BOOK 1
🅿3️⃣2️⃣
*RAMLA*
Tun daga lokacin da ta ɗauki kuɗin nan ta bashi bai sake ma maganar kuɗin ba bare har ta saka ran zai biya ta bashin da ta bashi. Gashi ita kuma ta san wannan kuɗin su ne madafarta tun da duk sana,ar da take yi kuɗin ribar cikin gidansa yake tafiya. Ita dai bata san me ya yi da kuɗin ba abu ɗaya ta sani bayan ya karɓi kuɗin da kwana biyar ta ga ya canja sabuwar waya, abin ya bata mamaki tun da ta san ita dai ba kuɗi gare shi ba amma da ta tambaye shi ya ɓata rai bai bata fuska ba a taƙaice dai ya ce mata, bashi ya karɓa a wani shago ya ce idan ya samu aikin gwamnati zai biya, lamarin ya yi kama da rainin hankali tun da dai ta san babu wani mahluƙi da zai ɗauki waya ya bashi da sanin cewar sai ya samu aiki, aikin da babu tabbas a samun sa.
Bayan wani lokaci ta tuntuɓe shi da maganar kuɗinta don ta ga ba ma shi niyyar biyanta kuɗin, wato babu niyya ango ya kwana da wando. Kamar wanda ya watsa masa man fetur ta cinnawa ashana haka ya hayayyaƙo mata da bala,i yana faɗin
"Ramla a kan wasu kuɗaɗe da basu taka kara su akrya ba ne har kike sakoni a gaba da tambaya, da a ce ina da halin kuɗin nan da tuni na biya ki, sannan da na san har za ki iya buɗa baki ki tambayeni da wajen wasu bare na je na ranta wataƙila su za su yi mini lamuni har zuwa lokacin da zan samu"
Abin ya ƙona mata rai ita ma cikin ɓacin rai ta ce
"Da ka san da wurin wasun da za su maka lamuni ka zo wajena? Daga tambaya sai cibi ya zama ƙari, tun da na baka baka ƙara min maganar ba haka nima na zura maka ido, amma yau ɗaya da na tambaya shi ne maganata ta yi zafi" Daga wannan kamar wanda yake jira, ya ringa masifa aikuwa itama ta biya shi suka ringa faɗi in faɗa, har yana faɗin saboda kuɗi ne ta masa wulaƙanci, lamarin ya yi tsamarin da ta je gida ta faɗawa mahaifiyarta saboda irin maganganun da ya faɗa mata, duk da ta san mahaifiyarta ba cikakkiyar lafiya ne da ita ba. Haka mahaifiyarta ta shiga mata faɗa da kuma nasiha a lokaci guda, duk da ta san a lan gaskiyarta take amma dai ta tunatar da ita cewar kar ta yi wa mutum ba daidaj ba a kan kuɗi, tun da babu kuɗin abin da haƙuri bai bata ba rashin haƙuri ba zai bata shi ba!.
Haka ta haƙura ta ƙyale shi. Lokacin da Humaira ta cika shekara guda, a lokacin aka yi bikin su Amal bayan kammala karatunsu na sakandire. Tana matsayin babba amma sai gudunmuwa ta gagare ta, dakyar ta samu ta bada abin da bai kai ya kawo ba saboda bata da kuɗi, ɗan kuɗin hannunta bai taka kara ya karya ba, daga ta samu yake tafiya a cikin gidan, don Abdulsalam dai bata ga wata sana,a da za ta ɗaga ta ce yana yi ba.
Ko anko da ta masa magana kalma ɗaya ce ya bata amsa da ita wato ya ce
"Bani da halin yi" Haka ta ƙyale shi ta nema ta yi kala ɗaya, duk da sauran ma sun zama dole amma ya ta iya tun da faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi.
Haka aka yi bikin aka kai amarya, taimakonta ɗaya da Allah ya yi ɗan uwan mahaifinsu ya tsaye musu a kan komai na hidimar bikin, saboda shi mutum ne mai riƙe amana da kuma taimakon ƴaƴan ƴan uwansa. Bayan biki da sati shida, mahaifiyarta hawan jininta ya tashi, lamarin ya yi tsamari da munin da bata san waye a kanta ba, tsawon sati bakwai tana ta faman jinyar mahaifiyarta, don gidan ta koma saboda komai sai ta yi wa mahaifiyar tata, duk da kafin ta tafi sai da suka kai ruwa rana ita da shi, a kan cewar sai dai kullum take zuwa tana dawowa, wato take wuni, ita kuma ta kafe a kan cewar dole ne ta koma gidan ta kula da mahaifiyarta ba za ta iya barin mahaifiyarta a wani hali ba, dakyar ya bari don sai da ta faɗawa Zahraddin ya same shi ya masa magana!.
A wata ranar asabar da daddare, kamar wanda aka buɗewa mahaifiyarta baki ta yi magana bayan ta kusa sati biyu bata uhm bata uhm-uhm.
Cikin zafin ciwo ta shiga yi wa Ramla nasiha a kan zaman duniya, da kuma zamantakewar aure, babban abin da ta daɗe tana nannaga mata shi ne haƙuri, duk runtsi ta yi haƙuri a gidan mijinra ta rungumi ƴaƴanta, duk da mahaifiyarta ta sanar da ita kar ta yi haƙurin da za ta cuyar da kanta ko zuciyarta, amma dai ta mata nasiha mai ratsa jiki. Ashe lokaci ne ya yi, tana ji tana gani mahaifiyarta ta rasu kan mahaifiyar a kan cinyarta, sannan daga ita sai ita, don su Amal zuwa suke su wuni su koma gidajen mazajensu.
Ta yi kuka ta yi baƙinciki da rasa mafi soyuwa a zuciyarta da duniyarta wato mahaifiyarta. Sai da aka yi bakwai ta koma gidanta, a sannan ne mutuwar ta dawo mata sabuwa, komai take yi maganganun mahaifiyarta su yi ta mata yawo a kwanya.
Tun daga nan komai ya zama mai wahala a wajenta, da tana da inda ko zuwa ta yi za ta ji sauƙin damuwarta amma mutuwar mahaifiyarta ya sa sai dai ta zauna a ɗaki da yi kuka ta share, tun da tana ganin ƙanennta yara ne kuma su ma sun buƙatar ta tallafi nasu damuwar, don haka sai take ɓoye damuwarta. Ko lamarin karatun ta tana ji tana gani ta haƙura domin wanda zai tallafa mata ya gagara ya tallafa ɗin, bayan shi ne ummul aba,isin jinginar da karatun nata lokacin tana gidansu ya mata alkawarin zai tsaye mata amma gashi abu ya gagare shi, har ta kai ga nata ƙarfin ya ƙare, duk da Asma,u ta yi iya yinta wajen ganin ta tsaye mata ta ƙarasa amma hakan ya faskara a ƙarshe ta haƙura da karatun.
Lokacin da ta yaye Humaira, a lokacin ne wata ƙaddara marar musali ta kutso kai cikin rayuwarsu, wato jinyar da ta faɗawa Abdulsalam, wacce jarabawa ce ta ubangiji da ya kan jarabci bayinsa da jinya. Lamarin da ya saka Ramla da shi Abdulsalam ɗin cikin tashin hankali, har ma da Zahraddin!.
Tun da aka tabbatar da cewar Abdulsalam yana ɗauke da ciwon ƙoda, daga lokacin ne komai ya canja, ya dawo wani abin tausayi Ramla wani sabon so da tausayinsa ya mamaye mata zuciya, musamman da ya kasance sai ya yi ta kuka yana bata wasiyya a kan cewar ta kula da Humaira don ya san shi mutuwa zai yi!.
Ta mayar da kulawarta kansa, daga ita sai Zahraddin, sai kuma wanda suke zuwa duba shi. Duk ta ƙare ta rame kamar wacce take kwance a asibiti. Tun abin bai yi tsanani ba har ya fara tsananin ga rashin kuɗi gabaɗaya ta rasa ma inda za ta saka rayuwarta.
Daga ta zauna ta yi shiru maganar likitan take faɗo mata inda yake cewa
"Ciwon ƙoda yana faruwa ne lokacin da ƙoda ta daina aiki yadda ya kamata. Ita ƙoda aiki take yi na tsaftace jini, fitar da ruwa, da daidaita gishiri a jiki. Idan ƙoda ta yi rauni kaɗan, ana iya riƙe ta da magani, wato a ɗora me ciwon ƙodar a kan magani.
Idan kuma ta lalace sosai, ana shirin dialysisi ko dashen ƙoda.
Ana bada maganin hawan jini, sukari, kumburi, da ƙarancin jini. Ana daidaita abincin me ciwon ƙodar ta hanyar rage gishiri, rage furotin, da nama, rage ruwa, rabe ayaba da lemo. Ana yawan bincika fitsari da jini kowane wata."
Duk wannan bayanan da ya mata su ne abin da take tunawa a kowane lokaci, tun da gabaɗaya yanzu alamomi sun bayyana a jikinsa na alamar ciwon ya fara tsamari a jikinsa.
Zahraddin ya yi fafutuka ya samu kuɗin da aka samu aka masa wankin ƙoda, amma bayan wani lokaci sai ciwon ya kai matakin da dole sai an yi masa dashe, bayan kuɗin wankin ma da aka samu dakyar da nema taimako, wankin ma da wai sau ɗaya bane.
Tun da aka ce za a dasa masa wata, ya tabbatar da tana tsakanin rayuwa da mutuwa don ya san a duniya babu wanda zai ɗauki ƙofa sukutum ya bashi. Ko da an bashi ba ya jin yana da kuɗin da zai biya a masa aikin barw ma ya san ba zai samu ba, kawai ya saddaƙar mutuwa zai yi.
Zahraddin ya ce zai bashi tashi, aikuwa Hasiya ta tada hankalinta tana rantse-rantse a kan wallahi bata yarda ba, tun yana lallashinta har dai ya haƙura tare da mata alƙawarin ba zai bayar ba, duk da daman gasa masa aya take a hannu sai yadda ta ce gashi tana raina abin da yake mata duk da kasancewarsa jarumi ne mai ƙoƙarin ganin ya sauke haƙƙin iyali!.
Abdulsalam ya shiga tashin hankali, haka ma Ramla jin furucin Zaharaddin na cewa ya fasa bada ƙodar sai dai zai yi iya yinsa don ganin ya samo wanda zai bashi, irin masu zuwa asibiti su ce za su bayar sadaka domin ceton rayuka, sai dai kash ba a dace ba don ba a samu ba!.
Jinya ta ci ta cinye Abdulsalam, ganin hakan Ramla ta yi ta maza ta bugi ƙirji a kan tana son ta bashi ƙodarta. Ta ji tsoron faɗawa su Amal saboda kar su shiga damuwa domin ita kaɗai suke gani su ji daɗi!.
Zaune suke da Asma,u tana ta mata faɗan duk ta rame ta fita hayyacinta, murmushj kawai ta yi, ta ce
"Saboda jinyar Abban Humaira ne abin yake damuna ki ga yadda duk ya kumbura yanzu ƙodar jikinsa ta lalace dole ana buƙatar dasa masa wata!"
Asma,u ta ce
"To yanzu mene ne abin yi, kawai a taya shi da addu,a Allah bashi lpia Allah ya kawo wanda zai tallafe shi ya bashi ƙoda a dasa masa" Ta faɗa cikin halin ko in kula don ita mugun haushin Abdulsalam take ji musamman yadda ya mayar mata da ƙawa kamar almajira, gashi ta sanadinsa ta kasa ƙarasa karatun ta.
"Ramla ta ce
"Haba Asma,u ya kike wannan magana shi ma fa ɗoriya ce daga ubangiji, sannan an yi ta neman inda za a samu wanda zai bada ƙodar ba a samu ba, Abdulsalam ya ce zai bayar amma ya fasa" Asma,u ta ce
"To daman kin san ai sadaukarwa ce, ko da ɗanuwansa ne na jini bare kuma aboki"
Ramla ta tashi tsaye, ta fara takawa cikin sanyin jiki har sai da ta je jikin windon falonta ta tsaya tana kallon tsakar gidan ta windon kasancewar labulen a ɗage saboda zafi, a hakan ta ba Asma,u baya ta ce
"Asma,u Abdulsalam maraya ne bashi da uwa bashi da uba bai shi da kowa a takaice, yanzu ya saddaƙar cewar mutuwa zai yi"
Asma,u ta zubawa bayan Ramla ido tana son ta ji ƙarshen maganar.
Ramla ta cigaba da faɗin
"Na kira ki ne in shawarce ki cewar zan ba Abdulsalam ƙoda ta guda ɗaya"Gaban Asma,u ya buga da ƙarfi tsabar kiɗima sai gata a tsaye, tana cike da mamaki a furucinta ta ce
"Ramla ki bada ƙodarki? Kina cikin hayyacin ki kuwa"
Ramla wacce daman ta san kwanan zancen ta ce
"Haka kika ji na ce"
Cike da bala,i Asma,u ta ce
"Ramla da gaske za ki iya cire ƙodarki ki ba Abdulsalam? Namiji fa Ramla ke baki san wasu mazan basu da halacci ba, shi ne har za ki sadaukar da rayuwarki ga namiji, wace irin sadaukarwa ce baki masa ba a cikin gidan nan, ke tun da kika haɗu da shi kike masa sadaukarwa, kin sadaukar da burinki na gama karatu ki yi aure, kika aure shi ba tare da kin gama ba, yanzu karatun dole kika haƙura saboda yadda ba za ki iya ɗaukan ɗawainiyar kanki ba, da ma sauran abubuwan da baki ba zai furta ba duk da kina ɓoye wasu amma ido mudu ne, fahimta kuma fuska ce, ina ganin bai ɗauke ki a bakin komai ba Ramla, ai alamar ƙarfi tana ga mai ƙiba, juma,ar da za ta yi kyau tun daga laraba ake gane ta"
Har lokacin idanunta suna kwaranyar da hawaye masu zafi.
Asma,u ta ce
"Amma kina son ki ɗauki sassan jikin ki ki bashi, kar ki manta kina da ƴan uwa, kina da ƴa shin su basa buƙatarki da za ki sadaukar da rayuwarki ga wani?"
Ramla ta ce
"Na san suna buƙatata ta, sannan inaso ki sani bada ƙodar nan guda ɗaya ba zai hanani cigaba da rayuwa ba, zan rayu kamar kowa, sannan da kike batun sassan jiki sai ka ce wanda zan bashi ƙafa ko hannu"
Asma,u ta ce
"Ai ko hannub aka ce na san za ki bayar Ramla, ke ko da ƙafafu aka ce ki bashi na tabbatar a yadda kika mutu a kan son sa kina iya bashi ƙafafun ki rayu gurguwa" Duk da hawayen da suke zuba a fuskarta sai da Asma,u ta sa ta murmusa!.
Ta ce
"Zan yi domin Allah, ina fatan ya saka mina amizani, sannan bana so Humaira ta yi maraicin mahaifinta wato ta tashi babu mahaifi"
Asma,u ta ce
"Mutuwa ƙarar kwana ce idan Allah ya yi rubutacciyar ƙaddararta ta rayuwa marainiya ce ke baki isa ki goge alƙaluman ƙaddararta ba, amma kike duba waye Abdulsalam ba kowa bane sai mutum mai son kansa, ya fi son kansa fiye da ke, ya fi tausayin kansa fiye da ke"
Ramla ta ce
"Baki fahimce shi bane"
Asma,u ta yi ƙwafa, tana jin kamar ta kama kawar tata ta mata dukan kawo wuƙa!.
Asma,u ta ce
"Ramla ni dai shawarara kar ki bada ƙodar nan, ki barshi Allah ya zaɓa abin da ya fi alkairi, na tabbata da a ce ke ce kike jinyar nan kina buƙatar dashen ƙoda sai dai ki mutu don wallahi ba zai bada ƙodarsa a dasa miki ba, shin ke baki ganin abubuwa masu yawa da suke faruwa dangane da sadaukarwa da mata suke yi wa maza? Duk da wasu mazan ne ba a taru an zama ɗaya aba amma mafi yawa mace ta fi juriya a lan jinyar namiji, mace ta fi sadaukar da lafiya da dukiya da lokacinta don ta tallafi mijinta, ke da a ce namiji zai kamu da cutar shanyewar ɓarin jiki da mace ta zauna a gidansa ta dawwama tana bashi kulawa, ko da a ce komai sai ta masa idan na ce komai ina nufin, ko da sai ta masa wanka, sai ta kai shi ya yi kashi ta wanke, ke ko da a ce zai ke mata kashi a wando ,a ta dawwama tana wanke masa ta wanke kayan, ba za ta taɓa gajiyawa ba, ba za ta taɓa nuna masa yin hakan ya gundure ta ba, ba za ta taɓa tafiya ta bar shi ba, ko da a ce har mu,amalar auratayya ba zai sake iya yi ba, mace ta gwammace ta zauna a haka har lokacin da ta Allah xa ta kasance wato ko dai ya mutu ya barta ko ta mutu ta bar shi" Ta faɗi hakan tana yin taku ɗaya biyu sai dai bata ƙarasa zuwa wajen Ramla ba ta dakata ta ɗaga kai zuwa jikin silin ɗin falon ta ɗora da faɗin
"Amma maza fa? Wasu mazan basu jure jinyar mace ko da zazzaɓi nr take yi, sai namiji ya kasa jure ganinta a halin jinya kwana ɗaya biyu zai fara mita cewar ya gaji, saboda ɗan aike-aiken gidan bata iya yi sannan kuma wataƙila ma ba za ta iya biya masa bukatarsa ba!. Bare a ce ta yi doguwar jinyar da sai an kwantar an tayar, wani tun daga kuɗin magani yake nuna gajiyawarsa, wata macen daga jinyar ta fara ɗaukan kwanaki sai dai a kaita gidan iyayenta, ke idan ma wani ya ga abu ya ɗi ci ya ƙi cinyeea ƙiri-ƙiri zai ce aure zai ƙara, duk da wasu mazan suna tsayewa kuma suna tausayawa sannan basa gajiyawa"
Duk maganganun nan da Asma,u take Ramla tana ji, sai dai hakalinta ya ƙi kwanciya a kan ƙin taimakawa Abdulsalam, saboda tana son sa bata so ta rasa shi, gashi tana tausayinsa ta ce
"Asma,u wallahi hankalina ya ƙi kwanciya da lamarin nan, sai in ke ganin idan ina zaune zai ke ganin ina da abin tallafa masa amma na kasa matsayina na matarsa!"
,Asma,u ta ce
"Zaman da kike da shi ma ai sadaukarwa ce mai girma, ga wasu abubuwa da kike ɗauka a gidan na wanda ni har ga Allah idan nice ba zan ɗauka ba"
Sai lokacin Ramla ta juyo, ganin idanunta da lemar hawayen da gasu nan wanda suka zubo a kumatun ta, sai Asma,u ta ji wani irn tausayinta ya tsarga mata
Ramla ta ce
"Asma,u mai haƙuri mawadaci ne, watarana zai dafa dutse har ya sha romonsa"
Asma,u tana aika amta harara ta ce
"Wannan dai faɗar mutane ce, sannna al,adace ta bahaushe, ai wani haƙurin idan ya yi yawa cuta ne!"
Sun daɗe suna tattaunawa, amma Ramla dai bata wani ɗauki maganar Asma,u ba. Asma,un sai da Abdulsalam ɗin da Zahraddin suka dawo daga asibiti sannan ta tafi.
Bayan ta tafi Zahraddin ya ce
"Ramla gashi nan mun dawo daga asibitin likita ya ce Ƙodar ta mutu sosai tana stage 5 kidney failure. GFR tana ƙasa da 15%kawai, magani da abinci basu ƙara taimakawa.
Likita ya ce
"Ƙodar ta dajna aiki. Idan ba a yi dialysis (Aiki ne da inji ne da yake tsaftace jini a maimakon ƙoda, lokacin da kodar mutum ta daina aiki)ko dasa wata ba, rayuwata tana cikin hallari, amma mafi a,ala shi ne dashen zai fi saboda dialysis wasu suna yinsa shekara biyu zuwa uku" Zahraddin ya ƙarasa faɗa cikin sanyin murya idanunsa suna cikowa da ƙwalla, shi daman Abdulsalam shi ya sunkuyar da kai yana kuka marar sauti .
Ramla da ta rasa abin cewa ta fara kukan itama.Abdulsalam dai ya shiga basu baki a kan kar ma su wahalar fa kansu shi ya san ya gama rayuwarsa tub da ya kai wannan matakin.
A take Ramla ta ce
"Ni zan bada ƙoda ta a dasa maka!!!" Zahraddin tsabar mamaki baki ya saka yana kallonta don abin ya daure masa kai.
Abdulsalam kuwa ya rasa bakin magana saboda sai ya ga kamar a mafarki.
Tun da ya ji haks ya tafi ya rungume ta, sannan ya ƙara tabbatarwa Ramla masoyiya ce ta gaskiya!.
Zaharaddin ya jinjina mata, sannan da suka keɓe da Abdulsalam ɗin ya ƙara jaddada masa cewar ya riƙe Ramla amana domin a duniyar nan ba zai samu macen da za ta masa sadaukarwar nan ba, ko da za a samu ma to basu da yawa!.
Wani ɗan siyasa da yake gaba da gidan Zahraddin shi Zahraddin ya je ya same shi da buƙatar kuɗin da za a buƙata da kuma na magani, nan ya yi alƙawarin ɗaukan ɗawainiyar Ramlar da ta Abdulsalam, har kuɗin maganinsu.
Bayan Asma,u da har daina yi wa Ramla maganata yi, saboda talaicin za ta ba wanda bai san darajarta ba kyautar ƙoda!. Amma ita Ramla ko su Amal bata faɗawa ba don kar su shiga tashin hankali.
An yi aiki cikin nasara, har sai da suka gama karɓar magani suka ɗan warware kafin aka samu aka sallame su.
*HAJIYA NAJA,ATU*
Tana nan zaune tana jiran kiran Mom don ita ranta ma ɓaci zai yi idan ta je gidan ta tarar da Mom bata gama kintsawa ba.
Jim kaɗan ta gaji da luguden baƙincikin da zuciyarta take azalzalarta da shi, da sauri ta tashi ta ɗakko kuɗi ta saka a jaka, ta saka wayarta ta fito daga part ɗinta lokacin ƙarfe takwas saura, tana fitowa ta nufi harabar gidan, lokacin ta tuna ma ashe bata sanar da direban ba, tana zuwa ta masa izinin ta ɗakko mota zai kaita unguwa, cike da bin umarninta bayan ya gaishe da ita ya ɗakko motar ya buɗe mata ta shiga ya rufe, Alhaji da yake sama ya ji ƙaran rufe ƙofar mota da mamaki ta ɗaga labule ya leƙa harabar gidan, don ganin wanda zai fita da safen nan.
Yana leƙawa a daidai lokacin direban yana shirin shiga, har ya shige ya banke tashi motar ya ja, tare da yin horn mai gadi ya buɗe musu suka fita. Alhaji ya saki labule ya je ya ɗauki wayarsa ya shiga kiran direban da ta fita da mota, kira ɗaya biyu ya ɗaga wayar yana rike sitiyarin da hannu ɗaya, ya kara a kunne yana faɗin
"Assalamu alaikum barka da safiya Alhaji" Hajiya jin ya ambaci sunan Alhaji ta san da walakin goro a miya, kuma sumin hauka zubar da yawu.
Alhaji ya ce
"Waye ya aike ka da safen nan?"
Direba ya ce
"Ba aikena aka yi ba, ni da Hajiya muka fita" Ya ɗan yi shiru yana nazarin inda za ta je da safen, kafin Alhaji ya ce wani abu Hajiya da take jin kamar ta warto shi daga wayar ta shiga bugunsa har sai ya suma ko ya daina numfashi ta daure ta ce
"Asibiti zan je kaina ke ciwo"
Direban jin furucinta da sauri ya ce
"Alhaji za munje asibiti ne Hajiya ce kanta yake ciwo" Ya ɗan yi shiru yana nazarin maganar amma don kar ya yi wani tunanin daban ya ce
"Tohm sai kun dawo" Kafin direban ma ya amsa Alhaji ya kashe wayar. Fuska ta yatsina ta tare da taɓe baki ta ja ƙaramin tsaki irin na kanka ake ji.
Yana ajiye wayar ta ce
"Gidanmu za ka kaini" Ya amsa cikin girmamawa.
Tun a hanya ta kira Mom, da Mom ta dauka ta ce
"Allah sarki Naja,atu yanxu nake shirin kiranki in ce ki taho, sai ga kiranki ya shigo"
Hajiya ta ce
"Ai gani nan na kusa zuwa ma, kin san ba zan iya jurewa ba"
Mom ta ce
"Gwara da kika taho, bari na fito mu wuce"
Tana faɗar hakan ta yanke kiran ta tashi ta ɗauke kofin shayin da ta sha ta kai kicin ta ajiye ta dawo ta ɗaure sauran ledar biredin ta ajiye ta zato hijabj ta fito.
Tana zuwa sun ƙaraso ta buɗe motar ta fita suka ja gefe da Mom ta ce
, "Mom ya za a yj da direban na kar fa ya ga inda za mu je ya tona mana asiri" Mom ta shiga ciccira ido sannan ta ce
, ",Da wannan dan wannan to idan bai kaimu ba waye zai kaimu ko dai mu hau napep?"
Hajiya ta ce
",Ko dai na gargaɗe shi a kan kar in ji kar in gani"
Mom ta ce
"Hakan ma za a yi ai idan kin gargaɗe shi, ƙaryarsa ta sha ƙarya ya faɗi abin da idanunsa suka gani" Da wannan maganar ta rufe gidan suka je suka shiga motar ya ja suka tafi.
Bayan ta masa gargaɗi mai lasisi, ta kwatanta masa hanyar da za su bi, Mom tana ƙara masa kwatance yana bi har suka je siririyar hanyar da ta kai su ga gidan bokan da suka yi wa tsinke!.
Direba yana ta bin bayansu da kallo lokaci da suka kama hanya domin zuwa ɗan ɗakin da bokan yake.
Sai jaddada lamarin yake don ko makaho ya laluma ya san me ya kawo su wajen, bayan kuma ya san ga inda ta sanar cewa asibiti za su je.
Suna shiga suka samu wuri suka zauna, boka yana wani zare ido kamar wanda ya haɗiyi barkono. Mom ta ce
"Boka daman muna tafe... Da sauri ya ɗaga mata hannu yana faɗin
"Tun kafin ku zo nan shekara ɗaya baya mun samu labarin zuwanku" Daga Hajiya har Mom juna suka kalla Mom ta ce
"Ka ji aikin hankali tun shekara ɗaya ma aka sanar da zuwanmu, mu har muka zo za mu ɓatawa kanmu lokaci wajen bayani"
Hajiya kai kawai ta gyaɗa.
Boka ya ce
"Maganar auren da mijinki ne zai ƙara, kike so a dakatar da wannan lamari, sai dai ina baƙjnciki da alhinin faɗa miki cewar wannan aure sai an yi, ba zai yiwu a dakatar da shi ba" Mom ta zaro ido yayin da Hajiya ta dafe ƙirji cike da tsananin tashin hankali, har suna hala baki wajen faɗin
"Mai ka ce boka?!"
Boka ya gyara zama yana janyo ƙwaya da wahi faranti gabansa ya shiga zana hoton wani abu kamar aljani, ba tare da ya basu amsar tambayar ba.
Suna cike da wannan fargabar musamman Hajiya da take jin tamkar zuciyarta za ta fasa ƙirjinta ta fito.
Sai da ya gama a tsanake ya ɗago yana kallonsu fuska babu walwala ya ce
"Duk wani aiki da za a yi sai dai a yi bayan auren amma dai aure ba zai hanu ba a binciken da na yi, domin auren yana cikin rubutacciyar ƙaddararsa ba zan iya aikin da zai dakatar da hakan ba!"
Mom fuska ba walwala ta.ce
"Amma ka san ba kowane aiki kake yi ba shi ne ake maka laƙabi da ƙare kukan ka"
Boka ya ce
"Ina yin kowane aiki amma dai ni iya abin da zan ce muku shi ne ba zan muku ƙarya ba tabbas aure sai an ɗaura" Tsaye Hajiya ta tashi tana wani huci kamar wacce ta yi tseren gudu a faɗace ta ce
"Ƙarya kake boka! Na fi ƙarfin a min kishiya, kuma ko zan yi yawo tsirara wajen ƙarar da duk wani abu da na mallaka to sai na ƙarar don daƙile wannan auren!"
Boka ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya wacce ta yj amsa kuwwa wa wajen ya jima yana ɓaɓɓaka dariyar wanda daga bisani ya ɓata rai kamar bai taɓa sanin wani abu dariya ba ya ce
"Ki je duk inda za ki je a faɗin duniya za ki ce na faɗa miki amma sai dai a miki wani aikin ba dai na hana aure ba"
Mom ta tashi tana gyara ɗaurin zaninta sa yake neman sincewa ta ce
",Duniya da faɗi ai maye ba zaj ci kansa ba, aikin banza da wofi "
Hajiya ta ce
"Banda wari ma babu abin da ɗakin yake"
Boka ya ce
"Ku ne dai kuke warin, tun da kuka zo wajen nan kamar an ajiye mushe,"
Mom ta ce
"Aikin banza babu abin da ka iya daman, a haka aka zo a haka za a koma ana zaune a dokar daji"
Boka da kakkausar murya ya ce
"Na baku minti ɗaya ku bar wajan nan idan ba haka ba sai na ɓatar da mashayar ɗan da take jikin ƙirjin kowacce daga cikin ku" Har neman yin gware suke yi wajen fita, kasancewar ƙofar ba wani girma ne da ita ba.
Gudu-gudu sauri-sauri suka ƙaraso wajen mota, direba ya da ya hango su kamar an koro su daman yana tsaye ya jingina da jikin motar, a sukwane ya buɗe motar ya zauna babu wacce ma ta jira aka buɗe mata. Suna shiga ya ja suka bar wajen da gudu don shi ya yi zaton wani mugun abu ne duba da yadda wajen yake dokar daji.
Ana tafiya Mom ta ce
"Ka ji ɗan jafa,i ya ɓatar mana da mashayr ɗa ina muka kama muka riƙe"
Hajiya ta ce
"Mom har gwara ma ke kin sha miya, ni da nake a tsaka mai wuya, miji kana da mashayar ɗa ma yana neman aure bare kuma aka ce na dawo ƙirji babu bambanci da nashi" Direba da yakr sauraronsu dakyar ya ci nasarar danne dariyarsa, sai da ya yj da gaske, da ya ji dariyar ma tana neman ƙwace masa sai ya tsiri yi tarin ƙarya.
Hajiya ta ce
"Mom ya za mu yi yanzu?"
Mom ta ce
"Haba Naja,atu ni kuwa lungi da saƙo, kusufa-kusufa na san wajen bokaye da malami don haka daga nan wani wajen za mu nufa!.
*FALMI*
Cike da rashin jin daɗin furucin ƴar uwar tata ta ce
"Amma Aunty ai kya ji daga bakina kafin ki yi saurin yanke hukunci"
Auntyn ta ce
"Falmi kenan! Ai duk namiji, namiji ne, in dai yana amsa sunan namiji to halinsa na zanen dutse yana rataye a wuyansa ki faɗawa kowa wannan, duk maza halinsu ɗaya"
Falmi ta tsurawa Auntyn ta idanu ta ce
"Aunty kina nufin har Yaya?" Ta tambaye ta, mijin Aunty take kira da Yaya, kuma ta san shi tsayayyan namiji ne a kan iyalinsa, sannan bai yarda wani ya wulakanta masa iyali ba bare har shi ya wulakanta, yana tattalin iyalinsa tare da faranta musu, matarsa ya mayar abokiya kuma aminiya.
Aunty ta ɗan ji kunya da furucin Falmi hakan ya sa ta ce
"A,a Falmi, ban da shi, ai kin san shi ya yi min halacci, irin halaccin da nake son kowane namiji ya yi wa matarsa, duk da cewa su ma wasu matan suna da laifi"
Falmi ta ce
"Aunty kamar yadda Yaya ya zama na daban inaso ki saka a ranki ba shi kaɗai me na daban ba, za a iya samun dubban maza irinsa, sannan tsohon mijina Aunty don ya kasance azzalumi ba yana nufin kowa haka yake ba, Yaya kaɗai ya isa ya zame miki abin buga misali!".
Aunty bata ma san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba. Falmi ganin ta saki fuska ta ce
"Aunty inaso mu yi magana ta fahimta, ke ce abokiyar shawarata, duk abin da kika yanke zan yarda da shi ko da zuciyata bata so.
Aunty ta ji tausayin ƙanwar tata ya kama ta, ta dafa kafaɗarta ta ce
"Ina sonki Falmi, gudun ki cutu ne ya sa nake faɗar komai, sai dai na san addu,ar da muka yi wataƙila Allah ne ya amsa tun da maza da dama sun nemi soyayyarki amma kika ƙi amincewa"
Falmi ta saka idanunta cikin na Aunty ta ce
"Aunty ina wannan wanda direbansa ya kaɗe ni, to shi ne ya ce tana sona" Ƙuri Aunty ta mata da idanu ta rasa bakin magana ta ɗora da faɗin
"Aunty ba zan ɓoye muki ba don ina da kyakkawar fahimta tsakanina da ke, don haka nima ina son shi, kuma da aure, sai dai abin da nake so in shawarce ki shi ne, shin kin yarda na amince masa? Kin ji ya kwanta miki a rai? Sannan abu na gaba shi auren nashi a hanzarce ya zo da shi, a cewarsa nan da kwana uku" Aunty kawai baki ta saki tana kallon ta. Sai da Falmi ta saka hannu ta ɗago mata leɓan ƙasan ta haɗe mata da na ƙasan tana dariya.
Falmi ganin Aunty bata ce komai ba ta kwashe komai da komai yadda suka yi da Alhaji Muhammad ta faɗa mata. Aunty ta yi shiru tana nazartar kalaman Falmi.
Sai da ta gama gano cewar Falmi ta kamu da son shi, sannan ta ce
"Falmi muna son ki, muna son abin da kike ao muddin ba za ki cutu da abin ba, sannan ni dai ta ɓangarena na miki sha,awar aurensa in har kina son shi, yadda kike faɗar kirki da karamcinsa, sai dai hanzari ba gudu ba ni ba zan yanke hukunci ba zan kira gida mu yi magana da su Baba, sai dai ko a mafarki bana jin auren zai yiwu a kwana uku duk da bamu san yadda ubangiji ya tsara ba, amma kin san halin Baba sai ya yi bincike da kyau, yadda muka yi zan faɗa miki"
Falmi da sauri ta rungume Aunty ta tana faɗin
"Sai da ke Yayata ta kaina, ai na san idan dai har kika faɗawa su Baba magana za su yarda musamman in kika ce musu mub jima da haɗuwa da shi" Ta mata hararar wasa tana faɗin
"Ba a ƙarya da ni"
Falmu ta ce
"Nima ban ce ƙarya ba, kawai dai kwaskwarima za ki ɗan yj" Suka washe da dariya su duka. Sosai ran Falmi ya yi fari tas bata tama zaton avin zai zo da sauƙi haka ba.
*A page 35 zan gama book 1 mai buƙatar cigaban labarin har ƙarshe zai biya 1k ta asusun faiza abubakar 9030283375 opay shaidar biya ta ***, karku yarda a yi wannan tafiyar babu ku akwai cakwakiya abin sai wanda ya bi labarin har ƙarshe ne zai gane*
MAMAN AFRAH *** [9/7, 7:28 PM] null: *KIBIYA A IDO* NA
MAMAN AFRAH