PAGE 35
Washegari tun six thirty ta gama shirin school saboda gand'oki, a gaggauce ta sauko dining, a shirye ta same shi tsab! Kamar yadda ta tsammata, sai dai tea da cake kadai ta iya sha shima kad'an, sake kallon agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ta yi, ganin bakwai saura yasa ta naima waje a parlour ta zauna tana kallon cartoon a tv duk da kallon kawai take amma hankalinta baya gurin, karfe bakwai dai-dai ta nufi upstairs, direct d'akin Mom ta nufa, tura kofar ta yi ta shiga ba tare da knocking ko excuse ba. Mom bata falo dama bata yi zaton ganinta a nan ba, kai tsaye ta nufi bedroom, muryar Mom da ya daki dodo kunnenta ne, ya dakatar da ita daga karasawa cikin d'akin.
Cike da tabbatarwa ta ke cewa "Kar ki damu Esther bani da kowa a duniyar nan bayan ke, ke kad'ai ne iyayenmu suna haifemu tare mu biyu kuma a yanzu basa raye, ki sani ita d'in ba komai bace a gareni fa ce tsanin cikar burina, lokacin dana dibar mana na daf da k'aratowa, sai na tabbatar da ya mallaka mata komai nasa daidai da tsinke bai bari ba, zan kashe shi, sannan daga baya ita......" Sauran zancen ne ya mak'ale lokacin da idanunta suka sauka a kan Joy rik'e da k'ofa, da alamar ta ji me take cewa' Jikinta ne yaso daukar rawa, amma tuna wacece Joy yasa ta dake rainonta ce, ta fi kowa sanin halinta bata da shiga sabgar da bai shafeta ba. "Excuse me." Ta fad'a tare da sauke wayar daga kunnenta, sakar mata murmushi ta yi, cike da wayancewa ta ware mata hannayenta tare da cewa; "Come to me my dearest princess." Martanin murmushi ta mayar mata ta k'arasa ta fad'a jikinta suka jungume juna, "Morning my lovely Mom." Joy ta fad'a tana zare jikinta daga na Mom, rike hanayenta Mom ta yi ta na kallon ta cikin ido don son karantar yanayinta ta ce "Morning my Happiness, har kin shirya? "Yes Mom har ma na yi breakfast." "Auh! Shine babu jira ko gud." Dariya ta kyalkyale da shi, "I'm sorry Mom na tashi da yunwa ne." "Ok no prblm." Mikewa ta yi tana cewa; "Bye bye! Mom till I came back." "Ok princess nima yanzu zan shirya na tafi gidan antynki Esther, tana can tana rigima da Mr Moses wai sai ya sake ta, yanzu ma da ita nake waya kika shigo Esther bata jin magana lamarinta ya fara isa na." Ta karashe maganar tare da dafe kai cike da takaici, "Ki yi hakuri Mom ki ci gaba da abin da kike yi na alkhairi zaki samu lada." Tana gama fad'in haka ta fice, a parlour n k'asa ta dauk'i jakarta ta fito compound, already Peter na jiranta basu 6ata lokaci ba, ta shiga ya tukata zuwa school.
Da biyu Mom ta fad'i wannan magana, don ta kauda hankalin joy daga zargi ne, hakan kuwa ya yi tasiri, da farko kalmar kisan da ta ji a cikin maganganun Mom sun saka ta a shakku, sai dai jin zancen Esther yasa ta yi watsi da lamarin don bata kaunar abin da zai had,a ta da tilon kanwar uwartata, tun a bedroom d'in Mom ta watsar da batun, ko kafin su isa school ta shafe babin batun a ranta.
Shiganta aji da mintuna kad'an Fatima ta iso, kasancewar babu teacher a ajin yasa ta tashi da gudu ta tare ta suka rungume juna, dakyar suka saki juna suka k'arasa sit suka zauna, sauran student na masu dariya masu jin haushin kawancensu kuma na ta6e baki da zund'en su.
"Teetee tell me about him, ki gaya min mana sai ja min rai kike yi." Dariya Fatima ta saka ta ce "Sai during break." Fushi Joy ta yi ta juya mata baya, magana Fatima ta dinga mata amma ta share da gaske fushi ta yi sosai don harda guntun kwallah ta share ba tare da sanin Fatin ba.
Abin da ya ba Fatima mamaki da kuma dariya ana ringing bell, Joy ta kalleta tare da cewa; "Oya tell me." Dariya Fatima ke son yi, amma sanin halin Joy na saurin fushi yasa ta danne, ta yi abinta a ciki, narai-narai Fatima ta yi da ido ta koma kalar tausayi kafin ta ce "Zan gaya miki amma sai kin saki fuskarki, kinji my beautiful friend." Murmushi ta saki, Fatima na dariya ta ce "Ba irin wannan ba gaskiya, idan ba haka ba kuma bazan fad'a ba." Ga mamakinta sai ji ta yi Joy ta kyalkyale da dariya. Gimtse nata dariyar ta yi tana binta da kallon mamaki, gira Joy ta d'age ta ce "A kan Yaya Ameen komai zan iya yi domin nima a yanzu shine komai nawa." Rass gaban Fatima ya fad'i da sauri ta kauda tunanin da yazo mata zuciya, jin Joy din ta ci gaba da cewa; "Shine ya bani matsayin kanwa, ya zame mina Yaya dan uwa abin da na nake tsananin kewa shekara da shekaru, ina jinsa har cikin bangon zuciyata." Murmushi Fatima ta yi ta ce "Umm! Kaji masu yayyi muma Allah ya bamu." "Amin!" Joy ta amsa mata a gatsile. Fatima ta ce tana murmushi, "To albishirinki." "Goro fari kal!" Ta amsa mata, "kawo kunnenki kiji." Matso da kunnenta ta yi fuskarta a washe yau dai finally zata ji abin da Teetee ke ja mata rai a kai kwana da kwanaki, Fatima ta kama kunnen ta matsa da bakinta cikin rad'a ta ce "Yaya Ameen ya yi budurwa very soon zai yi Aure, zai auriAnty Amira....." 6at tattausar murmushin dake kwance a kan fuskarta ya ba ce within second, kamar saukar gudumar wuta haka kalaman Fatima suka daki zuciyarta take idanunta suka fara juyawa, wani irin dunkulallen abu ya tokare mata kirji, take numfashinta ya shiga sama da kasa kamar mai cutar Asthma.
Jin shiru yasa Fatima kallon ta, a tsorace ta zaro idanu tare da furta "Na shiga uku." A bayyane "Joyyy!"ta kira sunanta da karfi tana jijjigata, suuu! Ta ta tafi zata fad'i, da sauri Fatima ta rikota cikin tashin hankali take kiran sunanta da karfi tana jijjigata, lamarin daya jawo hankalin yan tsirarun student d'in dake ajin, da gudu wasu suka yo kansu suna tambayar menene, ya yin da wasu suka tafi kiran class teacher d'in su. Wata cikin yan ajin ne tayi dabarar fasa pure water mai sanyi da ke hannunta ta shiga antaya mata daga kai zuwa fuskarta, wani irin ajiyar zuciya mai karfi ta shiga saukewa tana kokawa da numfashinta tare da kokarin hadiye kululun daya tokare mata wuya amma ina! Abin ya ci tura. Tuni Fatima ta dad'e da fara kuka, hannayenta bisa kai, ta ke cewa; "Na shigo uku! Joy dan Allah kar ki mutu ki barni, wasa nake yi miki." Ana cikin haka class teacher ya shigo bayan shi nurs na school d'in ne cikin uniform d'in su, d'auke da first aid box.....
Kishin balbal๐ฑ
***********
A karo na babu adadi ya sake trying lambar, yana kallo har kiran ya katse kamar koda yaushe ba'a d'aga ba, text ya shiga rubuta ma shi na ban hakuri, tare da tabbatar mashi a kan lallai yana so su had'u a kwai story.
Ajiyar zuciya Aliyu ya sauke lokacin da ya gama duba sak'on, ya tabbatar ya zuwa yanzu abokin nasa ya yi laushi, zai jaraba sa'ar shi wata kila ya dace. Replay ya yi ma shi cewa; Zai shigo after magrib.
Karfe bakwai da yan mintuna a k'ofar gidansu Ameen ta yi Aliyu, zama ya yi a kan dakalin wajen ya zaro waya da niyyar kiran shi, sai ga shi, babu yabo babu fallasa Aliyu ya ba shi hannu suka yi musabaha, zama ya yi kusa da shi yana murmushi, ya dafa kafad'ar shi ya ce "Timekeeper nawa, har yanzu kana nan da dabi'arka ta r'iko ko?" Ba tare da ya kalleta shi ba ya amsa da "E kamar yadda kaima dabi'arka ta kafiya bata canza ba haka nima." Murmushi ya sake yi ya ce "Baka ce min ya jikina ba." Dage kafad'a Aliyu ya yi ya ce "Naga ai ba ka damu da lafiyar taka ba bare aje yi maka ya jiki." Dariya ya yi ya ce "To naji baka tambayeni ya jikin My Meerah ba." "Wacece haka?" Aliyu ya tambaya, amsa mashi ya yi da cewa; Masoyiyata mana Amira wacce kake fushi da ni saboda ita." Sai lokacin Aliyu ya d'ago ya kalle shi. Ajiyar zuciya Ameen ya sauke a nan ya kwashe duk abin da ya faru bayan wucewar shi ran nan har zuwa yanzu. Ya daura da "Aliyu ina matukar tausayinta, na amince zan zama maji6ancinta zan rayu da ita koda a zuciyata babu d'igon soyayyarta." "Bare ma baza a rasa ba." Aliyu ya fad'a yana hararanshi, murmushi kawai ya yi ba tare da ya tanka ba, sun dad'e suna hira, sosai Aliyu ya nuna mishi jin dadinsa game da amicewarsa da Amira ya k'ara da nusar da shi alfanun hakan ga shi karankanshi, sai dai koda wasa bai sako zancen Dr Abdul ba, don so yake ya bi komai daki-daki.
Tare suka yi isha'i bayan sun dawo daga masallaci ne, Aliyu ya shiga gida suka gaisa da Ummi, ya ce "Ummi ya mai jikin nan na kwanaki." Fara'ar fuskarta ce ta fadada ta ce "Hmmm! Aliyu mai jiki ta ji sauk'i sai hamdala, kar kaso ka ganta yanzu kamar ba ita ba." "Masha Allah, Ubangiji ya k'ara mata lafiya." "Amin Amin Aliyu nagode sosai." "To Ummi ni zan tafi a gayar da Fatima idan ta tashi." "To zata ji Aliyu a gaida mutan gida."
Tare suka fito da Al'ameen don yi masa rakiya, "Aboki ya kamata ka kira Amira mu gaisa, ka gabatar dani a matsayin babban aboki tun yanzu." Harara Ameen ya watsa masa, ya ce "Dalla Mallam muje na raka ka, matata mai tsada ce ba'a ganinta haka a arha." Rik'e ha6a Aliyu ya yi ya ce Ya ce "Da bamu san asalin balbela ba da sai tace mana daga saudiya take." Had'e rai Ameen ya yi ya ce "Me kake nufi."dariya Aliyu ya yi ya ce "Naga dai bada wani yare na yi magana ba ko?" "Kai dai ka sani ja'iri." Haka suka yi ta raha suna wasa da dariya har ya rako shi bakin Babar titi a nan suka yi sallama kamar kar su rabu.
Direct gidan su Amira Al'ameen ya nufa, ta sheka wanka da kwalliya tana jiran shi, jin sallamar shi yasa ka yin wuf ta mike, kallon da Mama ta watsa mata yasa ta yi saurin k'asa da kai, Aysha dake kallon abinda ke faruwa sai dariya take mata, hararar ta ta yi ta gefen ido tare da yin kwafa.
Shiga falon ya yi ya zauna bayan ya risina ya gaisar da Mama, Aysha da sauran kannenta suka gaishe shi, da gefen ido ya saki kallon side d'in da take, jin idanunta na yawa a kan shi, gaba d'aya ta shagala da kallon shi, Mama jin kowa ya gaishe shi banda ita yasa ta kallonta, ganin yadda ta shagala yasa ta cewa "Amira." Ina sam bata ji ba, don ta yi nisa Sam bata jin kira, ganin haka yasa Mama sake kiran sunanta a karo na biyu a tsawace "Amira!!!!" Firgigit ta yi ta kalli Mama, wani irin kunya ce ta lullu6eta sai kawai ta tashi da gudu ta bar falon, tafa hannaye Mama ta shiga yi tana sallallami.
Juyowa ta yi da zumar yiwa Al'ameen magana, sai dai wayam! babu shi babu mai kama da shi a falon sam babu wanda ya kula da sanda ya sudad'e ya fice, ai sai ta sake rafka salati tana rik'e haba take cewa; Aysha kin ga abin da na gani kuwa, dariya Aysha ta kyalkyale da shi, cike da nishad'i, "Ikon Allah, yaran zamani ka haifesu baka haifi halinsu ba ai kuwa banga ta zama ba ni hafsatu, wannan abin farin ciki har ina." ta fada tana mikewa tsaye............
Comment and share masoya
Oum Ummeetarh *** [12/29, 2:47 PM] AyshaNalado: ๐๐ *JOY* ๐๐
~FARHAT~