Introduction
بِسْمِ اللّٰهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيْمِ
GABATARWA
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Maɗaukakin Sarki, Mai rahama kuma Mai jin ƙai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (SAW), da iyalansa da sahabbansa baki ɗaya.
Waheeda labari ne mai cike da tausayi, soyayya da kuma tsantsar nadama. Labarin ya yi duba ne a kan rayuwar wata yarinya da ta taso cikin ƙunci da wahalhalun rayuwa. Rashin mahaifiyarta tun tana ƙarama ya jefa ta cikin yanayi mai sarkakiya, inda ta fuskanci ƙalubale iri-iri da suka kusan karya mata guiwa.
A tsawon rayuwarta, Waheeda ta dandana raɗaɗin talauci, da kuma rashin gata. Duk da haka, ta ci gaba da gwagwarmaya da rayuwa cikin haƙuri da juriya, tana fatan wata rana al'amuranta za su sauya zuwa alheri.
Wannan labari zai kai ku cikin duniyar tausayi da baƙin ciki, amma kuma zai nuna muku cewa bayan kowace wahala akwai sauƙi. Labari ne da zai sa ku dariya, kuka, da kuma tunani a kan darussan rayuwa masu muhimmanci.
Waheeda labari ne mai cike da tausayi, soyayya, da tsantsan nadama, wanda tabbas zai taɓa zukatan masu karatu.
Kudai ku biyo ni domin karanta littafin Waheedah
Deejarth Abdoul 🖊️