Chapter 12
Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: ***
*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*
✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧
𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆
*Talla👇👇👇*
***
*INA MATAN DA SUKASAN DARAJAR GYARA❓DAKU NAKE MACE MAI GYARAN BATA ZAMA BORA❌*
*KUZO GA INGANTATTUN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI💪BA MUNA KAYABA❌ HAJIYA KIZO KISAI KAYAN MATA WURIN DA BAZAKIYI ASARAR KUDIN KI BA*
*INA MASU CEWA NI KO NASHA KAYAN MATA BASAMIN AIKI HMMM HAJIYA BAKIDAI SIYA KAYA MASU INGANCI BANE, KAYANMU SUNA KARA NI'IMA, TAYARDA SHA'AWA, DADI, TIGHTENING (MATSI), CIKO DA GABAN MACE (DUK BUDEWAR SA), DUMIN GABA GA, KAMSHIN GABA GA KUMA NA KARA DANDANO OVER 💃💃💃💃💃👉 GA KUMA INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI DAGARGAZA SANYI KODA YA SHEKARA 10 A JIKINKI* ***
*A DAYA BANGAREN KUMA MUNADA SABAYA MAI GYARAN NONO DUK LALACEWAR SA KO KIN HAIHU GOMA SABAYAR MU ZATA CIKO MAKI DA BREAST SUYI GIRMA SOSAI MADAME*
*GA KUMA TA HIPS (MAZAUNAI)SU CIKO SUYI BULBUL NONO YA CIKO SOSAI HJY KIYI KIBA YAR DAIDAI SKIN DINKI YAYI KYAU KI KOMA TAMKAR TARWADA*
AKWAI KUMA NA GYARAN NONO WANDA BAYA SAKA KIBA💃💃💃
GASKIYA NA YARDA DA INGANCIN KAYANTA👆👆👆
*Chapter - 12*
Kun ji ni shiru kwana biyu sakamakon rashin da muka yi. Amman Alhamdulillahi ala kulli halin.
______________________
Ta dade shiru bata ce komai ba kamar bata jikin wayar har sai da ya dauke wayar daga kunnesa ya duba ya sake mayarwa.
“Safaeena ina tunanin saboda kina da magana da ni ne kika kira ni”
Cikin muryar kuka ta soma magana.
“Ka canja min Kareem, daga lokacin da ka hadu da mahaukaciyar yarinyar nan gaba daya hankalinka ya tashi daga gareni ya koma gareta, yau har ta kai ta daga wayarka ka fada min magana son ranta, Wallahi da ban yi kokarin rike kaina ba da Allah kadao ya san abun da zan aikata a yau din nan kuma Allah ya san halin da zan shiga”
Ya sauko daga matakalal dake gurin yana rike da wayar a kunnensa.
“Ina kokarin shata liyi ne a tsakaninmu, akwai abubuwan da idan suka yi yawa, rashin tunani yana shiga ciki ya zauna, kamar yadda yake kike tunanin son haihuwa da ni yayinda kike da aure da wani, abun da kika yi niyar aikatawa ya tsorata ni, kuma ya bani mamaki, sannan ya farkar da ni daga dogon bachin da nake”
“Baka ji tsoro ba? Lokacin da na ce maka cikina ya zube saboda kishinka? Baka yi tunanin zan iya shiga damuwa idan ka guje min ba, Kareem a can baya ma da muka yi soyayya kawai da na rasa ka sai da na rasa mijin aure saboda na kusa haukacewa, aka rasa namijin da zai aureni sai Abdull, balle kuma yanzu da na riga na san ka farin sani ka tsara jikina ta yadda bana jindadin mu'alama da miji sai da kai, ka san duk yadda zaka yi ka kawar min da kishina ka faranta zuciyata, Kareem saboda ina sonka ne ya saka nake son na haihu da kai, saboda ina da mafarkin da nake son ya tabbata a nan gaba, Wallahi ina sonka Kareem na sabu da kai, idan ka sake guje min a karo na biyu ba zan hakura ba...”
Wani dogon numfashi ya sauke ya juya ya kalli kofar da ya fito sannan ya ce.
“Safeena na san kina so na, ni ma ina sonki amman Allah be kaddara mu zama ma'aurata ba, be kamata mu yi ma yaran mu haka ba, be kamata ke ma ci amanar mijinki ba, ya kamata mu karbi kaddarar mana ko dan karin imaninmu da yafiya daga zunubanmu”
Yana jin lokacin da taja majina tukuna ta amsa.
“Mun karba, shiyasa kake auren wata macen ni kuma nake auren wani namijin da ba kai ba Kareem”
“Idan har zamu cigaba da aikata abun da muke aikatawa kazantar ta yi yawa abun yayi muni, kuma hakan yana nufin ba mu karbi kaddarar ba Safeena”
Ta yi dariya da zai iya ji.
“Ba akan mu farau ba Kareem, kuma shi Allah mai yafiya ne a koda yaushe, ba haka za mu dauwama ba, wasu ma suna matsayin budurwa da saurayi suke yi balle mu da muke da aure, wannan abun duk kauna ce ta kawo, karka bari yarinyar nan ta canja min kai”
“Babu ruwan Noor a alakata da ke, ni ba soyayya nake da ita ba, kawai dai an yi sara ne akan gaba ne, amman ba aurenta zan yi ba”
Fashe masa ta yi da kuka.
“Kana cewa mu rabu kamar abu ne mai sauki Kareem, kana kokarin juya min baya bayan kuma na saba da komai na ka, taya kake son na jidadin rayuwa babu kai a kusa da ni? Wallahi saboda kai bana sha'awar Mijinta yayi sati daya a garin nan, saboda kai bana jindadin duk wata mu'alama da mijina, kullum mafarkina da burina akanka ne Kareem, ka juya min baya a lokacin da na fi bukatarka, yanzu kuma mun sabu da juna kake kokarin guje min a karo na biyu? Ko ka manta wacece Safeena a gurinka Kareem....?”
Tif... Ya kashe wayar ya sauke ajiyar zuciya, jin kamar kalamta na kokarin saukar masa da tausayinta kuma suna kokarin kusanto da rauninsa.
“Me na jefa kaina a ciki? Me yasa na bari zuciyata ta yi nesa? Ba zan sake aikatawa ba, ba zan sake ba, ba zan sake cutar da wani ba, ba zan sake bari zuciyata da yaudari da jindadin da ba zai tabbata ba a gareni”
Ya saka wayar aljihu sannan ya sake sauke ajiyar zuciya a karo na Biyu ya juya ya koma ciki. A bude ya samu office din babu kowa a ciki ma'ana dai Hafiz ya fita daga office din. Wayarsa ya fara cirewa daga aljihu ya dora a saman teburinsa sannan ya zauna ya dafe kansa. Abu da yake a bayyane gurin kowa kuma sirri dake aje a zuciyarsa yana son Safeena irin son da yake jin ba sai taba samun mai maye masa gurbinta ba, irin son da ya tabbatar sai dai ya mutu da shi domin ba zai iya aurenta ba a yanzu kuma baya jin zai iya cigaba da mu'alama da ita ta kazamtacciyar hanyar da ya sabawar kansa. Sai bayan sallah Isha'i Kareem ya koma gidansa, yana shiga falonsa ya samu Yusura zaune tana duba waya, laramin danta dake cinyarta ya zo da gudu ya tare shi.
“Daddy Oyoyo”
Kareem ya cillashi sama ya cafke sannan ya sauke shi ya shafa kansa yana murmushi.
“Areef ya kake?”
“Lafeeya lau, amman Momy bata da lafiya”
Kareem ya daga kai ya kalleta sai ya ga har lokacin idonta yana kan wayar dake hannunta kamar ma bata san da shigowarsa ba. Ya maida dubanshi gurin Areef
“Me ya same ta?”
“Jikinta da zafi ta yi amai kuma ta yi kuka...”
“To yayi kyau je dakinka ka kwanta gobe akwai makaranta, ina Tine”
“She's sleeping”
“Okay kai ma je ka kwanta”
Ya sumbance shi yaron ma ya mayar masa sannan ya sake shi ya nufi sama da gudu yana waigensa. Sai da ya haye sannan Kareem ya karasa gurin da Yusura take zaune yana daga tsaye zai yi magana ta riga shi ba tare da ta kalleshi ba.
“Ga abincinka a dinning room”
Ya kalli dinning area din sannan ya sake dubanta.
“Ai da baki girka ba, tun da baki da lafiya kuma abinci ba wani damuna yayi ba...”
Ta tsayar da taba wayar da take ta dago ta kalleshi.
“Idan har ban girka abinci a gidan nan ba, wata kila ina ciwo ne mai tsanani da ba zai bar ni na iya tsayuwa da kafafuwana ba, amman girka abinci, gyara gida, kula da yaranka da kuma tsare mutuncina, wani abu ne da addinin da al'ada suka taru suka samar mana, ina yi ne saboda sauki nauyi na matar aure a gidan Kareem, ba wai ina yi ne saboda Kareem ba, ina jin tsoron tsayawa a gaban mahaliccina ya tambaye ni wani hakki na bawansa na kasa amsa masa, ko Kareem ya ci abinci ko kar ya ci Yusura zata girka, ko ka tsare mutuncinka ko kar ka yi Yusura zata tsare nata, ko ka kula yaranka ko karka kula Yusura zata ba su tarbiya gwargwadon halinta...”
Ya hade wani abu da ya ji yana masa yawo na rashin dadi ya danne zuciyarsa ya sake yin furuci a gareta.
“Ya jikin na ki? Me yake damunki?”
Ta sake daga kai ta dubeshi.
“Kana da bukatar wani abu?”
Ya saka hannunsa aljihu ya ciro wallet dinsa ya cire ATM dinsa ya aje mata a hannun kujerar da take zaune.
“Gashi idan kina bukatar wani abu ki siya, idan kuma kina bukatar ganin Likita ki je ki ganshi, 5885 is the pin”
Yana dauke hannunsa daga aje ATM din ta mike tsaye.
“Bana bukatar komai daga gareka, ina da rufin asirin da zai wadace na yi ma kaina komai, sai da safe”
Ta bar a gurin tsaye ta nufi stairs. Binta yayi da kallo har sai da ta haye sama sannan ya zauna a inda ta tashi ya ja hular kansa baya ya kai hannunsa yana murza gaban goshinsa dake masa ciwo ya rufe ido.
YUSURA POV.
Tana shiga dakinta ta maida kofar dakin ta rufe ta zauna bakin gadonta hawaye suka sauko mata. Ba burinta ba ne fadawa mijinta bakar magana ba burinta ba ne yin zaman auren da babu farinciki a cikinsa, amman tsananin kiyayyar da take yi ma Kareem ya hana ta mallaka masa ruhinta, daman ita zuciyata ta san ba zai taba samunta ba, domin bata taba jin wani abu akansa ba duk tsawon lokacin da suka dauka a tare, tana kone zuciyarta ne kawai tana azabtar da kanta. Kareem yana da kyau da cikar kamala irin wadda yana da kudi ya shahara a cikin sa'aninsa masu irin aikinsa, amman babu dalili daya da kai ya saka ta so Kareem domin ba shi take so ba tun farko, aure da matar da ta rike ta a matsayin uwa ta hada, a lokacin da ba zata iya ce mata a a ba.
“Har zuwa yaushe zan yi ta zama a cikin wannan yanayin? Sai yaushe zaki tafi Momy? Mutuwarki kadai nake jira, ko kuma ta Kareem na yi takaba na wanke wannan bakincikin, bana fatan mutuwa da aurensa, saboda bana son na tashi tare da shi gobe alkiyama, wata kila dai ba zan iya cin wannan jarabawar ba, kiyayyar da kike ganin kamar zata iya zama soyayya ba zama ba Momy, ta ma kara rura wutar kiyayyar da zata iya hada kasashen dake cikin zuciyoyi yaki da ta yi”
Magana take da kanta zuciyarta na mata zafi, abu ne da ta riga ta sani har abada ba zata taba son Kareem ba, ba kuma dan be kai a so shi ba, ba dan yana mata wani abun ba, sai dan bata taba jin tana kaunarsa ba tun farko, shiyasa kullum take jin kamar a kurkuku take ba a gidan aure ba. A hankali ta kwanta gadon tana kallon gefen dakinta tana ta nazarin rayuwa.
NOOR POV.
A wahale na wuni a ranar, daga mama har Ya Nabil babu wadda ya sake bin ta kaina. Hana ce kawai ta taimaka min ta kwashe aman da na yi bayan ta dawo daga makaranta. Ina jin lokacin da Mama take mata fada wai ai da ta bari na kwashe taya zata kwashe min amai ai shagwaba ni da ake ne yasa nake son lalacewa. Wani abun da Mama bata saba min da shi ba shi ta yi min a yau, wato horo da yunwa ta hana ni abinci rana da hana ni na dare ko da wata safiyar ta waye jikina har rawa yake domin na saba ci ba kadan ba gashi kuma na wuni na kwana ban ci ba. Bayan Hana ta wuce makaranta na fito waje ina jin jikina kamar ba nawa ba, na nufi tukunyar dumame na bude na duba babu komai a ciki, sai na lashe tukunyar na dawo dakinmu na zauna ina jin rashin kyauta abun da na aikata tun farko...
Da sannu na sabarwa kaina da zaman daki bana sha'awar fita ko'ina tun a wacan ranar da Zafeer yayi min huduba. Kwana hudu na shafe ko kofar gidanmu ban leka ba, kullum kuma ina sauraren yaron da zai shigo yace Zafeer yana sallama da Noor amman shiru. A ranar da aka cika kwana biyar ne mutumen da yayi ma Baba alkawarin siye masa gida ya zo aka yi maganar gidan da wani abokin Baba amatsayin shi ne mai gidan aka yi ma gidan kudin miliyan uku da yan kai a take ya biya kudin, duk abun da suke ina jin domin ina cikin dakinmu kwance. Ban motsa ba har sai da abokin Baba ya fita tare da shaidun da suka yi shaidar gidan da aka siyarwa Baba. Kareem din da abokinsa suka bukaci ganina. Sannan na saka hijabina na fito daga dakin ban kalli kowa ba har na zauna na natsu sosai kamar ba ni ba, domin ni kaina na san na canja.
“Noor”
Kareem ya kira sunana sai na daga kai na kalleshi. Shi ma yayi rama kamar dai ni, Murmushi ya sakar min yana tambayar ya jikina, a madadin na mayar masa da murmushin sai hawaye suka cika ido na ba tare da dalili ba, na yi ta yunkuri kirkiro murmushin na kasa.
“Waya cire miki bandajen?”
“Ni na cire”
Na amsa ina maida kaina kasa.
“Kina shan maganinki dai ko?”
Na daga masa kai, domin bana son dogon zancen ni yanzu babu wadda nafi bukatar gani kamar Zafeer. Ban san me ya hana shi zuwa ba kusan sati daya yau, gashi Yaya Baya shiri da ni balle na ari wayarsa na kira shi na ji ko lafiya.
“Ko dai wani abu aka mata Baba? Na ga ta canja? Kamar ba ita ba kuma ta yi rama”
Baba ya juyo ya kalleni yayi dariya.
“Ba abun da aka yi mata, mu kan mu muna mamakin yadda ta zama haka”
Abokin Kareem din da ya siyawa Baba gida ya dube ni.
“Duk lokacin da na fada maka wani abu akan yarinyar nan baka yarda ai, she's very simple and easy going cikin kankanen lokaci zata iya canjawa daman”
Kareem din yayi kamar be ji shi ba, ya cigaba da magana da Baba ta zuba godiya kamin ya miko min wayarsa
“Duba ki gani irin wannan maganin ne da na rubuta miki kike sha?”
Na karbi wayar, a madadin hoton magani ko sunansa wani rubutun ne na gani zube a screen din wayar da Kareem ya miko min.
“Me ya faru Noor? Why the sad face? I Miss the old you, indai damuwarki akan Zafeer zamu taimaka masa, idan kuma akwai wata matsalar bayan ita rubuta min yanzu”
Na dago na dube shi sai na ga daga shi har abokinsa idonsa suna kaina, na girgiza masa kai.
“Ba shi ba ne”
“Amman dai babu wata matsala ko?”
Na daga mishi kai.
“Babu...”
Na yi murmushin domin furuncin na cewar zai taimakawa Zafeer ya faranta min rai siye da siyen gidan Baba da suka yi a bisa karya. Ya miko hannu ya karbi wayar ya saka aljihu ni kuma na juya na kalli Mama da ta fito tana musu godiyar siya mana gida da suka yi.
“Ba komai Mama ayi dai cigaba da hakuri da Noor da halinta, wata rana sai labari gashi dai yanzu ta janyo muku alheri”
Cewar Hafiz abokin Kareem, sai Baba ya fashe da kuka kamar gaske.
“Haka ne haka ne, Allah dai ya saka muku da alheri, ita kuma Allah ya kara mata hankali, ya kawo mata miji na gari...”
“Ameen”
Suka amsa ni da Kareem muna kallon juna kasa kasa kamar wadanda suka kula wani munafurci. Wata kila Baba ji yake kamar ba su fahimci zaren addu'ar ba, wata kila kuma sanadi ne da ni ma zan ji halin da ake ciki game da Zafeer domin tsinkayo Baba muka yi yana fadar abun da ban san an yi ba kuma wani be fada min halin da ake ciki ba.
“Shi wannan yace be shirya ba, wai ba shi da hali yanzu, ya turo yan'uwansa sun zo nan kwana uku da suka wuce da dare yana neman a daga har nan da shekara biyu ko daya da rabi, shi ma kuma ya zo da kansa amman ni na fada musu ba zan iya ba, domin so nake na aurar da Noor na huta, ba karatu take ba, kuma ba wani aiki take tare mana ba balle ace za a daga har lokacin Ƴa mace da ta tasa kyauta dakin miji, balle kuma irin Noor kara na aurar da ita tun ina da rai”
Na kalli Baba da sauri hawayen da ban san yaushe suka taru a ido ba suka zubo min. Sai dai wani kyauta da dadi sai na kasa cewa Uffan ba kamar da ba, wata kila da zan iya daka tsalle na rantsewa Baba na kunyata shi ko a gaban waye nace Zafeer nake so domin shi ne zabin raina... Amman a yau sai na kasa furta ko da kalma daya ne.
“Baba Noor tana son saurayin nan nata, kuma shi ma yana sonta, be kamata ka shiga tsakaninsu ba, da dai zaka duba ka ba su damar zai fi, inda aka fito be kai inda za'aje ba”
Kareem ya fada sai na juyo ina kallonsa da kamar damuwa a fuskarsa.
“Ba wai bana son ta aure shi ba ne, samarin ne na yanzu sai a hankali ni har na fi sha'awar Noor ta auri mai mata sun fi rikon aure, kuma ita Noor ai ba wani so ta sani ba, ita dai barta ga shirmenta mu lokacin da muna yara ai ba wani soyayya muka sani ba, sai dai kawai ace an maka mata kuma sai ku yi zaman aurenku lafiya lau, zamani ne ya lalace har aka san wani lobe lobe, kuma ita Noor ai kawai dai ayi sha'ani...”
Baba ne yake maganar ya karasa da dariya irin wadda ke nufin Noor bata san abun da take ba. Abokin Kareem ya ce.
“Gaskiya, kuma ance abun da Babba ya hango yaro ko hau tsauni ba zai hango shi ba, to Allah yasa hakan ne mafi alheri, kuma kana da gaskiya ba Baba idan yarinya bata karatu babu inda ya fi dacewa da ita irin gidan aure, ko da ma tana karatun balle kuma irin Noor cikin kankanen lokaci zata fara son wani ma”
Shi ma dai kallonsa na yi wata kila ya manta da ina zaune a gurin yake wannan zancen, kamar Kareem ya san abun da yake zuciyata sai ya dubi abokin nasa ya ce.
“Hafiz dan Allah karka zuga Baba ya aurawa Noor wadda a shi take so ba, baka san komai game da auren wadda baka so ko baya sonka ba, idan ba zaka lurar ba, to karka lalata”
Mama ta tashi ta shige dakinta, ni kuma na mike tsaye ina jin Baba na fadar.
“Ai gaskiya ya fada babu wata zuga, Noor ai tana da saukin kai sosai kowa ya same ta ya zamu mata ba dan tana ƴata ba, sai dai ace bata jin magana amman tana da saurin sabo sosai”
Daga haka ban sake juyo me suke tattaunawa ba, har suka ci suka shude suka fita ban san anyi ba, domin hankali ya karkarta a gurin Zafeer ina ta hararon dalilinsa na rashin zuwa, Allah kadai ya san me Baba yace masa ko yan'uwansa, amman me yasa Mama bata fada min hali da ake ciki ba? Shim ba ni da hakkin sani ne? Ko kuma ita ma din bata sani ba? Ko kuma saboda sun mayar da ni wawuya marar hankali da tunani ne? Tun da na yi alwala azahar ban sake fita ba dakin ba har aka yi Isha'i da ita na yi sallah, abinci ma da Mama ta kira tace na zo na dauka na dare sai na kasa fita na ji kamar bana bukatar abincin.
Misalin karfe tara da yan mintuna yaro yayi sallama ya ce Zafeer yana sallama da Noor, kamar ina jira ba tashi da sauri daman akwai hijab a jikina na fito waje na saka talkamina zan nufi kofar sai Baba dake kishingide yana sauraren redio ya ce.
“Ina zaki?”
Na yi shiru na rasa me zance, domin na san ya san dalilina na fita a yanzu.
“Na fa fada masa zan miki miji tun da shi be shirya ba, na san halin wasu yaran yan iskan unguwa sai su nemi lalata yarinya ma idan suka ga ba su samu damar aurenta ba, gashi ke ba wayo ba balle na ce”
Mama dake zaune gafensa ta ce.
“Haba Malam.. Ai ko da ka fada masa haka be kamata ka hana ta fita ba, baka san me ya zo da shi ba, kuma ba san abun da Allah zai yi a gaba ba, ko rabuwar za'ayi ai ta mutunci tafi, Wallahi Allah kadai yasan zagi da za'ayi maka a unguwar nan saboda kin dagawa yaron nan kafa da ka yi”
Baba ya juya ya kalleta a fusace.
“An dade ba a zage ni ba, a cikin masu zagin akwai mai wani mudu daya na shimkafa? Ko akwai mai ba ni dari biyar na kara na yi chefane? Ni fa ban hana shi aurenta ba, amman na fada masa muddi be shirya ba to kar ya batawa yarinya lokaci kuma ni na gaji da halayarta ina son na aurar da yata, ai Annabi S. A. W ma cewa yayi idan wadda kuka yarda da addininsa da mu'alamarsa ya zo son yarku to ku aura masa, addinin musulunci ya bawa iyaye damar zabar wa ƴaƴansu mazajen aure, daman can ni ban wani yarda da tarbiyar yaron nan ba, waya sani ma ko zuwa yayi ya hure mata kunne ta bishi su gudu?”
“Zafeer din Baba?”
Na furta da kaina kuka yana cin karfina. Sai ya zabura ya tashi zaune.
“Zafeer din fa, ko ubanki ne shi ko kanen uwarki ne? Dan'adam babu abun da ba zai iya aikatawa ba ai, ke kuma kwakwalwar kifi ce dake gaki sokuwa sai ya tsara miki ki yarda ki hau ki bi, to daga yau sai yau kar ya sake sallamawa ki fita, ke ban ma yafe miki ba ki kula shi ko a hanya, ban yafe miki ba wata magana ta sake shiga tsakaninki da shi”
Mama ta tashi tsaye dukan kirji.
“Malam kana lafiya kuwa? Wane irin abu ne wannan? Saboda wani ya bullo ya nuna yana son Noor cikin kankanen lokaci ya siye bakinka da zuciyarka da dukiyar da baka san hallaci ko haramcinta ba zaka yarda ka rusa soyayya da baiko shekara uku dake tsakanin yaran nan? Duk irin iya shegen da Noor take haka Zafeer ya ganta yace yana so sai kuma ka shiga tsakani yanzu da yake hararo gaba? Haba Malam kar ka yi abun kunya mana kar kasa hakki ya bibiyemu”
Baba ya mike tsaye ya dauke Mama da mari.
“Duk wata doka da zan saka a cikin gidana ke kike rusa ta kuma ke kike ba su damar rusawa, ko a addinance ba ni da laifi tun da shi yace be shirya aurenta ba a yanzu, kuma wannan yaro da kike zargi Allah ya isansa domin har yau be fito yace min yana son Noor ba, dan haka ya barki da Allah da zargin lalata alaka da kika masa, kuma bari ki ji na fada miki idan yaron nan ya sake yin sallama kika bar Noor ta fita abakin aurenki....! Wato yan unguwa su yi da ni, na shigo cikin gida ki dora min tukunyar masifa, to ba zai yiyu ba, daman can Allah yayi ba matarsa ba ce”
Ya saka talkaminsa ya dauki radio ya fice babu ko hula akansa. Mama ta dube ni ta kara min da wani bakincikin.
“Allah ya kara, duk abun da ya faru ke kika ja, shegen shishigin tsiya da iyayi da yawo da shashanci shi ya ja miki, kuma ni ba zan bari aurena ya mutu ba saboda ke, domin ba zan koma neman gurin zama ko rabawa ba kuma zan yarda rayuwar Hannatu da Nabil ta shiga wani hali ba saboda ke, kadan ma kika fara gani, hawayen da kika yi ta saka ni ina fada miki gaskiya kina bijirewa yau ga sakamakon kin fara gani, kuma wannan so min tabi ne baki san me zai biyo baya ba, sai ki zuba ruwa kasa ki sha...”
Tana maganar tana nuna ni ta muryarta nake karantar kukanta domin nawa hawayen sun hana ni ganin fuskarta. A kananen shekaruna na fara dandana zafi da bakincikin rabuwa, Baba ya sauya tunanina ya rusa burukana, ya wargaza shirina, ya saka ni a wani gidan kurkuru da ban isa na fitar da kaina ba, ban san ma ya kofar fitar take ba....