Family Affairs
by @maidambu41
_....ZAYN MALIK....✿_
*EXQUISITE WRITERS FORUM*
Mai_Dambu
*FREE PAGE♡*
CHAPTER-02
Family Affair🎊
بسم الله الرحمن الرحمن
Kakkabe hannun shi yayi sannan ya juya yana me barin wurin, idanun shi ta sauka akan wata kyakyawar budurwa, murmushi yayi mata kamar yadda ya saba matukar zai ga yan mata toh wallahi sai yayi broke heart din yarinya, wani kallo yayi mata tare da d'age mata gira daya. Dauke kai tayi zata wuce ya tsare hanyar.
"Ke yar wancan mutumin ne?" Yadda yayi tambayar he look like innocence, cikin matukar shakkar shi tayi baya.
"Ina son nayi amfani da wannan damar na gaya miki You are so cute" Wayyo Allah, wani narkewa tayi, sannan ya juya yana kallon Alhaji Musa Me Gari, yana mishi gargadi tare da nuna mishi yar shi." Sannan ta wuce. A hankali ta bi bayan shi da ido, ba karya he look hot and sexy. Kamar munafika ta wuce abinta.
Shiga mota yayi yana sauke ajiyar zuciya.
"Kai banza dan daudu kunna min Mandula"
"Not in my car!" Brrst Bashir Zayn Malami ya fada cikin daurawar fuska.
"Hm! Kawai ce min jobless" shiru Brrst yayi bai tanka mishi ba, dan yasan ba abu ne me wuya ba, ya yarfa shi ba, haka suka isa yana murde mandular shi, har suka shiga cikin gidan.
Tun a bakin kofar main falor ya hadu da Mahaifin shi, cikin matsanancin bacin rai ya kunna tv.
"Abin da muke fama da shi kenan, dan gidan sakataren shugaban kasa Alhaji AbdulMalik Zain Malami bamu isa muyi wani abu ba, idan yayi laifi yana da daurin gindi a gwamnati."
"Aikin kenan!" Ya fada yana d'aga kafadar shi.
"Zayn!!"
"Yes dagus!" Wani sabon bakinciki ne ya kuma rufe Alhaji AbdulMalik.
"But you know what you"
"Abba ba laifin shi bane sanata Musa Me Gari ne fa ya haɗa kome." Inji Abul Khair.
"Kai ma ya saye ka ne da baki?" Ya kalli dan uwan shi.
"Bashir kana ganin abinda Yaron nan yake min? Talatin da wani abu babu aure babu aiki?"
Wata dabi'a da Zayn yake da ita shine matukar Baban shi zai fusata toh, ko shine da gaskiya zai kwantar da kan shi yayi ta bada hakuri, yawan nada hakurin zai saka ka dauka ko gobe ba zai kuma ba, kuma zai kuma zai ba da hakuri,
"Allah ya huci zuciyar ka Abba" daga haka bai kuma cewa kala ba, sai shigowar Hajiya Umma.
"Towwww! AbdulMalik! Cinye shi kake da bakin ku na yan siyasa? Tun daga cikin gidan na zata a gidan rediyon ake magana ashe shalele ka saka a gaba, kai taso muje na baka laula maganin baki domin ba zan so a cinye min kai da baki ba, na shiga duniya na rasa wurin zama ba."
Ta janyo hannun Zayn tana watsawa Abban shi kallon banza.
"Muje yau zan bar gidan AbdulMalik na huta da gorin da yake maka nq ka fita Zakka a cikin gidan nan!" Ta fada tana jan hancin ta,
"Hajiya kiyi hakuri!"
"Nice hawainiya! Ai ko A musulunce nima mahaifiyar ka ce, idan na D'aga maka nono zai bika, balle shi da na haifa. Su Yara bin su ake da addu'a ba da bakin cin goro ba, waye zai ce bai san halin dan yau ba? Koda na tsufa ai nasan me nake yi, wai ma tukun kai dan kaniyar ka baka yi amfani da kariyar nan bane ka dirke yar mutane da ciki?"
"Hajiya umma"
"Toh ai dole na tambaye ka ko Uban masu gida. Allah ya jikan malami, mutumin kirki, kai ma gadon shi kayi domin ba karamin kuzari ne da kai ba, ikon Allah toh amma an zubda cikin ko?"
"Hajajju bafa ni nayi mata cikin ba, sharri aka makala min"
"Haba dan albarka ko nace, ai nasan kaf garin Kaduna babu na Allah irin ka da ce iyaye zasu fahimci irin baiwar da Allah yayi maka na son addini da ibada ba zasu zarge ka dan ka saka gajeren wando ba"
"Hajiya!"
"Na'am Zainu!"
"Yunwa nake ji!"
"Toh dan albarka, tabawa!" Ta kwalawa me aikin gidan kira, da sauri matar ta shigo tana yarfe hannu ta, da take wanke Allahu.
"Hajiya Umma gani"
Daukar medical glass dinta tayi tana kokarin sakawa ta kalli fuskar tabawa ta ce mata.
"Malami yana son cin abinci me yau aka mana?"
"Hajiya umma ai tuwo ne miyar ganye ban kammala ba"
Cikin kwantar da murya ta ce mata.
"Haba tabawa, tun yaushe ake girki a gidan nan ba a gama ba har yau? Salon nayi magana kice nayi hakuri"
"Kiyi hakuri wallahi Muhideen ne ya mai da min aiki ba, ba dafa mishi"
"Toh Allah ya kyauta, ki cewa talatu"
"Hajjos bar shi naje da kaina kinsan na mata laifi"
"Allah sarki dan Albarka ai ni na jima da sanin Allah yayi baiwar tausayi a ranka da haka yara suke ba zan yi kaico da yaran gidan nan ba" ta fada cikin takaici.
Mikewa yayi sannan ya fita yana wani uban tsalle wanda ya zame mishi dabi'a da al'ada kamar wanda ake cilla shi da karfen mayyen karfe.
Da wani irin kaunar shi da Tausayin shi take bin shi, akwai abinda ta sani ya zame mata dole kaunar Zayn Malik, ya zame mata dole kiyayye kome, ya zame mata inuwar Gajimare, ya zama farin cikin ta a lokacin da ta rasa nata. "Zaynu" ta furta a hankali.
"Wallahi Mama ba zan iya zuba ido yana zubar da mutuncin gidan nan ba, haba don Allah akan shi aka fara samun farin ciki?"
"Kulu! Bana son haka" shiga cikin falon yayi da sallama, cikin kauna da farin cikin ganin shi ta zuba mishi ido. Tsayawa yayi ya zuba hannu a cikin Aljuhun gajeren wandon shi, mikewa tayi ya nufi hanyar kitchen, a hankali ya shiga takawa falon.
Yana zuwa wurin Yar shi ya ce mata.
"Ki gayawa mijin ki ya sauya Uban daki, idan ya cigaba da bibiyar Musa Me Gari toh wallahi sai na karya mukamikin shi" ya D'aga kafada yana wucewa kitchen.
"Banza dan jagaliya"
"Na yarda shi yasa ya boye Miki gaskiyar ya ajiye mistress a kinkinau ba" ya fada yadda ita ɗaya zata ji.
"Zaynnnnn!" Ya shige abin shi kitchen din.
A hankali ya samu tana Juye abinci a trey, tana ajiye kome a wurin shi, zuwa yayi ua daura kan shi a kafadarta.
"Mama!"
"Zayn Malik!"
Ta kira shi,
"Am sorry!"
"You didn't right"
"But" juyawa tayi ta mika mishi trey din daidai shigowar Kulu.
"Mama!! Kice ya maimaita abinda ya fada!"
Kallon Zayn tayi sannan ta ce mata.
"Duk abinda zai fada yana kan hanyar gaskiya. Babana sake fada"
A shagwab'e ya ce mata.
"Mama mijin ta mistress ya ajiye a kinkinau, sannan babu amfanin kullum tana hanyar gida"
Ajiye trey din yai sannan ta ce mata.
"Mama me ta rasa? Degree biyu gare ta, sannan bata haihu ba tana zaune tana bautawa wani kato yana tara yan mata suna abinda suke so. Ahhh am so curious matsamin na wuce ban da uncle Bashir yana dakatar dani dan uban mutum tuni ban karya mishi kwankwaso ba."
"Kayi magana in loyalty mana ai kaine kasa da ita" ajiye abincin yayi kafin ya Kum dauka ya fita abin shi, murmushi mama tayi sannan ta ce.
"Ya tsaya a cikin gidan ya tsaya a waje taya ba zan kauna ce shi ba?"
Yana fita side din shi ya wuce, a barandar da zai kai shi side din shi yaji muryan Ghali mijin Basmah sai D'aga murya yake, ajiye trey yayi ya nufi wurin, Mami sai hakuri take bashi. Kowa a wurin hakuri ake bashi, amma kamar wanda ake tunzura shi.
"Dan iskanci nace taje tayi family planning amma ta kuma ɗaukar wani cikin, wallahi ba zan dauki nauyin cikin ba sai dai a zubar" ita kuwa abin tausayi sai kuka take Basmah.
"Idan ta zubar ta min waya nazo mu koma"
Shiru yayi yasan qanwarsa da Mami ba jika take ba, amma ganin yadda Abba ya sunkuyar da kai ya bashi haushi.
Yana zuwa ya cakume wuyar Ghali kamar zai damfara shi da ƙasa.
"Dan Uban ka waye ya hana baka je an cire maka jijiyar ka ba? Dan akuya shi ne da mutuncin uban mu zaka zo ka yarfa shi? Waye ya mata cikin"
"Alhaji Zayn wallahi Ni ne! Alhaji Zayn duk abinda kace na rantse daga yau nabi Allah na bika"
Sauke shi yayi yana gyara kwalar rigar shi.
Jan hancin shi yayi, sannan ya juya tare da rike kugun shi.
"Ka ganta?" Cikin fusata ya wani dunkule hannayen shi, kamar dai rufe shi da duka.
"Sabida su ko kallon yaran wasu bana yi gudun kar a musu abinda nake yi! Idan kaga ba zaka iya aure ka tara iyali ba me yasa tun farko ka fara? Kannena mata jin su nake kamar na goya su ba baya, shine kazo kana mishi ihu akai, Mami na baka hakuri kana kuncewa babban abu kazan uba, wannan ya zama karo na farko da na karshe,na kuma ganin ka a kofar gidan mu wallahi sai na karya kafar ka banza."
"Allah ya huci zuciyar ka, wallahi an gama" da gudu Basmah ta nufi Zayn tana me rungume shi.
"Nagode Yaya" idanun shi ne ya cika da kwalla. Yana nuna mishi yatsa,
"Ka tafi gobe zan kawo ta" jan hannun ta yayi zuwa barandar ya ajiye ta a restchair dake barandar ya saka mata abincin.
"Yaya!"
"Keep quiet and eat" cikin shashekar kuka take cikin Abincin tana kallon shi, kokarin danne emotions din shi yayi ya shiga dakin shi ya dauko mandular shi, ya kunna yana zukar ta, kafin ya kunna wakar sahibin shi bomm Marley.
Yana gyada kai, yana kara jin ina ma da a zamanin bomm Marley yazo wallahi sai ya tafi har Jamaica, yana sha yana kara gyada kai a wakar shi me suna. Stand up. Sai wani jinjina kai yake kamar ya samu Abin yi.
Daga can baradan Hajiya Umaima da suke kira Mami ita ce take kallon shi, duk da ta tsani Zayn amma bai hana yau wanke mata rai ba.
"Haka yake,.ba iya abokan shi yake karewa ba hatta dangi da iyaye yana karewa, dazun kana fada dan ya daki Alhaji Musa Me Gari, toh kome shi ya shirya da fari na zata kawai yana adawa da kaine dan zaka fita karar Gwamna yanzun sai na kara fahimtar ai shi ka tsare mishi wani abu ne na daban. Ka gan shi can tsuma kan shi yayi a ruwa kawai"
Alhaji Uwaisu ya ce.
"Yaya ka nima mishi aiki mana, ya daina zaman gidan anan baki daya baba jin dadin abinda yake"
Kallon shi barista Bashir yayi sannan ya ce mishi.
"Yaya Uwaisu Meye laifin shi? Yana da degree a fanin kimiyya da fasahan na'ura inda yayi karatu a jami'ar Boston na Amurka. Sai me aiki ne yaki!"
"Amma ai ga Khalid nan matar shi haihu na biyu zata yi ko Bashir? Ni da kaina na tura shi aikin soja shekara uku da suka wuce aka Kore shi, ko sai sa nayi magana da AAM akan shi ya ce takardan shi yana nan an dakatar shi ne idan har yana bukatar aikin shi zai dawo. Na nima mishi aure ya watsar me kake so nayi mishi? Hajiya da kai da Talatu kuka lalata min Yarona wallahi"
"Shiru ma alamar magana ce Allah ya baka hakuri idan zan tafi Demark zan tafi da shi haka yayi maka?" Inji barista Bashir,
"Toh duniya ba yarda Alhaji ka mishi magana ya dawo min da Y'ata ban yarda da shi ba wallahi tsoro yake bani"
"Sai kije ki dauke ta" Alhaji AbdulMalik Zain Malami ya bata amsa,dama sun saba haka takan ce yana fifita Zayn akan Yaran ta, shi yasa take kara tsanar shi a kullum kamar ta kashe shi. Hajiya umma tana yawan gaya mata cewa.
"Ayayinda kika kare tsanarki da hassadar ki, toh anan ne Allah zai nuna miki shi yake sawa yake hanawa"
Sannan ita kanta ba zata ce ga Exactly abinda Zayn yake mata ba, amma ta tsane shi, kuma tsana me karfi.
"Ke Basmah zoki wuce, kar ganin abinda aka miki ki zata ba za a iya turmushe ki bane" lumshe idanun shi yayi yana kara jin tana burge shi, duk abinda zai mata ba zai taba burgeta ba, dan haka cikin natsuwa yake zurka mandular shi, ya dauki trey din da ta gama cin abincin ya nufi cikin gidan da shi, bayan ya kashe wiwin. A kofar kitchen din waje ya ajiye sannan ya juya zai tafi aka ce mishi.
"Huuuu!" Kallon ta yayi kafin ya rab'a gefen ta ya wuce.
" Ya Zayn sabida kai nazo"
"Dake kiran ki nayi ba?" Ya yab'a mata bakar magana.
"Hmm Ya Zayn kasan yadda na damu da kai"
Sai da yayi shiru kafin ya wuce abin shi.
"Baka san yadda na damu da kai bane?"
"Ai ni ba ciwo bane da zaki damu kanki da Ni!"
"Amma ka yi smoking?"
Shiru yayi domin ya fara gundurar da tambayar ta.
"A'a hura wuta ake a kirjina shi yasa nake kaurin hayaki"
Kallon shi tayi tare da cewa.
"Allah ya baka hakuri sai an jima"
Banza yayi da ita sannan ta wuce side din shi ya rufe kofa, ban daki ta shiga ya kwace kaya, sannan ya zauna ya cika ruwa kafin ya shiga cikin ruwan ya zauna, sai da yayi wanka sannan ta shirya ya nufi masalaci dukda ya rasa sallolin shi amma a masallaci zai yi sallah, a can yayi har sallah shafa'i da wuturi, yasan yau yayi abu mafi muni baya wasa da sallah duk inda zai shiga baya wasa da sallah lokaci biyar din nan, koda ya idar kwanciya yayi a cikin masallacin yana azkar har barci ya dauke shi. Dake masallacin a cikin gidan yake wurin sha biyu saura ya farka bayan yayi addu'ar tashi barci, sannan ya nufi side din shi yayi wanka sannan ya kuma shiryawa cikin wasu fitinannun kayan wanka, ya saka turare ya dauki key mota ya fito zai tafi, a bakin kofar gidan ya hadu da Abba.
Dauke kai yayi sannan ya shiga cikin motar ya bata wuta, a hankali yake Bin karatun Sheikh Abdulrahman Gwangola.
Tafiyar minti talatin ya kai shi club, yana parking motar ya nufi wurin shiga yana shiga aka fara ihu.
"Zayn Malik!!!!!" D'aga hannu yayi sannan ya wuce ya nime wuri ya zauna yana me daura daya akan daya.
"Hi Baby!" Wata yar gajerar budurwa ta D'aga mishi hannu tana sanye da wata bakar short gown, yadda take tafiya tana juyi zai tabbatar maka da babu ko dan kamfe a cikin rigar. Dauke kai yayi yana kallon Abul da yake romance da wata kirista, dauke kai yayi yana kallon wayar shi.
Zama yarinyar tayi tana son.matsawa jikin shi amma yadda fuskar shi tayi ta shanun nan ya sara kulawa ta mike tare da barin wurin, a hankali suka gama lashe juna sannan ya dawo wurin Zayn Malik suna tafa.
"Kana jin dadin kodimo?"
"Bari chilling akwai dad'i ita ta kawo min kanta, toh laifi ne idan nayi abinda take bukata....
PAID BOOK