6
by @phartybb
Gidan Alhaji Mamman Bashir.
Da dare Alhaji Mamman ya samu labarin zuwan yaran gurin Mami Sadiya, faɗa yayi ta yiwa Amma Jidda da abin ya ɓata mamaki, har tana cewa.
"To wai naga mahaifiyarsu ce, ta ya za ka rabasu, duk yadda kayi fa ɗa baya gudun mahaifiyar shi."
"To ki kiyaye ni, na faɗa miki kar ki ƙara kai su tun da ita ta ƙi bin shawarar da na yanke ta rabu da su." Ya ce cikin faɗa.
Shuru kawai ta mishi tana juyar kanta, haushin maganganun shi take ji. Sannan ƙasan ranta tana son sanin menene Alhaji Mamman ya nema Mami Sadiya ta ƙi yi har take ganin gwara ta bar yaranta.
...
Fushin kwana biyu yayi ya sauƙo don tace ba za ta sake kai su ba, amma tasan ƙarya ta mishi kawai don ya daina fushi da ita.
....
Tun daga ranar Amma Jidda a ɓoye take kai yaran gurin Mamin su shima sai a hutun ƙarshen mako. Sannan ta gargade su kar su ƙara sanar da Abban su.
Mami Sadiya tana jin daɗin haka don yana ƙara mata shaƙuwa da yaranta, haka kuma da yar uwar su Nuratu da in ta gansu ta dinga miƙa hannu su ɗauketa don ta gane su.
Mami Sadiya tana ƙoƙarin kyautata Amma Jidda dan yadda ta riƙe mata ƴaƴa, kullum sai ta mata godiya sai dai Mami Sadiya tayi murmushi tace ta daina gode mata.
"To wai so kike duniya ta zage ni ace na raba uwa da ƴaƴanta, a'a ni kam bana so gwara ki zama shaidana ko da an zage ni."
Murmushi kawai Mami tayi tace.
"Bama mai zagin ki sai yabon ki."
Aunti Zarah da ta samu labari itama tayi farin ciki tana yabawa Amma Jidda dan da wuya a samu matar uba mai irin halinta.
A cikin haka Amma Jidda ta haifi ƴarta nace mai sunan mahaifiyarta tana ƙiranta Walida
****
Bayan shekaru goma.
Abubuwa da yawa sun faru cikin rayuwar su da suka saka shi cikin kundin Ƙaddarar su.
Yara sun girma su Rahma sun girma shekara goma sha huɗu ba wasa ba, Hasiya mai bi mata da ita suna aji uku na sakandare, Muhsin yana ajin ƙarshe na Firamare sai Nuratu da Walida ajinsu ɗaya suna aji huɗu sai Rukayya data fi su da aji tana aji biyar, Muhammad Al-ameen ya wuce makarantar gaba da sakandare wato digiri a garin Zaria wajen dangin mahaifin shi da yake zama a can gaba ɗaya ya koma.
Tun lokacin da Nuratu ta isa shiga makaranta Amma Jidda ta haɗa da Nuratu ta sakata tare da ƴarta Walida. Mami tayi mamaki dan tana da burin sakata makarantar sauran yaran sai gashi ta shammace ta. Godiya ta mata tace sai ta bari za taci gaba da biya mata kuɗin Amma Jidda tace babu komai.
Yaran sun shaƙu da juna musammam matan, Rahma, Hasiya, Nuratu da Walida, duk ƙanƙantar su baka bambanta ya'yan waye.
Tun lokacin da Rahma da Hasiya suka fara girma suka fahimce Mami da Abban su basa tare.
Kasuwanci da Mami Sadiya take yi Allah ya sanya masa albarka sai bunƙasa yake, gidan da take ciki ta sayeshi dukka a hannun mijin ƙanwar Zarah ya zama halal ɗinta, ta ƙara gyarashi. Tsakanin ta da Zarah har yanzu suna mutumci.
Alhaji Mamman kuɗi ya zauna masa sosai, kasuwanci ya buɗe, Company sai samun cigaba yake, hankalinshi kwance yake rayuwarshi ya riga ya mance da wata Sadiya balle ƴarta da har yau bai san sunanta ba ko kamanninta.
Shekaru na ta tafiya abubuwa na ta faruwa, wani da daɗi wani babu, wani mai kyau wani marar kyau, shekaru sun ja kwanaki sun wuce sun zama satikai, sati ya shuɗe ya zama watanni.
....
Leaders Private School.
Makaranta da yayi tashe ake ji dashi a cikin garin Damaturu jihar Yobe.
Yaye ɗalibai ake na ajin ƙarshe da suka kammala karatunsu suka fita da sakamako mai kyau. Ciki har da Rahma da Hasiya da suka gama tare.
Sunyi kyau abinsu sai murna suke zasu kammala sakandare, Rukayya Nuratu da Walida da suma sun zama ƴan mata sai murna suke ganin yayunsu musamman Nuratu data kasa rufe bakinta murmushi kawai take zubawa da yake saka kumatunta lotsawa yake ƙara fito da kyan fuskarta.
Taro a kayi sosai da hotuna Alhaji Mamman yazo shi da Amma Jidda, ana zuwa yin hoton iyali dukka suka haɗu waje ɗaya har Nuratu. Bayan an ɗauki hoton Alhaji Mamman yana lura da Nuratu da duk inda yaran su kayi tana binsu tare suke.
"Wacece wannan? Kawar ku ce?"
Ya tambayi yaran.
Kafin Amma Jidda tayi magana Rukayya tace.
"Ƙanwar mu ce fa Abba, ta gidan Mami."
Kallonta yayi sosai baƙace bata da hasken fatar sauran amma tafi su kyan fuska sosai. Sai lokacin ya kalli kamannin Mami Sadiya a fuskarta dan sauran da shi suke kama ban da Rahma da itama da Mami ta ke kama hatta farin fatarta na Mami Sadiya ne.
"Ke zo nan!"
Yace a tsawace yana haɗa rai.
Nuratu da ta san da ita yake ta tashi ta taho gurin shi ta tsugunna kanta ƙasa.
Rankwashi ya kai mata da taji zafin shi har tsakar kanta tana sosa gurin idonta cike da hawaye.
"Menene haɗin ki da yarana, baki da alaƙa dasu ko kaɗan dan haka ki daina binsu kar ki shafa musu farar ƙafa. In ma uwarki ta turo ki kije ki sanar da ita haka. Idan na ƙara ganin ki dasu sai na ɓata miki rai. Tashi ki bar min guri."
Sum Nuratu ta miƙe ta bar gurin tana share hawayenta. Bata san mai ta mishi ba tun tasowarta ta nemi sanin wanene shi Mami ta kasa sanar mata sai ita da kanta ta san matsayin shi gareta. Yau kaɗai ta fara ganinshi duk yadda suke faɗan sunan Abban su amma ya faɗa mata wannan maganar.
Lokacin data fara tasowa ta ɗauka mahaifinta daban sai da tayi wayo ta gane suna duk iri ɗaya suke amfani dashi na uba. Data tambayi dalili Maminta ta sanar da ita shine mahaifinta tace mata eh ta kasa sanar da ita dalilin da yasa baya basa tare ko bata tare da ƴan uwanta. Duk yadda take son zuwa gidan su Rukayya hanata Mami take sai dai su suzo wataran har kwana suke in Abban su yayi tafiya.
To ita kuwa mai tama Abban su ya tsaneta. Mai yasa ba'a barinta taje gidan itama kamar sauran yayunta tunda shine Abban ta.
Cikin class ta shige tana cigaba da kukanta ba wanda ya biyo bayanta domin a gaba Abban su ya sasu ya musu faɗa sosai akan su daina mu'amala da ita ƙarshe ma ya ɗauke su suka wuce gida kowa yana tunanin halin da ya bar Nuratu. Amma Jidda tafi kowa shiga damuwa dan gani take bata kyauta mata ba, tare ake ɗaukarsu a sauƙeta a gida kafin sauran yaran. Bata san ta ya zata tafi gida ba yau.
Nuratu kam kukanta tasha har aka fara watsewa ta leƙo ganin wasu har sun fara tafiya ya sata fara duba su Rahma, duban duniya tayi bata gansu ba ta hakura ta zauna zaman jiran azo a ɗauke su. Har aka gama watsewa babu alamar su Rahma.
Nuratu duk tsoro ya kamata sai lokacin tunanin kar fa Abban su ya ɗaukesu yazo kanta haka ta miƙe ta fara tafiya. Tafiya nisa tsakanin makaranta da unguwar su. Haka taci tafiya sai wajen huɗu saura ta isa.
"Lafiya kika daɗe haka?"
Mami ta tambayi Nuratu da isowarta ta kwanta mata shame shame a ƙasa.
"Da kafa na dawo Mami."
"Da kafa dai? Ina Amma ɗin? Ko bata je ba."
"Amma taje tare da Abba, Mami yau naga Abban mu dasu Aunti Hasiya yake kama. Mami wai mai nama Abba ne? Ban taɓa kallon shi ko mishi magana ba, sai yau muka haɗu amma bai tare ni ko kallona a matsayin ƴarshi ba sai hantara da faɗa. Anya Mami shine mahaifina? In kuma shine mai na mishi haka ya tsane ni?"
Mami da take sauraron Nuratu ta gama maganarta kafin tace.
"Shi ya haife ki kamar sauran, wani camfi nashi can ya haddasa mishi tsanar ki, amma ba komai kar ki damu komai zai wuce ki zame masa MADUBIN GOBE. Dalilin da yasa ma bana son kije gidan su Rahma na san hakan zai faru, kinga kuwa yanzu sai ki kiyaye."
Kai kawai Nuratu ta ɗaga tana son fahimtar maganganun Maminta ganin haka Mami ta miƙe tana cewa.
"Kar kisa damuwa a ranki ko tunani, ki tashi kiyi sallolin daya same ki a hanya."
Tashi tayi tayi sallah taci abinci kasa aikin komai tayi dan ciwon kafa daya fara damunta. Da dare sai da Mami ta mata gashi da ruwan ɗumi dan ciwo ta shafa mata man zafi.
Tun daga ranar Nuratu ta kauracewa duk abinda zai haɗata da Abban ta dama ba su taɓa haɗuwa, har lokacin ƙasan ranta tana son sanin dalilin da yasa ya tsaneta.
Tsakanin ta da ƴan uwanta sai dai su zo dan an bada hutun makaranta kuma islamiyya ba ɗaya suke ba.
Alhaji Mamman duk shekarun da aka ɗauka ya tsammaci Amma Jidda taji maganar shi sai yau da ya saka yaran gaba yana musu faɗa tace ita take kai su ba laifinsu bane. Faɗar da ya mata har yana mata barazana da igiyar aurenta ta tsorata sosai ta bashi hakuri.
****
Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ta da ake shi ya farkar da ita daga tunanin abin da ya shuɗe ta sake labulen window ɗakin ta juya tana bada izinin shiga.
Nuratu ne ta shigo ɗakin cikin sauri fuskarta alamun damuwa.
"Menene kuma?"
Mami ta tambaye ta.
"Mami Aunti Hasiya ba lafiya tana asibiti. Yanzu Aunti Rahma ta sanar dani."
"To ko dai labour ne."
"Ni ma shi nake tsammani. Dan Allah muje mu dubata."
Nuratu tace kamar za tayi kuka.
"To ɗauko mayafinki muje."
Ai bata jira Mami ta gama magana ba ta fita da sauri, a falo ta tarar Mami suka fita. A motar Mami suka tafi, ita take jan motar Nuratu a gefe ta buga uban tagumi. Wayarta yana ta ƙara ta kasa ɗauka.
"Ba ki ji ana ƙiran ki ba ki ɗauka mana. Haihuwa na biyu fa, ni ba dan ke ba maa ba zan zo ba, in ta haihu na je."
Kallon fuskar wayar tayi taga Dr Awwab ne yana ɗaya daga cikin mutanen da suke da muhimmanci a rayuwarta. Kasa ɗauka tayi ta tura mishi saƙon zata ƙira shi anjima ta kashe wayar. Bai ƙiranta ba bayan ya karanta saƙon.
Bayan sun isa asibitin sai kuma ta kasa shiga.
"Muje ko."
Taji Mami tace ta girgiza kai tana kama jikinta waje ɗaya, fahimtar haka ya saka Mami cewa.
"Ki kwantar da hankalin ki babu komai, muje."
"Ba zan iya shiga ba Mami."
Nuratu tace da taji kanta yana neman juyawa, anan asibitin wasu abubuwan suka faru da ba zata iya fahimtarsu ba a lokacin balle yanzu.
"Ke fa kika dame ni muzo."
"Mu koma gida kawai."
Tace tana kwantar kanta ta rufe idanunta zuciyarta yana bugawa da sauri sauri, tsoro ya fara shigarta kamar kullum in ta tuna ko tayi tozali da abun da ya shafe rayuwarta na baya.
Shurun mintuna biyu Mami tayi tana dubanta hakan yasa ta kasa shiga ta kasa komawa gida. Wayarta ta ciro ta ƙira Aunti Rahma take tambayarta tazo, Aunti Rahma ta sanar da ita Hasiya ma ta haihu tun ɗazu an sallamesu yanzu zasu wuce gidanta ba sai tazo ba.
Bayan sun kashe wayar Mami taja motar suka bar harabar asibitin. Sai da ta hau titi tace.
"Nuratu buɗe idonki mun bar asibitin."
Sai lokacin ta ji hankalinta ya fara kwanciya ta buɗe ido tana kallon titi. Mami ido kawai ta zuba mata lokaci zuwa lokaci ganin yanayinta ya canza.
Har yanzu ta kasa cire abinda ya faru a ranta, tasan dama da wuya hakan ya kasance, tayi ƙoƙari ma na ganin ta dawo da walwalarta kamar baya duk da wani lokacin tasha kamata cikin tunani ko damuwa. Girgiza kai tayi cikin ranta tana mata fatan ƙarin lafiya.
Vote
Comments
Share
Da dare Alhaji Mamman ya samu labarin zuwan yaran gurin Mami Sadiya, faɗa yayi ta yiwa Amma Jidda da abin ya ɓata mamaki, har tana cewa.
"To wai naga mahaifiyarsu ce, ta ya za ka rabasu, duk yadda kayi fa ɗa baya gudun mahaifiyar shi."
"To ki kiyaye ni, na faɗa miki kar ki ƙara kai su tun da ita ta ƙi bin shawarar da na yanke ta rabu da su." Ya ce cikin faɗa.
Shuru kawai ta mishi tana juyar kanta, haushin maganganun shi take ji. Sannan ƙasan ranta tana son sanin menene Alhaji Mamman ya nema Mami Sadiya ta ƙi yi har take ganin gwara ta bar yaranta.
...
Fushin kwana biyu yayi ya sauƙo don tace ba za ta sake kai su ba, amma tasan ƙarya ta mishi kawai don ya daina fushi da ita.
....
Tun daga ranar Amma Jidda a ɓoye take kai yaran gurin Mamin su shima sai a hutun ƙarshen mako. Sannan ta gargade su kar su ƙara sanar da Abban su.
Mami Sadiya tana jin daɗin haka don yana ƙara mata shaƙuwa da yaranta, haka kuma da yar uwar su Nuratu da in ta gansu ta dinga miƙa hannu su ɗauketa don ta gane su.
Mami Sadiya tana ƙoƙarin kyautata Amma Jidda dan yadda ta riƙe mata ƴaƴa, kullum sai ta mata godiya sai dai Mami Sadiya tayi murmushi tace ta daina gode mata.
"To wai so kike duniya ta zage ni ace na raba uwa da ƴaƴanta, a'a ni kam bana so gwara ki zama shaidana ko da an zage ni."
Murmushi kawai Mami tayi tace.
"Bama mai zagin ki sai yabon ki."
Aunti Zarah da ta samu labari itama tayi farin ciki tana yabawa Amma Jidda dan da wuya a samu matar uba mai irin halinta.
A cikin haka Amma Jidda ta haifi ƴarta nace mai sunan mahaifiyarta tana ƙiranta Walida
****
Bayan shekaru goma.
Abubuwa da yawa sun faru cikin rayuwar su da suka saka shi cikin kundin Ƙaddarar su.
Yara sun girma su Rahma sun girma shekara goma sha huɗu ba wasa ba, Hasiya mai bi mata da ita suna aji uku na sakandare, Muhsin yana ajin ƙarshe na Firamare sai Nuratu da Walida ajinsu ɗaya suna aji huɗu sai Rukayya data fi su da aji tana aji biyar, Muhammad Al-ameen ya wuce makarantar gaba da sakandare wato digiri a garin Zaria wajen dangin mahaifin shi da yake zama a can gaba ɗaya ya koma.
Tun lokacin da Nuratu ta isa shiga makaranta Amma Jidda ta haɗa da Nuratu ta sakata tare da ƴarta Walida. Mami tayi mamaki dan tana da burin sakata makarantar sauran yaran sai gashi ta shammace ta. Godiya ta mata tace sai ta bari za taci gaba da biya mata kuɗin Amma Jidda tace babu komai.
Yaran sun shaƙu da juna musammam matan, Rahma, Hasiya, Nuratu da Walida, duk ƙanƙantar su baka bambanta ya'yan waye.
Tun lokacin da Rahma da Hasiya suka fara girma suka fahimce Mami da Abban su basa tare.
Kasuwanci da Mami Sadiya take yi Allah ya sanya masa albarka sai bunƙasa yake, gidan da take ciki ta sayeshi dukka a hannun mijin ƙanwar Zarah ya zama halal ɗinta, ta ƙara gyarashi. Tsakanin ta da Zarah har yanzu suna mutumci.
Alhaji Mamman kuɗi ya zauna masa sosai, kasuwanci ya buɗe, Company sai samun cigaba yake, hankalinshi kwance yake rayuwarshi ya riga ya mance da wata Sadiya balle ƴarta da har yau bai san sunanta ba ko kamanninta.
Shekaru na ta tafiya abubuwa na ta faruwa, wani da daɗi wani babu, wani mai kyau wani marar kyau, shekaru sun ja kwanaki sun wuce sun zama satikai, sati ya shuɗe ya zama watanni.
....
Leaders Private School.
Makaranta da yayi tashe ake ji dashi a cikin garin Damaturu jihar Yobe.
Yaye ɗalibai ake na ajin ƙarshe da suka kammala karatunsu suka fita da sakamako mai kyau. Ciki har da Rahma da Hasiya da suka gama tare.
Sunyi kyau abinsu sai murna suke zasu kammala sakandare, Rukayya Nuratu da Walida da suma sun zama ƴan mata sai murna suke ganin yayunsu musamman Nuratu data kasa rufe bakinta murmushi kawai take zubawa da yake saka kumatunta lotsawa yake ƙara fito da kyan fuskarta.
Taro a kayi sosai da hotuna Alhaji Mamman yazo shi da Amma Jidda, ana zuwa yin hoton iyali dukka suka haɗu waje ɗaya har Nuratu. Bayan an ɗauki hoton Alhaji Mamman yana lura da Nuratu da duk inda yaran su kayi tana binsu tare suke.
"Wacece wannan? Kawar ku ce?"
Ya tambayi yaran.
Kafin Amma Jidda tayi magana Rukayya tace.
"Ƙanwar mu ce fa Abba, ta gidan Mami."
Kallonta yayi sosai baƙace bata da hasken fatar sauran amma tafi su kyan fuska sosai. Sai lokacin ya kalli kamannin Mami Sadiya a fuskarta dan sauran da shi suke kama ban da Rahma da itama da Mami ta ke kama hatta farin fatarta na Mami Sadiya ne.
"Ke zo nan!"
Yace a tsawace yana haɗa rai.
Nuratu da ta san da ita yake ta tashi ta taho gurin shi ta tsugunna kanta ƙasa.
Rankwashi ya kai mata da taji zafin shi har tsakar kanta tana sosa gurin idonta cike da hawaye.
"Menene haɗin ki da yarana, baki da alaƙa dasu ko kaɗan dan haka ki daina binsu kar ki shafa musu farar ƙafa. In ma uwarki ta turo ki kije ki sanar da ita haka. Idan na ƙara ganin ki dasu sai na ɓata miki rai. Tashi ki bar min guri."
Sum Nuratu ta miƙe ta bar gurin tana share hawayenta. Bata san mai ta mishi ba tun tasowarta ta nemi sanin wanene shi Mami ta kasa sanar mata sai ita da kanta ta san matsayin shi gareta. Yau kaɗai ta fara ganinshi duk yadda suke faɗan sunan Abban su amma ya faɗa mata wannan maganar.
Lokacin data fara tasowa ta ɗauka mahaifinta daban sai da tayi wayo ta gane suna duk iri ɗaya suke amfani dashi na uba. Data tambayi dalili Maminta ta sanar da ita shine mahaifinta tace mata eh ta kasa sanar da ita dalilin da yasa baya basa tare ko bata tare da ƴan uwanta. Duk yadda take son zuwa gidan su Rukayya hanata Mami take sai dai su suzo wataran har kwana suke in Abban su yayi tafiya.
To ita kuwa mai tama Abban su ya tsaneta. Mai yasa ba'a barinta taje gidan itama kamar sauran yayunta tunda shine Abban ta.
Cikin class ta shige tana cigaba da kukanta ba wanda ya biyo bayanta domin a gaba Abban su ya sasu ya musu faɗa sosai akan su daina mu'amala da ita ƙarshe ma ya ɗauke su suka wuce gida kowa yana tunanin halin da ya bar Nuratu. Amma Jidda tafi kowa shiga damuwa dan gani take bata kyauta mata ba, tare ake ɗaukarsu a sauƙeta a gida kafin sauran yaran. Bata san ta ya zata tafi gida ba yau.
Nuratu kam kukanta tasha har aka fara watsewa ta leƙo ganin wasu har sun fara tafiya ya sata fara duba su Rahma, duban duniya tayi bata gansu ba ta hakura ta zauna zaman jiran azo a ɗauke su. Har aka gama watsewa babu alamar su Rahma.
Nuratu duk tsoro ya kamata sai lokacin tunanin kar fa Abban su ya ɗaukesu yazo kanta haka ta miƙe ta fara tafiya. Tafiya nisa tsakanin makaranta da unguwar su. Haka taci tafiya sai wajen huɗu saura ta isa.
"Lafiya kika daɗe haka?"
Mami ta tambayi Nuratu da isowarta ta kwanta mata shame shame a ƙasa.
"Da kafa na dawo Mami."
"Da kafa dai? Ina Amma ɗin? Ko bata je ba."
"Amma taje tare da Abba, Mami yau naga Abban mu dasu Aunti Hasiya yake kama. Mami wai mai nama Abba ne? Ban taɓa kallon shi ko mishi magana ba, sai yau muka haɗu amma bai tare ni ko kallona a matsayin ƴarshi ba sai hantara da faɗa. Anya Mami shine mahaifina? In kuma shine mai na mishi haka ya tsane ni?"
Mami da take sauraron Nuratu ta gama maganarta kafin tace.
"Shi ya haife ki kamar sauran, wani camfi nashi can ya haddasa mishi tsanar ki, amma ba komai kar ki damu komai zai wuce ki zame masa MADUBIN GOBE. Dalilin da yasa ma bana son kije gidan su Rahma na san hakan zai faru, kinga kuwa yanzu sai ki kiyaye."
Kai kawai Nuratu ta ɗaga tana son fahimtar maganganun Maminta ganin haka Mami ta miƙe tana cewa.
"Kar kisa damuwa a ranki ko tunani, ki tashi kiyi sallolin daya same ki a hanya."
Tashi tayi tayi sallah taci abinci kasa aikin komai tayi dan ciwon kafa daya fara damunta. Da dare sai da Mami ta mata gashi da ruwan ɗumi dan ciwo ta shafa mata man zafi.
Tun daga ranar Nuratu ta kauracewa duk abinda zai haɗata da Abban ta dama ba su taɓa haɗuwa, har lokacin ƙasan ranta tana son sanin dalilin da yasa ya tsaneta.
Tsakanin ta da ƴan uwanta sai dai su zo dan an bada hutun makaranta kuma islamiyya ba ɗaya suke ba.
Alhaji Mamman duk shekarun da aka ɗauka ya tsammaci Amma Jidda taji maganar shi sai yau da ya saka yaran gaba yana musu faɗa tace ita take kai su ba laifinsu bane. Faɗar da ya mata har yana mata barazana da igiyar aurenta ta tsorata sosai ta bashi hakuri.
****
Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ta da ake shi ya farkar da ita daga tunanin abin da ya shuɗe ta sake labulen window ɗakin ta juya tana bada izinin shiga.
Nuratu ne ta shigo ɗakin cikin sauri fuskarta alamun damuwa.
"Menene kuma?"
Mami ta tambaye ta.
"Mami Aunti Hasiya ba lafiya tana asibiti. Yanzu Aunti Rahma ta sanar dani."
"To ko dai labour ne."
"Ni ma shi nake tsammani. Dan Allah muje mu dubata."
Nuratu tace kamar za tayi kuka.
"To ɗauko mayafinki muje."
Ai bata jira Mami ta gama magana ba ta fita da sauri, a falo ta tarar Mami suka fita. A motar Mami suka tafi, ita take jan motar Nuratu a gefe ta buga uban tagumi. Wayarta yana ta ƙara ta kasa ɗauka.
"Ba ki ji ana ƙiran ki ba ki ɗauka mana. Haihuwa na biyu fa, ni ba dan ke ba maa ba zan zo ba, in ta haihu na je."
Kallon fuskar wayar tayi taga Dr Awwab ne yana ɗaya daga cikin mutanen da suke da muhimmanci a rayuwarta. Kasa ɗauka tayi ta tura mishi saƙon zata ƙira shi anjima ta kashe wayar. Bai ƙiranta ba bayan ya karanta saƙon.
Bayan sun isa asibitin sai kuma ta kasa shiga.
"Muje ko."
Taji Mami tace ta girgiza kai tana kama jikinta waje ɗaya, fahimtar haka ya saka Mami cewa.
"Ki kwantar da hankalin ki babu komai, muje."
"Ba zan iya shiga ba Mami."
Nuratu tace da taji kanta yana neman juyawa, anan asibitin wasu abubuwan suka faru da ba zata iya fahimtarsu ba a lokacin balle yanzu.
"Ke fa kika dame ni muzo."
"Mu koma gida kawai."
Tace tana kwantar kanta ta rufe idanunta zuciyarta yana bugawa da sauri sauri, tsoro ya fara shigarta kamar kullum in ta tuna ko tayi tozali da abun da ya shafe rayuwarta na baya.
Shurun mintuna biyu Mami tayi tana dubanta hakan yasa ta kasa shiga ta kasa komawa gida. Wayarta ta ciro ta ƙira Aunti Rahma take tambayarta tazo, Aunti Rahma ta sanar da ita Hasiya ma ta haihu tun ɗazu an sallamesu yanzu zasu wuce gidanta ba sai tazo ba.
Bayan sun kashe wayar Mami taja motar suka bar harabar asibitin. Sai da ta hau titi tace.
"Nuratu buɗe idonki mun bar asibitin."
Sai lokacin ta ji hankalinta ya fara kwanciya ta buɗe ido tana kallon titi. Mami ido kawai ta zuba mata lokaci zuwa lokaci ganin yanayinta ya canza.
Har yanzu ta kasa cire abinda ya faru a ranta, tasan dama da wuya hakan ya kasance, tayi ƙoƙari ma na ganin ta dawo da walwalarta kamar baya duk da wani lokacin tasha kamata cikin tunani ko damuwa. Girgiza kai tayi cikin ranta tana mata fatan ƙarin lafiya.
Vote
Comments
Share