7&8
by @realeshaa
*KISHIYA KO BAIWA???*
_(TRUE LIFE STORY)_
*NA MARUBUCIYA*
*REAL ESHAA ~*
*WATTPAD* _Realeshaa_
*_Ya Allah ubangiji kajikan mahaifina ya Allah kagafar tamasa kurakurensa ya Allah kakai haske kabarinsa ya Allah kajikan dukkan musulman dasuka rigamu gidan gaskiya ya Allah kasa innamu yazo mucika da imani_*
*PAGE 7&8*🖌️
________________________📖Dasauri tatura wayar 'kar'kashin pillow tana kakalo murmushin dole"wuceta yayi batare dayace komai ba ya kwanta agefenta tare da lumshe idanunsa, matsowa kusa dashi tayi tadaura kanta afaffa'dan 'kirjinsa tare da sanya hannu tashafo sashen fuskarsa,cikin yanayi na damuwa tace dan Allah honey ka kwantar da hankalinka wlh bana kaunar ganin ka acikin damuwa bawai nabaka record din nan dankashiga damuwa bane a'a sedan kasan cewa Sukainat da kawayenta basa sona hasalima sede su 'kuntatawa rayuwa ta dubi irin zagin da kawarta keyimin wai hadda kirana jahila,!wai nice jahila?,takara mai maitawa hawaye nazuba daga idanunta.
Lumshe ido Ahmad yayi yanajin kukanta har cikin ransa,hakika beta 'ba danasanin yin wannan auren ba se yau"dayasan haka Sukainat take tunfarko to tabbas babu abinda zesanyashi cewa ze aureta bare harta dunga tozarta masa mata tana aibuntata"da dayanda ze gujewa wannan auren da babu shakka yaguje masa domin baze jure cin mutunci ba, sede kash!!bakin alkalami yariga da yabushe"Saide yayi alkawarin daukar tsatsauran mataki Wanda se sunyi dana sani daga ita har 'kawartata.
Kiyi hakuri nine sanadin janyo miki haka anma ki kwantar da hankalinki insha Allah zandau mataki dabasuyi zatoba"dasauri ta dago kanta dansan jin wani irin mataki ze dauka,!Cikin kissa da son jin abinda zece tace Honey nikawai kayi hakuri base kadau matakin komai ba tunda de kaga lokaci yakure Kuma kaga za'aceni ni nake shiga tsakanin ku,kuma wani irin mataki ma zaka dauka akai?,karkidamu ki kwanta ni nasan matakin da zandauka akai insha Allah"kwanciya tayi badan tasoba,anma taso ace cewa yayi yafasa auren ma baki daya"Rungumeta yayi dahaka bacci yayi awun gaba dasu,
Kowa da tunanin dake aransa musamman ma Nadiya da kishin mijinta ya addabi zuciyar ta ganin daga gobe yabar mallakinta ita ka'dai yakoma su biyu,yayinda Ahmad zuciyar sa kesake tabbbatar masa da hukuncin da yayanke shine daidai....
******
Makil cikin Gidan yake da al'ummah tako wanne lungu da sako mutane ne suke hidindimu Cike da farin ciki,baki daya Gidan yakaure da hayaniya masu aiki nayi masu surutu nayi sede fuskar kowa bayyane yake da farin ciki dakuma jin dadi wannan auren daza'ayi domin Sukainat nada shiga ran jama'a saboda kyawawan halayyarta"hakan yasa tayi jama'a sosai duk dakuwa kasancewar ita bame magana bace....
Babban masallacin juma'ar dake bayan federal sectaria na Jahar Bauchi, Cike yake makil da al'ummah babu ko masaka tsinke,Daga cikin masallaci najiyo 'daurin auren Ahmad Isma'il Ahmad"da Amaryarsa Sukainat Ahmad waziri"abisa sadaki naira dubu 'dari al'ummah suka shaida.
Daga can gefe Ahmad da Isa ne tsaye cikin wasu fararen gezna masu kyan gaske anyi musu dinkin babbar riga da yar ciki,bakaramin kyau Ahmad yayi ba tamkar kasace shi kagudu fuskarsa tamkar gonar auduga danfarin ciki da murna" 'yan uwa da abokan arziki se Allah sanya alkhairi suke yimasa dakuma Allah yabada ikon rikewa, Cike da farin ciki yake amsawa.....
****
Haba, haba, Nadiya wai dan Allah kukan nan be isa haka bane?, wannan ma aise kisa ayi mana dariya sekace akanki akafara kishiya?,duk kibi kitashi hankalinki da koke koke da me wannan yarinyar tafiki?karfa ki manta Ahmad atafin hannunki yake se yanda kikaga damar juyasa, tomeye abin tashin hankali da damuwa aciki? dan kinji andaura auren,dubi yanda duk kika bata kwalliyarki"dan Allah kigoge hawayen ki kafin munafukai suzo susami abin ya'dawa...hannu tasanya ta goge hawayen tare dacewa wlh bakomai keyimin ciwo ba hema se idan natuna wai zamu raba Ahmad da wata wannan Abu yana kona min zuciya ni Ahmad zerabawa kwana dawata ayau"tsaki Hema taja tace haba Nadiya sekace bakisan kankiba ko kuma bakisan waye Ahmed ba?, kisa aranki cewa *BAIWA* za akawo miki cikin gidanki ba *KISHIYABA* dan haka ki kwantar kitashi kije ki wanke fuskarki kizo asakeyi miki make-up kinuna musu cewa auren beda mikiba"sake share hawayen tayi tace taya kike tunanin zan Iya nunawa bedameni ba bayan kuma kinsan nafi kowa shiga tashin hankali da dimuwa akan wannan auren..
'Daure fuska Hema tayi tace tunda bazaki yiba shikenan kije kiyi duk abinda ki kaga dama.dasauri Nadiya tamike ta shiga cikin toilet sake wanka tayi tazo aka tsantsara mata make-up Cikin wasu rantsatsun kaya tashirya masu kyau da daukar hankalin me kallansu,hannu ta hema tarike sukazo Cikin compound din gida"manya manyam woofer da speaker suka kunna inda suka sanya wakar Burna boy,me taken any body,rawa suka dinga tika daga wannan wakar yakare se sukoma wancan tamkar basu da matsala kaya kuwa tacanza sunfi kala goma acewarta batason reni dole ta nuna wa makiyanta tafi karfinsu....
****
Bayan anwatse daga wajen taron 'daurin auren ne Ahmad yanufi wajen Malam Ahmadu wato mahaifin Sukainat shida Isa,Malam Ahmadu yana hango nufowar Ahmad wajen sa seya fita daga cikin taron mutanen dayake ya tunkarosa"Har kasa Ahmad da Isa suka tsugunna tare dagaisheda Malam Ahmadu,Cike da fara'a Malam Ahmadu ya amsa fuskarsa bayyane da yalwataccen murmushi,shiru Ahmad yayi nawasu mintuna kana daga bisani yace baba daman ina Neman alfarmane?,wace irin alfarma kake nema Ahmadu??Yatambayeshi yana kara murmushin fuskarsa"sajen fuskarsa yashafa,Wannan yana daya daga Cikin dabi'un Ahmad shafa sajensa aduk sanda yake magana ". yace daman banason tarone dawasu bidi'o'i hakan yasa nace anjima da daddare zanzo indauki matata base ankaika ba idan babu matsala yin hakan yafada kansa a'kasa.
Shiru Malam Ahmadu yayi kana daga bisani yace bakomai Ahmadu ai matar kace duk shawaran daka yanke yayi kuma wannan ma shawarace me kyau"Baki ya washe yace mungode baba ubangiji Allah yakara girma"ameen malam Ahmadu ya amsa tare da cewa da misalin karfe nawa zakazo Daukarta?,karfe 9:00 insha Allah zanzo"
toh Allah yakaimu, ameen suka amsa sannan sukayi masa sallama sukatafi.....Bayan sunshiga mota Isa yamaida kallon sa ga Ahmad Cike da kulawa yace Ahmad meyesa kayi haka taya zakace bazasuyi taro ba kuma bakasanar musuba se yanzu zakafadawa mahaifinta?.
Hakan shine dede domin Sukainat batada tunani batasan meson ta dagaskiya ba irin yanda Nadiya kenuna mata kauna aibata cancanci wulakanci awajenta ba,anma sekaji irin zagin cin mutuncin da Sukamata itada kawayenta,yakarashe Cike da takaicin abin"Kai Isa ya jinjina yace anma hakan dakayi bashine mafita ba tunda tunfarko baka fada musuba,sannan kasan mata da kishi baka tunanin plan Nadiya tashiryawa Sukainat "Aharzu'ke yadaga masa hannu yace ya isheka haka taya kakeson daurawa Nadiya laifi bayan kasan kokadan batada fitina.Kai Isa yajinjina akaro na biyu yace da alama haryanzu Ahmad ba kasan mata ba kaidinsu da sharrinsu yawuce inde kake tunani danhaka kabi Ahankali. Shiru Ahmad yayi bece komai ba dan kalaman Isa bakaramin bata masa rai sukayi ba,Shima Isa tsuke bakinsa yayi dan yalura sam Ahmad besan lefin matarsa"dahaka suka Isa Gidan Isa batare dakowa yace da dan uwansa komai ba...
Wani irin kyau Sukainat tayi naban mamaki tamkar kasaceta kagudu sanye take cikin wani golden din material me masifar kyau Wanda yayi matukar amsar fatar jikinta, yayinda aka kawata fuskarta da make up meban sha'awa duk Wanda yakalleta yaga Amarya,aunty Aliyah da sauran mutane seyaba kyawun datayi suke,Sofi'a ma bakaramin kyau tayiba,kowa kagani acikin Gidan masha Allah...
Lokacin da Malam Ahmadu yasanarwa da Ummi cewar Ahmad da kansa zezo daukar matarsa bata nuna damuwar komai ba sema fatan alkhairi datayimu su.Murmushi Malam Ahmadu yayi yace seki fadawa 'yan uwa da abokan arziki,dan masu tafiya sutafi kar sutsaya jira....Kamar yanda Malam Ahmadu yafada haka Ummi tamayar ma aminanta dakuma yan uwanta,Rai abace Aunty Aliyah tace anma wannan airenin hankaline Yaya tayaya baze fada da wuriba harseda lokaci yakure,a gaskiya wannan yaron akwai gyara acikin al amuransa taya zedinga yiwa mutane ra'ayi da gadara sekace....Hannu Ummi ta daga mata cikin taushin lafazi tace in banda abin ki Aliyah menene abin tashin hankalin aciki a yanzu Ahmad yafimu iko da Sukainat kinga kuwa in haka ne! yana damar yanke duk hukunci daya so akanta,Dan Allah kibar maganan,'daya daga cikin Aminan Ummi ne wato mahaifiyar Sofi'a me suna Hjy Amina tace"hakane Aliyah kibar maganan kawai.Kallon ta Ummi tayi tace yanzu kitashi kuje Gidan kiduba duk abinda beyiba se kugyara"mikewa Aunty Aliyah tayi suda wasu kawayen Ummi suhudu suka tafi Gidan Ahmad...
Tunda suka shiga compound din gidan sukajin kida natashi kamar ze tsaga gidan,tsaki Aunty Aliyah taja aranta tace lalle wannan yacika Mara mutunci wato yabar matarsa tayi abinda taga dama can kuma yahana ayi taro saboda rainin hankali dasamun waje irin nasa,wajen tanufa kasancewar sashen Nadiya Dana Sukainat ahade suke corridor kawai ya banban tasu" A?Kanabin Corridor zesadaka dasashen nasu"Tsayawa sauran matan sukayi suna gaishesu anma daga Nadiya har kawayen ta basu San Allah yayi tsiron hallittarsuba,aunty Aliyah kuwa takaici ne yacikata dan haka batace komai ba tayi wufewarta direct sashen Sukainat,danyi abinda yakawo su.Harsukayi aikin suka gama ko ruwa ba akawo musuba bare kuma abinci,lokacin dasuka fito kawai se Nadiya suka fashe da dariya tare dacewa se ayi mugani intusa zehura wuta"kojuyawa Aunty Aliyah basu yi ba bare sukanta musu...koda Aunty aliyah suka koma gida direct dakin Ummi ta shiga inde tasame ta da aminiyarta wato mahaifiyar Sofi'a, Rai abace aunty Aliyah tace agaskiya yaya wannan matar Ahmad din ba yar mutunci bace..kai Ummi tadafe tace Aliyah rayuwar nanfa hakuri akedashi dan Allah kibar wannan maganan banason abin fitina ki kyaleta duk abinda tayi kanta tayiwa"Shiru Aunty Aliyah tayi domin baki 'daya hakurin Ummi Sukainat ta'dibo...
Da daddare kamar yanda Ahmad yafada misalin karfe 9:00pm yazo daukar matarsa,lokacin duk anwatse se 'yan uwa dakuma bakin dasukazo daga nesa suka rage.
A parlour Malam Ahmadu aka sauki Ahmad badadewa aka kawo Sukainat daketa kuka"Da Addu'a Malam Ahmadu yabude taron sannan yafara yimusu nasiyya meratsa jiki bayan yagamane Ummi da Hjy Amina sukayi musu nasu nasiyyar meratsa jiki" aunty Aliyah ce karshe cikin yanayin ta na zafi tace toh Ahmad ga amanar Sukainat munbaka ita karkaci amanarta ko kuma kazalunceta kasane muddin kazalunceta Allah baze barka ba domin Sukainat nitsatstiyar yarinyace munsan da ikon Allah bazata bamu kunya ba sannan kazamto me adalci a tsakanin matanka kada kazalunci kodaya acikinsu...Cike da ladabi yace insha Allah zakusameni me rikon amana zan kula daita dakuma tarbiyanta,mikewa Malam Ahmadu yayi yarike hannunta sannan yariko na Ahmad yace kuje Allah yabaku zaman lafiya medaurewa" 'kan'kame hannun Malam Ahmadu Sukainat tayi tafashe dakuka metsuma zuciya cikin muryan kuka tace dan Allah Abba karku bari yatafi dani ninafasa auren banason rabuwa daku,Rarrashinta Malam Ahmadu yayi tayi da 'kyar akasamu akafita da ita akasanya ta amota tawani irin kuka metsuma zuciya.....
YANZU AKAFARA LABARIN
_VOTE_ ✅
_COMMENTS_
*And*
_SHARE_
*_ESHAA CE~_*🤙