KURKUKUN ƘADDARA (TAKUN FARKO)

Episode 45

by @bossbature88

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*



A hankali yake ja da baya batare da ya juya ba, kamar yana kallon su, Har sai da ya kai bakin benan tukunna ya juya da sauri ya haura benan ya fuce daga cikin ɗakin.


Ko sautin rufe ƙopar bai farkar da su ba, kamar matattu, yaushe rabon da su yi irin wannan baccin su kansu sun manta, tsawon lokaci babu wanda ya farka, har dare ya yi, Hasken ceilling ya ɗauke, Na floor lamps ya kunna kan shi.


Azeeza ce ta fara yin motsi zata farka, hannunta dafe da mararta, wani irin azababben fitsari ne ya matse ta, da kasala a jikinta ta yunƙura ta miƙe zaune saman shimfiɗarsu, idanuwanta biji biji bata iya ganin komai.


muryarta cikin shessheƙar kuka ta soma magana tana laluban Jikin Angel.


"Angel ki tashi ki raka ni toilet, fitsari ni ke ji ya matse ni sosai....pls Angel ki tashi kada in yi shi a wando,"


Ko motsi Angel ba ta yi ba, balle har ta sa ran za ta farka.


Jamimah ce ta jiyo muryar Azeeza da ke ta yin kuka, farkawarta kenan, ta zame jikinta daga na Angel, ta miƙe zaune tana mutsustsuka idanuwanta da yatsun hannayenta, fuskarta a ɗaure babu annuri.


Ƙura ido ta yi a kan fuskar azeeza Dake ta kerma tana kuka, Muryarta da alamun bacci bai isheta ta ambaci sunanta"Azeeza...' tana jin muryar jamimah tai saurin katse kukan nata tare da cewa"Jamimah fitsari nake ji, dan Allah ki taimaka ki raka ni toilet, ya matse ni" baki asake Jamimah ke kallonta,


"Toilet dinne saina raka ki? Ke baki iya zuwa? Ko tsoro kike ji ne"? ta yi tambayar tana binta da kallon rainin wayau.


Jamimah ba ta san cewa azeeza na fama da lalurar rashin gani ba, Muryarta na rawa tace"Jamimah bana gani, idan dare yayi, makauniyace ni...."


Ta6e baki jamima tayi mata tare da cewa"ƙarya ne, Ni zaki raina ma wayau? Idan da gaske baki gani to ya akai da rana kike gani? Nafa san me nake yi,"


Takaici ne ya ishi azeeza duk yadda taso ta fahimtar da jamima taƙi yarda cewa bata gani, hakan yasa ta miƙe a makance ta soma tafiya tana laluban hanya, jamimah sai kallon bayanta ta ke yi, abun ya ɗaure mata kai ganin yadda ta ke ta sanya hannu tana laluban hanya, cikin rashin sa'a Azeeza ta nufi bango gadan gadan duk a tunaninta ta ƙaraso bakin ƙopar shiga sashen toilet ɗin ne, ta daddage zata buga kanta, Jamimah ta kware murya tare da cewa"Bango ne fa ba ƙopa fa",


Ta yi maganar tare da miƙewa da gudu ta nufi in da Azeeza ta ke a tsaye jiki na kerma don ba ƙaramin firgita ta yi ba, da taji muryar jamimah tana faɗa mata cewa bango ne ba ƙopa ba.


ba ta yi tsammanin zata taimaka mata ba, sai jin hannunta ta yi a cikin nata, ta ruƙo ta tare da jan ta zuwa cikin sashen, kafin su ƙarasa toilet ɗin tuni ta fara sakin fitsarin a wando, Suna shiga ciki ta zame wandon jikinta, da sauri jamimah ta kawar da kanta gefe don kada taga tsiraicinta, bayan ta gama yin fitsarin, ta yi tsarki kafin ta maida wandon jikinta, ta kira sunan jamimah, ta taimaka mata a daddafe su ka nufi ƙopar fita.


"Amma dai idon ki a rufe ya ke lokacin da nake cikin yin fitsarin ko? Azeeza ce tai maganar, murmushi jamimah ta saki tare da cewa"naga komai, daga yanzu sai ki daina raina min wayau kina kira na ƴar yarinya, nima ae kina min wanka, kuma kina ganin nawa"


Shiru Azeeza ta yi ba tare da ta tanka mata ba.

A lokacin sun fito daga sashen toilet din

"Amma wai dagaske baki gani da daddare? To ya akai kike gani da rana? yamutsa fuska azeeza tai"ko nace maki eh, ba yarda za ki yi dani ba, ki bari idan Angel ta farka daga bacci ki tambaye ki ji, " ta amsa mata da toh.


A lokacin sun shiga cikin ɗakin nasu, har zasu nufi shimfiɗar da Angel ta yi musu, ba zato ba tsammani idanuwan Jamimah suka sauka akan Gado mai ɗauke da no 3, dakatawa ta yi da yin tafiyar, ta ƙurawa gadon ido ta hango mutun naɗe cikin bargo, tunani ta shiga yi wanene saman gadon? Saboda a iya saninta tunda aka kwashe mazan cikin su, babu mai kwana saman tsaffin gadajen su sai Angel! Ita kaɗaice ta ke kwana saman gadon Danish, da sauri jamimah ta juya ta kalli ɗayan 6angaren don taga ko wani daga cikin su Hibba ne Ya dawo saman gadon ya kwanta, sai dai ko da tabi gadajen su da kallo kowannan su yana nan,'


A firgice ta wurga eye balls ɗin ta kan shimfidar Angel don ta tabbatar idan Angel ɗin tana nan, lamarin ya yi matuƙar razana ta ganin Angel baje saman bargo sai sharar baccin ta ke yi.


Azeeza da ta gaji da tsayuwa jin taƙi motsawa su tafi, muryarta a kasalance tace"Jamimah! Ke fa nake jira naji kin dakata da tafiya, Me kike yi ne, dan Allah ki kaina saman shimfiɗarmu in kwanta,"


Hankalin Jamimah ba ƙaramin tashi yai ba, muryarta atsorace ta furta"Azeeza Genie a ɗakin mu, saman gado no 3" ta yi maganar tana zazzare idanuwanta.


duk da Azeeza bata iya gani hakan bai hanata zare idanuwanta ba, zuciyarta ta yi wani irin bugu tamkar zata faso kirjinta, Azeeza sarkin tsoro,


"Innallahi wa'inna ilaihirraji'un! Jamimah ki faɗa min gaskiya, ko dai ƙarya kike yi min, wani irin genie kuma a cikin ɗakin mu, ki dai duba da kyau,"


jamimah tace" kin san Allah dagaske na ke maki, kamar mutun ne saman gadon, kuma na dudduba su hibba mun cika mu goma sha ɗaya, na saman gadon shine cikon na sha biyu."


Girgiza kai azeeza tai jiki nata 6ari tace"jamimah bargo ne da pillow ba mutun ba, ni dai mu je mu kwanta, " ta yi maganar tana ƙoƙarin jan hannunta, duk tabi ta tsorata kanta.


"Ni dai sai naje na duba gadon inga wanene, ke ki ke je ki kwanta"


Ran Azeeza ba ƙaramin 6aci yai ba, zuƙunnawa ta yi ƙasa tana rarrafawa don ta gano inda shimfiɗar Angel ta ke.


A hankali jamimah ke tafiya tana tunkarar gadon, ga tsoro tana ji amma ta nace sai taga wanene, tana ƙarasawa bakin gadon, ta ɗan dakata, tare da miƙa hannunta yatsunta nata yin kerma ta ruƙo bargon, wani irin tsorone ya ziyarci zuciyarta, a hankali ta yaye bargo, a gigice ta runtse idanuwanta ta daddage ta fasa wata irin firgitacciyar ƙara wadda ta yi silar farkawar masu yin bacci.


A matuƙar ruɗe Azeeza ta faɗa saman jikin Angel da ke kwance, Allah yaso ta isa ga shimfiɗar da kuwa zuciyarta ta buga silar ƙarar da jamimah ta fasa.


Bakomai ne ya tsoratar da ita ba face Sumar kan matashiyar dake akwance saman gadon, dama can a tsoroce take shiyasa bata iya tantance gashine ko ba gashi ba, ita dai taga abu kamar hauka, Mai uban yawan gaske ya nanannaɗe, idanuwanta ne suka dinga nuna nata kamar gashin yana motsi, aiko ta rushe da kuka da gudun gaske tabar bakin gadon har tana tuntu6e garin gudu, hankalin su Deeja ba ƙaramin tashi yai ba, ganin yadda jamimah ta furgice tana kuka, bata nufi ko'ina ba, sai saman jikin Angel ta faɗa mata, suka ƙanƙameta ita da azeeza, sun tada mata hankali, ko motsi sun hana tayi tun da tafarka, duk sunbi sun furgice.


Babu wanda ya lura da abunda ya tsoratar dasu.


"Me ke faruwa ne? Wanene ke yi mana kwaratsi a cikin ɗaki"? Parveen ce ta yi maganar fuskarta a yamutse, deeja tace"Jamimah ce, bansan me suke ma ihu ba" ta yi maganar tare da saukowa daga saman gadonta, tare da nufar shimfiɗar Angel.


Su yasmin duk suna zazzaune saman gadonsu basu motsa ba, idanuwansu akansu Jamimah.


Zuƙunnawa Deeja ta yi agabansu tare da ambaton sunayensu


"Jamimah! Azeeza! Lafiya ku ke yin ku ka? Wani abu ya faru ne"? Bakin Angel ya mutun, takasa magana, saboda faɗuwar da gabanta ke yi.


Cikin shessheƙar kuka Jamima tace"Ge..nie a ɗakin mu, ga ta can kwance saman gado number 3"


Jin ta ambaci bed no 3 yasa kowan nan su yin saurin kai idanuwan shi kan gadon, ganin kamar mutun ne yasa su ka soma kallon junan su, a ƙoƙarin su na su gano wanene acikin su yaje ya kwanta gadon, Ɗaya bayan ɗaya suka dinga saukowa daga saman gadajen su, tun daga kan Eve yasmin hibba hannah rubina, Sarah, kaf ɗinsu, A tsananin tsoroce su ke ƙarewa gadon kallo sai faman zazzare idanuwansu su ke yi.


"dagaske mutunce kwance saman gadon batul ɗin mu"! Jin wannan maganar da Parveen ta yi ne yasa Angel ware idanuwanta, ta sanya hannu tare da janye su Azeeza daga Jikinta.


Ta yunƙura ta miƙe jikinta na rawa ta nufi gadon Itama Deeja tabi bayanta, Ya rage saura azeeza da jamimah, sun fi kowa tsorata, rungume juna su ka yi kamar zasu haɗe jikinsu ya zama ɗaya.


A kewaye da gadon suka tsaitsaya curko curko, suna ƙare mata kallo, farat ɗaya Angel ta gane wacece muryarta na rawa ta ambaci sunanta da ƙarfi


* "BATOOL!" *


Ras! Gaban kowan nan su Ya faɗi, a ruɗe su ke kallonta, Basu tabbatar cewa ita bace, har sai da Angel ta hau saman gadon, Jiki na rawa ta sanya hannayenta biyu ta yaye sumar kanta gefe ɗaya, kyakkyawar fuskar batul ta bayyana, zazzare idanuwansu waje su ka yi, abun ne da basu tsammace shi ba, ba zaka iya tantance yanayin da su ke a ciki ba, suna so su yi farin ciki sai dai suna fargabar ace batul ɗinsu wani abu ya same ta, tun daga kan fuskarta su ka shaida hakan, kamar an ninka hasken fatarta, dama fara ce sol kamar Angel ko tabo babu a jikinta, hatta gwiwar ƙafarta jawur ta ke, ta canza masu sosai ta rame kamar an ɗibi naman jikinta, brownish lips ɗinta sun ciza sun bushe ƙamas, hankalinta a kwance ta ke fitar da numfashi sai dai kamar a firgice ta ke.


Halin da suka shiga furta shi 6ata baki ne, Zuciyoyin su sun karaya, Jiki yayi la'asar, Idanuwan kowannansu hawaye ne kwance a cikin su.


Muryar Angel cikin shessheƙar kuka ta furta"Ya Allah kasa ba mafarki na ke yi ba, Batul ɗina ce ta koma haka? Waye ya dawo mana da ita? Ta ina ta shigo? Dama dagaske ne abunda Gabriel ya faɗa min na cewa yaga matashiyar yarinya tana gudu asaman third floor! Batul ɗina ce kenan! ' Zuciyarta a hautsine ta yi maganar, ita kanta batasan ta furta hakan ba. yayin da idanuwanta ke akan jikin batul.


Hawaye ne masu ɗumi suka wanke fuskarta, ta ɗaura hannayenta biyu saman kafaɗunta, ta ɗago da ita, tare da kwantar da ita saman ƙirjinta, nan take taji wani irin yanayi mara misaltuwa ya ratsa jikinta, hakan ya ƙara tabbatar mata da cewa Batul ɗinta ce babu tantama, cikin rauni na murya ta shiga faɗin"wlh itace! Batul ɗin mu ce aka dawo mana da ita, tsawon wata uku, till today ashe da rabon zamu sake yin tozali da ƴar uwar mu! Alhamdulillah ya Allah bazan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba........" Sosai ta fashe da matsanancin ku ka tamkar ranta zai fita, suma sauran ƴan uwan nasu suka kama yin kukan farin ciki.


A gefe da gefen gadonta kowannan su Ya zauna, wasu ma saman gadon suka haye, kamar sun samu tv suna kuka suna kallon ƴar uwarsu dake a kwance jikin Angel, don tunda ta ƙanƙameta bata saketa ba, sosai ta yi tighting ɗinta a jikinta kamar zata mayar da ita cikin cikinta, Allah sarki tsohuwar zuma, Gaba ɗaya sautin shesshekar kukansu Ya karaɗe cikin ɗakin, bakomai yasa su yin kukan nan ba face tsabar farin cikin da su ke aciki, sai dai duk da hakan akwai fargaba acan ƙasan zuciyoyin su, saboda ba su san me aka yi mata ba, na tsawon lokacin da ta ɗauka a hannun su.


suna matuƙar jin fargabar abunda zasu ji daga gare ta, wani abu da ya ƙara tada masu hankali, Taƙi farkawa, duk wannan koke koken da su ke yi baisa ta buɗe idanuwanta ba, Azeeza dake rungume da jamimah tun da taji muryar Angel tana ambaton sunan Batul, tabi ta ruɗe ta shiga laluban hanyar da zata kai ta gare su, sai dai takasa, sai rarrafe ta ke yi a tsakiyar ɗakin tana ambaton sunan batul.


Jamimah ce ta taso itama tuni ta daina yin kukan jin cewa ƴar uwar su ce ba Aljanna, sai taji hankalin ta ya kwanta, tafiya tayi zuwa inda azeeza ta ke a zuƙunne ta ruƙo hannunta ta miƙar da ita, tare da yi mata jagora zuwa gaban gadon batul inda su Angel su ke a zazzaune, da taimakon Hannah ta samu ta haye gadon bayan sun matsa mata hanya, muryarta da zumuɗin ta ke faɗin ina batul ɗin ta ke ne? Dagaske itace aka dawo musu da ita?


fuskarta sharkaf da hawaye ta ke yi masu tambayar.


Makanta ba ta yi ba, idanuwanta akansu Angel saidai bata iya ganin su, ganin yadda take ta sharar ƙwalla tana ambaton sunan batul, Yasa deeja ta ruƙo hannunta ta ɗaura shi saman sumar kan batul data cika bayanta.


shafa gashin ta dinga yi da hannunta, muryar hanna a sanyaye tace mata"azeeza bacci ta ke yi, bata farka ba, tana rungume ne a jikin Angel ne" koda hanna ta yi mata magana, bata haƙura da laluban jikinta ba, har saida ta ɗaura hancinta a saman bayan batul, ta tabbatar da cewa ita ɗinta ce, tukunna hankalinta ya kwanta, farin ciki ya cika zuciyarta, sai zabga murmushi ta ke yi, Angel fa taƙi basu damar su rungumi ƴar uwarsu, tunda ta ƙanƙameta a jikinta taƙi sakinta, yadda kasan uwa da ƴarta, hannayenta biyu daddafe da bayanta, ko lokacin da azeeza take shasshafa sumar kan batul duk tana ji, sai dai bata motsa ba, gani take kamar in ta saketa za'a ƙara rabata da ita ne, Angel na matuƙar ƙaunar batul, fiye da tunanin mai tunani, irin ƙaunar da ta ke yi mata bata da banbanci data uwa da ɗanta, ji take kamar ciki ɗaya suka fito da batul.


Sarah da ke a tsaye tun ɗazu tana kallonsu, bata furta komai ba, sai dai da alama itama ta tayasu kukan don hada hawaye kan fuskarta, bakomai ne ya ta6a zuciyarta ba, face yarda taga sunata kuka, da kuma yarda Angel ta ƙanƙame ƴar uwar ta su a jikinta, hakan ya tabbatar mata da irin son da su ke yi mata, duk da batasan wacece batul ba, amma tana yawan jin suna ambaton sunanta, ta shaida irin ƙaunar da suke yi mata, ba ƙaramin burgeta su ka yi ba.


"Angel har yanzu bata farka ba? Ya za'ae muna so musan awani hali take ciki, A ƙagare muke da mu rungumi ƴar uwar mu, muji ɗuminta a jikin mu, tsawon lokaci bama a tare" Deeja ce tai magnar, fuskarta a yamutse don hankalinta ba'a kwance yake ba.


Dare ya koma masu tamkar da rana, babu mai jin bacci a cikin su, dama sun sha bacci yau.


"Bari na ɗebo ruwa a yayyafa mata ko mun samu ta farka" acewar rubina, kafin tayi yunƙurin mikewa Yasmin ta dakatar da ita ta hanyar yi mata magana"ai ba suma tayi ba, bacci ta ke yi, bana so mu takura mata, tunda tana nunfashi mu jira har zuwa time da zata farka"! Fasa zuwa ɗebo ruwan rubina tayi,

Cikin sanyin murya parveen tace"Allah yasa kada ta farka tana jin yunwa, wlh da ace mun san yau za'a dawo mana da ita, ai da mun ajiye mata abinci dayawa," ta yi maganar tana matse ƙwallar idonta, ɗakin yai tsit masu yin shessheƙar kukan duk sun dakata.


Sun yi zugudum kamar masu zaman makoki, kowa da abunda yake saƙawa a cikin ranshi dangane da tsintar batul da su ka yi a cikin su, Damuwace ƙarara akan fuskokinsu, fatansu Allah yasa ba acutar masu da ita ba, duba da irin baccin da take yi mai nauyin gaske, deeja ce tai tunanin yi magana akan suje su kwanta.

"Yakamata kuje ku kwanta ku yi bacci, dare ne sosai, nasan kafin gobe da safe in sha Allah zata farka......" tun kan ta kai ƙarshen maganar, su ka haɗa baki wurin cewa"ai bazamu iya runtsawa ba, idan har ƴar uwar mu bata farka ba, kusan wata uku bamu atare da ita, till today aka dawo mana da ita, Ta yaya kike tunanin zamu iya yin bacci? Ba tare da mun gana da juna ba"


Ita kanta Deeja ta yi masu maganar ne kawai, don tasan ba kwanciyar za su yi ba, duk wannan maganganun da suke yi Angel bata fahimtar su, domin kuwa hankalinta na akan batul ɗinta, dake kwance saman ƙirjinta, ta natsu tana sauraron bugun zuciyarta, sai faman lumshe idanuwanta ta ke yi, waɗanda suka canza launi saboda kukan da tasha, har yanzu hawayen basu daina gangarowa ta cikin idanuwanta ba.


"pls Angel ki kwantar mana da ita, yadda zamu samu damar ganin fuskarta da kyau, munyi kewarta sosai" Acewar eve, shiru Angel bata motsa ba, babu alamun zata kwantar da ita, hannu Deeja ta kai saman bayan Angel ta ɗan bubbugata don ta dawo hayyacinta.


"Angel muna son ganin fuskarta, ki kwantar mana da ita" deeja ce tai maganar, still bata tanka masu ba.


"Ko dai ta yi bacci ne"? Hibba ce tai tambayar, Sarah dake a tsaye ta matso kusa da gadon, ta sanya hannayenta biyu da niyar ta raba jikin batul daga na Angel, amma ta kasa, Lamarin ya ɗaure masu kai, suka dinga kiran sunanta taƙi amsa masu, kuma ba bacci ta ke yi ba.


Parveen da Deeja ne suka haɗa hannu wurin ƙoƙarin 6an6are batul daga jikinta, abun ya ɗaure masu kai, yadda taƙi sakinta, kamar su fashe da kuka saboda yadda suka ƙagara da son ganin fuskarta.


"Bani na ruƙe ta ba, itace ta ruƙe ni"


Muryar Angel ce ta yi masu magana, abunda basu sani ba, tun lokacin da Angel ta rungumo batul a jikinta ta farka daga baccin, koda taji jikin ƴar uwarta ne, ta ƙanƙameta sosai, hannayen batul na abayan Angel ta zagayo da su, sumar kan Angel ce ta rufe su shiyasa basu lura da cewar itace ta matse ta a jikinta ba, tun da farko da su ka buƙaci ganin fuskarta, Angel tai ƙoƙarin sakinta, sai dai ita batul ɗin taƙi bari ta raba jikinta daga nata, that mean batul ta farka daga bacci tuntuni.


Sun yi mamakin jin abunda Angel tace masu, na cewa itace ta ruƙeta, muryar Deeja a sanyaye tace"Batul, idan kina jin mu ki juyo ki fuskance mu, mu ma minyi missing ɗin ki sosai, muna buƙatar mu yi hugging ɗin ki a jikin mu......."


Kafin Deeja ta rufe bakinta, batul ta zame hannayenta daga ruƙon da ta yi ma Angel, kamar bata son raba jikinta daga nata, slowly ta zame kanta daga saman kafaɗar Angel, ta ɗago da kanta, yayin da ta ke ƙoƙarin buɗe idanuwanta kamar sunyi mata nauyi.


Angel sai kallonta ta ke yi, hatta su parveen sun zagayo ta inda zasu dinga ganinta da kyau, a wani irin yanayi ta buɗe kyawawan idanuwanta akan fuskar Angel da ke kallonta kamar zasu haɗiye juna, tun daga kan kallon da ta ke yi mata zai tabbatar maka da cewa ta yi matuƙar yin kewarta, ta yi kukan rashinta atare da ita, A hankali ta ɗauke idanuwanta daga kan fuskar Angel ta mayar dasu kan fuskokin su Deeja, Ɗaya bayan ɗaya take ƙare masu kallo kamar yau ta fara ganin su, haka suma su ke ta kallonta kamar sun samu tv, tambayoyi suka shiga jera mata kamar ƴan jarida



"Batul kina lafiya? Babu abunda ke damunki? Kin gane mu kuwa? Meyasa kike ta kallon mu! Ba zaki iya magana ba? Ko akwai inda ke yi maki ciwo? Dan Allah ki yi mana magana, mun damu dake sosai, munyi kewarki, munyi kuka rashinki kamar mu zauce........" suna magana hawaye na bin fuskokin su, basu yi tsammanin zata tanka masu ba.


Tausasan la66anta ta soma motsawa muryarta a sanyaye ta soma ambaton sunayensu ɗaya bayan ɗaya


Angel, Hannah, Hibba, Deeja, Parveen, Eve, Yasmin, Rubina," tsabar farin ciki yasa suka fasa ihu Jin ta kira sunayen su hakan na nufin Tana acikin hayyacinta, wani irin farin ciki ne ya lullu6e Su, kamar waɗanda akayiwa albishir da mukullin fita daga cikin kurkukun ƙaddara.


Tana so ta bayyana masu irin kewarsu da tayi sai dai takasa magana, saboda hawayen da suka ciko idanuwanta, daƙyar ta iya buɗe masu hannayen ta tare da yi masu alamar su matso kusa da ita, da sauri suka matsa ta haɗa azeeza da parveen da deeja ta rungumesu, sai lokacin ta samu damar fitar da kukan da take 6oyewa, sosai ta fashe masu sa ku ka, suma kukan suke yi an rasa me lallashin wani acikin su, ta ɗauki tsawon lokacin kafin ta saki su deeja, ta miƙa masu Hibba hannu suka matso suma ta rungume su a ƙirjinta, dukkan su saida suka ji ɗumin jikinta, da hannayensu suka dinga share mata hawayen dake akan fuskarta, itama ta sanya hannunta tana share ma kowannansu na kan fuskarshi.


Cikin sanyin murya ta furta"ashe da rabon mu sake ganin juna nida ƴan uwana! ashe mafarkina zai zama gaskiya na sake yin rayuwa a cikin ku? Jan numfashi tai kafin taci gaba da cewa"duk yadda zan faɗa maku irin kewarku da nayi ba zaku fahimta ba, haukane kawai banyi ba, amma naji jiki na rashin ku atare dani, na zubar da hawayena kamar bazan rayu ba, Allah ne kaɗai yasan irin raɗaɗi da ƙuncin da na shiga........" kasa ƙarasa maganar ta yi saboda kukan daya ciyota, da sauri Angel ta sanya hannayenta biyu ta dafa shoulders ɗinta tana lallashinta.


"Batul ki daina kuka dan Allah, kuma ku daina zubar da hawayen ku, godiya yakamata mu yi ma Allah daya dawo mana dake lafiya, duk da naga sauyi atattare dake, bamu san ina aka kaiki ba! Me a ka yi maki na tsawon watannin nan! Na yi maki tambayoyin nan ne saboda su ne damuwar mu, amma bamu buƙatar amsar su ayanzu, saboda kwanciyar hankalin ki mu ke so, ashirye mu ke da mu sanyaki farin ciki, wanda zaisa ki manta da duk wata damu da kika shiga na rashin mu atare dake,"


Kalaman Angel ba ƙaramin sanyaya mata zuciya su ka yi ba, atare suka ɗaga hannayensu sama suna yiwa Allah godiya haɗi da yi ma ƴar uwarsu batul addu'a, duk tana sauraronsu, wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, bayan sun kammala yi mata addu'ar ne, ta ɗago da kanta daga jikin Angel, Ganin tana kallon gadajensu Danish yasa duk suka sha jinin jikin su, aruɗe take ƙare masu kallo, abun da basu ta6a tsammanin zata tambayesu ba, sai ji su ka yi tace"Ina Danish!" shine mutun na farko da ta fara tambayarsu, sun yi mamakin hakan duk irin abunda yayi mata, cigaba da tambayarsu ta yi cikin ruɗu.


"Meyasa bangan su asaman gadajen su ba? Ina Haris ina Javed da Mubeen da Naufal? Ina su ka je ne? Ko sun shiga toilet ne"?


Angel ce ta yi mata magana"ki yi haƙuri batul, zuwa gobe da safe zamu faɗa maki komai, yanzu dare yayi sosai, ki kwanta ki huta ," ta yi maganar tare da ruƙota, ta kwantar da ita tare da janyo bargo ta lullu6a mata shi saman jikinta zuwa ƙirjin ta.


Ta yi mata hakan ne duk don ta kawar mata da tunaninta, na tambayarsu agame da su Haris.


Mayar da dubanta ta yi gasu Deeja"Ku je ku kwanta, Zuwa gobe za mu yi magana da ita" Ba don sunso ba suka miƙe kowa ya nufi tsohon gadon shi, duk don saboda ita suka kwanta saman su yau, itama sarah ta nufi shimfiɗarta ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe saƙe dangane da ƴar uwarsu batul da ta gani yau, da alama akwai wani abu daya ɗan sha mata kai.


Mutun biyu ne ya rage Azeeza dake zaune saman gadon batul, sai jamimah dake zaune gefen gadon sai gyangyaɗi ta ke yi kamar zata faɗo ƙasa.


"Azeeza taso muje in raka ki ki kwanta," maƙe kafaɗa Azeeza tayi tare da cewa"Inaso na kwana a gefen batul" shiru Angel ta ɗanyi tana kallon fuskarta, taci burin ta kwana tare da batul dinta, ga Azeeza ta nuna tanaso.


Ita kanta batul ɗin, bata son Angel tabar gadon nata, sai satar kallon juna su ke yi, da alama akwai wani abu daya ɗaure masu kai agame da canjin da kowan nan su ya yi, Sai da Angel ta ruƙo azeeza ta kwantar da ita gefen batul, tukunna ta sauko daga saman gadon, still idon batul akan fuskarta.


"Zanje na kwanta, ki kulamin da kanki, gobe zamu yi magana" ta ƙarasa maganar tana sakar mata murmushi. lumshe ido batul ta yi tare da ɗan jinjina mata kai, hawaye ne masu ɗumi suka soma gangarowa ta cikin idanuwan nata, nan take Angel taji gabanta ya faɗi, sai dai bata tambayeta hawayen menene ba, ta bari sai zuwa gobe su yi magana.


kasa tafiya tayi, komawa tayi daga gefen gadon ta ɗan zauna tare da duƙar da kanta saitin fuskar batul, ta manna mata kiss saman forehead ɗinta da cheek nata, a hankali batul ta ɗan ware idanuwanta tana duban Angel wadda tuni ta miƙe daga gefen gadon, sai da ta fara ɗaukar jamimah, kafin ta juya ta kwantar da ita saman gadon Danish itama ta kwanta daga gefenta tare da rungume jamimah a jikinta, sai kallon juna suke yi ita da batul da ke akwance saman gadonta, Da yake suna fuskantar juna.


Tsawon lokaci sunata ta kallon juna, ɗakin yai tsit baka jin sautin komai, sun ƙi bari bacci ya ɗauke su, gani su ke yi kamar in suka runtsa za'a ƙara zuwa a ɗauke masu ita, zuciyoyinsu a cike suke da tambayoyi iri iri da suke son su yi mata, idan gari ya ware, sun kwana da wadataccen farin ciki acikin zukatansu saboda dawowar ƴar uwarsu batul, kaɗan daga cikinsu ne suka samu damar tuntsawa.


❤PRISONERS💖


A washe garin ranar tun da sassafe, ta soma jin hayaniyarsu a cikin kunnanta, muryoyinsu da alamun farin ciki atattare da su, a hankali ta ɗan buɗe idanuwanta, biji biji ta fara ganinsu a kewaye da gadonta, har saida ta ɗan firgita, daga bisani ne idanuwanta suka dawo normal taga fuskokinsu a washe sai murmushi suke sakar mata, azeeza da ke a gefenta kwance, ta ɗan tada kanta saman gwiwar hannunta, ta ƙura mata ido sai kallonta ta ke kamar zata lashe ta.


"Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah! Allah mun gode maka daka dawo mana da ƴar uwar mu batul, Nifa jiya da daddare dana kwanta, gabana ya dinga faɗuwa gani nake kamar in na runtse idanuwana zan farka inga babu batul ɗin mu" Deeja ce ta yi maganar fuskarta ɗauke da murmushin farin ciki.


Parveen tace"wlh nima haka naji araina, shiyasa yau da safe ina farkawa nai wuff nazo gaban gadonki don in duba in ga ko kina nan" ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar batul, ta rasa akan wa zata tsayar da idanuwanta, sai faman jujjuya eye balls ɗinta ta ke yi akan faces ɗin su.


"Ni kaina da mafarkin ki na kwana, ƴar uwata rabin raina" da sauri ta wurga eye balls ɗinta kan fuskar Angel wadda zuwanta kenan, Tana agefen Hibba, wani murmushin ne ya ƙara bayyana akan fuskarta, wanda ke nuni da irin farin cikin da take a ciki.


"Fatan ba mu takura maki ba, mun tada ki daga bacci, wlh mun yi kewarki ne kamar mu zauce" acewar hibba, calmy ta soma magana"Nafi so ku takura min hibba, aini abunso ne a wurina, in gan ku atare dani, ko na minti ɗaya bana son wani a cikin ku ya nisanta dani, ba dan ƙaddara ta rabani da ku ba, ku kan ku kun sani, da ƙafafuwana bazan ta6a yin nesa da ku ba" muryarta na ɗan rawa ta ƙarasa maganar, tuni idanuwanta suka cicciko da ƙwalla, ita kaɗai tasan irin raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyarta.


"Batul pls don't cry, idan har ba so kike zuciyoyin mu su raunata ba, mun fi buƙatar farin cikin ki ayanzu, ki daure pls," Deeja ce tai maganar, lumshe idanuwanta ta ɗanyi yayin da take binsu da kallo, su kansu sun fahimci akwai wani abu dake damunta.


"Azeeza irin wannan kallo haka, " daƙyar ta furta maganar, tana kallon azeeza, murmushi ta sakar mata tare da cewa"Ƙaunarki nake yi batul, dole in kalle ki don baki san irin kewarki da nayi ba. Kamar in haɗiye ki" tayi maganar tana wage bakinta, Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ta basu ba.


Ita kanta batul ɗin saida ta ɗan murmusa, a hankali ta yunƙura ta miƙe, itama azeeza ta miƙe zaune saman mattress ɗin, Saukowa ta yi daga saman gadon taci gaba da tafiya tana bin ɗakin nasu da kallo, ganin irin sauye sauyen da a ka yi mashi, gaba ɗaya suka bi bayanta suna tafiya atare da ita, dakatawa tayi da yin tafiyar tare da juyowa ta kallesu tace"Jiya na tambaye ku amma ba ku bani amsa ba, ina Danish dasu haris su ke ne"? Deeja ce tai ƙarfin halin faɗa mata cewa anzo an tafi dasu almost one week, An riga tafiya da Danish," iya abunda ta sanar da ita kenan, bata faɗa mata awani hali aka tafi da shi ba, jinjina kanta ta yi ba tare da tace komai ba, sai dai fuskarta ta nuna alamun damuwa, kuma idanuwanta hawaye ne acike dasu.


"An kawo mana sabbin prisoners ne? Jiya kamar naso inga wata ƙaramar yarinya," tai tambayar tana kallonsu "naga kuma sabbin gadaje, kusan goma sha biyar" yasmin ce ta bata amsa dacewa"Eh, bayan tafiyarki aka kawo su, Amma mutun biyar ne prisoners ɗin, sai dai daga cikinsu Giants sun tafi da mutun uku, yanzu biyune atare damu. jamimah itace ƙaramar sai Sarah," ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa"ku bani labari mana, dame dame ya faru bayan bana nan"? A taƙaice Angel ta sanar da ita duk wani abu da ya faru bayan bata nan sai dai bata faɗa mata wanda zai sanyata damuwa ba.


"Mu koma mu zauna batul," yasmin ce tai mata maganar, ganin sai yawo su ke yi cikin ɗakin, ga shi daga gani jikin nata babu ƙwari, ga ƴar guntuwar rigar dake a jikinta sai ɗagewa ta ke yi.


"Kina jin yunwa" parveen ce tai mata tambayar, ɗaga mata kai ta yi alamar eh, langwa6e kai parveen"wayyo Allah, ga shi babu abinci sai giants sun kawo mana" ƴar dariya Batul ta saki kafin tace"Ki kwantar da hankalin ki, kallon ku da na ke yasa naji na ƙoshi, babu wani yunwa atare dani,"


"Batul baki bamu labarin ina aka kai ki ba tsawon wata uku? Sannan waye ya dawo mana dake ko giant ne, mun ga kin canza mana sosai, kin rame kamar babu ƙoshin lafiya atare da ke" rubina ce tayi maganar,


Shiru ta ɗanyi kamar bazata amsa mata tambayoyin ta ba, duk su ka tsareta da ido suna kallonta, tun kafin ta fara magana Angel ta raya aranta cewa batul baza ta faɗa masu gaskiyar abunda ya faru da ita ba, ko dan kada ta sanya su damuwa.


A tsanake ta soma magana"bakomai ne zan iya tunawa ba, tun time da aka tafi dani, na dai san ba a cutar dani ba, ramar da ku ka gani a jikina bata komai bace face rashin ku atare dani, na tsinci kaina acikin wani ɗaki ina rayuwa ni kaɗai, ban rasa ci da sha ba, ana kawo min lafiyayyen abinci, ina yin wanka har ma in kwanta in yi bacci, mafi yawancin lokutta, ina yawan yin kukan rashin ku, in dinga ihu ina ambaton sunayen ku don kuzo ku ɗauke ni sai dai shiru babu mai jina........." iya abinda ta faɗa masu kenan, kuma sun yarda da maganarta, banda Angel, don koda tana basu labarin idonta akan Angel don tasan bazata yarda da ita ba, abunda yasa su deeja suka yarda da labarin da ta basu, saboda an dawo masu da ita ba kamar yarda aka saba dawowa dasu ba, Cikin mawuyacin hali, wasu ma basa a cikin hayyacin su.


"Batul yakamata kije ki yi wanka, akwai sabbin kaya da muka fada maki tsohuwa tamira ta bamu zamu ɗauko maki naki ki sanya, sannan muna so zamu gyara maki gashin kan ki" fuskarta ɗauke da murmushi tace masu toh, Eve tace"wai ina Uniform ɗin ki su ke ne? Ya akai aka sanya maki wannan guntuwar rigar launin Ja"? Muryarta da en ina tace"am..in..nima bansani ba, bansan waye ya canza min ita ba, kawai rana ɗaya na farka na ganni da ita a jikina" wani irin kallo Angel take binta dashi, kallon ban yarda da maganar ki ba, sai faman wurwurga ƙwayar idanuwanta ta ke yi, da zarar sun haɗa ido da Angel saita kawar da kanta gefe.


Ganin hakan yasa Angel ta ruƙo hannunta a cikin nata sosai ta damƙe shi tare da cewa"Muje na taimaka maki kiyi wankan" da sauri ta girgiza kai tare da cewa"Zan iya Angel, ki bari zanje nayi da kaina" a ruɗe tayi maganar, hakan ya ƙara tabbatar ma Angel abunda ta ke hasashe akanta, ta 6oye masu abunda ya faru da ita.


Gyaɗa kai Angel tayi"Its ok, amma mu fara shiga toilet ɗin, mu wanke maki kanki, In yaso daga bisani saimu fito mu barki ki yi wankan" muryarta adarare ta amsa mata da toh.


Mutun uku ne suka haɗu wurin wanke mata gashin kanta saboda yawanshi, Angel da Hanna sai Seeja, Sosai suka murje gashin kan nata, Bayan sun kammala wanke mata kan, suka barta cikin toilet din don tayi wanka, Angel fa jikinta duk ya yi sanyi, a ƙagare take da su samu damar da zasu ke6e da ita don suyi magana, sai dai ga dukkan alamu ita batul ɗin bata son su yi magana, shiyasa take kakkauce mata, Bayan wasu ƴan mintuna, Batul ta fito daga wakan, dama tun kafin fitowarta Angel ta ɗauko mata sabbin kayanta, ba tare da 6ata lokaci ba, ta zura uniform din a jikinta, Masha Allah, zayyana irin kyan da batul tayi a cikin kayan nata 6ata baki ne, abunka ga fara sol, Sun ƙara fiddo mata da kyanta, don ma ta ɗanyi rama.


daga ciki ta sanya red vest dinta, sama ta ɗaura wrap coat dinta, kafin ta sanya black trouser din, Angel ce ta taimaka mata wurin ɗaure igiyar coat ɗin, ta ɗaura mata Cotton scarves ɗinta saman wuyanta, Bayan ta kammala gyara mata su tsaf a jikinta.


Su Parveen sai santin kyanta su ke yi, Hannu biyu angel ta sanya wurin janyota a jikinta, sosai ta rungumeta, tana ɗan bubbuga bayanta, in a low voice ta furta mata"Ina son magana da ke, amma na lura kamar baki so why"? Muryarta na ɗan rawa tace"Angel, banason tuna abunda ya faru dani, pls kada ki matsa min kada ki tambaye ni komai, na roƙe ki, kuma bana so hakan ya 6ata maki rai" suna yin maganar ne ba tare da sun raba jikinsu daga na juna ba.


"Shikenan batul, bazan tambaye ki ba, ni kaina bana son na takura maki, zan jira ki har zuwa time da kika ji zaki iya sanar dani sai ki faɗa min" ta amsa mata da toh," Deeja dake ta kallonsu manne da juna ta fahimci cewa magana su ke yi, bayan sun raba jikinsu, ta dinga bin su azeeza tana rungume su a jikinta tana faɗa masu irin kewarsu da ta yi, Deeja kuma taja hannun Angel su ka koma gefe ɗaya,


Tambayarta ta yi me suka tattauna da batul, ta sanar da ita cewa ta tambaye ta ne game da abunda ya faru da ita amma bata faɗa mata komai ba, Deeja tace"kada mu takura mata, tunda ta nuna bata son mu sani, mu ƙyale ta kawai, wata kil hakan zaifi mana kwanciyar hankali," Angel ta gamsu da maganar deeja.


Badajimawa ba, Giants suka kawo masu lafiyayyan abinci, Saboda tsabar ƙauna, a baki suka dinga ba batul tana ci, sunƙi bari ta sanya hannunta taci, hakan ba ƙaramin karya mata zuciya yayi ba, tabbas an zalunce ta da aka raba ta da ƴan uwanta, amma yanzu Alhamdulillah tunda gata a cikinsu, da ranta da lafiyarta.


Bayan sun kammala Cin abincin, Giants suka tattara Farantan suka tafi dasu, A saman shimfidar sarah, suka zazzauna suna fira tare da batul, Angel tana zuƙunne gaban akwatinansu, Ta buɗe ta ɗauko Nail cutter da nail filler tare da madubi, ta dawo ta miƙe ma Sarah tace gashi ta gyara ma ƴar uwarsu akaifa, Murmushi sarah tasaki, tare da sanya hannu ta kar6a, Kafin su fara gyaran akaifar, Angel tace ta ɗan dakata, tana so su kalli faces ɗinsu a cikin madubi, ita da ƴar uwarta batul, Gefen batul ta zauna tare da ɗaga madubin, Ta haɗa fuskokinsu wuri ɗaya, Suka natsu suna kallon juna, hakanan Angel ta dinga jin faɗuwar gaba a yayin da take kallon fuskar batul ta cikin mirror, su azeeza sai faman leƙo da fuskokinsu suke yi suna kallon su.


"An ta6a faɗa maku cewa, Kuna bala'en kama da juna" Sarah ce tai maganar, parveen tace"wlh kuwa nima saida ki ka yi maganar nan tukunna na lura da hakan, Angel da batul suna kama sosai, musamman ta wurin shape ɗin bakinsu, duk da ba launi ɗaya bane, da kuma hasken fatarsu, gashin kansu ma Ya yi shige, hatta tsawonsu iri ɗaya,"


Deeja tace"ae hatta Yatsun hannuwansu dana ƙafafuwansu iri ɗaya ne sak babu bambanci, najima da sanin wannan ban ta6a faɗi bane" sarah tace"to kodai ƴan gida ɗaya ne"? Girgiza kai Yasmin tai tare da cewa"A labarin da Angel ta bamu, ita kaɗaice Awurin daddynta, mommynta ma, tun tana yarinya ta gudu tabarta, bata da ƴar uwa mace tun da ta taso a rayuwarta,"


Sarah tace"hmmm adai yi shiru kawai amma fa ni akwai abunda nake zargi, ina da wata baiwa da ku ba ku sani ba, tun kasancewa ta a prison, nake wannan hasashen, nasha ganin masu kama da juna wanda su basu lura da hakan ba, sai dai ina tunanin zaman tare ne yasa muke kamanceceniya da juna, yanzu a cikin ku nan, kaf ɗinku Naga kamanceceniya atsakaninku da junan ku, Hatta wannan yarinyar da aka kawo mu tare da ita, Me take da suna....." Eve ce ta ƙarasa mata maganar da cewa"Kina nufin Ƴar gidan daddy" jinjina kai tayi "eh ita nake nufi, akwai kamanceceniyarta da wani acikin ku, amma bazan faɗi ba" tana ƴar dariya ta yi maganar,


"Ko kina nufin azeeza? Don kinga kalar gashinsu yayi shige da launin fatarsu," girgiza kai tayi"a'a, ba azeeza ba, bana so na faɗi maku ne"


Roƙon ta su ka dinga yi haɗi da yi mata magiya akan ta faɗa masu da wa take kama, da kuma sauran waɗanda ta ke hasashen suna da kamanceceniya a tsakaninsu, tace masu itafa su daina yarda da maganarta, Ƙarya ta ke yi masu"


Haushin da suka ji ne yasa suka dunƙule hannu suna yi mata dundu abayanta, Abun saiya koma wasa, duk wannan abun da suke yi Angel da batul suna sauraronsu, sai dai hankalinsu ba akansu Ya ke ba, Yana akan junansu, Sai kallon fuskokinsu suke yi ta cikin madubi kamar zasu lashe juna, Sai da suka gama ƴar buge bugen da sarah, kafin daga bisani, kowannansu Ya natsu, suna ta nishi kamar waɗanda suka sha gudu.


Bayan sun samu natsuwa, Sarah ta soma gyarama batul akaifarta, Allah yayi mata baiwar Iya gyara akaifa, Batul taji daɗin ganin yadda ta gyara mata akaifarta, ta dinga yi mata godiya, Sarah tace tadaina yi mata godiya, domin kuwa babu godiya a tsakanin prisoners,"


Ataƙaice, Cikin ƴan kwanakin nan da aka dawo masu da batul, Sun samu farin ciki mara misaltuwa, Tamkar an ya ye masu damuwar dake damun so, koda yaushe suna atare da ita, dama batul akwai iya kalami mai ratsa zukata, haka zata zauna tana kwantar masu da hankalinsu, da deeja tare da Angel, waɗannan mutun ukun sun zama tamkar iyaye agare su, yanzu batul ta fara murmurewa, tsawon sati biyu da aka dawo da ita Jikinta yafara dawowa normal, babu ramar nan, hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba, har tambayar Angel tayi bayan bata nan an ƙara ɗaukar wani cikin su Hibba, ta sanar da ita cewa ba a ƙara zuwa ɗaukarsu ba, saboda babu wanda ya ƙara yin jinin a cikinsu, Allah ya yaye masu, sun samu salama, har cikin ranta taji daɗin jin hakan, Angel taso ta tambayi batul game da labarin da Gabriel ya bata na yarinyar daya gani tana gudu saman hawa na uku, saboda a suffar da aka dawo da batul yayi dai dai da yarda ya zayyana mata ita, hada guntuwar rigar daya gani a jikinta, Tabar abun a cikin zuciyarta ne, tun da ta nuna bata son maganar.


Har ila yau shiru ba'a dawo dasu Haris ba, Sun zuba ma sarautar Allah ido, addu'a kawai suke binsu da ita, A 6angaren Angel bata ƙara tada zancen dura tagar nan ba, saboda alƙawarin da Danish yace ta ɗaukar mashi akan bazata haurata ba, duk da a lokacin bata amsa mashi ba, sai dai taji ba za ta iya karya mashi alƙawarin ba..........


💔PRISONERS💔


Kwakkwance suke saman gadajensu, suna ta sharar bacci, har safiya ta yi amma basu farka ba, Jiya sun aikatu sosai, sai da suka wanke uniform ɗinsu duka da tsafaffin da sababbin kamar yarda suke yi in zasu wanke su sai su ɗaura bargunansu a jikin su,


Bayan sun kammala wankin su ka shanyasu zuwa lokacin da suka bushe suka mayar da tsoffin a jikinsu, sababbin suka ninninke su acikin akwatinansu, basu huta ba saida suka wanke bargunansu, suka shanyasu saman igiya, bayan sun kammala suka wanke toilets dinsu duka uku, suka bama furennin nan ruwa, Daga bisani, suka dawo cikin ɗakinsu, shima suka gyara shi tsaf tsaf komai Ya koma normal, a lokacin dare yayi suka kwanta don su huta, in the midnight Angel ta tada kowannansu don su yi addu'a kamar yarda suka saba, ga bacci a idonsu da gajiya amma ahaka suka zaune tare da ɗaga hannayensu sama suna kai kukansu wurin Allah, bayan sun kammala ne wani baccin ya ƙara yin awon gaba dasu, Shiyasa har gari ya waye basu tashi ba, saboda basu samu isasshen bacci ba jiya.


Azeeza da Jamimah suna a kwance saman gaɗo ɗaya, sarah tana a kwance ƙasa saman shimfiɗarta, yayin da batul ta ke a kwance saman gadon Danish ita da Angel, ƙudundune cikin bargo, atakure su ke gadon ya yi masu kaɗan ahaka suka kwana, su parveen duk suna asaman nasu gadajensu.


Wata irin zufa ce ta soma wanke fuskarta, ta dinga tsastsafo mata daga jikinta, Yatsun hannayenta da ƙafafuwanta suka soma kakarwa, Mafi yawancin lokaci idan hakan ya faru to mafarki ne ta ke yi acikin baccin ta,


_Ta tsinci kanta acikin wani gini mai girman gaske, mai ɗauke da tagogi babu ƙopa ko ɗaya a jikin shi, tsananin tsoro da firgici ya kamata, ta dinga kuka tana ambaton sunan Allah akan ya kawo mata ɗauki, wasu halittu ne ke fitowa ta jikin bango ɗauke da suffar namun daji, munanan gaske, gaba ɗaya ita suke tunkarowa, gashi babu hanyar da zata gudu daga cikin ginin, fashewa tayi da matsanancin kuka mai cin rai tana girgiza kanta tamkar zai 6alle, Halittun na dab da ƙarasowa gabanta, Sai ga wata halitta ta faɗo ta saman ginin ɗauke da manyan fuka fuki sai shawagi take yi tana kewaye tsakiyar Ginin, kafin ta karyo kwana ta sanya hannayenta biyu ta ɗauke Angel tayi sama da ita ta fuce daga Cikin Ginin_


A dai dai nan mafarkin nata ya katse, A firgice ta farka daga baccin tana faman zare idanuwanta, hannunta ɗaya dafe da saitin zuciyarta da ke ta harbawa, zufa duk ta wanke fuskarta, muryarta na rawa ta soma ambaton


"A'oothu billaahi minash-Shaytaanir-rajeem" sau uku tana ambatonta.


Bayan ta kammala taji sauki acikin ranta, ta juya ta kalli batul dake ta sharar baccinta, ajiyar zuciya ta sauke tare da zuro ƙafafuwanta ƙasa ta sauko daga saman gadon, zuciyarta acunkushe da tunanin mafarkin da ta yi yau, ta rasa gane me ma'anar mafarkin ke nufi kodai shaidan ne ya haddasa mata yin shi, sai dai tana ji acikin ranta kamar akwai wani abu da ake son nuna mata acikin mafarkin, Taya zata iya fahimtar hakan? Wani ginine ta gani acikin mafarkinta? Babu ƙofa a jikin shi sai dai tagogi, ga wasu halittu na ƙoƙarin kawo mata hari, abun da ya ɗaure mata kai, wannan halittar data 6ullo ta saman ginin dake a datse babu ƙopa, taya akai ta shigo ita? Harta taimake ta kuma ta fitar da ita daga cikin ginin da babu ƙopa a jikin shi?


Ganin tana ƙoƙarin burkita lissafin ƙwaƙwalwarta ne yasa ta dakata da yin tunanin, da sauri ta juya ta nufi toilet don ta yi fitsari, shiga ciki tai tare da jan jam lock ta datse ƙopar, Juyawar da zatayi keda wuya taji gabanta ya faɗi ras! Ba tare da sanin dililin hakan ba, Acikin zuciyarta ta soma ambaton Innalallahi wa'inna ilaihirraji"un"


kusan sau shida har saida taji zuciyarta ta ɗan lafa tukunna ta ƙarasa shiga ciki, Tayi abunda ya kawota, bayan ta kammala kafin ta fita ta ɗan juya ta kalli furennin dake acikin tukunyar, wannan dogon furen daya kere tsayin sauran launin punch pink, ganyayyakin Jikin shi sunyi baƙiƙƙirin dasu, hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, da sauri ta koma ta ɗebo ruwa a bucket takai shi bakin tukunyar ta zuƙunna tana goge bakin jikin shi da hannayenta gani take kamar goga mashi baƙin akayi, sai dai koda ta goge babu abunda ya canza har ruwa ta zuba mashi ta wanke shi yaƙi canza launi, miƙewa tayi taje ta ɗauko detergent tsabar hauka hada Soso ta zuƙunna gaban tukunyar ta dinga goge ganyayyakin jikin furen don su koma launinsu na asali, sai dai kash sunƙi komawa, kamar tana ƙara masu baƙi, a ƙarshe data gaji ta maida soson da omon, ta fito daga Cikin toilet ɗin Jikin ta ba ƙwari, hakanan ta dinga jin kamar faɗuwar gabanta yana da nasaba da canzawar launin ganyan furen nan, duk da batasan ran wanene akan shi ba.


A bakin ƙopar toilet ɗin ta jingina bayanta, Idanuwanta acike tab da ƙwalla, daga Cikin ɗakinsu ta soma jin motsin buɗe ƙopa, da farko ta yi tunanin giants ne masu kawo masu abinci, shiyasa taƙi motsawa


kwatsam! Ta soma jin shessheƙar kukan mutun acan cikin ɗakinsu, Da gudun gaske ta faɗo ɗakin a sukwane ta kai idanuwanta kan benan inda take jiyo sautin, Bakowa idanuwanta ke nuna mata ba face Majnoon fuskarshi ta yi jawur da ita, jan tabo ta ko'ina a jikin shi, jini ya kwanta sosai, daga shi sai jan wandonshi a jikin shi babu riga, ya rame sosai, kamar ba mutun ba, hankalin ta ba ƙaramin tashi yai ba, tana ƙoƙarin motsa la66anta donta kira sunanshi karaf idanuwanta suka sauka akan fararen ƙafafuwan mutumin dake a gefen shi, a matuƙar ruɗe Angel ta shiga bin ƙafafuwan da kallo daga gani macace, koma wacece taji jiki na fitar hayyaci ta jigata sosai, duba da irin yarda jikinta keta kerma babu alamun lafiya atattare da ita, Hannunta ɗaya ruƙe da pant na mata launin Pink colour..........."


Adai dai nan na ajiye alƙalamina✍️🤟




*Idan Allah yakaimu next week zan Kammala Free pages of Takun farko, zan ɗauki hutu, kafin acigaba da middle step, saboda in samu natsuwa kafin in dasa, ba jimawa zanyi ba, ƴar tazarace, Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za'ayi adding naka a paid group kuma za'a sanyaka a comment section, Sa'annan Ba'a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*


*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*


*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*


*3196407426*

Bature Hafsat Muhammad

First bank


*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (***) ko kuma ta (***)*