PAGE-18
________________________________________________________
*TO MASOYAN FARUQ ALLAH YA YI DAI ADDU"AR KU TA KARBU BA MU SAN KO NAN GABA BA...*
*Xayyeesherth Fans Grp ina nan a kan ba ka ta ko ku gyara ko in kulle grp din last warning ⚠ ⚠ ⚠*
Kafarasa sai Sakina juyo ta nufesa tare da fadin, "Laaa Honey na, na manta ba mu shigo tare da addu'ah ba."
Murmushi Faruq ya yi tare janyota shi kuma ya koma gefe.
Addu'ar shiga gida suke tare ya rikye ma ta hannu kan suka shiga da bismillan su.
Daga Safiya har Mama abin ya mutukar bata mu su rai domin kuwa Sakina ta bata ma su aiki.
Mama kawai jan yarta ta yi fuu su ka nufi daki.
Sakina ta ce, "Honeey ya na sun ta fi ko gesawa da Mama ba mu yi ba fa."
Faruq ya ce, "Ohoo ni ina nasani muje ciki ai ta na nan inkinyi wanka k'e je ku gesa."
Murmushi Sakina kawai ta yi domin ranta ya ba ta akwai wa ni abu.
Maryam ce ta taimaka ma ta tai wanka, ta sa kaya sannan ta yi sallah.
Ta na idarwa ta ce, "Maryam zo mu je mu gaida Mama."
Maryam ta taso suka nufi dakin Safiya.
Safiya na nan Mamanta na ma ta wa'azin agwagwa dan ba na ce na mutum ba tun da shedananci a ke koya ma ta.
Da Sallama Sakina da Maryam su ka shiga ai ko suna shigA MAMAN safiya ta ba ta rai, Sai Safiya ce ta fara yakyen dole ta amsa da hike makirace, *Ma ko yi ya fi mai koyarwa* Dan yanzu kam Safiya ta ninka Mamanta a makirci,kisisina tare da kissa.
Jikin Sakina ya yi sanyi kai a kasa take fadin, "Ina Hini Mama".
Mama tai kaman bazata amsa ba sai da Safiya ta dan tabata.
Jim sai ta ce, "Lafiya ya jikin na ki." magana ta ke kaman ta ga wani muchachcan bera na wari.
Sakina ta ce, "Da Sauki."
Safiya ta ce, "Ai jiki ma ya yi kyau sose ga shi har shek'i ki ke yar uwa."
Murmushi kawai sakina ta yi tare da ta shi suka fita ita da Maryam, domin ita maryam tafara gane take-taken su hakan yasa ta ko geshesu ma ba tai ba.
Su na fita Mama ta ce, "Ahir din ki Sakina kar in karaji kin kira wannan makiyiyar ta mu da Yar uwa, abin da har yanzu mun kasa kwasan rabon mu ta dalilinta kawai."
Safiya ta ce, "Comman Mama calm dwon please, ta ya za ta saki jiki da ni in ban na nuna ma ta soyayya ba, ke kinsan shi kan shi Faruq din zuwanta ne fa yafara kulani, SO dole ne in ma ta biyayya in nuna ma ta so, Mama ni da kika ganni fa nasan abin da na ke sarai ki barnj da su kawai zan na chusa ma ta bakin ciki ne batare da ta gane ni ce ba, ni dai yanzu damuwata Faruq ya ta ka wajen nan ko ya ya ne."
Mama ta ce, "Woo diyar kirki sai yanzu na fahimci cewa har kin kusa kereni, kar ki damu zai ta ka insha Allah."
***********
Sakina kuwa suna zuwa daki ta ce wa Maryam, "Meyasa ba ki geshe su ba? haba Maryam."
Maryam ta ce, "Anty Sakina kina ganin abin da su ke mana fa, ni wallahi da ni ce ke ma bazan shiga harkar ta ba dan makirace wallahi."
Sakina ta janyo kanwata kusa da ita tare da fadin, "Ke yarinyace Maryam ba zaki gane ba, ni daj Nasan da zuciya daya na ke zaune da ita in ma ta chutar da ni Tawa kan ta,ita da Allah."
Maryam za ta kara magana kennan Sakina dakatar da ita.
Karfe Biyar Faruq ya mai da Maryam gida ita kuwa Mama na nan har karfe takwas su na ta kintsa tsiya ita da yar ta, sai kusan tara ta bar gida.
Faruq har ya je ya ma Safiya sallama akan zai tafi dakin Sakina.
Ta fara marairaice ma sa da makircin ta shi ko ya nuna ko ajikinsa Ya yi fitowar sa.
Cije baki tai tare da binsa a baya har sun rufe kwofa ta buga ma su.
Faruq ya ki budewa Sakina ce ta tashita bude.
Tana budewa kuwa taga Safiya na kuka.
Tuni Sakina ta rikice tare da fadin, "Me ya Faru Safiya shigo ciki."
Shiga tai tana rikye cikin ta tare da fadin, "Cikina ke ciwo ku ma bazan iya barci ni daya ba, Faruq kar in matsa mu ku ko zaka kai ni gidan mu in kwana."
Sakina ta ce, "Aa ba ayi haka ba, Honeey ka je ku kwana kawai."
Faruq ya ce, "To ke zski iya kwana ke daya ne ko dai kawai duka mu kwana anan?"
Tuni Safiya ta ji ras kar fa Sakina ta aminci. Ta ce,"Aa nikam kawai a kai ni gida."
Sakina ta ce, "Bakomai fa ni naji sauki kuje kawai ba komai."
Faruq ya yi murmushi tare da damko kumatun Sakina ya ce , " Matar kirki nagode ki kulamin da kan ki kinji."
Safiya an sami abin so tuni ta damko Faruq irin a dole ita bazata iya tafiya ba sai an rikyeta.
Daukan ta kawai ya yi tare da fadin, "Ni karki wahalar da ni da Tafiya muje ki sha magani."
SAKINA ba ta san lokacin da hawaye Su ka fara zubo ma ta ba.
Urs Xayyeesherth [11/08 à 00:18] Shalelen Mamata🥳🥳: *AZZAWAJUL-MUKADDAR* *الزواج المقدر*
_(Auren kaddara)_
_A True Life Story_
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
______________________________________ _We Are Here To Educate,Motivate And Entertain Our Readers_ ______________________________________
_*LABARI/RUBUTAWA*_✍️ ⬇️ _*Aisha Mohammed Sani*_ _*(Xayyeesherth)*_
_Domin samun littafan mu a saukakye shiga shafukan mu kamar haka👇_
*Instagram page* _@zamani_writers_association_
*Youtube channel* _Zamani_writers_association_