2.
by @nuceeyluv
πππππ
*SARAUTA TAH CE*
*Free page*
By
Nuceeyluvπ
2...
"What is this?" Prince yaseer ya sake furta Hakan yana karewa mitsi-mitsin nonon ta kallo tamkar kwallon goruba.
Huda data gama sakankan cewa domin harta fara shiga yanayi ta kamo hannun sa ya fisge hade da maka mata harara Yana yatsina fuska ganin Hakan yasa ta mike Dan gwada dabarar ta Dan jawo hankalin sa sbd takai makurar matsuwa sannan Bata damu d yadda yake karewa halittar kirjinta kallo ba, shafo kirjinsa tayi cike da kwarewa cikin yanayi na ban hakuri tace,
"I'm sorry prince..."
Ransa a mugun bace ya ture hannun nata Yana kokarin tashi daga kan gadon da tasan waye prince da yadda yake matukar son Albarkatun kirji da Sam bata yi gigin zuwa da Wannan kananun nonuwan nata ba, sake rarrafowa tayi zata bashi hakuri ya zame Yana kokarin maida towel dinsa a kugu hade da nuna mata bakin kofa yace,
"get out"
Kin fita tayi domin gaba1 ya gama sakar mata lakar jiki ba Abinda take bukata a yanzu sama da taji dumin jikinsa Abinda ta dade tana kishirwa kenan kusan shekara guda tana dakon samun shiga jerin matan da yarima Yaseer ke mu'amala dakyar aka dace a Wannan karon tana dab da cimma burinta na dandannar zumar sa ace ta tafi? Kai inaa data tabka babbar asara kuwa...cikin yanayi na Jan hankali tace,
"prince yasee...."
"I said get outttt"
Prince yaseer ya furta Hakan cike da karaji ba shiri ta mike tana jawo 'yan kananun kayanta tayi waje a guje.
Tsaki me daci prince yaseer yaja Yana me janyo wayar sa dake kan dressing mirror hade da latsa kiran Musa., Musa dake zaune daga waje yaga kiran yallabai, jiki na rawa ya daga bakinsa na fadin,
"yallabai kana da bukatar...."
"Sa me ni a parlo."
Yarima yaseer ya furta Hakan a takaice Yana katse wayar ransa na zafi. Gwalo ido bafaden sa Musa yyi yana tunanin yau wanne lefi Kuma yyi? Dan a yadda yaji mgnr sa kasan cewa lalle Ransa a bace yake, da Wannan tunanin suka kusa cin karo da Huda dake fitowa daga parlon cikin sauri, tarar ta yyi d mmki yace,
"madam lpy haka da wuri?"
Harara ta ballo Masa tana kawar da Kai tayi hanyar fita, kama haba Musa yyi a Fili yace,
"badai ni nakar zomon ba..."
Yana Ida mgnr ya shige parlon kansa a sunkuye cike da biyayya yace,
"Yallabai gani."
Prince yaseer dake zaune kan sofa daga shi sai er karamar t shirt da wando 3quarter sai girgiza kafa yake Yana cije lips dinsa a hankali gaba1 hankalin sa a tashe yake ba Abinda yake bukata a yanzu sama da ya sauke Abinda ke damunsa domin kugunsa sai daurewa yake yana Masa zafi.
"Yallai...."
"Shut up"
Prince yaseer ya katse bafaden sa Musa a zafafe yanajin kamar ya tashi ya make shi Dan haushi. Jikin musa ne yahau rawa prince yaseer yace,
"I gave you 5mins just 5mins ka turo min wata or else...."
prince yaseer ya cije kasan lips dinsa Yana lumshe ido hade da fitar da huci me zafi...tun kafin ya bude ido ma tuni Musa ya bace a wajen har Yana tuntube a rude yyi waje kadan ya rage suyi gware da wata hadaddiyar budurwa data zo gidan take bafaden Musa ya saki wata irin nannauyan ajiyar zuciya yana kallon budurwar data dubeshi a yatsine yace,
"Thank God, you are here Samantha..."
Wara ido Sam tayi tana jiran Karin bayani Musa yace,
"Prince yaseer yana bukatar wata yanzu it's urgent pls nasan gurinsa kikazo tohm u'r lucky today bcos Yana cikin bukata yanzu.."
Wani irin annuri ne ya mamaye fuskar Samantha hatta fararen hakoran ta Saida suka bayyana tana kallon Musa cike da doki tace,
"Thanks you...bye."
Ta furta Hakan da sauri tana me karasawa cikin gidan.
Duke ta samu yarima yaseer ya kifa kansa a jikin kujera sai cije lips yake, Wani irin murmushin jin dadi sam ta saki tana kaunar kasancewa da yarima yaseer ba karamin enjoying take ba aduk sanda ta kasance dashi batajin tunda take ta taba samun cikakken namiji Wanda yasan salo-salo na Wannan harkar sama da prince.
*MASARAUTAR MANARAS*
"Mami ya kukayi dashi?"
Cewar Wani saurayi dake kishingide akan lallausan kilisi gefe guda basket ne a gabansa shake da kayan marmari iri-iri a ciki hannun sa dauke da tuffa Yana gutsira a hankali. Kwarkwara sa'adiyya ta kalli bewarta dake Mata tausa a hankali kallo na yadda zata fahimci cewar tana bukatar ta Bata wuri Hakan kuwa akayi ko Bata furta ba baiwar ta fahimta Hakan yasa ta mike da sauri tana yin waje, kafin sa'adiyya ta dawo da hankalin ta kan saurayin daya kurbi tacaccen lemon inibi a tambulan dinsu na SARAUTA hade da tsare mahaifiyar tasa da ido ya sake furta,
"mami ke nake sauraro."
Numfashi me karfi kwarkwara sa'adiyya taja tana me saita nutsuwarta Hade d Dan mikewa a hankali ta zauna sosai sannan tace,
"Akwai mahalukin daya isa yasha gabanka ne yarima na?"
Wani irin kayataccen murmushi *yarima Yazeed* ya saki har fararen hakoran sa na bayyana shima ya tashi daga kishingidar da yyi yace,
"matukar inada ke mami babu Wanda ya isa ya haye karagar MULKIN Nan Saini."
Ya furta Hakan yana me nuna hannun sa akan kirjin sa. Bushewa da dariya sa'adiyya tayi har na tsawon sa'o'i uku kafin ta gimtse tana me kallon yaron nata yarima Yazeed daya gama tayata dariyar shima Kuma suka gimtse a tare tace,
"nidin Nan sa'adiyya kwarkwarar sarki nasha Alwashin cewar ko a mutu ko ayi rai Amma tabbas Wannan kujerar mulkin tamu ce"
"gskyr ki ne mami tabbas SARAUTA TAH CE."
Murmushi jin dadi mami tayi kafin tayi kasa da murya tana sanar da yarima Yazeed irin mugun shirin da suka kulla akan yareema yaseer idan ya dawo.
Sosai yareema Yazeed ya nuna farincikin sa cike da Alfahari da mahaifiyar sa yace,
"harna kagara ya dawo mami tabbas baza muyi jinkirin batar dashi a Wannan masarautar ba idan ta kama ma saimu batar dashi a duniyar."
"Kana da fahimta Dana."
Cewar mami dake gutsirar tuffa a bakinta.
β’β’β’β’β’ββ
"When is he come back ummi?"
Cewar wata budurwa data sa wata matar a gaba tana mata tmby.
"I don't know suhaima"
ta Bata amsar tana kawar da Kai,
"wai kema fushi kike dashi ummi? Yanzu tohm da wanne ya yaseer zaiji? Da fushin mahaifin sa? Ko kuwa Dana mahaifiyar sa?"
Ajiyar zuciya fulani taja ranta babu dadi tace,
"banajin dadin Abinda yayanki yake yi suhaima gashi tun abin Yana a rufe harta Kai ga cewar memartaba yasan da munanan halayyar sa ta zaman sa a America, gaba1 baya son zaman kasar kusan 3months fa kenan da gama second degree dinsa Amma be dawo gida ba sbd gani yake ya takura ba zaiyi Abinda ransa yakeso ba..."
ta Ida mgnr tana fashewa da kuka.
"Oh..ummi pls don't.. Dan Allah ki daina zubarwa yaya kuka abin zaiyi Masa worst, just pray for him, Addu'ar mu yake bukata ummi especially you Dan Allah ki daina kuka pls."
Mahaifiyar yareema yaseer kenan Gimbiya Falmata. mata ta biyu kenan a wajen sarki Abdallah Wanda Allah ya azurta da yara biyu yareema yaseer sai kuma kanwar sa suhaima.
Dakyar dai suhaima ta lallashi mahaifiyar tasu tana me goge hawayen itama a boye cike da kewar yayan nata gaba1 yanzu batajin dadin zaman gidan ba karamin takura take ba idan ta kasance a cikin sauran yayunta mata yaran babbar matar sarki mama sarauniya itace matarsa ta farko yaranta hudu duka mata an aurar da biyu, saura biyu a gida. A yadda ake yada mata mgn a kaikace abin na Sosa zuciyar ta kowa ya fahimci yayanta womanizer ne, yanada biyewa mata sosai Kai kace Wanda akayi ma Asiri koda yake Asirin ne ma tunda Yana tare da magauta a kusa.
*ASALIN LABARIN*
πππ
*MASARAUTAR MANARAS*
Sarki Abdallah Usman Yusuf shine Nan sarki na goma sha biyu a cikin Wannan masarautar ta MANARAS dake jihar Adamawa state. Asalin fulani kenan Wanda suka tsatso kyau tun kaka da kakanni. Hajia Aisha itace Nan matar sarki ta farko wacce aka hadasu aure a dalilin iyayen su ita din 'yar abokin mahaifin sa ne wazirin Bauchi. Inda ta Haifa Masa yara hudu duk mata habiba, sumayya, hajara, Khadija.
Sai akan Hajiya falmata 'yar sarkin MANILA dake can jihar Borno, Yyi auren soyayya, Wanda haduwar su ta auku ne lkcn da akaje aikin hajji Acan Allah yyi nufinsa har suka kasance masoya daga Nan takai ga aure, Hajia falmata Saida ta shekara uku babu koda batan wata bare asa ran samun haihuwa Wannan abu ya dagawa sarki Abdallah hankali sosai a lkcn Yana a matsayin yarima bekai ga hawa karagar MULKIN ba amma ya sani matukar Yana Raye Toh kuwa dole a nemi magajin SARAUTA,
Hakan yasa suka dage da Addu'a ba dare ba Rana fatansa ko a wajen uwargida ko amaryar sa a samu cikin da namiji Amma shiru kkeji ba labari, Tsoho me ran karfe sarki Usmanu Yusuf mahaifi ga Abdallah ya kwallafa rai matuka yaga jikansa namiji Dan haka batare da shawarin komai ba Kai tsaye ya daurawa dansa Abdallah mata biyu tashi guda...abin ya girgiza sarki Abdallah da kuma matansa haddai ma Gimbiya Falmata da Bata taba haihuwa ba gwara ma mama sarauniya tanada yaranta hudu duk mata.
Bazai iya musu ga mahaifin sa ba Dan haka ya amince da auren Hakan ya jawo cikewar matansa hudu cif. Hajia Aisha, Hajia Falmata, Hajia zainab ta karshen Kuma Hajia Mairo. Zama ake zama na nuna isa da izza, amaren biyu har suka kwashe kusan watanni bakwai babu batan wata ko sau daya Wannan shine ikon Allah.
Ba'a dade ba sarki Usmanu tsohon da yyi shekaru sosai yyi murabus hade da nada dansa Abdallah sabon sarki na MASARAUTAR MANARAS. Take Kuma aka hado Masa da kwarkwarar sa sa'adiyya daya daga cikin bayi.
Dadi ne ya kama kwarkwarar sarki sa'adiyya a lkcn data je wajen bokan ta Markus yake shaida mata cewar lalle tana dauke da ciki harna sati hudu Kuma namiji ne Hakan ya faru ne bayan hada makwanci da tayi da sarkin MANARAS wato Abdallah. Take ta fara hango kujerar sarautar sarki, tana ayyana cewar nan gaba kadan itace Nan mahaifiyar magajin masarauta domin kowa ya sani sarki Abdallah bashi da Wani magajin har yanzu yaransa mata kanana da basu wuce 7yrs ba babbar cikin ce ma me shekara bakwai, dayar biyar mebi mata shida sai ta ukun 4 data karshen 3. Sauran matan sarki kuwa har yau jiya iyau babu me batan wata a cikinsu.
Baki a washe ta dubi bokan ta Markus tace,
"lalle ka cancanci kyauta mafi tsoka da girma ka jirayi Sako na anjima."
Kwarkwarar ta furta Hakan zuciyar ta fess ta mike cike da izza tanajin kanta itama wata ce a cikin masarautar MANARAS ta nufi sashen ta tana me kissima yadda zata sanar da sarki Wannan babban Albishir din zuwa anjima.
A Kuma Wannan ranar ne Wani babban Al'amari ya faru ga Gimbiya Falmata, Suna zaune Hajia Falmata dake duban matar dake gabanta ta kasa gaskata zancen Dr. Lami likitar masarauta dake kula da sashen matan sarki ta girgiza kai cikin Kara Tabbatar wa tace,
"iyakar gskyr kenan gimbiya."
Sujjadar godiya ga Allah S.W.T Gimbiya tayi cike da tsantsar farinciki ta cire golds din wuyanta da hannun ta harda Dan kunnen ta tana me mikawa Dr. Lami tace,
"Wannan karamar kyauta ce daga gareni ki jirayi sauran anjima."
Dr. Lami ta risina bakinta har kunne ta amshi dankareriyar sarka da warwaron da Gimbiya Falmata ta Bata hade da fadin,
"godiya nake gimbiya Allah ya tsare gaban ki da bayanki."
Murmushi Gimbiya tayi tana me daga mata hannu kawai alamar taje.
Tashi Dr. Lami tayi tabar dakin bayan ta aje mata duk wasu mgni da zata bukata.
Lumshe ido Gimbiya Falmata tayi tana me jawo tuffa a hankali takai bakinta Abinda take iyaci kenan kwanakin Nan Bata gane cewar ciki bane sai yanzu da Dr. Lami ta sanar mata tana dauke da cikin wata hudu, Kuma Namiji Kaiii she can't believe..., Abin kamar a mafarki. Koda yake ikon Allah ya wuce Nan.
Dake ranar girkin Gimbiya Falmata ne abin yazo mata a daidai ta yadda zata sanarwa da sarki Wannan babban Albishir.
Ado taci sosai tana shining fuskar ta cike da annuri ta isa sashen sarki Abdallah, Sarki Abdallah ya tari masoyiyar tasa hannu bibbiyu kamar yadda ya saba, Gimbiya Falmata ta dukar da kai tana Dan tankwasa hannu alamar jin kunya, sarki Abdallah ya dubeta a tsanake ya fahimci cewar lalle akwai Abinda take son sanar dashi Dan haka ya kamo hannunta a nutse yace,
"Zanso ace naji lbrn Abinda ya sanya gimbiyata farinciki a yanzun Nan Kuma ya sanya mata kunyar kasa gaya min komai"
ya Ida mgnr yana tallafo fuskar ta, murmushi Gimbiya tayi tana boye fuskar ta a jikinsa kunya ta sake rufeta Bata iya cewa komai ba, shima murmushin yyi yace,
"haba Mana gimbiyata fadamin Abinda ya sanyaki Annuri haka?"
Dakyar dai Gimbiya ta iya budar baki tace,
"muna kyautata zaton cewar kwai zai fashe a gidan Nan bada jimawa ba."
Tayi Masa mgnr a kaikaice. Dake sarkin akwai BASIRA dan-danan ya fahimci abinda takeson sanar Masa cikin tsananin farinciki yace,
"Dgske? Dan Allah na kusa samun Rabo daga jikin ki my luv?"
ya furta Hakan cikin sigar Jan hankali yana me shafo cikinta zuciyar sa fari tasss, cikin nuna Tabbatar wa Gimbiya Falmata ta Kara Dora Masa da cewar namiji ne...OMG! Sarki Abdallah ya Rasa yadda zaisa ransa sai kawai ya rungume ta Yana jujjuya ta a hankali a tsakiyar dakin Kai kace ba sarkin MANARAS bane koda yake idan ya kebe da matansa cire rawanin sa yake a gefe ya gurji soyayyar sa Dan bawa matansa hakkin su.
Turus tayi a bakin kofa kafarta na rawa zuciyar ta na zafi taja Baya a hankali hankalin ta a mugun tashe a daidai lkcn da kunnuwan ta
Suka jiyo mata cewar Hajia Falmata nada ciki Kuma na miji take hankalin ta yyi mugun tashi jikinta na rawa kwarkwara sa'adiyya ta juya ta barauniyar hanyar data biyo Dan ganin sarki bayan ta gama bada cin hanci ga bayin dake ta wajen kofar kafin ta samu ta wuce ita a dole so take ta cusawa Hajia Falmata takaici tunda tasan itace agun sarki Abdallah Kuma yafi sonta sai kuma ta jiyo Wannan mummunan labarin me figitarwa gareta.
Wannan shine mafarin lamarin..Wannan shine dalilin tsanar yaron da tun kafin yazo duniya ake yi Masa, ba ga matan uban ba, Baga kwarkwarar data haifo nata namijin ba, saidai yareema yaseer Dan gidan Gimbiya Falmata shine Nan babba ya bawa yareema Yazeed Dan kwarkwara wata biyar na haihuwa. Abinda Sam kwarkwarar bataso ba kenan, Kuma kauna da burin danta ya haye karagar MULKIN kullum Kara hauhawa yake, da tsanar yareema yaseer dake Kara tsanani a ranta musamman da duniya tasan irin mugun son da sarki keyi Masa tun Yana ciki har aka haife shi baya iya boye soyayyar dansa Hakan ya jawowa yareema yaseer bakin jini sosai, musamman wajen kwarkwarar sa'adiyya dake ganin ai ba Wani tsirar shekaru yareema ya bawa danta ba Amma idan yareema yaseer na wajen sai a mance da Wani yareema Yazeed a wajen Hakan yasa zuciya da zafin hasada yasa Bata Wani Bata lkci ba tasa bokan ta Markus ya juya Al'amura tashi guda yareema yaseer ya zama mazina ci sosai Wanda yake mu'amala da mata Sam baya gajiya dasu, tun yanayi a boye har mahaifin sa ya sani a lkcn daya kai Masa ziyarar bazata America ya tarar d gidan da yake zama mata biyu a jikin yareema daya na Masa tausa, dayar na lashe shi abin dai ba kyan gani, tun daga Wannan ranar mutuncin sa ya zube a idon mahaifin sa, fara'ar da yake gani ya dinke Masa Tsakanin su gaisuwa ce kawai.
Wannan Abu ba karamin dagawa Gimbiya Falmata hankali yyi ba da er autar ta suhaima wacce ta Haifa tun bayan shekara bakwai da haihuwar yareema daga kanta haihuwar ta tsaya. A bangaren kwarkwarar kuwa Hakan ba karamin dadi yyi mata ba domin a yadda taga sarki yafi bada hankalin sa kan yareema Yazeed yanzu sai abin yyi mata dadi matuka kuma mutanen gari na yawan ganin yareema Yazeed a Duk Wani sha'ani na SARAUTA, koda ace hawan sallah ne yareema Yazeed zaka gani, Hakan yasa ta sakankance da cewar SARAUTAR tasu ce, saidai kashh...
A Wannan Dan lkcn boka Markus yyi mata kiran BAZATA dukda basu shirya haduwa ba amma a yadda ya sanar da ita cewar Yana tafe ne da muhimmin Sako Kuma abin ya shafi yareema Yazeed da masarauta ba shiri sa'adiyya ta sameshi a Inda suka saba haduwa a cikin masarautar cikin yanayi nata na badda kama ta iske shi, a Wannan lkcn yake sanar da ita cewar a cikin binciken sa ya gano cewar lalle yareema yaseer ne Zai gaji Wannan masarauta bawai danta yareema Yazeed da take kwadayin yahau mulkin ba.
Wannan Abu ya dugunzuma hankalin sa'adiyya cikin zafin rai da dacin zuciya ta zare takobi hade da bashi umarnin lalle duk yadda za'ayi yasan yadda zai Samo mafita bazata lamunci Wannan bakin labarin ba.
*CIGABAN LABARI*
*Zaki iya biyan kudin ki yanzu a saki a paid group*
It's 300 via... Access bank 1445626295
Nusaiba Mustapha
Then show your evidence ta Wannan numberππ»
***