PAGE 8
by @1239900
"Shin kina da saurayi? Ko nace kin taba yin saurayi?"
Wata iriyar faduwa gaban Jameelah yayi, amma sai ta maida hakan wani irin salo na yaran da ba su san komai ba ɗin nan.
"Yah Umar saurayi kuma? Ni Jameelah da yin saurayi a shekarun nan nawa? Tabdi jam, ai ni da ka ganni ban taɓa yin saurayi ba ban qi ba idan ka ce ki na da masu son ki? Sai in ce maka akwai masu so na da aure da yawa, amma ni ko zance ma ban taɓa fita ba dan kuwa ba a bari na a gida, yaran lungun mu na zuwa dai amma ni kam Baba baya bari ni kaina ma bana so balle nayi,"
Kamar ta ɗauki ruwa mai tsafta ta wanke masa zuciyar shi haka Umar ya ji, sai ya gyad'a kai kawai ba tare da yace mata komai ba, cikin matsuwar taji meye ra'yin shi akan ta har ya mata wannan tambaya ta kalle shi cikin wasa tace,
"Yah Umar kai fa? Ko mun kusa shan biki ne?"
Sosa kai yayi tare da yin murmushi sannan ya nuna ta da yatsa yana kad'awa ya ce,
"Jameelaah, Jameelaah, kin cika tambaya ba a wajen karatu ba, ba wajen surutu ba,"
Dariya tayi zuciyar ta na zillo dan kuwa ta gama gane menene a ran shi game da ita,gyarawa ya umarce ta da tayi dan su wuce ya ajiye ta a gida.
Ba haka ta so ba ta so ya bayyana mata matsayin da ya bata a zuciyar shi,ta na so ta ji ya furta mata kalma mai tsada wato kalmar so,dan kuwa ta san tabbas akwai wani abu a game da ita a ran shi.
Ramai na zaune tana kwashe tuwo a zauren girki,Baban su Jameelah kuma na d'aki yana shafa mai dan bai jima da ya fito daga wanka ba, Bukar kuwa na qofar gida yana ta uban musu da matasan gidan akan ball lokacin sallah ya qarato ko a jikin su, iyayen su na ta hada-hadar haɗa abincin dare, kowa dai yana ta harkokin gaban shi.
Jameelah ta shiga gidan ba sallama ta faɗa d'akin su a gaggauce ta gaida Baban su da ke shiryawa, nan da nan wasu a gidan suka hau gulmar ta, wasu kuwa suna taya iyayen ta murnar gyaruwar ta cikin ɗan qanqanin lokaci,kaya ta sauya dan ta riga tayi wanka a gidan su Umaimah sai ta fito tsakar gida suka hau hira da Ramai,anan ne Ramai ke tambayar ta a kwasa tuwo da ita,Jameelah sai ta yatsina fuska ta ce,
"Habaa Ramai ni nan da ki ka ganni a qoshe nake, haka kawai sai yanzu na wani ci tuwo da dare? Gaskiya ni Ramai bana son irin cimar da ake yi a gidannan, gaba ɗaya gidannan ma ya fita akai na, yanzu na dawo daga gida me rab'a AC iya AC alaji,kamata ya yi yanzu ace koda haya muke yi na samu na koma gidan mu mu kaɗai ba wai na dawo nan gidan ba kamar wata kasuwa,"
Baban ta dake d'aki yana saka riga ne ya saki baki dan jin kalaman ta a ran shi yake fad'in,
'Biri yayi kama da mutum, wato saboda tana zuwa gidan masu hali shine take raina gidan nan, lallai zan d'au mataki babba akan hakan, tinda take su basu taɓa zuwa ba gidan nan ba sai itace ke liqe da su, saboda ɗan banzan kwad'ayi' cikin ɓacin rai ya hau k'wala mata kira kuwa,
"Jameelah ! Jameelaah ! Zo nan,"
Miqewa ta yi tana wata iriyar tafiya ita a dole ranta b'ace yake ta isa wajen shi ta tsaya qiqam,cikin mamakin yarinyar ya ce mata,
"Me naji kina fada? Wato ke gaki kina da gida biyu maganin gobara ko? kije can ki wuni ki zo nan ki kwana sannan mu iyayen ki da muka haife ki ki zage mu, daɗin abun naga anan aka haife ki tin farkon auren mu nan na zauna, ko kina da inda yafi nan ne?"
"Bab...."
"Yi min shiru 'yar wofi kawai, to bari kiji wani albishir da zan yi maki yanzu, Jameela kar na sake ganin ki kin je masu gida in ba su zo nan ba ki tsahirta da zuwa gidan mutane ya isa haka, ke baki san meye kamun kai ba kina mace? Haba Jameelaah a zato na fa kin sauya halin ki ne tsakanin ki da Allah ashe abun ba haka bane,dan Allah ki dinga tsayawa a inda Allah ya aje ki,"
"Baba kana jin fa yanda yanzu na iya karatu sosai a wajen Umaimah nake koya, inna daina zuwa ya zanyi to?"
"In kika roqe ta ta dinga koya maki a makaranta zata dinga yi maki, ko ki roqi malaman ku su koyar da ke ba dole sai ita ba, ko ki jira na dawo saina dora maki,"
Dariya ta kwashe da shi ta na kallon shi a karkace wai shi zai koya mata karatu, da karatun makarantar allon zata yi karatun da zai birge Umar da iyalan shi?
"Habaa Baba, Allah ya kiyaye na zauna a koya min karatun zaure kaga ana ta kiran sallah bari na zuba maka ruwan alwala a tafi a sauke faralin sallah,"
Ficewa ta yi tana ta surutai akan ba zata daina zuwa gidan su Umaimah ba har sai ta samu nasarar samun Umar a hannun ta, sai da yayi alwala sannan ya tafi masjid take sanar da Ramai yanda suka yi, dariya sukai tayi suna gulmar shi.
Da dare ya yi Babawo ya aiko mata da gasasshiyar kaza da kuma Viju guda biyar sai dan lemo da ayaba, ya sha wanka da gayu yana jiran ta a waje, dan yayi tinanin wannan 'yar son abin duniyar da Babar ta in bai sake kuɗi ba ba zai dinga samun hutawa da ita ba.
Aiko ba laifi ranar Babawo ya samu abinda yake nema a wajen Jameelah a ranar,dan kuwa sai da ta ci kazar nan ta gyatse Ramai na ta zagin ta akan ta yi sauri taje kar ya gaji da jira,tana gamawa ta wanke baki da brush ta fesa turaruka sannan ta fice, zaune yake kan bencin su da suka saba zama.
Wani shan qamshi ta isa ta na yi tare da ɗauke kai, nan take tana zama Babawo ya zura hannayen shi bibbiyu a cikin rigar ta tare da sakin ajiyar zuciya mai qarfi sosai itan ma ajiyar zuciya ta sauke,Babawo ya yi kewar ta sosai haka zalika itama.
Sun dad'e suna abun su da suka saba yi idan sun haɗu, kafin daga qarshe su samu nutsuwar rabuwa da junan su, bayan ta sallami Babawo ta kama hanya za ta shiga gida a bakin qofa ta haɗu da Mamalo sanye da kaya masu nuna surar jikin ta, dariya ta fashe da ita dan kuwa Mamalo na nan kan bakar ta ta na so Sadeeq ya samu yana yi mata irin soyayyar zamanin nan, shi ko kan shi a qasa ya kasa kallon ta a haka yake bata labarin gari da abinda garin ke ciki, daga qarshe ya hau roqon ta dan ta sa baki iyayen ta su bashi izini ya turo maganar auren su.
Cike da tsokana Jameela tace,
"Washhhh Allah ! bawa ya ji daɗin shi bari ya je ya miqe ya yi bacci da saleb'a, Babawo ya hadu a rayuwa ...... Ahhh Mamalo kece a nan ?sannun ku ya na gan ku a tsaye haka, Ko ku naku salon a tsaye ne?"
Cike da takaici Mamalo ta buɗe baki zata fara zubawa Jameelah surutu sai Jameelah ta shige ciki tana ta dariya, ta na shiga ciki ta dawo baya ta tsaya tare da leqa kan ta waje,nan taga matan layin nasu na zuba soyayya yanda suka ga dama kowa da irin zaman da suke yi da masoyin ta, da kuma irin soyayyar da ake zubawa a wajen,murmushi ta yi ta ce,
" MAZAUNA GIDA kenan, na bariki na can ana buga harkar arziqi"
Dik wani iskanci da Jameela take aikatawa bata san tayi wankan tsarki ba,iyaka ta wanke gaban ta tayi zaman ta a haka, a cewar ta ba wanda ya taba saduwa da ita, dan haka ba wankan da ya kamata,koda kuwa ta fidda abinda ke wajabta wanka wato (maniyyi) kunji aikin jahilci, sannan ba zata je yin wanka ba a gane abinda ta aikata. Matasa masu soyayyar zamani in baku yin wankan tsarki kuna cikin azaba da gararin rayuwa, ga sabon Allah an aikata sannan ga zama babu tsarki, tayaya zaku yi ibada to ba tsarki?
*******************
"Mum tinda yau alkhamis ko zamu je gidan su Jameela? Bamu taba zuwa ba ina matuqar son naje,"
"kar ki damu zamu je ne kamar kin shiga zuciya ta, inshaa Allahu zamu je amma sai anjima in yayan ki ya dawo sai ya kaimu,"
"Ok Mum Allah ya kaimu,"
"Ameen"
"Mum me zamu kai masu?"
"D'aga ni to na je na ɗan dudduba me zan kai ma ita mahaifiyar ta ta,"
'Yan kayan sawa sabbi, guda biyu, da kayan ciye ciye da shaye shaye(bana maye ba😂) ta haɗa masu, sannan ta d'au turare wanda za ta ba wa mahaifin Jameelah guda biyu.
Da yamma liss Umar ya dawo daga makaranta bayan ya ci abinci ya yi wanka yana hutawa Umaimah ta shiga d'akin shi ta zauna a gefen shi ta ce,
"Yah na zo maka da saqo daga wajen Mum,sai dai naga kamar ka gaji bari na barka ka huta zuwa anjima sai na sanar da kai,dan na kula karatun ku na son hutu, in ka huta zan dawo na baka labari,"
"Ai kuwa dai na gaji kamar an min duka haka nake ji na, amma ina zaku da yamman nan haka na ga kun ci kwalliya?"
"Gidan su Jameela zam....."
Kan ta qarasa ya miqe zaune daga kwancen da yake ya ɗauki Key ɗin motar shi, da kallo Umaimah ta bishi ta na tuhimar sa da idanun ta shin ina gajiyar da ta gani a tattare da shi ɗazu? Lallai ma yayan nan, me yake nufi akan Jameelah ne?
"Muje," Umar yace ya na sosa kan shi da hannun sa na hagu ya na murmushi.
Bata yi masa maganar komai ba ta wuce d'akin ta bayan ta sanar da Mum Yah Umar ɗin zai kai su,hijab ɗin ta ta saka taje ta taya Mum d'iban kayan dake cikin ledar da zasu tafi da shi.
Sun isa layin nasu da yamma liss, 'yan mata an sha kwalliya an fara fitowa qofar gida, yau Jameela bata jin zuwa ko ina dan haka kwance take a d'akin su tana ta zabga tsaki lokaci zuwa lokaci, kyaun ta ace ita yar wani hamshaqin ce, yanda gari yayi kyau ɗin nan ta tafi shopping da Dad ɗin ta ko Mum ko kuma ita ɗaya a mota, amma dan rashin sa'a a rayuwar ta gata kwance gidan yawa ana ta hayaniya.
Juyi tayi tare da sakin sabon tsakin dayafi na da ,da sauri ta miqe zaune dan jin shigowar Ramai tare da ɗaukan mayafin ta da ke rataye a jikin qusar d'akin mayafin yayi maqal maqal da datti.
"Ke tashi ga wata hajiya nan da diyar ta sun zo ina kyautata zaton sune su Umaimah,"
Wata iriyar sufa tayi ta d'akko qur'anin ta ta buɗe ta ajiye a gaban ta ta na motsa baki, sannan ta yane kan ta da hijab kamar yanda ta saba idan ta na karatu a gidan su Umaimah.
Ramai ce tayi ma su Mum iso su kuwa suka shiga cikin d'akin da ke da duhu sai Mum ta yi amfani da wayar hannun ta ta kunna haske dan su dinga ganin ina suke jefa qafar su, ba laifi d'akin a share yake sosai, amma ba wani wajen zama sai ledar d'akin da ta ji jiki d'akin cike yake da tarkacen kayan su ko ta ina a qulle a zani.
Cike da jin kunya Jameelah ta tsaya kallon qur'anin tana murmushi alamar na gan ku amma sai na kai aya zan yi magana.
Shafa kan ta Mum tayi tare da sanya mata albarka, tana jin daɗin kamun kan Jameela, waje suka samu a gefen tabarmar da Jameelah ke shimfid'a ta kwata idan dare ya yi suka zauna, ta na gama muimui da bakin nata ta washe baki ta na fad'in,
"Mum sannun ku da zuwa, Umaimah shine baki faɗan zaku zo ba yau?"
"Ta ina zan sanar dake baki da waya, an baki kuma kin qi Karb'a, yanzu dai gamu mun yi maki zuwan bazata, na karya surutun ki na bana zuwa gidan ku gashi mun zo har da Mum da yah Umar ya na can waje duk na kawo maki su"
"Aka dai kawo ki, ka ji bakin ta a wajen"
Dariya suka yi baki ɗayan su Ramai ta kawo masu kunun aya da zobo, dibulan da kilishi, ashe dik dad'ewar da ta yi aikan data karkasa yara a sayo mata kenan, Mum taji daɗin karamcin Ramai kwarai ainun.
"Mama ! bari na kai wa Yah Umar shima tare suke yana waje,"
Ramai ke ta zazzare ido jin an kira ta da Mama, taji matuqar daɗi kuwa a ran ta.
Ɗaukan gora ɗaya na zob'o ɗaya na kunun aya tayi ta saka cup ta sa hijab ta tafi kai masa a waje.
Yana zaune cikin motar ya qurawa hanya ido yana jin kamar ya fada gidan ya gan ta ko zai samu sauqin abinda yake ji game da ita a qoqon zuciyar shi ta fito.........
*Wai ni Umarrrr what do u mean? Iyyee? Nace what is ur nufi ne akan Jameelaa?* [11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH