4&5
*📲Tyiping*
*✨DARASI!!✨*
Ummu Maher(Miss green🍀)
04/05
. . . . . Sakinat aranar ta koma Abuja Don firgici da tsoro,duk hatsabibancin Sakinat tana matuƙar jin tsoron Ammar don shima hatsabibin kanshi ne,wannan asirin da ta yi mishi ma da wani babban jigo ta haɗashi har aka samu abinda a keso.
Har gudawa Sakinat ta yi don ta tsorata da ganin Ammar a Adamawa,to yaushe ma ya dawo ba tare da ya sanar mata ba?kuma me yaje yi Adamawa?abin tambayar ta shine ba dai gidan mahaifiyarsa yaje ba?da sauri ta tashi daga zaunen da ta ke,tana girgiza kai tana cewa"no.no.no ba zai yiyu ba ace yaje wajen mahaifiyarsa ba,don tafi kowa sanin cewa farraƙu ta saka aka yi musu a tsakaninsa da mahaifiyarsa.
Har dare Sakinat tana sukuku gashi ta kira aminiyarta Falmata ringing yafi goma bata ɗaga ba,ƙarshe ma taji an kashe wayar wayar.
"Wato ma kada in dame ta shiyyasa ta kashe wayar ko?shegiya mayya kawai ai nasan tunda ta ce baƙo za tayi to lallai tana cen tare dashi"ta yi wurgi da wayar hankalinta a tashe,ga ta da tarin tambayoyi amman kuma babu mai amsa mata.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.
Ammar kuwa yana isa Adamawa ya kira Aliyu babban abokinsa mazaunin Adamawa amman wani lokacin yana Abuja Babban gidan da Ammar ya sai mishi,yana kiransa bugu ɗaya ya ɗaga yana tsokanarsa da angon sakinat,"mlm bar wannan tsokanar kana cikin gari ne?kazo zaka yimin jagora wajen AMMI."
"Welldone aboki na ina yiwa Allah godiya da ya karkato da hankalinka akan mahaifiyarka,insha Allah yanzu zanzo.
Sai da Ammar ya jira yazo sannan suka tafi suna ta hirarsu ta abokai,daman su uku suka tashi Amir,Ammar,sai Aliyu,ana kiransu da first A.
Khalisat tana tafe tana bitar karatunta na hadda alokacin ta fito kenan za taje islamiyya,sauri ja da baya ta yi don ganin motoci kala sunfi goma a bakin gate Ɗin gidan kana ganin motocin ba sai an gaya maka ba kasan sun haɗu sosai.
Aliyu ne ya fara fitowa yana kallonta cikin murmushi,itama murmushin ta mayar masa tana sake kallon motocin gabanta yana faɗuwa.
Ƙafar sa ya fara sakowa kafin ya fito,da sauri Khalisat ta ja da baya kamar za ta faɗi badon tsohuwar motar Ammi ta tare ta ba da tuni ta faɗi.
Ya.ya.ya.ya.sai kuma ta zunduma da gudu ta yi cikin gida tana kiran Ammi!ammi!!Ki fito kiga wani abu,kafin ta gama rufe bakinta tuni Ammar ya shigo shi da amininsa Aliyu.
Kusan daskarewa Ammi ta yi a tsaye tana kiran sunan Allah tare da godewa Allah daya dawo mata da farin cikinta wato ɗanta Ammar.
Da gudu ya rungume Amminsa yana kuka yana kiran"ilove u my Ammi na ki yafe min don Allah,na tuba bazan sake ba ya haɗa hannayensa alamar neman yafiya.
Ita ma kukan ta ke tana "son na yafe maka Allah na gode maka da ka dawo min da farin cikin raina".
aranar waɗannan Familyn suna cikin farin ciki sosai,ya yiwa Ammi alƙawarin sai ya yi sati biyu kafin ya koma don ya samu hutu,sosai Ammi taji daɗi tana ƙara saka mishi albarka,don tasan duk abinda ya yi ba da sanin sa bane asiri ne.
Tunda Ammar yaje bai kira Sakina ba,hankalinta ya tashi sosai ta dinga kiransa a waya amman yana gani yaƙi ɗaukar wayar ƙarshe ma ya kashe wayar.
Suna zaune da daddare suna cin abinci Khalisat ta kalli yayanta,ta ɗauki ruwa ta fara sha ai Ammar yana ganinta ya yi saurin ƙwacewa yana ce wa"inye lallai Khalisat kin samu sarari yanzu ruwa ki ke sha kina cin abinci?.
"Wallahi Yaya" ranƙwashi Ammar ya kai mata yana ce wa"me ɗan ƙaramin baki kawai.
Murmushi Ammi ta yi tana kallon ƴaƴan na ta cikin so da Ƙaunar su,tana roƙon Allah ya bar maya ƴaƴanta guda biyu da ta mallaka a duniya.
*** *** ***
Amma ta ƙara matsamin sosai yanzu don talla na ya ƙaru yanzu inyi na safe inyi na rana inyi na dare,bani da lokacin hutu Baba na babu yadda zaiyi don yanzu ma har ya fara shiru da bakinsa,tunda ita dai amma ba dai na wa za ta yi ba,don haka ya tattara ta ya watsar da ita don rashin kunyar da ta ke mishi abin yana damunsa.
Ni daman ba a zancen arabi ballan tana boko kullum ina yawo a gari gayyar talla.
Rannan da daddare ina tafe tsoro fal a ciki na don ban taɓa yin dare irin na yau ba,don nasan idan na koma gida sai Amma ta yi gunduwa2 dani.
Wani kango nazo wucewa naji wari kamar nawiwi,na toshe hancina ina kakarin amai,kawai sai naji wani yana ce wa"kai Ba-ba waccen yarinyar me ta ke toshewa hanci ne?".
"oho bari muje muji me ta ke toshewa hanci. . . ...
Anan zan tsaya don rashin comments.
*Miss green ce*