77-78
by @nooriman
🍇🍇PAPI NE!🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
EDITING IS NOT ALLOWED❌❌❌
Page 77-78
.....Nu'aym kuwa K'anshi ya rufe a daki, yana jin wasu tashin hankali a jikinsa, abinda yake ji yafi zazzabi, tamk'ar aka saka aɗɗah ana daddatsa ko wani part na jikinsa, ya kasa yarda cewa baby'nsa za a yi wa aure, kuma an rasa waye mijin sai ranar auren za a sanar, Shi kam ya na cikin tsaka mai wuya...
Ta bangaren Nu'aiymah kuwa sosai ta damu da rashin kiran da papi da bai yi ma ta ba, amma da tayi magana su Al'ameen kan kwantar mata da hankali hadi da lallaɓa ta.
***************
*RANAR DAURIN AURE*
A yau ya kasance ranar da za a d'aura wa Nu'aymah aure, ko ina dangi ne a cike, duk da cewa basu gayya ci wasu mutane da yawa ba, amma hakan bai hana bikin cika ba, Saboda dangin su yawa garesu...
Da misalin karfe goma sha daya na safe, kamar a mafarki aka d'aura auren NU'AYM AHMAD TARE DA NU'AIYMAH AL'AMEEN BISA SADAKIN NAIRA DUBU DARI.
Take fusk'ar Al'ameen ta wad'atu da murmushi, dama yasan cewa babban yayan su zai yi adalci, amma rashin sanin abinda ke ransa ya sanya shi cikin damuwa da wasi'wasi.
Fidda tsadaddiyar wayar sa yayi ya dannawa Nu'aym kira wanna karon domin yi masa albishir. Domin sosai yake son Nu'aym tamkar dan cikin shi ko yace kani, domin sam baya masa kallon suruki.
Kwance yake gabadaya babu kwari a jikin sa, banda fuskar sa da mutum zai gane cewa yana cikin tarin damuwa babu abinda zai sa mutum yasan cewa akwai damuwa a tare dashi, domin bai rame ba, Saboda ginanan jikin sa, ga kewar baby'nsa daya yi masa yawa, ya ma kasa Kiran ta, abubuwa sun yi masa yawa yama rasa abun yi.
Ringing din wayar sa ya sanya shi bud'e idanunsa, har ta katse bai daga ba, kira na biyu ne ya sanya shi kallon wayar, lambar daya gani ya sanya shi bud'e idanunsa gabansa na faduwa...
Hannu na rawa ya daga kiran, cikin kamala yaji muryar Al'ameen yace "mijin Nu'aiymah Alkawarin Allah ya cika, a yau dai burin mallakar 'yarka Nu'aiymah ta cika, yanzu haka muna wajen daurin aure, an d'aura, Allah Ya tabbatar da alkhairi, ya baku zaman lafiya" yan fadin hakan ya katse Kiran, yana murmushi.
Tamk'ar gunki haka papi ya tsaya ya zubawa wayar ido, sosai yayi mamaki, take ya kara jin sautin amon muryar Al'ameen na sanar dashi ya zama mijin Nu'aiymah.
can kuma kamar an tsikare shi da allura ya kwala wani uban ihu cikin zallan farinciki...
Birgima ya shiga yi kan gadon sa, yana murna tamk'ar yaro dan shekara biyar, Kaka da ta shigo da gudu ta tsaya turus ganin abinda yake yi, ganin kaka ya sanya shi durowa daga gadon ya nufe ta, ganin haka ya sanya Kaka sarkin tsoro rugawa a waje da sauri abin Dariya, taku uku yayi ya rungumeta yace "kaka na mallaki baby, zamu rayu da baby nah kamar yadda muka fara, kaka ki yi farinciki Na zama mijin baby Nu'aiymah" ya karasa a nutse, Yayinda hawaye zallan farinciki suka zuba masa...
fadin farincikin kaka ba ta lokaci ne, sosai tayi farinciki da wanna auren, har da kukan ta. Nan dai suka shiga shirin tafiya jigawa, wani hada'dd'en farin shadda babban riga papi ya sanya, duk da ya taba sawa sau daya, amma tamk'ar sabo haka yake, hula, takalmi, agogo, duka to match ya saka, sosai yayi kyau ya kuma fito sak angon Nu'aymah sai baza kamshi yake.
Bayan ya fito da babur dinsa, suka rufe gidan hadi da kashe abubuwan wuta tunda ɓa nan kusa zasu dawo ba, Kaka da ta sha sabuwar atamfa da gyalen ta ta dane babur tana jawa papi kunne kan karya yi gudu da ita a babur da haka suka tafi, fusk'ar su fess Saboda farinciki, bare ma Nu'aym.
Ta bangaren Habib Husain kuwa kamar yadda yayi tunanin hankalin sa zai tashi sai yaga ba haka bane, duk da tabbas yaji ba dadi rasa K'yak'yyawar yarinya kamar Nu'aiymah, amma ikon Allah hankalin sa bai wani tashi ba, ya kuma sanar da mahaifiyar sa cewa aje a nema masa auren yarinyar nan daya dan shanshantar da maganar ta mai son waseelah, inda aka saka lokacin biki wata uku masu zuwa...
Wanna kenan.
***************************
Bangaren Mariya kuwa da kyar ta samu wani mai a kori_kura ya taimaka ya saka ta a bayan booth zuwa garinsu.
Sosai iyayen ta suka yi mata fada, kana sunyi fushi sosai da ita, ba kuma halin Kiran Al'ameen su roke shi tunda dai saki uku ne, haka ta cigaba da zama a gidansu tana jinyar kafar ta, gashi ta tarar gidan nasu ba kamar da ba, kullum sai sun ci tuwo gashi ita ta saba da abinci masu rai da motsi.
Ga raini wurin kannenta biyu mata da suka rage basu yi aure ba, komai dai ya lalace mata, kullum cikin nadama take, domin bata ga ribar muguntar da ta yi ba, tunda daga karshe ma itace ta kasance cikin mayuwancin hali...
*****
Sai karfe biyu na rana suka iso Jigawa, da taimakon kwantance da Al'ameen yayi musu suka isa har gidan, sosai suka tarar da gidan a cike babu masaka tsinke, Al'ameen da kanshi yayi musu iso, bayan sun gaisa sosai domin har runguman Papi Al'ameen yayi, domin tabbas yana kaunar Al'ameen kamar yadda yake kaunar 'yarsa Nu'aiymah.
A sitting room suka zauna, nan aka kawo wa su kaka abinci iri² yayinda wasu cikin dangi ke zuwa kawo gaisuwa wa kaka musamman da suka san cewa sune suka kula da Nu'aiymah har girman ta, kaka fadi take
" A kawo min Nu'aiymahtou na ganta, nayi kewar ta"
ai nan Al'ameen ke sanar da ita cewa
" kaka ai ba ta ma san cewa bikinta aka yi ba, domin babu Wanda ya sanar mata, dama jira muke idan kun zo sai a yi komai a tare" ƴa fadi haka, hadi da kiran Raliya...
"kanwata ku zo da Nu'aiymah, ga su kaka sun iso muna setting room" ya fada yana katse kiran....
comment dinku ya yi kasa fa, dan kun ga na kusan gamawa ko.🥺
Share fisabilillah habibtie's
Comment
Noor💋