MASOYA UKU

Chapter 1

by @nanahaleema11

*MASOYA UKU*


_(True love, intense jealousy & betrayal)._





Not edited 🤙


............"Mama nifa wallahi bazan iya zaman aure da Yaya Ammar ba dan bana son sa kuma banjin zan so shi har abada" wata kyakykyawar matashiyar buduwa ta fad'a cikin tsiwa da rashin kunya.


"Wai ke Amatullah meke damun kine? Ana yi miki magana kina mayarwa dan baki da mutunci, ki nutsu ki dawo hankalin ki ki tsaya muyi magana cikin fahimta tun kafin Dadyn ki yazo kin san dan ya Zane ki ba wani abun bane a wajan sa" matar wacce baza ta haure shekaru Arba'in da biyar ba ta fad'a cikin fusata.

Zama Amatullah tayi tana kunbure-kunbure tana kunkuni, Wacce take amsa sunan Mama tace, "Amatullah hak'uri zakiyi ki amince da auren Prince kodan farin cikin mahaifin ki ni kaina ba son wannan auren nake ba har ga Allah amma sabida halin mahaifin ki yasa na amince dole, ki nutsu ki San abinda ke miki ciwo rashin amincewa da auren Prince shine rashin kwanciyar hankalin ki a cikin gidan nan sanin kanki ne akan wannan auren mahaifin ki zai iya tsine miki a matsayi na na mahaifiyar ki ina so ki amince a auren nan". 


" Tabdijam yanzu akan wancan banzan sai Dady ya tsine min? Shege sai girman kan tsiya kamar shine Yariman duniya gabadaya wallahi na tsane shi kuma ni Wallahi bazan aure shi ba." ta fad'a tana kauda Amatullah gefe.

Cikin fad'a Mama tace, "Shikenan kije kiyi duk abinda kiga dama na cire hannu na daga kanki tunda ke taurin kan tsiya gare ki sai kije Allah ya bada sa'a" tana gama fad'a mata haka ta mik'e a fusace ta fita daga parlourn.


Tab'e baki Amatullah tayi tace, "Haka kawai a tauye min hakki ko bani da Wanda nake so ai bazan auri wancan basamuden ba balle ma ina da My Anwar haka kawai ina yarinta ayi min auren dole" haka ta dinga magana ita kad'ai har ta gaji ta mik'e ta haura sama.


Wani k'aton bedroom ta nufa tana shiga ta fad'a kan gado tare da d'auko iPhone 11 pro max ta danna tare da karawa a kunne, "Kina ina ne wai?".


Daga can side din akace, "Ina gida mana da Labari ne Besty?". Tsaki tayi tace, " Hmm Labari kai wai Dady ni yake so yayiwa auren dole kuma a rasa Wanda za'a had'a mi dashi sai wannan prince din."


Cikin zumud'i wacce ake wayar da ita tace, "Wanne Prince kenan Amatullahi?". " Mtsw kefa banza ce wallahi akwai wani Prince da ya wuce wannan mugun doctor din na gidan Umma."

Wani ihu tayi tace, "Wayyo Allah na amma naji dad'in wannan labarin, Bestie zan zo na samu Dady da kaina nima ina goyan baya wallahi." Cike da mamaki tace, "Lallai Rahma na yarda kin daina sona har kike so ayi min auren dole da wannan mutumin."


"Sorry Dear ba haka bane wallahi kawai dai abin ya sani farin ciki ne sosai, kinga maganar nan baza ta yu a waya ba bara na kammala abinda nake yi yanzu ki ganni".


Yatsine fuska tayi tace, A'a bara nazo da kaina babu abinda nake yi a nan kuma daman Mama ta bani sako na kawowa Umma" bata tsaya jin abinda zata ce ba ta kashe wayar tare da mik'ewa ta saka mayafi ta yafa ta sakko daga saman.

Dake basu da nisa da gidan Sarkin Kano tana fito baya kawai ta zagaya sai gata a k'ofar gidan, babu Wanda yayi mata magana Dan ansan wace ita sai zubewa da ake ana kwasar gaisuwa ita kuma tana amsawa cikin fara'a.


Da sallama ta shiga parlourn dake b'angaren Umma babu kowa a parlourn sai bayi da suke ta aikin su, gaishe ta suka yi ta amsa sannan ta wuce ciki, kamar yadda tayi tunanin tana zaune tana karatun alkur'ani mai girma.


Kusa da k'afar ta ta zauna tana Wasa da adon lace din dake jikin zanin Umma, sai da ta kai aya sannan ta rife Alkur'anin tayi murmushi tare da kallon ta tace, "Amatullahi na barka da zuwa".

Cike da shagwab'a tace, " Umma barka da yamma" cikin fara'a tace, "barkan ki kin wuni lafiya?".

" Lafiya lau Umma na, ina Bestie take?". Murmushi Umma tayi ta girgiza kai tace, "Daman nasan wannan zuwan badan ni kika yi shi ba sai dai Rahma to tana cikin d'akin ta."

Bud'e baki tayi tace, "Kai Umma danke nazo fa kawai tausaya mata nayi na tambaye ta amma ni wajan ki nazo mu sha hira". Dariya Umma tayi sosai tace, " To Shikenan zan gani indai wajan nawa kika zo."


Umma tace, "Ya makaranta?" Amatullah ta amsa da, lfy qalau umma muna Nan muna fama da karatu". Umma tayi murmushi tace, "Masha Allah haka ake so, Allah ya bada sa'a" ta amsa da Amin.


Shiru ne ya biyo baya Amatullah ta kalli Umma da take kallon wani waje daman, har ga Allah so take ta tashi taje wajan kawar ta.


Mik'ewa tayi tace, " Umma fitsari nake ji bara naje d'akin waccan yarinyar nayi" bara jira mai Umman zata ce ba ta shige ciki da sauri.


Dariya Umma tayi tace, "Ikon Allah ka haifi da yace zai maka wayo, halin Amatullah sai ita".


Tana shiga ta tarar da ita tana karatu ta kalle ta tace, "Allah sarki Exam's ta saka min kawa a gaba" ta fad'a tana dariya harda rik'e ciki.

Rahma tayi murmushi tace, "Dad'in bani kadai Zan zana ba har da ke, wai ke baza ki Fara karatun ba kodan kin San kina da malam isa?, Tsaki amatullah tayi tace, "Ke Kika sanshi," murmushi Rahma tayi tace," ni ba wannan bama zo ki bani labarin Prince din ki."


Bata rai tayi ta k'araso ciki ta zauna tace, "Kedai bari wai ni za'a yiwa auren dole kuma a rasa Wanda za'a bani Sai doctor ko ya suke so nayi da my Anwar oho" ta fad'a tana yatsine fuska.

Dafa ta tayi tace, "Nidai shawara ta gare ki Bestie ki amince da duk abinda iyayen ki suke baki zaki ci riba anan gaba". Kallon ta Amatullah tayi tace, "okay dake bake za'a yiwa ba Shiyasa kike fad'a min haka, sanin kanki ne tun a dah jinin mu bai had'u dana Prince ba Abu kad'an yace min yar lukuta kuma yace min ido na na munafukai ne amma in baiyi Wasa ba wallahi wata rana sai na zaune shi".


Dariya Rahma tayi tace, " Kunfi kusa dai ke dashi tunda yanzu shine angon naki insha Allah, wai! Abin zaiyi dad'i fa ace Yah Ammar ya zama mijin wayyo dad'i" ta fad'a tana rik'e ta cikin farin ciki.Tsaki tayi ta mik'e tace, "Kinga ni zan tafi banga amfanin fad'a miki bama Wallahi tunda dariya kike min" tana gama fad'ar hakan ta fice daga d'akin ranta a bace.

Biyo bayan ta tayi tana dariya tana kiran sunan ta amma tasan halin ta tunda ta fito baza ta koma ba, a inda ta bar Umma ta ganta ta kalli Umma tace, "Umma na zan koma".

Kallon ta tayi tace, " Har an gama fitsarin kenan? To ki gaida Maman zan shigo zuwa gobe nima insha Allah ". Dariya kawai tayi ta fice daga parlourn.

Tafiya suke a hankali ana zubewa ana kwasar gaisuwa, Amatullah tayi tsaki tace, " Ke nifa kinga dalilin da yasa na tsani zuwa gidan nan ni ba yar sarki ba aita zube min ana gaishe ni wani ma yayi jika dani". Murmushi tayi tace, "to dani dake din ai babu banbanci sai ma kin shigo gidan nan a matsayin matar....." Bata bari ta karasa ba tayi gaba da sauri ko juyo ba tayi ba har ta fice daga gidan.

Dariya tayi sosai itama ta biyo bayan ta.


A bakin gate ta had'u da Amatullah ta rik'e baki tana mamakin ganin dogarai a k'ofar gidan su da alama dai wani daga cikin gidan sarki ya kawo musu ziyara Rahma ta kalle ta tace, "Dear me kike yi nan baki shiga ba?".


Kallan ta tayi tace, " Wai Takawa ya dawo ne?". Kallon dogaran itama tayi sannan tace, "A'a bai dawo meye?".


Tab'e baki tayi tace, " Babu komai, muje" ta fad'a tana shiga cikin gidan. Basu tsaya kallon kowa dake wajan ba suka shige abin su.

A d'akin Amatullah suka yada zango, karar wayar Amatullah ce ta katse musu maganar da suke yi, d'aukar wayar tayi tare da yin murmushi ta kara a kunne tace, "Hello my Heart kana lafiya"

Murmushi ta sake yi tace, " Lafiya Qalau nake sai dai rashin ganin ka yana Neman saka min sabuwar cuta". Shiru tayi alamun ana bata amsa daga d'aya b'angaren, "to Shikenan a fito lafiya sai ka k'araso, love u my heart" tana gama fad'ar hakan ta kashe wayar tare da dora ta akan kirjin ta tana sakin murmushi.

Rahma ta kalle ta tace, "Kaga iyayen soyayya wannan Anwar din badai nacin soyayya ba." Hararar ta tayi tace, "naji Sai me yafi min wannan Prince din wallahi."


"Ya kamata ki dinga saita bakin ki fa ko babu komai Yah Ammar dan uwan kine bai kamata ki dinga fad'ar ko wacce magana ba akan sa."


Bata kula ta ba sai danna wayar tama sa take yi, sallamar da Mama tayi ya saka ta d'ago kai suka amsa mata a tare.


Mama ta kalli Rahma tace, "A'a yaushe kika shigo?". Dariya tayi tace, " Bamu jima sosai ba yanzu nake shirin naje na gaishe ki daman".


"Babu komai ai ya mutan gidan suna Lafiya?". " Lafiya Qalau suke Mama Umma tace zaku yi waya."


"Eh har munyi ma ai, ke Amatullah kije parlourn Dadyn ki yana Neman ki yanzun nan".Dafe kirji tayi tace, " Mama lafiya dai amma?". Girgiza kai tayi tace, "Banda abin ki ya za'a yi na sani kije dai ana jiran ki" tana gama fad'ar hakan ya rufe musu k'ofar ta fita.


Kallan Bestie tayi tace, "Dear taso muje ki raka ni". Rik'e baki tayi tace, "Akan me? Jeki zan jira ki anan" ta fad'a tana kwanciya akan gado.Fita tayi ta kyale ta.


Tun a k'ofar parlourn gaban ta ya fara fad'uwa hakan ya saka ta sunkuyar da kai ta shiga parlourn da sallama.


Amsawa Dady yayi da murmushi a fuskar sa, a kasan carpet ta zauna har lokacin bata d'ago ba, Dady yace, "To Alhamdulillah tunda ta k'araso gata nan sai Ku gaisa ni bara na shiga ciki" yana gama fad'ar hakan ya mik'e ya bar musu parlourn.


Yana fita ta Mik'e ta dawo kan kujera har lokacin kuma bata kalli Wanda Ke zaune a wajan ba sai ma danna wayar ta da ta fara yi, kamshin turaren sa duk ya cika Mata hanci, sai da suka kwashe a kalla mintina goma babu Wanda yayi magana ita a zuciyar ta ta kudure baza tayi magana ba tunda a ka'ida shi ya kamata yayi mata magana, jin shirun yayi yawa ya saka ta d'ago ido a fusace dan taga waye wannan mai cike da izza.

Ido hud'u suka yi dashi tana ganin sa ta Tab'e fuska tace, "Daman nasan ai sai kai din" ta fad'a tana kauda fuska gefe.

Matashin saurayin mai cike da izza da kwarjini ya d'ago fuska tare da k'ara had'e rai kamar bai tab'a dariya ba yace, "Ke malama kin ishe ni da magana" yana fad'ar hakan ya maida kansa ga wayar dake hannun sa.

Masha Allah yadda yake danna wayar ma abin kallo ne duk inda kake neman namiji mai kyau da cikar zati ya kai, sanye yake shadda ash colour sai kyalli take hular kansa ash colour itama, hannun sa daure da agogo mai kyau da tsada yatsu biyu dake hannun daman sa sanye yake da azurfa mai kyawun gaske.

Amatullah ta mik'e cike da rashin kunya tace, "tunda ba Neman ka nayi ba ai zaka iya tashi ka tafi kuma......" Yadda ya d'ago kai ya zuba mata golden eyes din sa yasa ta kasa k'arasa abinda zatace hakan yasa ta juyar da kai gaban ta na faduwa Dan harga Allah tana shayin da tsabar rashin kunya ne yasa take dannewa,

Murmushin gefen baki yayi ya mik'e cike da isa ya k'araso gaban ta cikin murya mai dad'in sauraro yace, "Kuma me? k'arasa mana ya kika yi shiru shugaban masu rashin kunya."

Bata kula shi ba sai k'ara juyar da fuska da tayi tana hararar gefe d'aya.

Cize baki yayi cike da kosawa ya koma ya zauna Dan yar maganar nan da yayi har kansa ya fara juyawa, cike da rashin kunya ta k'ara cewa, "koma dai meye nidai bazan aure ka ba sabida bana son ka ina da Wanda nake so."

Lumshe ido yayi ya jinginar da kansa a jikin kujera tare da fad'in, really? "Nima ai ba son naki nake ba an fad'a miki kina daga cikin irin matan da nake so? Kawai dai zan bi umarnin iyayen mu ne na kuma taimaka miki before na samo zab'in raina" yana gama fad'a mata haka ya mik'e yana niyar fita ta tsayar dashi da fad'in,

" Never wallahi, Nafi karfin ka taimaka min sai dai ni na taimaka maka kuma ni auran ka din ne bazan yi ba ina da Wanda nake so kuma shi zan aura ni ba kai ba."

Juyowa yayi ya kalle ta yace, see u,"Nima ina da wacce nake so din ai kawai dai umarni ne in ba haka ba me zanyi da yar lukuta kamar ki? Kuma ni ma tabbatar kina sona ga kishi nan ina gani a idon ki dan nace ina da wata."


Zaro manyan idon ta tayi tace, "god forbid Wallahi ni bana son ka balle kishin ka."

Murmushi yayi yace, "okay, indai har kina so na tabbatar shine kar ki sake kice baza ki aure ni ba koda wasa in ba haka ba zargina zai tabbata nasan kuma baza kiso hakan ba, amma indai kika amince babu musu na tabbatar bakya sona taimaka min kika yi, na bar ki lafiya" yana gama fad'a mata haka ya fita daga parlourn cikin takun isa da tak'ama.

Rasa abinda zata yi tayi inda abinda ta tsana a duniya bai wuce a ce mata yar lukuta ba, zama tayi ta fara tunani kenan in ta ki yarda bata aure shi ba kamar yadda yace kenan zaice tana sonsa shikenan mutuncin ta ya kara zubewa a idon sa, In kuma ta amince ta yaya zata iya zama dashi da wannan halin nasa na miskilancin tsiya ita tayi mamakin ma yadda yayi doguwar magana a lokacin infact ma bata son sa ko babu halin sa ma tana da Wanda take so, ajiyar zuciya tayi a fili tace, "Dole na samo mafita" ta mik'e itama ta fita daga parlourn ta nufi nasu part din.


Topah ya kuke ganin Wannan Labari zai kasance? Amatullah zata amince sa sharadin Ammar kuwa.?