji wayarshi da yake kiranta da ita,yaji dadin hakan,don dama ya taho da ita ne saboda yana da plan din daga nan ya leqa wajenta.


   Miscal wajen hudu yana hangota daga inda yake,tana ganin kiran take dauke kanta,daga bisani ta soma tsaki,yana hango saurayin na mata magana kan ta daga,sai a kira na shida sannan ta daga din,sallama ya soma mata ta amsa da qyar tana wani basarwa

"Hala na katse miki wani abu mai muhimmanci...."

"Kusan haka ne,don bacci nake...na dawo daga makaranta na gaji ina buqatar hutu don Allah....ko kudin sun samu ne?"

"A'h...muryarki dama kawai nake da muradin ji"

"Ohk....idan sun samun zaka iya kirana saika gayan ranar da zaka zo" ko kafin ya kashe tashi wayar tuni ta datse nata layin,yana iya hango yadda take yatsina fuska sannan daga bisani ta wurga wayar jaka ta sake tattara hankalinta ga saurayin.



   Yana shirin dauke idanunsa ya hangi sanda ya amshi jakarta ya saka mata kudi a ciki,kanshi ya kawar sannan ya miqe tsaye bayan ya ciro wayarshi yaba laluben number mas'od ranshi a bace,shi yasa ya tsani jira,badon mas'ood din ya tsaida shi da alqawarin yana hanya ba da bai zauna wajen har idanunsa sun gane masa abinda ya gani din ba

"Afwa boss,afuwa don Allah"

"Is too late....nayi cancel schedules dina na yau na zauna jiranka duk da muhimmancin da lokacina yake da shi.....saidai wani lokaci kuma idan na samu chance....na kiraka ne na gaya maka karka qaraso baka kuma sameni ba" ya qarashe fada yana shigewa bayan motarshi da jibril ya bude masa sannan ya kashe wayar ya ajeta gefanshi,idanunshi na kansu har sanda driver ya soma jan motar suka soma barin wajen,idanunsa ya lumshe sanyin A.cn dake cikin motar yana ratsashi,sosai zuciyarsa na zafi...dukkan wani hope nashi yana sake raguwa sosai fiye da kowanne lokaci,sunayen Allah yake jerowa daya bayan daya cikin zuciyarshi kamar yadda ya saba duk sanda yaji bacin rai,bai yadda ya zauna zuciyarshi na soyuwa hakanan ba tare daya kira Allah ba.



*mrs muhamma ce*👑