67-70
by @nooriman
🍇🍇PAPI NE!🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
EDITING IS NOT ALLOWED❌❌❌
Page 69-70
...........Amma ina baby'n Papi bata motsa ba, sosai hankalin su ya tashi, bare ma Nu'aym, kara jijjiga ta yayi yace "please baby wake up! Nine mahaifin ki, nine komai naki, ki tashi please karki min haka, kaka kin ga abinda kika janyo ko? Miye amfanin fadin gaskiyar? ga halin da gaskiyar ya jefa baby nah a ciki" ya karasa yana jijjiga ta ɗa ƙarfi, jiyoyin kansa sun mike sunyi rudu² alamun tashin hankali da bacin rai...
"Na shiga uku ni zainabu, Nu'aiymahtou ki tashi dan Allah karki mana haka, wayyo dana sani ban tona sirrin boye ba" kaka ta fada tana sharban hawaye da majina...
Cikin zafin nama Nu'aym ya dauke ta ya dora kan kafadun sa ya nufi hanyar waje da ita cikin tashin hankali, Al'ameen da Raliya dake sharban hawaye da kowa dai suka mara wa Nu'aym baya, bayan Al'ameen yace a mayar da Mariya a rufe har su dawo, larai kuwa ta tasa keyar ta tana hadawa da bugun ta har cikin guide room....
Wajen gate din Nu'aym ya nufa, duk kiran da kaka take masa bai amsa ba, burin shi kawai ya sada Nu'aiymah da hospital...
Mota Al'ameen yace kaka ta shiga su cimma Nu'aym a waje, ai kuwa ta shiga, haka ma sauran yan'uwan kowa ya faɗa mota.
fitar su ke da wuya suka ga Nu'aym ya tari keke napep har ya shige, hakan yasa su bin bayan shi....
Basu wani jima ba suka isa babban asibitin private, Sallamar mai napep Nu'aym yayi ba tare da ya tsaya amsar sanji ba ya nufi asibitin cikin gudu....
Ganin emergency ya sanya nurse suka turo gadon nan na marasa lafiya zuwa gaban Nu'aym, kwantar da ita yayi, kana cikin sauri ya shiga turo keken bai ma bari nurses din sunyi aikin su ba, domin a ganin sa baza su yi sauri ba.
Sai da ya shigar da ita emergency ward kana babban doctor din ya bukaci ya fita domin suyi aikin su, ba dan yazo ba, ya fita waje ya zauna yana dafe kan sa dake mugun Sara masa, hakika bai taba tunanin zuwan wanna ranar ba, bai taba tunanin zai ga wanna tashin hankalin ba...
Haka su kaka suka zauna a reception suna jiran doctor ya fito, Yayinda Nu'aiym ke bakin kofar dakin da take kwance yana jiran doctor ya fito, yaji halin da baby'n sa take ciki....
Tun Nu'aym yana kirga mintuna, ya dawo awanin, sosai hankali shi ya tashi, haka ma na su Al'ameen, kaka kuwa tun tana kuka muryar ta na fita har ya d'awo baya fita...
Sai bayan awa hudu likita ya fito yana share gumi, cikin sauri Nu'aiym ya nufi shi yana tambayar wani hali take ciki? Haka ma su kaka suka marmatso gaban likita suna jiran ya basu amsa, ajiyar zuciya likita ya sauke kana yace a biyo shi office....
Ai fa Nu'aym ne a gaba, bayan sun shige office din, Amma yayi musu kadan Saboda yawan su, hakan yasa wasu ke a waje, cire glass doctor yayi yace "ku kwantar da hankalin ku, shock ne ya kamata hakan yasa zuciyar ta bugawa da karfi, amma zata iya farfado wa a ko wani lokaci in sha Allah" ajiyar zuciya mai sauti Nu'aym ya sauke, wanda yasa su jin tausayin sa...
********
A tak'aice dai, kwanan Nu'aiymah biyu kana ta farfado da sunan papi a bakin ta, nurse da ta zo duba ko ruwan da ake mata ya kare, tayi saurin fita domin sanar da Doctor, a tare suka dawo da Doctor'n nan ya duba ya ga lafiyar ta kalau, sai rashin kwarin jiki.....
"P...pa..pi" likita yaji muryar Nu'aiymah ta daki dodon kunnen sa, a hankali.
"Sorry patient bari a kira miki shi ko" Idanunta a rufe ta jinjina masa kai, Yayinda hawaye yake zuba ta kunnen ta.
Fita likita da nurse suka yi, ai kuwa suka yi kicibis da Nu'aym "kaine papi ko?" Likita ya tambaya yana kallon Nu'aym ɗin.
"Eh nine" nu'aym ya fada cikin rawar baki.
"Sunan ka kadai take ta ....." Ai bai tsaya jin karashin ba, ya fada dakin, girgiza kai likita Yayi yana mamakin wanna shakuwar dake tsakanin su...
Taran likita su Al'ameen sukayi suka hada baki wurin fadin
"likita zamu iya shiga?"
"Eh toh! Amma banda hayaniya dan Allah" ya fadi haka suka Shiga wani daki da nurse, ɗomin duba marasa lafiya...
Bakin gadon Nu'aiym ya karasa da sauri, hannun ta ya riko cikin nasa, Yayinda yake shafa kanta yace "b...ba..by, how are you feeling now?"
Sosai abubuwan da suka faru suka dawo k'wak'walwarta, kuka ta fashe da shi tace "pa..pi am not fine, zuciyata ba dadi, papi is that true? Gaskiya ne cewa ba kaine ubana na ba? Na san karya ne ko papi nah?, dan Allah kace karya ne, bani da kowa sai kai da kaka ko? Tayaya yanzu zaku ce ba kune ahalina ba, shin kun gaji da zama da ni ne....."
"Shhhhh! Baby stop that" Nu'aym ya fada yana dora hannun sa kan labb'an Nu'aiymah yayinda idanunsa suka yi jajur kana ruwan hawaye ya cika cikin su taf...
"To gayamin papi, ina mahaifiyata? Duk lokacin dana tambaye ka bacin rai kake nunawa? Shin wacece mahaifiyata, ko bata duniya ne papi, dan Allah ka fadamin, a yau ka warware min komai papiiiiiiiiiiiiii" ta fada cikin kuka har wani sama² numfashin ta yake, duk da ta gama sanin komai dangane da rayuwar ta, amma brain dinta ya toshe, tamk'ar wacce bata fahimtar komai haka ta dawo...
"Nice mahaifiyar ki" suka ji muryar Raliya ya daki dodon kunnen su.
a zubure Nu'aymah ta juya, soaai ta kurawa Raliya dake kuka ido, ƴayinda ta kasa magana.
"Yanzu wata gaskiyar ko nace shaida zai bayyana kan shi" Al'ameen ya fita da sauri, basu fahimci inda kalaman sa suka dosa ba, hakan yasa suka bishi da kallon..
Mintuna biyar suka d'awo tare da likita, jinin Al'ameen da Nu'aiymah ya dauka domin ayi musu DNA TEST.
Bayan awa d'aya da rabi result ya fito, likita ya kawo, result kuwa ya nuna NU'AIYMAH JININ AL'AMEEN CE...
Ai nan wasu sabon ƙoke_ƙoke ya fara, cikin kuka Raliya tace " my daugther come, please come to me, come to your biological mother (ƴata zo gareni, dan Allah ki zo gareki, kizo ga mahaifiyar ki ta asali)" tamkar status haka Nu'aiymah ta tsaya.
Nu'aym ya mikar da ta, hannun ta riko har gaban Raliya dake sharar hawaye, kallon juna suka yi na yan mintuna kana Nu'aiymah tayi saurin fadawa jikin ta, wani yanayi mai dadi da bazai mitsaltu ba ya shiga ratsa ta, sosai wani dumin dadi da iska na musamman ya shiga kada Nu'aiyamah, tabbas uwa daban take, yanayin ne na musamman, Sosai suka k'amk'ame juna suna kuka, a yanda suke manne da juna zaka dauka yan biyu ne masu matuk'ar kama da juna (identical) shekaru kawai Raliya ta fi Nu'aiymah.
Sun jima a haka, Nu'aiym dauke kanshi Yayi, bai san yanda zai kasance ba, in har ace za a raba shi da baby'n shi...
Shima Al'ameen dake sharar hawaye tamkar mace Saboda tausayi ya nufe su, ya rungume Nu'aiymah a jikin sa yana jin raɗaɗɗin bakin cikin shekara sha shida ya kau, wani zunzurutun son 'yar sa ƴa shiga ratsa shi, daga karshe ma rungume su ukun Yayi cikin farinciki, haka sauran dangin aƙa shiga rungume Nu'aiymah kowa na Nuna farinciki sa...
Al'ameen da kan shi ya rungume Nu'aiym, sosai ya shiga godiya da nuna farincikin sa, hadi da Kyawawan addu'a agare shi, haka zalika kaka har kasa Al'ameen da Raliya suka duka a gaban ta suna godiya ga kaka hadi da add'uar fatan alkhairi, haka sauran dangin kowa yayi godiya a garesu, domin add'ua kadai zasu iya musu, amma duk wata Kalmar godiya tayi kadai, haka zalika baza su iya biyan su dawainiyyar da suka yi Nu'aiymah ɓa, sai dai suyi musu add'uar fatan alkhairi kawai...
Sun jima suna hira sosai, tamk'ar sun saba, Nu'aiymah zaune jikin Raliya da Al'ameen, da dangi ta ko ina, meya fi wanna farinciki? Fuskar Al'ameen tamkar farin wata dan farinciki, kowa dai ka gani yana cikin farinciki, nan aka shiga kiran yan'uwa na nesa dana kusa cewa anga 'yar raliya da aka sace shekaru sha shida da suka wuce, sannan an ga sabon ɗan da ta haifa, kuma ikon Allah sai ya da kani suka hadu, sannan mutumin daya sinci yayar(Nu'aiymah) shine ya tsince kanin (Adeel) wanna ba komai bane face ikon Allah, sun kuma yi mamakin jin cewa Mariya ce mai wanna rashin imanin, wani karin farinciki kuma Raliya ta warke. Ai fa nan labari ya shiga zaga dangi na nesa dana kusa, Sannan kowa yace dole zai so domin ganin Nu'aiymah...
ADEEL ne ya katse musu hira da kukan sa, mika wa Raliya kaka tayi tace "'yar nan, bashi ya sha, acici mala'ikun tauna ya fara, ya ma yi kokari tun shekaran jiya madara yake sha, bayan ga uwar sa" dariya suka yi jin kaka tace acici mala'ikun tauna...
"Baby zo ki ƴi sallar da ake bin ki kinji, na siya miki MacLean da brush" ya fada yana zura hannu a aljihu, ya matso MacLean din a brush kana ya mika mata, bata fuska tayi tace "PAPI ni sai ka raka ni"
"your wish is my command 'yar papi" ya fada yana riko hannunta.
"Kai Nu'aiymahtou yanzu har bandakin sai ya kara ki saboɗa sharri, wanna iyayin har ina, kai ma Allah ya kara, ba kai ka gama shagwa'ba ta ba" kaka ta fada.
Take kuwa Nu'aym ya gwaleta, ai fa nan yan dakin suka sanya dariya, domin draman ya burge su ainun.
Da Kallo su Al'ameen suka bi su Nu'aiymah, basu damu ba, domin sun sa Nu'aiymah ta riga ta saba da papi ta yanda rabuwar su abu ne Mai wahalar gaske, kuma zai dauki lokaci kafin ta daina masa kallon uba.
Nan kaka baki ya bud'e, ta shiga basu labarin draman su, da gwaletan da suke yi, da shakuwar su, hadi da yarintar Nu'aiymah. Sosai su Raliya suka sha dariya Kuwa, duk da sunyi mamakin tsananin shakuwar su, domin wasu ma tare da uban su na ainahi suke, amma basu yi irin wanna shakuwar ba, sun kuma ji dadi da Nu'aym ya taka rawar matsayin uba agareta, ya bata tarbiya, domin za a iya cewa Nu'aiymah rainon papi ce! Tarbiyan papi ce!! amma kaka ma ta taka muhimmiyar rawa a rayuwar 'yar tasu, take Nu'aym ya samu matsayi mai girman gaske a zukatan su, bare ma Al'ameen da Raliya...
Har Nu'aymah ta gama rama salolin dake kanta hajiya kaka bata daina basu labari ba, ganin jikin Nu'aiymah garau yasa doctor ya basu sallama...
Su Al'ameen sun so tafiya jigawa a yau, amma kaka tace su tafi gida wajensu su kwana idan yaso gobe sai su tafi, tunda yamma ya fara yi, basu musa ba, domin suma zasu so su ga muhallin da yar tasu ta rayu tsahon shekaru masu yawa, bayan duk sun biya charges din asibitin kana kowa ya shiga mota suka nufi gidan....
Share fisabilillah