SHU'UMA

E9

by @shaabandaughter01

*SHU'UMA*


_'Yar mutan zazzau Naanarh M Sha'aban_


*Sadaukarwa ga Yaayana d'an baiwa đŸ„°*


_Wannan page d'in na ku ne Khadija Shu'uma team😂ku ji dad'inkuđŸ˜‚đŸ˜†â™„ïž_


*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*


_Ku sauke arewabooks a playstore kamar yadda ake bud'e account a wattpad haka ake bud'e shi, masu iPhone ku shiga ta website ku bud'e account, book 2 chan zamu koma posting._


Website

http://Arewabooks.com


Kuyi following d'ina.

http://arewabooks.com/u/shaabandaughter01


Book 1

E9


Adam ya kid'ime ya d'ago ya kalli mahaifinnasa jikinsa na rawa, bakinsa na karkarwa ya fara k'ok'arin magana, Baffa ya dakatar dashi da cewa "ba na buk'atar ka ce komai na gama magana, ku tashi ku je ku cigaba da shirin biki, D'alhat ya kama hannun d'an uwannasa suka fita daga bukkar jikinsu duk a sanyaye, tun da suka fito D'alhat yake faman rarrashin Adam, amman ina Adam hankalinsa gabad'aya a tashe yake, ranar wuni sukayi zuciyoyinsu a k'untace, D'alhat kuwa yafi ma Adam d'in damuwa saboda gani yake duk ta dalilinsa d'an uwansa yake cikin k'unci dan da ace bai bijiro da maganar aurensa ba, da Baffa ba zai yi wa Adam d'in auren dole ba, shawara ya yanke a zuciyarsa akan ya janye maganar aurensa dan Baffa ya hak'ura da yi wa Adam auren dole, idan yaso duk lokacin da Adam d'in yake son aure sai su yi tare, da wannan shawarar ya kwanta dan ya san lokacin Baffa ya dad'e da bacci da zuwa zai yi ya sameshi, daga D'alhat har Adam babu wanda ya iya rintsawa ranar, da sassafe D'alhat ya tashi ya tafi gurin Baffa, a tsakar gida ya sami Baffan yana zaune yana shan fura, har k'asa ya tsugunna ya gaisheshi, Baffa ya amsa fuskarsa kunshe da fara'a, zama yayi akan takalminsa, yayi shiru na d'an wasu lokaci kafin ya d'ago ya fara magana "Baffa ina so a fasa aurin aurena, ba na son yin aure yanzu" A daidai lokacin Adam ya fito daga d'aki ya ji abinda D'alhat yace, tsayawa yayi ya kasa motsawa daga inda yake, dan maganar d'an uwansa ba k'aramin dukanshi tayi ba, Baffa cike da mamaki yace "Me ka ke cewa ne? kai fa ka nuna ka na son aure yanzu kuma kace ka janye, anya ka na da hankali kuwa D'alhatu?'',"Na san duk saboda ni ka ke k'ok'arin janye aurenka, ba zan tab'a jin dad'i ace an fasa aurenka duk ta dalilina" Adam ya fad'a tare da k'arasawa inda D'alhat d'in yake zaune, "k'anina nima zan so ace anyi aurenmu tare" D'alhat ya juyo yace "Yayana nasan ba ka son auren da za ayi maka, shiyasa nima zan hak'ura da auren duk lokacin da ka ji ka na son auren ma yi tare" Adam ya zauna tare da kallon Baffa yace "Baffa Ina cike da farin cikin zab'in da ka yi min, na ji dad'i har cikin raina zamuyi aure tare da d'an uwana" Baffa yayi ta shi musu albarka, suka tashi suka shiga shirye-shiryen d'aurin aure.

Wajen k'arfe 12 na rana aka daura auren Adam da D'alhat, haka su ka cigaba da yin shagulgulan bikin, gabad'aya garin kamar ya hargitse da yin biki kamshi ne kawai yake tashi ta ko ina a fad'in garin, da daddare aka kai amare gidajensu da Baffa ya gina musu.

Haka suka cigaba da yin rayuwar sau cikin farin ciki da annashuwa, Adam ya koma makaranta ya bar Safara’u bayan yayi mata alk’awarin duk sati zai dinga zuwa ya koma ranar litinin da asuba, sannan ta yarda amman da ta nuna sam ta k’i yarda ya tafi.

Kwanci tashi ba wuya wajen Allah, Ladidi ta fara laulayin ciki ita da Safara, da yake ita Safara cikinnata mai wahala ne duk abinda ta ci sai ta yi amanshi, dan haka Adam ya tattaro ya dawo gida da zummar idan ta ji sauk’i sai ya koma, duk gari ya karade da maganar cikinsu Ladidi, wasu har lissafi suke yi sauran wata nawa su haihu, dan sun san za’a sha shagali k’ila ma har kyaututtuka mai gari zai yi saboda Ladidi ita kad’ai ce ‘yarsa kuma yana k’aunarta sosai. Adam sai da yayi wata biyu a gida ya tabbatar Safara ta fara samun sauk’i sannan ya koma makaranta.


Lokacin da cikin ya cika wata tara da ‘yan kwanaki aka shiga shirye-shiryen bikin haihuwarsu, A ranar wata Alhamis Ladidi ta haifi samtalelen d’anta mai kama da ubansa a gida, da yake haihuwar ta zo mata da sauk’i murna wajen Adam da Dalhat abin ba’a magana, wuni aka yi ranar ana kid’an garaya a garin, kamar ranar ne suna.

Washe gari wajen k’arfe 10 na safe, Safara ita ma ta haifi d’anta namiji sak kamarsa d’aya da Adam, Dalhat ya rasa inda zai sanya ransu shi da Adam, Ladidi ma tayi murna sosai da ta ji Sarafa ita ma namiji ta haifa.

Ranar suna anyi b’arin naira yara sun ci sunan kakanninsu, D’an D’alhat aka saka masa sunan mai gari Abubakar suna ce masa Baba, inda D’an Adam aka saka masa sunan Baffa Nazeer ake ce masa Papa ko Baffa, yaran sun ta so cikin gata da soyayyar iyayensu, gashi kansu a had’e, sunyi koyi da iyayensu dan komai tare ake musu, kullum yaran suna gidan mai gari sai da daddare ake dawo da su.


Lokacin da su Nazeer suka cika shekara tara Adam ya saka su a boko da arabiyya, dan yana da burin ya ga yaran sun jik’u da karatun boko da arabiyya, Dalhat yayi farin ciki sosai, dan kuwa shima yana da burin ya ga d’ansa yana zuwa makarantar boko dan kuwa yana ganin amfanin da take dashi tunda ga d’ansa babu abinda bai iya ba rubutu da karatun nasara duk ya iya, Abubakar suna da shekara goma su Ladidi ta sami ciki, a wannan karan ta sha bak’ar wahala domin kuwa har cikin ya cika watan haihuwarsa yana wahalar da ita, ranar wata Lahadi ta haihu ‘yarta mace zankad’ed’iya mai kama da mamanta, tun a lokacin mai gari ya rok’i D’alhat alfarma akan ya saka sunan mahaifiyarsa “Khadija” D’alhat duk da cewa ya so ya saka sunan Inna, amman tunda har mai gari da kanshi ya rok’i alfarmar nan ba zai tab’a k’i ba, dan haka ya amince kuma ya rad’awa yarinyar suna Khadija, Ladidi ta ji dad’i sosai dan kuwa tana tsananin k’aunar kakarta sai kuma ta mutu a lokacin da take bukatarta sai gashi mijinta ya faranta mata rai ta ji dad’i sosai, ranar suna anyi suna an watse cike da farin ciki, mai gari ya raba kyaututtuka da dama, dan rago da shanu biyu aka yanka, lokacin da Khadija ta cika wata bakwai Adam ya kammala makarantarsa ta gaba da sakandari inda ya karanci Medicine, yana k’ok’arin had’a kayansa ya dawo k’auye wani abokinsa ya nemar masa aiki a wani babban Asibiti da ke garin Kaduna, Adam yayi murna sosai kuma ya ji dad’i, a ranar ya je gida yake sanarwa Baffa da Inna ya samu aiki, Kuma idan zai koma zai tafi da Safara idan yaso ya kama musu gida a chan, da Inna ta so ta k’i Baffa ya hanata, haka ta hak’ura amman kuma da sharad’in ba za su tafi da Nazeer ba, Adam ya amince da sharad’inta, lokacin da D’alhat ya ji zancen Adam zai koma da iyalinsa Birni ya ji ba dad’i amman da ya ji ance banda Nazeer zasu koma sai ya ji dad’i sosai dan yana son Nazeer sosai.


Haka Safara ta had’a kayanta bayan ta je ta yi sallama da iyayenta ta biya ta yi wa Ladidi sallama washegari suka d’auki hanyar Kaduna, suna isa da yake Adam ya bugawa Abokinsa waya ya fad’a masa yana son gida na haya, amman mara tsada, a ranar ya nemo musu gida ya biya, gidan kuwa yayi kyau, Adam sai ya ba gidan yake, Safara ma ta ga kyan gidan sosai.


Bayan Shekara d’aya

Khadija ta girma sosai, dan idan kika ganta ma, aka ce miki shakararta d’aya da ‘yan watanni ba za’a yarda ba, dan kuwa za’ayi tunanin shekararta uku, tun a wannan lokacin Khadija ta fara rashin ji, idan Mamanta tayi girki ta rufeshi, zata d’ibi k’asa ta zuba a ciki, ko kuma idan miya ce ta d’auki gishiri duk yawanshi haka zata zuyeshi, babu irin dukan da bata sha ba gurin mahaifiyarta, amman kullum kamar tinzirata ake, bata dai na wa ko yaushe da irin tsiyar da zatayi, akwai wata rana Nazeer da Adam suna bacci, ta d’auki dakakken yaji ta jik’a a kofi ta zuba musu a fuska, sun sha azaba sosai, ita kuma ranar ta ci dukan tsiya dan kuwa mahaifiyarta da carb ita zaneta, Abbakar ma bayan sun wanke idonsu yayi mata dukan tsiya, ta sha kuka ta fita waje, gidan mai gari ta je ta kai k’ararsu, har gida ya zo da ita, yana ta fad’a akan me za’a daketa, su ka fad’a masa abinda ta yi, anan fa ya fara masifa ai ba wani abu tayi mai muni ba, da za su yi mata wannan dukan mutuwa, juyawa yayi ya koma da ita sai da tayi sati d’aya a gidan sannan ta addabeshi da kuka ita gida zata koma gurin Innarta, haka ya dawo da ita bayan ya kora musu gargad’in kar su sake dukanta.

Suna shiga gida, ta ga Nazeer yana cin abinci ta je ta zauna a cikin kwanon abincin, Inna ta fisgota ta murd’e mata kunne ta rankwasheta, “ke wato kunnan k’ashi ne da ke, kin na so ki zama shaid’aniya ne, kullum cikin sakani magana kike, to tunda kin zama mai kunnan k’ashi ni kuma ba zan fasa dukan ki ba dan uwarki” juyawa tayi tana kallon Nazeer wanda ya d’aure fuska yana yi wa Khadija kallon k’iyayya tace “yi hak’uri ka ji yarona ka je ka zuba wani abin cin” mik’ewa yayi tare da cewa “to Inna” Kullum Khadija tantirancinta k’ara cigaba yake, a lokacin da Khadija ta kai shekara goma, su Abbakar suka gama makarantar gaba da sakandari, inda Nazeer ya karanci Accounting Abubakar kuma ya karanci Law, Adam ya samar musu aiki a garin Kaduna, suka koma chan anan ne Nazeer ya had’u da abokai b’ata gari suka koya masa shaye-shaye da kuma neman mata, har ya kai ga tun yanayi a b’oye iyayensa suka sani, ransu ya b’aci sosai ganin d’annasu k’walli d’aya yana k’ok’arin zama tantiri, wannan dalilin ne yasa Adam ya yanke shawarar had’a Nazeer da Khadija aure ko zasu samu ya nutsu.


A cikin satin Adam ya je k’auye ya sanar da danginnasa, akan had’in da yake so ayi musu, D’alhat ya ji dad’i dan kuwa daman yana da niyyar yi wa Khadija aure dan kuwa wannan maganganun da take ja masa a gari, yana ganin idan yayi mata auren zata nutsu duk da kuwa k’arancin shekarunta, D’alhat ya nunawa d’an uwannasa amincewarsa d’ari bisa d’ari, dan kuwa ce masa yayi idan da hali ma a d’aura auren a yau idan yaso gobe a kai amarya d’akinta, Adam ya ji dad’i sosai yadda d’an uwannasa ya amince da buk’atarsa, kamar yadda D’alhat ya buk’ata a ranar aka d’aura aure, da yake yanxu Adam yana samun kud’i sosai, shine babbar likita a garin Kaduna, ya gina babban gidansa, Khadija kuwa tunda ta ji an d’aura mata aure da Nazeer take fushi dan ko abinci ta k’i ci, zaune suke ita da Innarta akan taburma “wai Inna ni da wannan mugun aka had’a ni aure, ni gaskia ba na sonshi” Juyowa tayi tana kallonta tayi dariya “au bakya sonsa, to ka da Allah yasa ki so sa mana, kuma wallahi zan kirasa na fad’a masa idan ki ka yi abinda ba daidai ba ya ci ubanki, ya soma min ke har sai kin yi hankali” Khadija tace “Chab ni d’in zai duka? Inna kin manta wacece ni, wallahi ni Khadija na ci dubu, tunda na addabi kowa to shima addabarsa zanyi, shi da kansa ma ai kin ji sunan da yake kirana kuma ‘yan gari suke kirana dashi su ma SHU’UMA” Inna tace “yaro bai san wuta ba sai ya taka, tunda ke SHU’UMA ce to ni kuma zan sa shi ya zama SHU’UMI sai mu ga k’aryar iskanci” Daria Khadija tayi ta shige d’akinta” Inna ta bi ta da kallo tana yi mata addu’a Allah ya shiryeta.

Washe gari da sassafe aka had’a kayan Khadija ta je ta yi wa kakanninta sallama mai gari har da kuka, ita ma Khadija kukan ta shiga yi, haka Adam ya kama hannunta suka tafi zuwa Tasha suna isa suka ga ana lodin motar Kaduna suka shiga, driver ya ja mota suka tafi, awa hud’u sukayi a hanya kafin suka isa garin Kaduna, suka sauka daga motar bayan ya biyashi kud’insa, adaidaita suka nema inda ya kai su har k’ofar gida.

Shiga gidan suka yi, hannun Khadija yana cikin na Adam, a babban falon gidan suka tarar da su, da yake daman sun san maganar auren Nazeer ne ya kai shi k’auye amman ba su san da Khadija za’a had’a shi ba, “Sannu da zuwa yarinyata” Khadija ta tafi da gudu ta rumgume Safara tana fad’in “Mommyna ta birni” Abubakar yace “ke kin shak’e mata wuya karki illata mana Mummy” d’agowa tayi ta maka masa uwar harara har da murgud’a baki, “kan uba ni za ki yi wa rashin kunya, billahillazi tattaka ki zanyi anan” Abba yace “kul karka kuskura Abbakar” Komar da kallonsa yayi kan Nazeer wanda ya duk’ufa yana daddana waya “Nazeer ga matarka nan, na ba ka amana, ba na son na ji ta kawo min k’ararka, ka kula da ita, za ku fara zama a gidannan a wanchan part d’in kafin na siya muku wani gidan” D’agowa Nazeer yayi yana kallon Abba yace “Abba ka na nufin Khadija ce matata?” Abba yace “kwarai kuma” Nazeer yace “Abba! Khadija fa bata da kirki wannan yarinyar SHU’UMA ce, kuma bata da wasu shekaru bata dad’e da cika shekara sha d’aya ba” Abba yace “ko da shekararta Tara ne, ita na zab’a maka idan kuma ba za ka bi umarnina ba, sai ka je ka nemi wani uban amman ba ni ba” Nazeer ya kalli Khadija suka had’a ido ta kanne masa ido d’aya tana Murmushin da ita kad’ai ta san ma’anarsa. Abbakar yace “Abba amman bai kamata a aurawa d’an uwana wacce baya so ba, tunda yace akwai wacce yake son aura Fanan da an barsa ya aureta” Abba yace “ai na san ya fad’a min yana da zab’insa amman ni batayi min ba, Khadija na ga tayi min kuma ita na ga damar aura masa” Nazeer yace “to shikenan Abba” yayi maganar tare da shigewa d’akinsa, Mummy tacewa ta tashi ta nuna mata part d’inta, tashi ta yi suka shiga part d’in Mummy ta nuna mata ta fito ta Barta a ciki zatayi wanka.


A cikin satin gomnati ta rabawa manyan likitoci kud’i masu tsoka a ciki kuwa har da Abba, wani babban gida ya siyawa Nazeer da Abbakar sun had’u gidajen sosai, shima Abba ya siyi mota, da yake akwai d’an gyare-gyaren da za’a yi wa gidan dan haka ba su koma ba, sai da aka gama, a cikin satin da za su koma aka yi bikin Abbakar da Fatima ‘yar abokin Abba, sun sha shagali sosai dan a Kaduna aka yi biki su mai gari sun zo.


Khadija da ta ga sun koma gida daga ita sai Nazeer ta ga irin yadda yake neman mata baya jin kunyar shigo da mata har gidan aurenta, dan haka ta shiga Shuka masa rashin mutunci kullum da irin shu’umancin da take yi masa shi da ‘yan matansa.

Wannan shine takaitaccen labarin Khadija da Nazeer.


Cigaba labarin....


*#Share*