Enamored
by @realsmasher
đź’ đź’ đź’ đź’ đź’
©®2021.
*♡IN-LAWS¸.•💥*
BĘŹ.
*HAWWA MUH'D USMAN.*
(Rᴇᴀʟ Sᴍᴀꜱʜᴇʀ).💕
*WATTPAD:REAL-SMASHER.*
*FREE PAGE*
07-08
#Enamored
Murmushi Abba yayi yana gyaɗa kai yace "tou Shaheed! Yanzu dai bazan iya cewa komai akan maganarka da *FADWAH* ba,saboda ban taɓa kawo zan yi mata aure da wuri ba,na so ace sai da tayi karatu kamar sauran ƴan uwanta,ta yanda ko ba na raye za ta iya dogara da kanta,ba sai tana nema ayi mata ba.. Sai dai kamar yanda ka mutunta ni,baka fara tararta a hanya ba,kazo neman izini na,wannan dalilin yasa na maka izinin fara zuwa gurinta,kuna gaisawa kafin Allah yasa ta ƙarasa secondary school ɗinta" wani murmushi Shaheed yayi cike da jin daɗi yace "in dai wannan ne Abba nima bazan hanata karatu ba ko da tana gidana,tunda na nima ƴan uwana suna yi" Abba yace "tou! Shi kenan,yanzu kana iya fara zuwa gurinta,even though suna shirin fara SSCE,and za tayi JAMB cikin watan nan" Shaheed yace "na gode sosai Abba,Allah ya saka da alkhairi ya ƙara girma.." Abba yayi murmushi yace "ameen²" cike da alkunya duk da zumuɗin da Shaheed yake ya ganni kafin ya wuce yace "Abba zan wuce gida.." Abba yace "baza ka jira tazo ku gaisa ba?" Shyly Shaheed yayi ƙasa da kai bai ce komai ba sai murmushin da yake yi,Abba yayi murmushi ya tashi ya shiga cikin gida bayan sun yi sallama,yana tafiya Shaheed ya ɗago kansa yayi wani murmushi yana lumshe idanuwansa,a hankali yayi baya yayi balance akan armchair da yake,then ya zubawa ƙofar shogowa idanuwansa. Sanda Abba ya shiga cikin gidan direct parlon Aunty ya nufo yayi sallama,dukanmu muna zaune su Yaa Umar suna hira,ni kuma gama cin abinci na kenan,sanda muka amsa yana kallona daga tsayen da yake yace "Fadwah tashi kije parlon baƙi ku gaisa" sanda na ɗago na kalli Aunty da su Yaa Umar kamar munafuka kafin nace "toh Abba!" Then na tashi na saka hijab ɗina har ƙasa na nufi ƙofa na fita,Aunty ta bini da kallo kafin ta janye idanuwanta akaina tana taɓe baki,Abba yayi murmushi ya juya zai fita yace "Asiya zo ina son magana dake" Aunty dai mamaki yasa bata iya magana ba ta tashi tabi Abba suka fita. Ina fita cikin sanyi na wuce parlon baƙin Abba,ta ƙofar cikin gida na buɗe,sanda nayi sallama kafin na shiga,idanuwansa suka sauka kaina kamar yanda ya gama sawa ransa,calmly ya amsa min har na zauna bai daina kallona ba,haka nan duk na ji na takura saboda idanuwansa da nake ji a kaina,ina lumshe lumshe idanuna nace "ina yini?" A hankali ya lumshe idanuwansa ya buɗe yana sauke numfashi ya amsa min,yace "how are u,and ur grad?" Ina fidgeting fingers ɗina nace "Alhamdulillah!" Yace "Allah ya sanya alkhairi,yasa na tsoron Allah ne.." Nace "ameen" daga haka dukan mu muka yi shiru,sai can shi yayi breaking silence ɗin yace "let me introduce myself to u kou?" Da yaga na yi shiru ban amsa ba,yace "My name is Muhammad Mahmoud,but siblings ɗina and all my family suna kirana da Shaheed.. I'm the first born of my parents,mahaifina shi ne Alh Mahmoud Tafeeda,i've 4 siblings,maza biyu mata biyu.. Na yi karatuna har zuwa masters in law department.. Now i'm working with a chamber.. Briefly wannan shi ne history na,sauran abunda ban sanar miki ba idan an kwana biyu za ki sani." Slowly na gyaɗa kaina bance komai ba,yace "and u?" Kaina a ƙasa saboda yau ɗin was the first day of my life da saurayi ya sakani gaba,duk sai nake jina not comfortably,kamar wanda idan nayi magana zai kama nace "sss.. Suna na.. Fadwah" sai nayi shiru na kasa ci gaba,yayi murmunshinsa mai kyau yana kallona yace "yes! Say whatever u want to,ba tafiya zanyi dake ba idan kin sanar min" calmly ina runtse idanuwa nace "I'm the last born of my parents,i've four elder brothers,Yaa Umar was the first born a gurin Aunty'nmu and he's a militant,and then Yaa Mukhtar,then Yaa Waleed da nake bi" murmushi yayi yace "woww! U gotta nice name" a hankali nace "thank u.." Yace "wane school kike zuwa?" Nace "bradford college.." Yana kallona yace "wane guri kenan?" Nace "gandu new layout behind trade fair.." Yace "oohhh! I understand.. When za ku fara exams?" Nace "soon" yace "how many days or weeks ya rage muku?" Nace "just 2 weeks" ya gyaɗa kai yace "maa sha Allah,Allah ya bada sa'a.." A hankali na amsa "ameen." Daga nan babu wanda ya sake magana,can da aka jima ya tashi yana kallona yace "i'm going Fadwahhh.. Thanks for ur time,sai na sake dawowa.." Wani irin thunder storm naji har cikin kaina,sanda naji kamar ya fi kowa iya faɗar suna na,na lumshe idanuwana na buɗe,calmly nace "nima na gode sosai.. A gaida mutanen gida" cike da zolaya yace "zan faɗa musu idan na koma,but wa zance tana gaishesu?" Not minded nace "Fadwah mana" yayi murmushi yace "ai basu san me sunan ba" a hankali na ɗago muka haɗa ido,na kautar da kaina ina murmushi na watsa hannuwa nace "tou ai nima ban san wa zance ba" yace "alright! Ni na san me zan ce musu" da sauri na wakgo ina buɗa idanuwa nace "me za kace tou?" Yace "ina ruwanki da abunda zan faɗa?" Shagwaɓe fuska nayi kamar zan yi kuka nace "ayyah mana Yaa Shaheed,ni fa ƙanwarka ce" sosai yayi murmushi yana buɗa idanuwansa akaina yace "woww! I really love it,do it again please" zaro idanuwa nayi nace "what?" Yace "shagwaɓar da kika yi nake son gani" saurin rufe fuskata nayi da palms ɗina shyly,yayi ɗan murmushi mai sauti yace "ohh! Har da kunya ma?" Na ƙyalƙale da dariya,a hankali ya dunga takowa sanda yazo kusa da ni ya durƙusa in a way style a gabana,calmly yace "ɗan buɗe fuskar tou zan tafi" slowly na fara yin ƙasa da hannuna,sai dai na kasa kallonsa,yayi min murmushi yace "thank u for everything.. I appreciate" murmushi kawai na iya yi masa,ya miƙe kaɗan hannayensa zube cikin aljihun light green ɗin shaddarsa,ƙamshinsa duk ya cika parlon yace "kiyi haƙuri na zo ban kawo miki gift ba.. But next time in sha Allah.." Nayi ƙasa da kai na ƙi cewa komai,yace "ko bakya so ne?" Na ɗago kaina kaɗan nace "what?" Yace "i said zan kawo maki gift ɗinki na ji kin yi shiru" still na sake kautar da kai ban ce komai ba,ya ɗaga shoulders yace "any ways.. Till we met" nace "Allah ya kaimu" yace "ameen.." Instead of ya tafi kamar yanda yace,sai naga ya tsaya yana operating tsadadden wayarsa mai idon mujiya (iPhone 12 pro) sanda ya kai wayar kunnensa yace "Hello! Where are u friend?" Yaa Waleed da ya ɗauki wayar yace "ina cikin gida" yace "okay! Fito muyi sallama zan wuce.." Daga haka ya sauke wayar ya ɗan juyo yana kallona yace "Oops! Ur digit please *My Jewel"* sanda na ɗago ina juya idanuwana nace "ba'a barni na fara riƙe waya ba" kallona ya tsayi kamar yana mamaki,sai kuma naji yace "okay! Amma za'a bari na baki?" Na watsa hannuwa nace "don't know" yace "ya kamata ki sani" nace "tou! Zan tambaya" yace "wa za ki tambaya?" Nace "Abban mu ko Aunty" yace "alright! But before na dawo,za muna gaisawa ta wayar Waleed?" Nace "ai basa ba ni wayarsu" yace "uhmn! Zan kirasa nace ya baki" a hankali na gyaɗa kai nace "tou!" Yace "bye.." Nayi murmushi kafin nace "bye" wayarsa ya fara ring,sanda ya ɗaga min hannu then ya juya ya fita yana ce min "ki gaisar min da Aunty da su Yaa Farouk" nace "za su ji" yana fita nayi baya a hankali na kwantar da kaina jikin wing ɗin chair ina sauke numfashi,ina ta mamakin kaina da yanda na sake da shi though ban sanshi ba,sanda na gama calming kaina down then na tashi na ɗauke tray na shiga gida ina sakin murmushi,zumuɗi duk ya cika ni kamar na janyo gobe nake ji,saboda yanda na matsu na sanarwa Umaimah labarin yau nima Abba ya barni na yi zance,kuma da kansa ma kira ni yace naje. Aunty kuwa lokacin da Abba ya kirata ta bishi,sanda suka shiga parlonsa,ya zauna saman kujera yana kallonta fuskarsa da murmushi ya fara bata labarin abunda ya faru,Aunty dai banda kallon Abbanmu babu abunda take yi,sanda yace "kawai saboda na san mahaifinsa shi yasa na barshi yazo gurinta amma da wani ne gaskiya haƙuri zan bashi" Aunty ta sauke numfashi tace "tou! Allah ya tabbatar mana da alkhairi" Abba ya amsa da "ameen." Ina kwance ɗakinmu around 9pm bayan tafiyarsa,Yaa Waleed ya ƙwalo min kira,lokacin har na yi shirin bacci na tashi na saka hijab na leƙo,yana kallona ya miƙo min wayarsa yace "dillah can karɓi ni ban son iyayi kin wani tsaya kallona" ina karɓa ya juya yayi shigewarsa ɗakinsu,na juya nima a hankali ina turo baki,sanda na shiga ɗaki na kwanta kan gado a hankali na kai wayar kunnena nayi sallama,calmly ya amsa min then na gaishesa,a hakankali ya dunga ja na da hira,sanda na saki jiki da shi sosai kafin yayi min sallama yace na kwanta,da ƙyar bacci ɓarawo ya ɗauke ni ranar cike da nightmares iri²,washe gari da safe kuwa ina gama abunda nake nace wa Aunty zan shiga gurin Umaimah,tace "a dawo lafiya.." Na fita da sauri na faɗa gidansu,a can muka shiririce,ranar banda hiran abunda ya faru babu abunda muke yi. A haka lokaci yaita tafiya,shaƙuwa tana sake shiga tsakaninmu,lokacin kuma gaba ɗaya kwanaki ne suka mana saura mu kammala neco ɗinmu,duk zuwan Yaa Shaheed gurina a lokacin bai wuce a ƙirga ba,duk da mun kusa 3 moths da haɗuwa,sai dai muna yin waya da shi sosai yanzu tun da ya siya min waya mai kyau da tsada,bai ba ni ba sai da ya sanarwa Abba. On the other side kuwa,duk abunda ke faruwa gaba ɗaya Hjy Umma bata da labari,kasancewar Abba bai sanar mata ba,ranar da muka yi final exam,bayan na dawo gida muna waya da Yaa Shaheed yace "My Jewel ina son zuwa na ganki" murmushi nayi cike da tsokana nace "when?" Yace "ko yanzu kika ce zan bar office nazo na ganki" zaro idanuwa nayi nace "no! Ba yanzu ba" yace "sai yaushe?" Nace "Mmm!" Nayi kamar ina tunani,ya sassauta muryarsa yace "please Jewel kin san na yi missing ɗinki,ki sassauta min ki bari nazo ko baza ki bari na jima ba,na ganki na tafi" dariya nayi nace "uhmn! Za ka zo ne?" Yace "ai baki ce kina son ganina ba" nace "tou kazo anjima" yace "alright! Thank u.. I love u" ina rufe idanuwana na faɗa saman kujera nace "nima.." Da sauri yace "kema me?" Da sauri nace "babu komai.. Sai ka zo" yayi murmushi yace "idan na zo za ki faɗa min abunda kika ce" muka kashe waya cikin farin ciki,it was there na tashi na cire kayana na wuce bathroom na watso ruwa haɗe da ɗauro alwala na fito saboda it's almost asr. After isha lokacin ina ina zaune bedroom time-time nake ɗaga kaina ina kallon agogo,na matsu banji ya kira ni ya ce min ya zo ba,duk na shiga damuwa ganin lokaci sai tafiya yake,nayi tagumi da hannu bibbiyu na zubawa wayata idanu,ji nake kamar zan fashe kuka,dai² nan kiransa ya shigo,da sauri na ɗauka,calmly yace "My Jewel ga ni a ƙofar gida" da sauri nace "ga Ni nan fitowa" yayi murmushi yace "a fito lafiya *My princess jewel"* murmushi kawai nayi na ajiye wayar hannuna,sanda na ɗauki turare na ƙara spraying a jikina na gyara veil ɗina then na fito,har ƙasa na durƙusa gaban Aunty nace "Aunty zan je Yaa Shaheed ya zo yana jirana" tace "a dawo lafiya.. Ki gaishesa." Na amsa na miƙe na fita,sanda na fita har ƙofar gidanmu,na sameshi a cikin motarsa,na fara tafiya idanuna a ƙasa,tunda ya hango fitowata ya buɗe motar ya sauko da ƙafarsa ɗaya,amma saboda mulki sai da ya jira har na ƙarasa,sannan ya fito ya rufe motar,yana sanye da wani men's cashmere navy blue,hular kansa ya turata baya can,sosai yayi kyau sai ƙamshi yake bazawa,sanda ya juyo yana kallona ya langaɓar da kansa yace "My Jewel.." Kunya ce ta kamani nayi ƙasa da idanuwana nace "sannu da zuwa" ya amsa yana kallona yace "i really missed u" ban kalleshi ba nace "mu ƙarasa" yayi min wani kallo yace "ina magana kina basar da ni,zan yi maganin ki fa" dariya nayi nace "me nayi kuma?" Yace "ohooo! Kin sani ai" na sake yin murmushi muka jera muna tafiya,na buɗe mana parlon Abba'nmu kenan za mu shiga Mardiyya ta leƙo ta ƙofar cikin gida muka haɗa ido,na ɗauke kai ban sake kallonta ba na bashi hanya ya shigo ya zauna,a hankali nace "ina zuwa please" yace "okay!" Na buɗe ƙofar na shiga cikin gida,a ƙofar ɗakin Hjy Umma naga su Juwairiyya suna leƙowa,ban kallesu ba nayi wucewata,sanda na ɗauko tray dana ɗora ruwa da lemo,sai snacks ɗin da Aunty tayi mana na murnar grad ɗinmu ni da Umaimah na fito,ina wucewa ta ƙofar ɗakin Hjy Umma naji suna magana Mardiyya tana cewa "wallahi Umma da saurayi na ganta,ta buɗe musu parlon Abba'nmu" Hjy Umma tace "saurayi? Da ita Fadwan?" Mardiyya tace "wallahi Allah da gaske nake miki,idan baki yarda ba ki leƙa da kanki ko kisa a gano maki" mamaki duk ya cika Hjy Umma ta kasa magana,na taɓe baki nayi sallama bakin ƙofar shiga,operating waya na tarar da shi yana yi,na janyo coach na ɗora tray ɗin hannuna,ban koma na zauna ba na buɗe lid ɗin apple flavor drink ɗin,ya ɗago yana kallon abunda nake yi,sanda na gama na ɗago muka haɗa ido nayi masa murmushi nace "Bismillah!" Yayi murmushi yace "na gode" then na koma na zauna...
*This book is not for free,it's #200 via 0060746882,Hauwa Muhammad Usman-Access bank. Then u show ur evidence of payment via my whatsapp digit *** to be added in the paid group. Ƴan Niger za ku iya tuntuɓar wannan number +22770766074.*
#Follow
#Vote
#Comment
#Share fisabilillah!
#Asli Smasher.