A CIKIN DUHU

09

by @kitty

A CIKIN DUHU...

Kitty💕

Wattpad @ Mssmeemah


09


Rufe baki Fatima tayi kuka na ‘kwace mata ta danne camerar a kan gadonta, girgiza kanta take zuciyarta na wata irin ‘kuna, yanayin da d’an uwanta ya mutu a ciki ya matu’kar girgiza ta ji take inama zata iya taso dashi ya samu ya nemi gafarar ubangiji kafin mutuwarsa, ya mutu a mummunar hanya da mummunan nufi a zuciyarsa “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, ya Allah ka gafartawa Abdulyassar Allah ka ji’kansa ka yafe mishi”. Tana wannan kukan Umamima ta turo ‘kofar d’akinta muryarta a sanyaye tace “Sister Abbu na kiranki”.


‘Dago kanta tayi tace “kice mishi ina zuwa”. Umaima bata fita ba ta nifi gadon Fatima ta zauna a gefenta ba tare da tace komai ba ta fara shafa bayan Fatima cikin sigar lallashi har fatima ta d’an samu nutsuwa suka nufi wurin Abbu. Tayi tunanin zaiyi maganar mutuwar sai taji baice komai ba yana ta jan yaransa da hira su kuwa kallonsa kawai sukeyi tamkar ba’ko musamman hammad da yake zaune a cinyar Abbu ya ‘kura mishi idanu tare da d’aga gira. Zee kuwa can gefe ta koma ta zubawa TV idanu umaima ce kawai ta zauna a gefensa yana mata tambayoyi tana amsawa har bacci ya fara d’aukansu.


Abbu da kansa ya kai kowannensu d’aki sannan ya koma parlor suka zauna shi da fatima, ba tare da ‘bata lokaci ba yace “fatima nasan zaki fi mahaifiyarki sanin halayen abdulyassar, banaso mu fad’i komai a yanzu domin mala’iku suna zagaywa suna Kar’bar mishi shaida, amma kina tunanin yarinyarnan ce ta kasheshi?”


Shiru Fatima tayi na tsawon lokaci sannan tace “nima ban saniba”. Numfashi Abbu ya sauke yace “shikenan tashi kije abinki”.

__________________________

“Hajiya kiyi mana bayanin abinda ya faru dalla dalla ni kuma zan tabbatar da hukunci ya hau kan yarinyarnan”.


Gyara zama Mum tayi tace “yarinyarnan na d’aukota ne wata shida da suka wuce tana tayani aikace-aikacen gida da kula da yara. A yau mun fita da yaran d’auko mahaifinsu a airport muka dawo muka tarar da d’akinsa a rufe domin shi baije ba baya jin dad’i, ina bud’e d’akin na sameshi a kwance ita kuma tana dur’kushe a kansa. Muka kaishi asbiti aka sanar mana ya rasu”.


Rubutu d’an sandan yayi sannan yace “dama tana nuna ‘kiyayya gareshi ko sauran yaranki? Ko kuma tana da wasu halaye wanda kike zargi?”


Shiru Mum tayi tana tunani sannan tace “gaskiya ba nace ba tunda yarana babu wanda ya ta’ba kawo min complain a kanta har shi marigayin sannan babu wasu alamu da take nunawa da zan zargi matsala, infact muna da CCTV camera a parlor ko da tayi wani abun zan iya gani”.


“Masha Allah abinda za’ayi ita ki barmu da ita zan saka a tambayeta sai ta fad’a da bakinta ita ta kasheshi sannan mu samu zuwa gobe ko jibi a mi’ka case d’in kotu, saurin amincewa da zatayi da laifinta ne zai taimaka ku shiga kotu da wuri idan bata amince ba zata jima anan gaskiya”.


Cikin damuwa Mum tace “duk abinda zakuyi mata kuyi idan ta kama ku karairayata ma duk kuyi ta furta da bakinta ita ta kashe min d’a, yanda ta kashe d’ana itama sai na tabbatar ta d’and’ani zafin mutuwa”.


Murmushi yayi yace “Hajiya indai wannan ne karki damu matu’kar zaki kula da wad’anda zasu tambayeta to zasu miki abinda kikeso, yanda za’ayi ki basu na shayin dare tunda kinga kwana zasuyi yanda zasu samu ‘karfin tambayarta yanda ya kamata”.


Babu wata-wata Mum ta zaro 10,000 a jakarta tace “gashi, idan na dawo da safe zan basu na kari indai zasuyi abinda ya kamata”.


Mi’ka kud’in yayi daidai da shigowar wannan d’an sandan da ya tsaya bincike, yana shigowa ogan nasu ya had’e rai yace “SERGEANT AHMAD me aka samu?”


Pocket knife d’in da ya tsinto ya ciro a cikin leda ya mi’ka mishi yace “wannan ne kawai suspicious evidence da na samu a cikin d’akin. Itama na duba nata d’akin babu wani abu a ciki”.


Kar’ba ogan nasu yayi yace “Good job, saida safe”. Kallonsa sergeant Ahmad yayi ya kalli Karime dake bayan canter a tsugune ko motsawa batayi saidai ba wannan ne damuwarsa ba kud’in da ya gani a hannun ogansa shine abinda ya tsone mishi idanu domin 700 ce a aljihunsa kuma ya fito ya bar kakarsa ba tareda kud’in cefane ba, tunaninsa ko 1000 ne ya ‘kara mishi ya samu ya musu cefane amma yafi kowa sanin halin ogan nasu. 


Fita yayi tareda alwashin wannan case d’in ba zai bar wajennan ba sai ya yagi iya rabonsa shima domin ya lura matar tana shirin fidda ko nawa ne. Yana tsananin bu’katar kud’i saboda haka zai shiga ya tabbatar ta samu abinda takeso idan har zata fiddashi daga talaucin da yake ciki.


Kiran Inna yayi a waya ya tambayeta abinda zai taho dashi tace babu komai amma yafi kowa sanin halin innarsa, zata iya zama da yunwa ta kwana da ita akan ta bud’e baki tace mishi babu wani abu.


Shinkafa ya siya rabin kwano sannan ya tafi gida. ‘Karamin gida ne sosai domin d’akuna biyu ne kawai a ciki da band’aki da kitchen sai ‘karamin tsakar gida. Sallama ya doka Inna ta amsa mishi daga d’aki tana mishi maraba.


‘Dakin inna ya nufa ya zauna tareda maida numfashi suka gaisa tace “tunda naga kayi dare na san akwai abinda ya faru, anya Ahmad ba cin hanci ka sake Kar’ba aka kama ka ba?”


Murmushi yayi saidai ransa babu dad’i amma bai nuna mata ba yace “Inna tunda nace miki bazan sake Kar’bar kud’in mutane a titi ba na dena Kar’ba, wallahi wani case ne aka kawoshi a darennan ‘yar aiki ta kashe d’an gida shine oganmu ya turani aka d’auko ta da wasu abubuwan sai yanzu na samu na kai mishi”.


“Kai amma abu baiyi dad’i ba Allah ya kyauta. Me ya mata ta kasheshi?” Inna ta furta tana ajiye carbinta a gefe, cikin ko in kula yace “ban sani ba amma dai ko me tayi zata sha wahala saboda yaron d’an masu kud’i ne sosai”.


Shiru Inna tayi bata sake tankawa ba ya mi’ka mata shinkafar da ya siyo da canjin yace “yau na fita ban bar komai ba ga wannan gobe sai a samu ayi ko da abin kari ne ko abincin rana”.


Murmushi Inna tayi tace “Allah yayi maka albarka ya ji’kan iyayenka. Ai dake ma bayan fitarka aka kawo min gero daga ‘kauye mai yawa sosai, na gyara shi na daka da safe sai nayi mana kunu”.


Murmushi yayi yace “masha Allag aiko sun kyauta da suka kawo, bari na shiga daga ciki”.


“To saida safe Allah yayi maka albarka ya tashe mu lafiya”


*****

Da Sasafe Ahmad yayi shirin fita saidai duk sammakonsa Inna ta rigashi har ta dama kunu ta ajiye masa da tuwon ‘bula da tayi d d’umamen na dare. A gurguje yaci tuwon ya fita domin tun biyar ogansu ya kirashi yace ya shigo da wuri.


Yana shiga police station d’in nasu ya fara jin shesshe’kar kuka, sai yanzu ya tuna da mai aikin da aka kawo bai bi ta kanta ba yaje yayi signing da abubuwan da suka kamata sannan ya tambayi masu night duty “tayi confessing kuwa?”


“Inafa, ai nidai ban ta’ba ganin yarinya irinta ba ga laifi ‘karara amma sai rantse rantse take mana ba ita ta kasheshi ba. Mun tambayeta har saida tayi passing out three times but still babu sauyi yanzu zamuyi handing over gareka saboda matarnan idan tazo taji bata amsa laifinta ba zamu shiga matsala, oga kanshi tun 4 am ya kiramu yana fad’a mun gaza gudanar da aikinmu”.


“Okay babu matsala ai ko bata amsa ba nasan yau oga zai shigar dasu kotu a can zata fad’i gaskiya ko bata shirya ba. Bari naje na ganta”.


A kwance ya tarar da karime bata motsi sai shesshe’kar kuka da takeyi, rigarta tayi kaca-kaca da jini ta wurare da dama ga gashin kanta ya bayyana, cikin muryarsu mai firgitarwa sergeant Ahmad yace “ke tashi ki zauna!”


Da ‘kyar karime ta zaune tareda jingina a bangon cell d’in mai bala’in datti, d’ago kanta tayi suka had’a idanu da Ahmad lokaci guda wani irin yanayi ya ziyarceshi da ba zai iya fasalta shi ba.


Fuskarta tayi rud’u-rud’u da shatin mari haka rinannun idanuwanta sunyi ‘kwala-‘kwala dukda uban kukan da tayi, sunkuyar da kanta tayi jin jiri ya d’auketa wanda yasa gashin kanta ya zubo gefen fuskarta ya sauka a ‘kirjinta, rabon da karime ta zauna babu hula ko d’ankwali tun ranar da aka mata wanka a gidan Mum sai gashi yau ta kwana da kanta a bud’e, d’an ‘karamin ribbon d’in ma ya cire saboda juyin da take jikinta kuwa ita kad’ai zata iya fasalta abinda takeji domin ciwukan dake zubda jini ma suna da yawa. Karime dai ta gama yanke rai da rayuwa jira kawai take su ‘karasa ta, domin idan har wannan dukan zasu cigaba da mata da sunan tambaya tabbas tana gab da amsa laifin wannan kisan gara ayi mata mai gaba d’aya ta huta da rayuwa.


Ahmad kuwa tunda ya ‘kura ma karime idanu yaji yawun bakinsa ya ‘kafe saboda wani irin kyau da tayi masa a yanayin da take ciki, tausayinta ne ya kamashi sai kuma ya tuna abinda ya kawoshi ya tsuguna ‘kofar cell d’in yace “ke taurin kai ba zaki fito ki amsa laifinki ba kin gwammace ki sha wahala ko?”


Girgiza kai tayi ta bud’e bakinta da niyyar magana saida babu kalmar da ta fito daga bakinta sai sha’kewa da tayi ta fara tari ya tashi ya d’auko pure water ya bud’e cell d’in ya shiga, tsugunawa yayi ya mi’ka mata ruwan da ‘kyar ta Kar’ba ta sha cikin dasasshiyar muryar tace “ba ni na kasheshi ba”.


“Idan ba ke kika kasheshi ba me kikeyi a d’akinsa a wannan lokacin ‘kofarsa a rufe?”


Hawaye ne ya gangaro fuskarta ta girgiza kanta tana cije baki, a cikin duhun rayuwarta bata ta’ba ganin duhu irin wannan ba. Ta rasa uwa da uba da duka ‘yan uwanta amma ko gudun ceton ranta bai kai wannan halin da take ciki ‘kuntatawa zuciyarta ba. Samari da dama sun mutu sanadiyyarta yanda ake fad’a a ‘kauyensu amma mutuwar sanin wawo da Abdulyassar su suka jefata cikin bala’i. Mutuwar sanin wawo tayi sanadin mahaifiyarta ta yiwu mutuwar Abdulyassar itace ajalinta. Gara ma danginsu su ‘kare ko a samu nutsuwa cikin al’umma domin yanzu kam ta aminta ita d’in masifa ce a cikin mutane.


Tambayoyi yake mata amma hankalinta ya fara gushewa sama-sama take jin muryarsa domin bacci ke d’ibanta dalilin jinin dake zuba a jikinta, a jinginen da take ta lumshe idanunta tayi loosing consciousness.


Ta’bata Sergeant Ahmad yayi yaga ta ‘bingire ya sanya hannunsa yaji numfashinta na fita amma sama-sama. Fita yayi cikin sauri ya d’auko ruwa ya kwara mata tayi wani irin firgita ta sake komawa ta rufe idanunta. Wannan ba sabon abu bane a wurinsu amma sai yaji hankalinsa yayi matu’kar tashi yanayin da yarinyar take ciki. Fita yayi daga cell d’in sukayi kaci’bis da ogansu ya shigo tareda Abbu



Free page


Littafina na kud'i ne 500 kacalđŸ„°đŸ„°ku nuna min solidarity ni kuma zanyi ‘ko’kari na baku abinda zu’katanku suke so😁😁


Account details

0472624453

Musa maryam Aminu

Gtbank


Ki a tuntu'beni ta wannan number

***