CHAPTER 13
by @ayshercool
_*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
***
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
***
PART1
Page 14
ELEGANT ONLINE WRITER'S
Sosai Yusuf yake ƙara samun haske akan lamarin binciken da yake yi, Sam babu specific lokacin da Widad take bawa Yusuf albashi, duk lokacin da ta bushi Iska sedai yaga alert ɗin kuɗi, kuma kuɗi masu yawa, sannan be isa yayi magana ba.
Yana ta tattara bayananan daze gabatar a gurin aiki na sakamakon binciken da yake yi.
Tunda Yusuf ya tafi Nurat take tunanin, ko ta gayawa Mahaifiyarta yadda suka yi da Yusuf, wata zuciyar ta gargaɗe ta akan hakan.
********************************
Gaba ɗaya Widad ta takura kanta, sam ko Babban falo bata fitowa, tana iya sashin ta daga ita se magenta, duk da haka Yusuf kullum se yaje koda baze ganta ba kuwa.
Lambar wani abokinsa likita ya dubo a wayarsa ya kirashi, se da ta kusa katsewa sannan ya ɗauka.
"Yusuf kana da kirki kuwa? Ace ka ɓata ko neman mutane baka yi?"
Yusuf yace "Amma ka tsaya mu fara gaisawa, sarkin ƙorafi"
Nan suka gaisa suka taɓa hirar yaushe rabo, sannan Yusuf yace "dama doctor Hamza ina da wata 'yar tambaya ne, dukda nasan tambayar da zan maka ba a fannin daka karanta kenan ba, amma na sanka da shige shige"
Hamza yace "shikenan ina jinka, Allah yasa nasan amsar tambayar taka, in babu amsar ma se'a nemo"
'Masha Allah, dan Allah Hamza wace irin larurar ƙwaƙwalwa ce take sa mutum ya dinga gudun mutane? "
Doctor Hamza yace
"Anthropophobia kenan, is a mental disorder, masu irin wannan larurar suna jin tsoron taron mutane, idan abun ya tsananta ma ko ahalinsu basa son su raɓe su, sedai wasu tsirari daga mutane, basu fiye son taron jama'a ba, ko shiga cikin mutane basa so"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "to me yake haddasa ciwon"
Hamza yace "eh to, abun da yake haddassa wannan larurar ga wasu, idan an taɓa cin amanarsu, mussaman wanda suka yadda da shi, ko kuma wani abu da ya taɓa faruwa dasu mara daɗi a rayuwarsu, wasu kuma hormones ne suke haddasa musu excessive fear ya danganta dai, zakaga wataran suna lafiya ƙalau ga wanda ciwon be tsananta a gare su ba, amma idan ya tashi zaka ga basa son haɗa ido da mutane, basa son suga ana kallonsu, kosu kasa bacci, ko yawan ciwon kai, bugun zuciyar su ya canza, wasu numfashinsu har ɗaukewa yake, ko su dinga karkarwa in sunga baƙo, ko wanda basu yadda dashi ba, ko kuma su dinga wrong perception akan abubuwa, ko su dinga ganin duk wanda ya raɓesu ze cutar da sune"
"Ok magana, nagode sosai Hamza amma meye maganin ciwon?"
"gaskiya babu wani sahihin maganin ciwon gaskiya, rehabilitation ne a dinga kwantar musu da hankali tare da ƙoƙarin canza musu tunani daga mummuna zuwa kyakkyawa, dan wasu in damuwar tayi musu yawa suna fara shaye2, ko dinga wasu tunani wanda ya saɓa da abunda yake a zahiri, ayi ƙoƙarin samar da wani abu daze dinga ɗebe musu kewa, koya ɗauke musu hankali daga damuwarsu, in kaga an basu magani mafi akasari sedai a basu magani akan sauran matsala, kamar bugun zuciyar, ko daidaituwar hormones ɗin ko makamancin hakan...
Shiru Yusuf yayi yana tunani, meye alaƙar ƙwayar daya gani a ƙasan kofin shayin da za'a bawa Widad da ciwon nata, Doctor Hamza Yana cikin yiwa Yusuf bayanin ne ya hango Widad ta fito, tana nufo inda yake zaune, gaba ɗaya fuskarta a haɗe kamar kullum, yauma shigar tata da ta saba ita tayi, jikin nan a tsuke a cikin ƙananan kaya.
Da sauri Yusuf yace "shikenan nagode sosai doctor, nagane Allah ya saka da alkhairi" ya katse wayar
Ya shiga wani tunanin, "to wace irin Allura akewa Widad haka? Amal tace masa ana mata wata Allura, ga kuma abunda likita yace"
Ta ƙaraso ta kalle shi a yamutse tace
"ɗakko mota, zamu airport ne yanzu"
Ya kalle ta yace
"me zamuje yi a Airport?"
"ban sani ba" ta bashi amsa
Ƙasa yai da idonsa yayi mata wani irin kallo sannan ya miƙe yai gaba, gaba ɗaya kasa gane kalar kallon tayi meya ke nufi da haka?
Ya ɗakko mota ya kunna suka fara tafiya, suna tafiya yana satar kallonta yana tunanin, me zeyi wa Widad wanda ze temaka gurin canza tunanin ta mara kyau zuwa me kyau, kamar yadda doctor Hamza ya gaya masa.
Yana cikin tunanin wayarsa ta fara ringing, sedai lambar ba suna, kuma yana tsoron ya ɗaga yaje a cikin abokan aikinsa ne, wani yayi masa kwaɓa, sekuma ya tuna halinta, yanzu yana ƙin ɗaga wayar zata masa wata fassarar, haka ya basar ya ɗaga wayar yasa a kunnen sa tare da yin sallama.
Siririyar muryar mace ce ta amsa tace
"Aboki ya kake?" se yanzu ya gane muryar Nurat, murmushi yayi yace "lafiya ƙalau, light ya kike?"
Wani murmushi ne ya suɓuce mata tace "lafiya ƙalau friend, dama cewa nayi bari in kiraka mu gaisa"
"Amma gaskiya kin kyauta Light, ina fatan kina lafiya ba kya cikin kowace irin damuwa? Kin san damuwa da yawan haɗe rai yana sa mutum ɓacin rai da saurin tsufa, kuma duk kyansa ya koma kamar wani abun tsoro"
Da sauri Widad ta juyo ta kalle shi, amma ya basar ya cigaba da wayar, yayin da Nurat tayi murmushi tace "Ni lafiya ƙalau nake, bani da wata damuwa ko matsala ina Widad?"
"tana gidansu, ko ince kina gaishe ta ne?"
Kamar Yusuf yana ganinta ta girgiza kai tace "Kamanta kace kar in gaya mata muna abota? Na tambayane kawai dan inji ko tana lafiya"
"Eh kuma fa hakane? Amma yaushe zakizo ki ganta?"
"Ai ban san wane irin kallo za tayi min ba idan nazo gidansu, inajin tsoror"
Tsaki Widad tayi ba tare da ta kalli Yusuf ba tace
"Malam ka isheni, ka cikamin kunne"
Murmushi Yusuf yayi yace
"light, se anjima Madam tace na cika mata kunne"
Jiki a sanyaye Nurat tace "Madam kuma? Dama kana da Aurene?"
Yusuf yace "Babba dani kice bani da Aure, ina da Aure mana muna tare da ita ma, munɗan fita ne, se anjima kar in sake ɓata mata rai"
Wani irin wulaƙantaccen kallo Widad tayi masa, dama yasan a rina
"ni kake cewa matarka? Baka da hankaline, ni ka kalleni ka cemin matarka"
"waye cemiki dake nake ne? Am just kidding idan ba haka nayi mata ba zata ga kamar na mata wulaƙanci ne, kuma babu daɗi ka Wulaƙanta mutum it hurts a lot, Yusuf baya Wulaƙanta mutane"
Wani tsakin ta kuma ja ta ɗauke kanta, yayin da shi kuma yayi murmushi, a ransa yace 'Insha Allah, sena canza miki dukkanin wannan gurɓatattun tunanin naki kafin in kammala bincike na"
Gurin wani restaurant sukabi, tace masa ya tsaya ai kuwa yayi parking, tana yi tana duba agogon hannunta, ta buɗe motar ta fita, shima ya fito yabi bayanta.
Cikin restaurant ɗin ta shiga ta samu guri ta zauna, Yusuf be jira unarninta ba shima yaja kujera ya zauna.
Aka kawo musu menu
(jadawalin Abincin da suke available)
Ta karɓa tana jujjuya menu ɗin, ɗan ɓata fuska tayi ta zaɓi Abunda take so,
Aka bawa Yusuf ma, ya kalli Menu ɗin ya girgiza kai yace
"Ni ban iya cin irin wannan Abincin ba gaskiya, Umma ta cika min ciki da ɗumamen tuwo dan haka ni ba abunda zanci"
Kallonsa tayi ta ɗauke kanta, yayin da waiter ɗin tayi murmushi ta karɓi menu ɗin ta tafi.
Karon Farko da Yusuf yaga Widad tana cin normal Abinci, sam bata damu da Abinci ba, sedai yaga tana 'yan ciye ciye, ta yaya mutum zeyi lafiya ba tare da cin cikakken Abincin da ze gina masa jiki ba, ko duk cikin rashin yardar ne oho mata.
Yanzun ma ba wani cin Abincin take ba, ɗan cakala take a jikin spoon, kamar wata ƙaramar Yarinya kamar me wasa da Abincin tana kaiwa bakin ta .
Yusuf ya ɗan ƙura mata ido yace "Madam are you really Hungry?"
Cigaba da cakalar Abincin ta tayi ba tare da ta kula shi ba.
Ko ɗaya bisa ukun Abincin bata ci ba, ko naman kai bata taɓa ba, ta ture Abincin ta ɗau tissue tana goge bakin ta, 'Iko se Allah, Abincin naira dubu huɗu akayi wa wannan cakalar aka barshi, wani yana nan yana fama da Yunwa'
"wai Harkin ƙoshi?"
"wai ina ruwanka dani ne? Ta yaya zan iya cinye wannan Abincin duka?"
"Amma kin san bazaki iya cinyewa ba kika sa aka kawo miki? Akwai dubban marasa ƙarfi da Abincin naira ɗari ma gagarar su yake a rana, kalli uban Abincin da kika bari, wataƙila yanzu wannan da kika rage sedai a zubar, ba kyau Wulaƙanta Abinci, wataran kema ze iya Wulaƙanta ki"
Ko kallonsa ba tayi ba, ta ɗauke kanta tana kallon wani gurin, amma tayi shiru tana saurarensa, gefe guda kuma ta shiga tunanin maganar sa, dagaske akwai wanda suke rasa Abincin naira ɗari ya gagare su? To wani irin Abinci ma mutum zeci da naira ɗari, se a samu mutum yace bashi da naira ɗari?.
Yusuf Yaja plate ɗin Abincin gabansa ya ɗau spoon ya fara cin Abincin da Widad ta rage.
Kallon Yusuf take, sosai mamaki yake bata shi sam be ɗau komai da zafi ba, Abincin data rage yake ci, ko dan dai shi talaka ne oho.
Yusuf ba ƙaramin mamaki yake ba yadda take ɗaga masa ƙafa, dan shi kansa yasan wasu lokutan yana wuce gona da iri, tana ƙyaleshi ne kawai
"ya naga kina kallona ko nayi wani abun ne na rashin yadda?"
Ɗauke idonta tayi daga kallonsa zuwa wani gurin daban.
Yusuf ya ciko spoon yace
"Kinga yadda ake cin Abinci a ciko cokali da Abinci, se mutum ya ƙoshi ba yadda kike yi ba, kamar kina wasan yara, koda yake yarinyar ce ai"
Ɗago ido tayi ta kalle shi, amma ya cigaba da cin Abincin yaƙi kallonta, lallai Yusuf ya samu dama a kanta ya fara rainata, tunda harya samu damar gaya mata maganganun da yaga dama, ita kanta Widad tana mamakin yadda take ƙyale Yusuf, ba yadda za tayi dashi wata ƙaddara me ƙarfi ta shigo dashi cikin rayuwarta, wanda ko dan albarkacin hakan yaci ta dinga ɗaga masa.
Seda ya kammala sannan ta ajiye masa ATM ɗinta, ta miƙe ta nufi hanyar fita, Yusuf kuma ya nufi gurin biyan kuɗin, kafin Widad ta kai ga ƙofar fita wani mutum da tunda suka shigo yake kallonta yabi bayanta.
Yusuf yace "ashe akwai mini Drama yau"
Ya biya kuɗin ya fito, sedai yana fitowa ya tarar tana zazzagawa Mutumin masifa.
"Kalle ka ni zaka biyo kace in baka lambata? Bazan bayar ba shashsasha an gaya maka kowa sakaraine irin ka?"
"Ni kike cewa sakarai?"
"Na gaya maka ko akwai abunda zaka iya ne?"
Yusuf ya ƙaraso da sauri gurin yace "haba bawan Allah, ya zaka biyo matar Aure kace kana so?"
Mutumin ya kalli Yusuf yace "Matar Aure kuma? Da wannan shigar tata?"
"koma wace irin shiga ce tayi ina ruwan ka? Haka muka tsara rayuwar Aurenmu, haka muka ga damar yi, idan har kasan shigar da tayi bata dace ba meye na biyo ta? Kana gurin nan muka zo tare mu kaci Abinci, danme zaka biyo ta kace kana so?"
Mutumin yace "Amma indai wannan matarka ce gaskiya kayi dacen Auren kyakykyawar mace, sedai bata da ɗa'a kuma bata san darajar Auren ta ba"
"bakomai a haka nake son a bata, sannan karka kuma gangancin kiran ta da wasu miyagun kalamai, ka gode Allah da ban ɗau mummunan mataki akanka ba"
Ya juya ya kalli Widad da mamaki ya hana ta magana, A fusace ta juya ta tafi mota ba tare da tace komai ba
Yusuf ya juya ya koma motar shima yana shiga ya zauna, ya kunna motar suka fara tafiya, ba tace komai ba se tafasa da zuciyar ta take yi
Ba zato ba tsammani, Widad ta Ƙanƙance ido tace
"i thinks you drunk something abusive today, kasan me ka faɗa kuwa? Which type of Weed did you take today? Wane irin rashin hankali ka aikata? Meye hakan kake ne dan me zaka dinga danganta kanka dani a matsayin mijina, kai ko Auren zanyi zan auri talakan mutum kamar Kane?"
Dukda yadda kalaman Widad suka daki zuciyar Sa haka ya daure, yayi parking ɗin motarsa, ya matsa Kusa da ita ya matsa yace "Abunda kika ci dai shi naci, dukda baki san meye So ba, ƙarewa ma kince baki yadda dashi ba, amma the magic behind Love is that, ba ruwan sa da talaka kome kuɗi, sannan wannan abunda nayi shine kaɗai mafita daze hana kowane kare da biri binki, da kuma ƙarewa surar jikin ki kallo, please Dress decently to avoid such type of people, dukda ina matsayin me miki aiki, aikin ma na direba, I have to tell you something, you have an attractive beauty Widad, stop exposing it anyhow yana taɓa zuciyata a duk lokacin da kika fito da wannan shigar naga wasu na ƙarewa wannan kyakykyawar halittar kallo, your beauty suppose to be only for your husband, duk wata mace me tsadace jikinta ma me tsada ne meyasa zaki dinga bari ana ganin naki?"
Ɗaga ido tayi tana kallon sa, gaba ɗaya Yusuf ya rufe mata baki, ya kulle mata kai, gaba ɗaya ta nemi izzar da jin kan da zata masa wulaƙanci ta rasa, yau wani irin kwarjini yayi mata data kasa cewa komai, shi kuma ya samu damar hakan yake ta abunda yaga dama, a baya zata iya rantsewa baze aikata haka ba, ganin yadda ko magana baya son yi.
Haka suka cigaba da tafiya kamar kurame, kowa da abunda yake saƙawa a zuciyar sa, gaba ɗaya tunanin rashin mutuncin da zata yi wa Yusuf take.
Har suka ƙarasa airport bata iya cewa komai ba, parking yayi amma bata buɗe murfin motar ta fita ba, shima zaman sa yayi yaƙi fita, ya sauke glasan suka cigaba da zama, lokaci2 ta dinga duba agogon hannun ta.
Buɗe ƙofar tayi ta fita, shima ya buɗe ya fito, Alhaji Nasir ne yake tahowa da brief case ɗinsa a hannun sa.
Yusuf ya ƙarasa da sauri yana gaida Alhaji Nasir tareda karɓar brief case ɗin hannun sa.
Alhaji Nasir yace "Yayana na kaina, fatan na sameku lafiya ya amana ta?"
Yusuf yay murmushi yace "Alhamdilillah"
Ya kalli Widad yace "my Lovely har yanzu kina fushi da Dad ko?" yai maganar yana rungume Widad, kamar anmata dole tace "Welcome Daddy"
Alhaji Nasir ya ɗan shafa bayan ta yace"thank you sweetheart" suka ɗunguma zuwa mota gaba ɗaya, suna tafiya Alhaji Nasir da Yusuf ne kawai ke hira, Amma Widad tunanin ta ta yaya zata hukunta Yusuf.
Har Yusuf ya gama aikin sa na ranar ya tafi Widad bata samu mafita ba.
***********************************
"Jama'a bafa a bori da sanyin jiki, wannan ce damar da yakamata muyi amfani da ita, tunda Allah yasa yarinyar nan tana ƙasar nan musan abunda za muyi" cewar Alhaji Munir
Alhaji Musa yace "Ni idan an samu abun nan falillahil hamd, amma babban burina be wuce in Wulaƙanta Alhaji Nasir a idon duniya shida ahalinsa ba kamar yadda ya Wulaƙanta ni ya ɓata min suna"
Alhaji Haruna yace "gaba ɗayanmu buƙatar mu ɗaya ce, kuma kunsan Alhaji Bukar shike bamu umarnin abunda zamuyi, karmu yadda muyi abunda ze waegaza shirin mu, yanzu yarinyar taje gidan yari tayi wa Hashim barazana akan indai da hannun sa akan wannan lamari daya samu Bala to tabbas zata ɗau mataki akansa "
Alhaji Musa yace " Umarnin Alhaji Bukar kawai nake jira, amma akwai yuwuwar shima a kauda shi, dan komai ze iya faruwa barinsa a doron ƙasa"
Alhaji Haruna ya zame akan kujera yana shafa tumbinsa yace
"Ni dai kam da zan samu yarinyar nan, So nake gaskiya, dan akwai ta da ƙira daidai gwargwado".
Tsaki Alhaji Munir yayi yace "kai ka fiye shirme, ana ta kai wake ta kaya, in in hutawa kake so, ka fita ƙasashen waje ga mata nan farare yadda kake so, amma yanzu ka bari idan muka karɓi abunda muke so, muka aika Nasir Daula kiyama, se kayi yadda kaso"
Wata uwar dariya suka saki hadda shewa.
**********************************
"Bulama tafiya tayi Alhamdilillah, na samu approval na fara business ɗina da China"
"Masha Allah, naji daɗin hakan, Allah yayi jagora"
Baban Widad yace "Ameen ya Allah, sedai ko kun samu saɓani da 'yar taka ne? Tunda na dawo naga bata walwala ko akwai matsala ne?"
Alhaji Bulama yai murmushi yace "hmm Widad' yata ta kaina, tabbas munyi faɗa, kasan tunda nace ayi mata Aure take jin haushi na, tazo ta sameni akan wai sena mata Visa ta koma naƙi, shine take fushi"
Alhaji Nasir ya girgiza kai yace "Nima wancan satin ta kirani tana kuka, akan lallai sena kiraka nasa an mata visa ta koma, ni kuma gaskiya bazan bari ta koma ba, idanma zatavkoma se bayan Auren ta da Fahad sa tafi tare"
"hakane, daga lokacin da ta fara tara iyali dole ta dena wannan halayen nata, sannan mamanta ta kawomin ƙararta akan yadda suke da direban nan, na kirata nayi mata faɗa, nanma ta sake yin fushi dani"
Alhaji Nasir yai murmushi yace "ina tunanin akwai wani ɓoyayyen al'amari a tattare da yaron nan, ba ƙaramin daɗi naji ba ganin shine mutum na farko bayan nida kai da Widad take sakewa dashi"
"Amma karfa muyi sake yazo suyi shaƙuwar da zamu yi da nasani"
"Insha Allah ba zamuyi ba, dan yaron yana da tarbiyya sosai"
"Amma idan soyayya ta shiga tsakanin su fa?"
Alhaji Nasir yace " Yarinyar da bata yadda da soyayya ba, ta ina zasu fara soyayya? Gaba ɗaya Widad ɗina a birkice take bata da alƙibla"
Bulama yace "Kasan bata da alƙibla ai kuwa ba abun mamaki bane ta fara soyayya da direban ta, tunda shi so baya sallama".
"to nidai duk abunda ze saka ta farinciki shi nake so, idan ta kawo shi tace tana so bakomai se in Aura nata shi"
Bulama yace "Allah ya kiyaye mu aura mata direba haba Daula"
"to masu 'ya, ai seka biye mata kuyi tayi"
Sukayi dariya suka shiga hirara duniya.
***********************************
Sintiri take a ɗakin ta, tana son gazgata abunda take ji a zuciyar ta game da Abokin ta. Dagaske na kamu da Son wanda yake daga ɓangaren maƙiyin mahaifi na, amma ban san alaƙarshi da Widad ba, amma tunda na gansu tare suna da alaƙa.
Shiru tayi tana tuna yadda ya zauna a kusa da ita yana mata magana, cikin rarrashi danta saki jiki dashi.
Kamar light da yake kiran ta dashi yafi komai yi mata daɗi, Amma dagaske yana da Aure? Ta tambayi kanta, anya za'a yarda a auramin me mata? Gashi kuma ɗan uwan Widad.
Dafe kai tayi tace "Subhanallah"
"ke lafiya kuwa? Sintirin me kike tayi haka kamar kinwa sarki ƙarya?"
Juyawa tayi ta kalli inda Maman ta ke tsaye tace "bakomai fa"
"bakomai, a hakan? Gaba ɗaya alamu sun nuna baki da gaskiya sam"
Ta ɗan tura baki tace "wallahi ina da gaskiya"
"shikenan, idan tayi wari maji"
Nurat ta koma kan gadonta ta zauna ta ɗakko wayarta ta shiga kiran layin Yusuf amma shiru baya shiga, tayi2 harta gaji ta ajiye, tana mamakin ya akayi hakan ta faru?
Shikuwa Yusuf tun ranar data kira shi agaban Widad, yana komawa gida ya cire layin ya ajiye gaba ɗaya.
**********************************
Oga Suleiman ne zaune akan kujera yana gwadawa Sakina wasu ayyuka a computer, sun maida hankali sosai kan aikin.
Abbas ne yayi sallama, suka ɗago gaba ɗaya suka dube shi tare da amsa sallamarsa, Sakina ta gaida Abbas, yayin da Abbas ya ƙamewa Suleman cikin girmamawa.
Suleiman ya bashi damar zama, sannan ya miƙa masa hannu suka gaisa, Suleiman yace "Abbas kwana biyu banga Yusuf ba fa, ya kamata ace yazo ya gabatar min da sakamakon binciken da yayi"
Abbas yace "ranka ya daɗe, nima kaina na kasa gane inda yasa gaba, gaba ɗaya kamar ba aikin yake ba, yaje ya shantake se abun Arziki yake samu a gidan, alherin da suke masa yasa gaba ɗaya hankalin sa baya kan aikin, da dai da hali a canza shi da wani kawai"
Suleiman yace "Amma kaika cemin ze iya aikin, da kai nace zan bawa ka nunamin ya fika haƙuri da juriya"
"Ai Oga sam ban san haka ze faru ba, ban taɓa sanin Yusuf yana da son abun duniya ba seda ya karɓi aikin nan, ba abunda yake se neman gindin zama a gidan da yake"
Sakina kam sakin baki tayi tana sauraren yadda Abbas ke ɓata Yusuf a gurin ogansu, wanda hakan ze iya jawowa Yusuf babbar matsala a gurin aikin nasu, Yusuf ya yadda da Abbas sosai, dan yana masa kallon ɗan uwa bama abokin aiki ba.
Oga Suleiman yace "shikenan, zan duba idan da dama zan kira shi a waya ma, inaga karɓar aikin zanyi daga hannun sa in bawa wani"
***********************************
Gidan shiru babu kowa, Yusuf yana inda ya saba zama idan yaje gidan su Widad, Murtalah ne yazo inda Yusuf yake yace "Malam Yusuf kana nan kana hutawa ashe?"
"wallahi kuwa Murtala ya aikin?"
"Alhamdilillah, ai kana fama Yusuf, kullum se kazo ko zakayi aiki ko ba zaka yi ba"
Yusuf yayi murmushi yace "to ya za'ayi tunda na yadda zanyi aikin, ai dole in cika ƙa'idar aikin"
Murtalah yace "hakane" suna cikin hirar Amal ta fito, ta ƙaraso inda Yusuf ke zaune, ranta a ɓace tace "kazo ana son ganin ka"
Ba musu ya miƙe yabi bayan ta, suna shiga babban falo har Yusuf zeyi hanyar ɓangaren Widad, dan yasan be wuce ace ita take kiransa ba, tunda Alhaji Nasir baya nan.
Amal tace "A'a, ba a nan ake neman ka ba"
Ta nuna masa hanyar ɗaya part ɗin dabe taɓa taka gurin ba, seda ya ɗanyi jimmm ya kalle ta sannan yace "shikenan muje"
Suka rankaya ɓangaren data nuna masa, tana tafe yana binta a baya
Wata ƙofa ta buɗe suka shiga, matsakaicin bedroom ne, me ɗauke da kayan more rayuwa sedai be kai haɗuwar na gimbiyar gidan ba.
Amal ta juyo ta kalle shi tace "Yusuf Meka ke nufi dani ne?"
Cike da rashin fahimta yace "kamar yaya? Kince ana kirana kuma kin kawo ni nan"
"Yusuf nina nake nemanka ba wani ba, na gaya maka abunda ke raina amma ka maidani kamar wata banza, Haba Yusuf me yasa baka da tausayi ne? Soyayyar ka nata wahalar dani amma hankalin ka yana kan waccan banzar mahaukaciyar, har dama ka samu a kanta wanda zaka rama irin wulaƙancin da take maka, ATM ɗinta kwanansa nawa a gurin ka? kamata yayi kayi amfani da wannan damar ka azurta kanka, tausayin mara tausayi asara, asara ne gagaruma ko dai dan Widad tana da kuɗi shiyasa kake Wulaƙanta ni?"
Yusuf be taɓa jin son Amal a ransa ba, ta yaya suna muzanta wadda suke cin Arzikin gidan su, ina gashi da yake bare? Kuma suna ta jadadda masa yayi wannan gagarumar sata haka?
"Amal ki fuskance ni, niba na Wulaƙanta mutane, sannan bani na tara musu dukiya ba, ta yaya zan musu wannan mummunan aiki? Ni ba Ɓarawo bane, dukiyar Widad bata gabana mutunci da girmamawa ya fiye min wata dukiya komai yawan ta, indai ban rasa ci da sha ba Alhamdilillah a yadda Allah ya ajiye ni, Widad batamin laifin komai ba, babu wani abu da tayi min wanda zesa in cutar da ita ko mahaifinta, tsakanina da su in musu aiki ne su biyani bisa ga yarjejeniyar da na sakawa hannu, Amma Amal tsakani na dake babu batun Soyayya duba da banbanci da kuma tazarar dake tsakanin mu, ke 'yar masu kuɗi ce, ni kuma talaka ne matsiyaci kamar yadda mutan gidan ku suke faɗa"
"Yanzu kana nufin ba zaka karɓi Soyayya ta ba Yusuf, ka zaɓi cigaba da wahalar da zuciya ta, mace me kima kamata ince ina sonka amma ka watsamin ƙasa a ido? To wallahi baka isa ba, zaɓi biyu ke gareka kodai ka karɓi Soyayya ta, ko kuma in shirya maka gadar zaren da idan ta rufta da kai har Abada ba zaka sake wani Amfani ba"
'Kiyi duk abunda ki kiga dama, tabbas da soyayyar gaskiya kike min da baki faɗi haka ba, tabbas na taɓa Soyayya nasan zafin ta, Amma ba' a dole a soyayya "
Yana gama maganar ya juya ya fice daga ɗakin, biyo bayan sa tayi tana ƙwala masa kira, Amma yaƙi tsayawa yana buɗe ƙofar part ɗin ze fita yayi tozali da gimbiya 'yar masu gida, Widad ce a tsaye a bakin ƙofar dake facing ɗin wadda ya fito, se muzurai take idanunta sunyi Ja, tana masa wani irin kallo me wuyar fassara.
Me kuke tunanin ze faru?
(Masha Allah, am speechless wlh, Addu'arku tayi tasiri a gareni ina miƙa muku godiya, masu tambayar jikin Daddy Alhamdilillah ya warke ras💃💃💃 almost done with the exams only some part remains, saura fatan Nasara, farinciki yasa nace bari inyi surprising ɗinku da posting, ina jiran jin comments me fasa waya, idan anyi Comment yadda nake so gobema akwai posting insha Allah 😍😍😍 ina godiya masoya)
Domin sharhi, gyara, ko shawara feel free to contact me
Ayshercool
***