FATY~ISLAM

SHAFI NA HUƊU

by @ummishatu

***




©️2 WRITERS EMPIRE ✍🏻✍🏻




💜💜 *FATY ~ISLAM*💜💜




    *_NA_*


_*UMMI A'ISHA*_




*4*





***Zuciyar Khalifa cike da tsoro da tarin tambayoyi kala kala ya isa office din daddy, tambayar kansa yake ta faman yi tun bayan da salahu yace yaje mai girma MD yana son ganinsa,


"wai dama ya sanni ne? Ko dai wani laifin aka ce nayi ne? Me ya faru da yake nema na? Ya Allah dai yasa lafiya...." haka yake ta sakawa a ransa yana tsaye gaban office din yana jiran a caje shi kamar yadda securities din suka saba checking duk wani wanda zai shiga in and out,


Duk abinda ke faruwa yana faruwa ne akan idon daddy wanda ke zaune yana kallonsu ta na'urar cctv camera daga cikin office din sa, ganin yana kokarin shigowa ya sanya daddy din tashi ya mike tsaye daga kan kujerarsa dan tarar Khalifa din,


"Assalamu alaikum warahmatullah...." Khalifa ya fada bayan ya shigo cikin office din,


"Wa alaikumussalam warahmatullah wabrakatuhu...." daddy ya amsa tare ta zuwa ya dafa kafadarsa bayan ya dan rungumeshi kadan zuwa falonsa da yake ganawa da manyan bakinsa,


"Ina kwana....?" Khalifa yace dashi bayan ya tsugunna har kasa,


"Lafiya lau Khalifa.... Ya aiki?"


"Alhamdulillah...."


"tashi zauna, magana na ke son muyi shiyasa na kiraka...."


"A'a ranka ya dade nan din ma yayi" ya fada yana shafa keya dan duk sai yaji kunya ta lullubeshi kasancewar kananan kaya ne a jikin sa bakar t shirt mai gajeren hannu sai blue black din wando jeans, 


Duk yadda daddy ya so akan ya zauna kan kujera ƙi Khalifa yayi dan sai yake ganin kamar idan yayi haka to yayi rashin kunya, ya za a ce Alhaji yana kan kujera shima yana kai kuma a haife dai ya san zai haife shi sannan idan Abban su ne yake zaune akai ai ba zai je ya zauna ba dan haka sai yaƙi maimakon ma ya tashi sai kawai ya zame ya zauna nan kan carfet ya tankwashe kafafuwansa hakan ya sake bawa daddy tabbacin lallai hakika yayi zabi wanda ya dace, 


"Khalifa wata muhimmiyar magana ce tasa na kiraka ko in ce wata alfarma nake bukata daga gareka...." 


"Allah yasa zan iya ranka ya dade" 


"Ina da ƴa kwaya daya wadda duk duniya ita kadai na mallaka.... A halin yanzu bani da burin da ya wuce na inga tayi aure ta haihu sai dai amma har yanzu shuru bata samu mijin aure ba kuma shekarunta kullum kara yawa suke dan a yanzu zata kai shekara 30 a duniya, to bana son ta kai wani lokaci wanda haihuwa zata yi mata wahalar samu ko kuma ta kare rayuwar ta ahaka, shiyasa nake son ka aure ta idan har ka amince zan rinka biyanka kimanin naira miliyan ɗaya duk wata amma bisa wasu ka'idoji da sharruda"


Khalifa dake zaune jin maganar yayi kamar acikin mafarki, to wannan wanne irin aure ne zai yi tunda ance biyansa za a rinka yi? 


"Ranka ya dade wanne irin sharudda ne da ka'idoji?" 


"Ba zaka wulakanta min ƴa ba ko tozarci sannan ba zaka taba nesa da ita ba koda yaushe kana tare da ita ta yadda zata samu kulawa daga gareka, sannan so nake cikin ƙankanin lokaci kayi mata ciki ta haihu...." 


Ai Khalifa ji yayi kamar kasa ta bude ya nutse dan tsananin kunya, sunkuyar da kansa kasa yayi ya gagara dagowa dan wadannan kalamai sun yi masa mutukar nauyi, 


" Khalifa baka ce komai? "


" ranka ya dade zan iya samun lokaci inyi tunani da kuma shawara?" 


"sosai kuwa Khalifa, kaje kayi shawara kuma kayi tunani, duk abin da ka yanke to kofa a bude take, bari na baka card dina sai ka kirani" 


"to nagode madalla" 


Karbar card din yayi ya tashi ya fita aransa yana jaddada kokari irin na yan boko su basa kunyar fadar duk maganar da take ransu in banda haka ta yaya Alhaji Mu'azzam zai ce masa wai so yake yana auran yarsa yayi mata ciki ta haihu, wannan wacce irin magana ce? Tun daga nesa ya hango ashraf yana jiran sa dan sai kaiwa da kowawa yake alamun kosawa, 


"Ya aka yi ne?" ashraf ya tambaya cikin son jin karin bayani, 


"zo mu tafi zan fada maka, amma mu bar wurin nan" hannunsa ya ja har sai bayan da suka fita daga cikin kamfanin sannan ya fara korawa ashraf jawabi, 


"kirana yayi akan zai bani auren yarsa kum ka san wani abun mamaki? Wai biyana zai rinka yi every month" 


"a'a, ikon Allah a baka aure sannan kuma a rinka biyanka? To a wanne dalili?" 


"shine nima ban sani ba" 


"to ko dai yarinyar tana da wata matsala?" 


"babu wata matsala malam, kawai dai halayya ce irin ta masu kudi...." 


"to amma meyasa duk kamfanin sai kai kadai ya zaba?" 


"Allahu a'alamu" 


"kai yanzu me kace masa?" 


"nace a bani time zanyi shawara amma wacce shawara ma zanyi? Kawai zan je in fadawa umma na samu matar aure shikuma zan kirashi in ce masa na amince" 


"kabi komai dai a sannu, kafara ganin yarinyar tukunna first dan kar fa ayi cinikin biri a sama" 


"kai... Wallahi yadda talaucin nan yake dukana tako ina kawai karbar auren nan zanyi, ka san irin bakar wahalar da nake sha dama duk daren duniya? Da kyar fa nake bacci kawai shiru nake bana fada tunda na san fadar babu maganin abinda zata iya yimin, ba shiyasa Kaga na nace akan wannan yarinyar Asiya ba, da so nayi a dan lallaba kawai in aureta, yanda auren nan yayi tsada komai ya tashi yanzu gashi zan samu sauki ka zo kana wani ce min inbi komai a sannu? Wallahi babu abinda zan bi a sannu, yanzun nan zan je in fadawa umma.... "


Dariya ashraf yayi ya kai masa duka a kafada kafin yace" harijin banza" dariyar shima yayi amma bai ce komai ba. 


Lokacin da ya koma gida bai boyewa umma komai ba duk abinda ya faru ya kwashe ya fada mata yace menene shawararta? Nisawa ta danyi kafin ta dube shi tace, 


"Babu abinda zance Khalifa illah muyi addu'a sannan ka karbi wannan alkhairi da Allah ya kawo mana da hannu bibbiyu, tun da bamu san adadin mutanen da bawan Allahn nan ya tsallake yazo gareka ba yace kai ya zaba, to bai dace babban mutum kamar wannan wanda yafi mu daraja da mutunci da kima a idon mutane ya dauko ƴa sukutum ya baka amma ka ki karba ba, abinda nake so da kai shine ka hana idon ka bacci a daren yau kayi addu'a sosai ka nemi zabin Allah nima kuma zan taya ka ubangiji Allah yasa albarka a ciki sannan ya kauda duk wata fitina..... Kaga yarinyar? "


" a'a ban ganta ba umma, amma na san dai zan ganta "


" to shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi "


" amin umma"


Shawarar da umma ta bashi ya dauka ya bi gaba daya daren ya raya shi da sallolin nafila da karatun alqur'ani sai tarin addu'o'i kan Allah ya zaba masa abinda yafi alkhairi, sai bayan da yayi sallar asubah sannan ya kwanta bacci, 


Koda ya tashi ji yayi ya tashi da dokin matar da Alhaji Mu'azzam ya bashi shi ba wai kudin bane damuwarsa duk da suma din yana da bukatarsu kawai farin cikin da yake yi Allah ya musanya masa Asiya da wadda ta fita, da bashi da kudin aure sai Allah ya dubi zuciyar sa ya kawo masa sauki kuma yaji har cikin ransa ya aminta, 


Wanka yayi ya karya da dumame sai ruwan liptop sannan ya fita kasancewar yau babu aiki weekend ne, business center din su ya tafi can ya samu Ashraf wanda shi ya jima da fitowa kasancewar akwai wasu yara da yake bugawa project, 


"Barka da fitowa...." 


"yawwa barka dai, ya aikin" 


"Alhamdulillah, ya labari?" 


"yau zan sanarwa da Alhaji na karbi wannan auren ai..." 


Dakatawa da abinda ashraf yake yi yayi ya kalli Khalifa, 


"wai Kaga yarinyar ne? Idan kuma ba irin zabinka bace fa? Sufa yaran manyan nan ka san ba ayi musu kishiya, in dai suka baka auren yar su to haka zaka hakura ko bata satisfying dinka, kai kuma kaga sha'awarka tana da karfi, Allah ka fara ganin ta before kayi signing wannan contract din.... "


Dariya Khalifa yayi ya daki keyar Ashraf din, 


" malam ya kake ta fada min magana ne tun jiya, jiya ka kirani da hariji yau kuma ka zo kana wani ce min inada karfin sha'awa wai menene haka? "


" to ai nafi kowa sanin girman bukatar ka ne, dan ko umma da ta haifeka bata san abin da na sani ba game da kai tunda ita dai bata san wanne sahu kake ba acikin maza ni kuwa na sani, komai sanyin duniya a makaranta sai kayi wanka da asuba kafin kayi salla, sannan da zarar kaji kamshin turare sai abin ya motsa maka, Allah ka bincika kafin ka karbi auren nan dan kar kaje ka auri malalaciya a shimfida ka zo kana yimin complain ko kana cizon yatsa.... Na fada maka rich kids dinnan ba ayi musu kishiya "


" oh dan ka san sirri na shine zaka rinka tona min asiri ko? Nagode zan rama babu komai, ni dai koma yaya ne zanyi wannan auren dan haka na karba "


" amma fa mu dawo maganar serious anya yarinyar nan babu wata damuwa da babanta zai dauketa ya baka? "


" ban son wulakanci me kake nufi? Oh ni bani da darajar da za a bani auren ƴa sai nakasasshiya? "


" ba wai haka ba, naga mafi yawan masu kudi sai yayan masu kudi irin su suke bawa yaransu mu kuma su bar mu da irinmu shiyasa nake tunanin anya kuwa babu lauje cikin naɗi? "


" babu wani lauje, shi mahaifin ma ce min yayi wai so yake muna yin aure inyi mata ciki ta haihu kaji wata magana.... "


" bukatarsa kenan? May be ko bashi da wasu yaran ne kuma he's eager to see his grandchildren.... Allah sarki,ka zama mijin yar gata kawai "


" kaji dashi dai, albashin farko wannan shagon zan zo in gyara maka "


Dariya ashraf yayi yaci gaba da aikinsa nan suka cigaba da tattauna maganar a junansu. A daren ranar Khalifa ya kira Alhaji Mu'azzam dan sanar masa da cewa ya amshi tayin da yayi masa, lokacin daddy yana zaune falonsa na ƙasa shida mommy wadda saukowarsu kenan daga wurin Islam wadda taketa bore tun yamma tana watsi da kayan sawarta wai sun yi datti, da kyar daddyn ya lallaba ta taci abinci ta kwanta,


Ganin bakuwar no yasa daddy cikin tunani na dan lokaci kafin ya dauki wayar,


"Assalamu alaikum" Khalifa ya fada,


"waalaikumussalam warahmatullah"


"ahhh barka da yamma ranka ya dade, Khalifa ne"


"Khalifa ya gida, ya aka yi?" daddy ya bukata gabansa na faduwa dan bai san wacce irin amsa Khalifan ya kira ya fada masa ba,


"Alhaji dama na kira ne in sanar da kai cewa nayi shawara da mahaifiya ta kuma mun yanke shawarar zan karbi auren ƴarka....."


"Alhamdulillah..... Nagode Khalifa, gobe insha Allah ina son ganin ku kai da mahaifiyarka domin mu tattauna....."


Bai jira amsar Khalifa ba ya ajiye wayar ya tashi yayi doguwar sujjada dan mika godiyar sa ga ubangijin rahama zuciyarsa kunshe da farin ciki marar misaltuwa......✍🏻




Ku shigo cikin daular mu domin samun labaranmu guda biyu wadanda zasu nishadantar daku, 


MASARAUTA tare da alƙalamin FATYMA XARAH 


FATY ~ISLAM daga alƙalamin UMMI A'ISHA 



 Dukka wadannan Labaran guda biyu zaku samesu kan naira dubu ɗaya kacal, ga mai bukatar biya sai ya tura kudinsa ta 0774712835 Aisha Ibrahim Access Bank sai a tura evidence of payment ta wannan no *** ko kuma recharge card na mtn ta wannan no *** da shaidar biya.




*_Ummi Shatu_*👌🏻