NAMIJIN GASKE book 1 to 3 complet

Littafi na daya 1 Part C

by @shuraih99

NAMIJIN GASKE


Littafina daya 1


Marubuci:- Shuraih Usman


Typing:- Shuraih Usman


Tel. ***


Part C


.


A cikin farfajiyar gidan sarki hinzur dakaru sai kai kawo suke


duk da yake cikin darene amma farfajiyar gidan a haskake take


yadda ko Allurace ta fadi sai anganta,


.


Ba zato ba tsammani sai gani akayi wata iriyar guguwa ta


bayyana


Gaba daya dakarun gidan suka mai da hankalinsu ga wannan


guguwa, cikin kankanin lokaci guguwan ya lafa , koda bacewan


guguwan sai su kallabu suka bayyana suna masu rike hannuwan


junansu.


Dakarun sarki hinzur na ganin bayyanarsu sannan sukaga


dukkansu suna dauke da muggan makamai,


Take sukayi kukan kura sannan suka zare makamansu daga


cikin kufe,


Sannan suka afka ma su kallabu,


Su kuwa su kallabu koda ganin haka sai suma sukai kukan kura


sannan suka falfala da gudu don su tarbi dakarun sarki hinzur,


Nan aka rincabe da azababben yaki


Farfajiyar gidan bakajin komai sai karafkiyar takubba da


karajin Dakaru, jini sai malala yake tamkar an yanka wani


babban dabba,


Aikoda aka fara wannan yaki sai dakarun sarki hinzur suka


raina kansu , domin yan fashin wani irin salon yaki suke ,sannan


gasu da juriya dacin rai da naci, don sai kaga badakare ya zabga


masu sara a jikinsu jini yayi fallatsi, amma sabida tsabar naci


haka zasu cigaba da yakin


.


A yayin da dakarun sarki suka fahimci muddin akaci gaba da


wannan gumurzu toh yan fashin na iya karar da su gaba daya,


hakan tasa wani badakare mai matukar girman jiki ya falfala da


gudu izuwa wani bangare na gidan,


Koda ya je wajenda yake son zuwa . Wata irin dogon ginice mai


tsayi wacce a samarta akayi mata rumfa,


Irin wannan ginin ana amfani da sune ta hanyar ganin wanda


yake wajen gidan sarki ko ta hanyar sada wani sako, ajikin


ginin da kwaita iriyar matattakala ta katako, da isan wannan


badakare sai ya kama wannan matattakala ta katako, ya fara


hayewa izuwa saman birnin ko da yakai ga karshen ginin sai, ya


dauki wata makekiyar mabushi, yana dauka ya kafata abakinsa


sannan ya ringa busawa har tsawon wasu dakiku sannan ya


saurara.


.


A yayin da ake tsaka da gumurzu lokacinda su kallabu suka fara


cin karfin dakarun sarki hinzur


Suna kara kusantar asalin babban kofan da zata sada mutum


izuwa cikin falon gidan sarautar,


,


Alokacinne suka ji wata irin busa na tashi,koda kallabu ya


saurari wannan busa sai zuciyarsa ta bashi lallai ba lafiya ba,


hakan tasa ya ayyana aransa ya kamata suyi sauri su aikata


abinda zasu aikata su wuce abinsu,


Rashin sani tafi dare duhu, lallai da yanfashinnan sun san abin


da zai biyo baya toh da sun gaggauta barin wannan gidan


sarautar don ceton rayukansu,


.


Wannan busar bana komai bani illa busan Yaki, kuma sanar da


mutane cewa gari babu lafiya.


.


Kwance yake bisa shimfidarsa daga shi sai gajeran wando, duba


daya zakai mai kagane cewa yana jin dadin wannan baccin da


yake


Gabjejen katone baki amma bakinsa bawai irin baki kirin nan


bane,


,


Ba kyakkyawa bane amma kuma ba a kirashi da mummuna ba,


Yana da tarin damatsa, jikinsa a cure take a waje daya ,


Kamar acikin mafarki sai yaji wannan busa , zumbur ya mike


sannan ya natsu don kara sauraron busar tabbas wannan busace


dake tabbatarda cewa birnin nan na cikin tashin hankali, nan da


nan ya sanya kaya ajinkinsa, sannan ya sanya sulken yakinsa,


Ya daoki takobin sa ya rataya , sannan ya fito farfajiyar gidan


Nan da nan ya nufi turkin dawakansa da zuwa ya haye kan wata


bakar doki


Take dokin tai rimi sannan ta fice daga cikin gidan.


Wannan gabjejen mayaki ba kowa bane face sarkin yakin


birnin Tehran mai suna ZABBAGI bin SHARMIL


.


Abin da su kallabu basu sani ba shine A lokacinda suka isa


gidan sarki hinzur Dakarun da suke fada dasu dakarune masu


kare lafiyan sarki su dubu daya,


.


Su wayannan dakaru basa rabuwa da wannan gidan sarautar sai


sati yadda za'a canja da wasu su wayannan suje su huta


.


Acikin gari kuwa koda Mayaka da dakaru suka ji wannan busa ,


Nan da nan duk wani mayaki kuma dakare na wannan birni yayi


shirin yaki sannan aka tasamma gidan sarki,


Sabida karan busar daga cikin gidan take fitowa,


Sarki hinzur na turakansa sai sharbar barci yake kwatsam sai


yaji karar wannan busar acikin kunnuwansa


Nan take ya mike daga kwancen daya ke ,


Koda ya fahimci busar na fitowa daga cikin gidansa ne sai ransa


ya baci,


Cikin kankanin lokaci gagarumin shigar yaki irin ta sarakai, ya


dora takobin sa akan kafadarsa


Cikin hasala da zafin rai ya bangaje kofan turakanshi take


kofan ta fadi kasa shirim,


Kofar na faduwa ya fito ya fara tafiya cikin izza koda yaga yayi


tafiya mai dan tsayi amma bai hadu da dakarunsa ba, sabanin


da, sai ya kara fusata nan da nan ya falfala da azabaBben gudu


Cikin kankanin lokaci ya iso bakin babban kofan da zata


sadashi da farfajiyar gidan,


Cikin kunan rai ya daki kofan da kafansa take kofan ta fadi


rikica ,


Kofan na budewa sarki hinzur yai arba da wayannan yan fashin


sai ratattakan dakarunsa suke.


Nan take ya kwala wata irin kara wacce tasa gabadaya mayakan


suka tsaida yakin sannan sukai dubi izuwa wajen da yake tsaye


.


Yanfashin naganin haka sai suka falfalo da gudun tsiya don su


afka ma sarki hinzur


Sarki hinzur na ganin haka sai shima ya ruga da gudu don ya


tarbesu,


Koda ya rage baifi saura taku kadan ba tsakaninsa da yanfashin


sai ya daka tsalle yai sama , a saman ne cikin zafin nama ya


shafttare,


Makogwaron yanfashinnan da sukai kansa su biyar.


.


Nan fa sarki hinzur ya cigaba da sara da suka baji ba gani duk


inda ya nufa sai de kaga sassan jikin mutun na yawo bisa


sararin samaniya, yadda kasan ana sassabe a gona, tabbas


masifa ba' a samata rana lallai da mutum yana wajen yana ganin


irin yanda sarki hinzur ke yiwa wayannan yanfashi kisan gilla


toh daya tabbata lallai sarki hinzur ya cika NAMIJIN GASKE


duk girman kato sai dai kaga yayi tsalle ya saka takobinsa ya


farke masa ciki take zakaga jini yayi tsartuwa, cikin kankanin


lokaci sarki hinzur ya kashe kasu biyu cikin kaso uku na


yanfashin


.


Koda yan fashin suka fuskanci muddin aka cigaba da wannan


yakin a haka toh tabbas nan da wasu yan dakiku za'a karar da su


Ai nan take yanfashinnan suka fara neman hanyar tsira, cikin


masifaffen gudu suka tasamma kofan fita daga gidan da nufin


su fice daga gidan sarautar,


Bazato sai gani sukai kofan gidan ta bude da kanta


Budewar kofan keda wuya sai ga sarkin yaki zabbagu ibn


sharmil da mayaka abayansa kimanin milyan daya ,


Nan fa sarkin yaki ya cigaba da fille kawunan yanfashinnan shi


kallabu koda ganin haka sai ya hankalinsa yayi matukar


dugunzuma take ya sadakar cewa ya rigaya ya mutu,


Tsulum sai ganin Kamsas yayi ya bayyana agabansa yana


baiyana ya kama hannun kallabu yana shirin furta kalmomin


dazu kenan kawai sai gani sukai sarki hinzur ya baiyana a


gabansu


Cikin matukar hassala sarki hinzur ya daga takobinsa sama da


nufin ya fille kan shugaban yan fashi kallabu da kuma kamsas ,


Koda Takobin tazo daidai saitin wuyan kallabu


Sai........


.


SAI ME


SHIN AGANINKU KALLABU ZAI TSIRA DAGA KAIFIN


TAKOBIN SARKI HINZUR KUWA


.


Part D is Coming Soon


Marubuci:- Shuraih Usman


Hakkin mallaka (m) Shuraih Usman


Company:- Shuraih 99%


(c) shuraih Usman 2017


Typing:- shuraih 99%