2
*📲Tyiping*
*✨DARASI!!✨*
Ummu Maher(Miss green🍀)
02
......yana Gama waya da Matarsa Sakinat ya d'aga wayarsa ya Kara a kunnensa cikin nutsuwa shiru sukayi gaba kidayansu sanin halin Ammar,Amir ya ce"Kai fa haka kake Ammar Amman sai Ka bugowa mutum waya Ka yi shiru"?.
Shirun Ammar ya k'ara yiwa Amininsa Amir Wanda yanzu ya ke a America da Matarsa da yayansa 4,Gajiya Amir yayi sannan ya ce"Ammar lafiya me ya faru?cikin damuwa Amir yake fadar hakan don yana matukar Jin tausayin abokinsa Ammar don ya hadu da shu'umar mata,baiyi tsammani ba yaji Ammar ya ce"so na ke Ka turomin da number Umma"!.
Mamaki da wasu hawaye ne suka Fara zubowa a fuskar Amir, bakinsa yana kakkarwa ya ce"yanzu Ammar number mahaifiyarka karasa acikin wayarka? abin ya daure min Kai".
"Don Allah Amir Ka tausayamin Ka turomin number Umma,na kasance cikin bakin ciki, kwakwalwata tana gab da tarwatsewa kunnuwa na suna yimin kuwwar muryar Umma na,ina San inji Muryar Umma na",sai wasu hawaye masu zafi suka zubo masa.
Kashe wayar Amir ya yi hawaye yana fitowa a idanuwansa ya saka handcachiep dinsa ya goge hawayen da ya zubo masa,ya Danna message ya Nemo number Umma yana kuka ya turawa Ammar number.
Tunda Amir ya kashe wayar Ammar ya tashi tsaye a office dinsa ya buga tebur idanuwansa sukayi jawur sosai kamar garwashi,allurar Soja ta tashi,gashin jikinsa ya Fara mimmik'ewa,ya Rasa abinda yasa duk wata mace in dai ba Sakinat ba,Baya taba ganinta da gashi ciki kuwa harda Mahaifiyarsa wato Umma,wacce take matukar sonshi da k'aunarsa itace ta dauki nauyin karatunsa tun kafin ya Zama wani Abu ta shige mishi a gaba ya zamo abinda ya Zama tun bayan rasuwar Mahaifinsa,yana cikin wannan tunanin Yaji k'arar shigowar sako,da sauri ya dauka yana sharce wata uwar zufar da ta zubo masa,hannunsa yana kakkarwa ya dauka ya duba number Umma ya kirawo Hannunsa sai k'erma ya ke.
Wayar tana hannun Khalisat wato kanwar Ammar,tana Assignment an Kira yafi sau 3 taki dagawa sai tsaki take tana cewa"gaskiya ko waye wannan ya iya nacin jaraba",ta Fadi hakan cikin yaran Fillo wato fulatanci,sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta d'aga cikin dakusasshiyar murya tace"waye"?.
"Common ki kawai wa Umma stupid!".
Da sauri jikinta ya Fara kakkarwa don tabbas ta gane muryar yayanta,hawaye suka Fara zubo mata da sauri ta haye step,tana kwalawa Umma Kira wacce alokacin ta ke sallar duha,wato sallar walaha, Khalisat cikin kuka ta ce Umma ya Yaya Ammar a waya"!.
Lokaci daya Umma taji kanta ya Shiga sarawa sosai,zuciyarta taji tana bugawa ta saka hannunta ta danne saitin zuciyarta daya tsananta buga mata.
Khalisat tasan za'ayi haka Amman sai ta goge hawayenta ta ce"Umma ki daga wayar nan kiji me zaice Miki,ki ajje fushinki a gefe ki janyo danki a jikinki don Allah".
Hannun Umma yana k'erma ta saka hannunta ta amshi wayar,sai dai ta kasa saka wayar a kunnenta.
Yaron da ta keso ta ke k'aunarsa Amman yau an wayi gari ya wofantar da ita,ya guje ta tamkar wata mujiya,idan Bata manta ba yau tsahon shekara 5 rabon da ta saka Ammar a idaniyarta balle har ya bugo mata waya.
Duk abinda a keyi Ammar yana Ji,kuma yana jiyo kukan Amminsa,hankalinsa ya tashi jijiyoyin kansa suka tashi sosai ya dafe kansa yana kuka.
Da sauri Khalisat ta saka wayar a handsfree don Umma taji muryar d'anta sosai,ai kuwa tana saka muryar taji Ammar yana cewa.
"Ammina"!
Sai kuka yaci k'arfin Ammar wani amai ya taho masa,ya ajje wayar ya ringa kwarara amai kamar me yaron ciki,ta cen bangaren Umma tana Jin Ammar ya Fara amai,hankalinta ya tashi ta Fara Kiran sunansa tana cewa"Ammar don Allah Kada Ka saka kanka cikin wani Hali Nima Ka sakani,don Allah kayi magana inji Muryar Ka".
Itama anan kukan yaci k'arfinta ta yarda wayar tana matsanancin Kuka,Khalisat ma hawayen ta ke tana sharewa Umma hawayen sannan tana bubbuga bayan Umman kamar k'aramar yarinya.
Kiran wayar Ammar Khalisat ta ringa yi Amman Bai daga ba,k'arshe ma taji an kashe wayar,hankalinta ya tashi ta Rasa Yadda zatayi gashi,ga Umma ciwon zuciyarta ya tashi da k'er ta Samu ta balli maganinta ta Bata ta Samu bacci,gashi kuma Yaya Ammar shima yana cikin wani Hali.
Kifa kanta tayi tana kuka me tsuma zuciya,tana kuka tana cewa"Anty Sakinat Baki kyauta mana ba kin rabamu da sanyin idaniyarmu,kin raba D'a da uwa,kin raba soyayya me k'arfi,Why me yasa kika yi mana haka?Meye ribarki?".
Nan dai Khalisat ta ringa surutai marasa Kan gado,daga Baya ta tashi ta yi alwala ta Fara sallar Nafila tana kuka tana rokon Allah subhanahu wata'ala ya kawo musu sauki da haske cikin wannan lamarin.
************
"Wallahi Fahima Kada ki sake ki dauki tallannan ki zubarmin da kudi,kika yarda kika zubarmin da kudina ranar saina ci ubanki a Gidanan".
"Na gode"
Na ji muryar Baba ya fito daga ban d'aki ya cigaba da cewa"Fahima Kada ki Dade kina zuwa idan kiga babu ciniki ki dawo".
Cikin sassanyar Murya ta na ce"Insha Allah Baba bazan dad'e ba".
Na dauki tallan na tafi ina tunanin Hali irin na Amma,ita dai zata Samu kud'i babu ruwanta da matsala,ko da hakan yana barazanar lalacewar rayuwar y'ayanta.
Yauma banyi wani cinkin kirki ba na taho gida saboda ƴan garuwar da muke siyarwa duk sun tafi gida don haka yanzu babu ciniki,gaba yana dukan 3 na taho gida don nasan yau Amma Bala'in ta akan babanmu zai ƙare.
Tun daga soro na kejin hayaniyar atika mai kayan gonjo da amma ana ta hira ana shewa,sam ban son matar Ƙwata2 saboda Atika duk wani rashin mutunci itace ta ke koyawa amma shi,ko kallon Atika banyi ba nayi hanyar ɗakinmu tare da yiwa Amma sannu da gida,ko amsamin bata yiba sai kallon kayan tallan kaina ta ke tana hararata,jikina ya hau rawa don idan nayi sa'a ne ma zai tsaya a zagi don nasan har duka sai ta yi.
"Ke zo nan don ƙaniyarki".
da sauri naje har ina haɗa hanya don tsoron Amma na ke ji kamar mala'ikan mutuwa.
"Yanzu ita Atikan itace abin wulaƙantawa a wajenki?idan Adama ƙanwar ubanki ce zakiyi mata haka?tsugunna ki gaisheta kafin inci ubanki la'ada waje don bazan zuba miki ido kina rashin mutuncin da kika dama ba.
"Hmm Amma dama kin ƙeleta yaran yanzu ai sai a hankali ballantana ma idan suka ga sun fara tashen balaga sai kaga abubuwa kala2".
"haba Atika ba tashen balaga ba Allah yasa tashen tsuntsaye ne wallahi ni babu ruwana dukan kawo wuƙa zanyi mata, daman ga haushin ubansu ina fama dashi ayi namiji kamar mai zuciyar karya baya ajje komai sai yawon ƙasan bishiya daga wannan ta tafi ya koma wancan inuwa."
zuciya ta ce naji tana ta tafarfasa kamar zata ƙone don naƙi jinin a zagar min uba abin yana taɓa min zuciyata sosai.
Ina cikin wannan tunanin sai kuwa naji Atika tana cewa"ni wallahi Amma dama birni kika bayar da wannan yarinyar aka kaita aiki da mun huta da ganinta tsogai2 tana yawo a gari.
Saurin ɗago kaina nayi jin maganarta wai a kaini aiki?
*ummu maher ce*
04/05
. . . . . Sakinat aranar ta koma Abuja Don firgici da tsoro,duk hatsabibancin Sakinat tana matuƙar jin tsoron Ammar don shima hatsabibin kanshi ne,wannan asirin da ta yi mishi ma da wani babban jigo ta haɗashi har aka samu abinda a keso.
Har gudawa Sakinat ta yi don ta tsorata da ganin Ammar a Adamawa,to yaushe ma ya dawo ba tare da ya sanar mata ba?kuma me yaje yi Adamawa?abin tambayar ta shine ba dai gidan mahaifiyarsa yaje ba?da sauri ta tashi daga zaunen da ta ke,tana girgiza kai tana cewa"no.no.no ba zai yiyu ba ace yaje wajen mahaifiyarsa ba,don tafi kowa sanin cewa farraƙu ta saka aka yi musu a tsakaninsa da mahaifiyarsa.
Har dare Sakinat tana sukuku gashi ta kira aminiyarta Falmata ringing yafi goma bata ɗaga ba,ƙarshe ma taji an kashe wayar wayar.
"Wato ma kada in dame ta shiyyasa ta kashe wayar ko?shegiya mayya kawai ai nasan tunda ta ce baƙo za tayi to lallai tana cen tare dashi"ta yi wurgi da wayar hankalinta a tashe,ga ta da tarin tambayoyi amman kuma babu mai amsa mata.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Ammar kuwa yana isa Adamawa ya kira Aliyu babban abokinsa mazaunin Adamawa amman wani lokacin yana Abuja Babban gidan da Ammar ya sai mishi,yana kiransa bugu ɗaya ya ɗaga yana tsokanarsa da angon sakinat,"mlm bar wannan tsokanar kana cikin gari ne?kazo zaka yimin jagora wajen AMMI."
"Welldone aboki na ina yiwa Allah godiya da ya karkato da hankalinka akan mahaifiyarka,insha Allah yanzu zanzo.
Sai da Ammar ya jira yazo sannan suka tafi suna ta hirarsu ta abokai,daman su uku suka tashi Amir,Ammar,sai Aliyu,ana kiransu da first A.
Khalisat tana tafe tana bitar karatunta na hadda alokacin ta fito kenan za taje islamiyya,sauri ja da baya ta yi don ganin motoci kala sunfi goma a bakin gate Ɗin gidan kana ganin motocin ba sai an gaya maka ba kasan sun haɗu sosai.
Aliyu ne ya fara fitowa yana kallonta cikin murmushi,itama murmushin ta mayar masa tana sake kallon motocin gabanta yana faɗuwa.
Ƙafar sa ya fara sakowa kafin ya fito,da sauri Khalisat ta ja da baya kamar za ta faɗi badon tsohuwar motar Ammi ta tare ta ba da tuni ta faɗi.
Ya.ya.ya.ya.sai kuma ta zunduma da gudu ta yi cikin gida tana kiran Ammi!ammi!!Ki fito kiga wani abu,kafin ta gama rufe bakinta tuni Ammar ya shigo shi da amininsa Aliyu.
Kusan daskarewa Ammi ta yi a tsaye tana kiran sunan Allah tare da godewa Allah daya dawo mata da farin cikinta wato ɗanta Ammar.
Da gudu ya rungume Amminsa yana kuka yana kiran"ilove u my Ammi na ki yafe min don Allah,na tuba bazan sake ba ya haɗa hannayensa alamar neman yafiya.
Ita ma kukan ta ke tana "son na yafe maka Allah na gode maka da ka dawo min da farin cikin raina".
aranar waɗannan Familyn suna cikin farin ciki sosai,ya yiwa Ammi alƙawarin sai ya yi sati biyu kafin ya koma don ya samu hutu,sosai Ammi taji daɗi tana ƙara saka mishi albarka,don tasan duk abinda ya yi ba da sanin sa bane asiri ne.
Tunda Ammar yaje bai kira Sakina ba,hankalinta ya tashi sosai ta dinga kiransa a waya amman yana gani yaƙi ɗaukar wayar ƙarshe ma ya kashe wayar.
Suna zaune da daddare suna cin abinci Khalisat ta kalli yayanta,ta ɗauki ruwa ta fara sha ai Ammar yana ganinta ya yi saurin ƙwacewa yana ce wa"inye lallai Khalisat kin samu sarari yanzu ruwa ki ke sha kina cin abinci?.
"Wallahi Yaya" ranƙwashi Ammar ya kai mata yana ce wa"me ɗan ƙaramin baki kawai.
Murmushi Ammi ta yi tana kallon ƴaƴan na ta cikin so da Ƙaunar su,tana roƙon Allah ya bar maya ƴaƴanta guda biyu da ta mallaka a duniya.
*** *** ***
Amma ta ƙara matsamin sosai yanzu don talla na ya ƙaru yanzu inyi na safe inyi na rana inyi na dare,bani da lokacin hutu Baba na babu yadda zaiyi don yanzu ma har ya fara shiru da bakinsa,tunda ita dai amma ba dai na wa za ta yi ba,don haka ya tattara ta ya watsar da ita don rashin kunyar da ta ke mishi abin yana damunsa.
Ni daman ba a zancen arabi ballan tana boko kullum ina yawo a gari gayyar talla.
Rannan da daddare ina tafe tsoro fal a ciki na don ban taɓa yin dare irin na yau ba,don nasan idan na koma gida sai Amma ta yi gunduwa2 dani.
Wani kango nazo wucewa naji wari kamar nawiwi,na toshe hancina ina kakarin amai,kawai sai naji wani yana ce wa"kai Ba-ba waccen yarinyar me ta ke toshewa hanci ne?".
"oho bari muje muji me ta ke toshewa hanci. . . ...
Anan zan tsaya don rashin comments.
*Miss green ce*