A CIKIN DUHU

10

by @kitty

A CIKIN DUHU...

Kitty💕

Wattpad @ Mssmeemah


GAMJI WRITERS ASSOCIATION


10


“Sunana Isma’il Muhammad nazo Bailing karima ne wadda matata ta shigar da ‘kararta jiya”. Abbu ya fad’a bayan DPO ya bashi wurin zama sun gaisa a office d’insa. 


Hard’e hannuwa DPO yayi yace “ranka ya dad’e ai bazia yiwu ba wanda ya shigar da ‘kara dole shine zai janye sannan wannan magana ake ta kisa, ko da kun janye dole yarinyarnan a hukuntata domin ha’kkin gwamnati ne ta hukunta mai laifin da aka kama a ‘kasarta”.


Had’e rai Abbu yayi yace “zancen banza zancen wofi, yaronnan d’ana ne kuma na fito nace a janye. Idan har gwamnati tasan da ha’kkin ‘yan ‘kasarta da tun fari yarinyar bata zo aiki gidana ba balle wannan tsautsayin ya rutsa da ita”.


Wani murmushi DPO yayi yace “Alhaji idan har ka cigaba da magana irin wannan zamu saka ka a jerin suspects a cikin wannan case d’in. Tunda har case yazo hannunmu ka barmu muyi aikinmu kawai”.


A fusace Abbu ya fito daga office d’in ya kalli Sergeant Ahmad dake tsaye a wurin, sunkuyawa Sergeant Ahmad yayi kad’an sannan ya danna kansa cikin office d’in DPO.

__________________________


Mata ne fal a cikin gidan ana ta harkokin d’aura tukwane, yanda ake kaiwa ana kawowa ba zaka ta’ba tunanin mutuwa akayi ba daga cikin gidan saidai idan ka fita kaga rumfunan maza a waje. 


Mum tana d’aki da wayarta a kunnenta tana kiran Atine saida ta mata kira uku a ba hud’u ta amsa. Sallama tayi saidai ba tareda Mum ta amsa mata ba tace “inason kizo gidana da yamma ke da matar da ta bani ‘yar aiki”.


“To? Hajiya wani abu ne ya faru?” Atine ta tambaya gabanta na fad’uwa Mum tace “ba wani abu bane inason dai ganawa da ita ne”. Atine dai zuciyarta bata aminta da hajiya ba amma tayi mata al’kawarin zasu je bayan magriba.


Mum na gama wayar ta fita parlor nan dai mata suka hau mata gaisuwa tareda mi’ko bu’katu akan girkin da akeyi ita kuma tana zaro kud’i tana mi’ka musu. Bayan ta gama sallamarsu ta nufi d’akin Fatima domin tunda mata suka fara cika gidan ‘yan uwa da abokanan arzi’ki fatima ta rufe kanta a d’aki. Tura ‘kofar Mum tayi tareda sallama ta zauna kan kujerar mudubin dake d’akin tace “Fatima ba zaki fito cikin mutane ba? Cousins d’inki sunzo Atleast ki fito su d’ebe miki kewa”.


Murmushi fatima tayi tace “Mum I’m okay i just need some me time. Mutanennan sunyi yawa ciwon kai zasu sakani kuma ba komai ya kawosu ba sai cin abinci. Indai mutanennan suna gidannan bazan iya fitowa ba”.


Numfashi Mum ta sauke tace “shikenan bazan miki dole ba fatima, Allah ya ji’kan Abdul nasan abinda kikeji shiyasa ma zan sanar miki wannan tun da wuri. Idan har Allah ya kaimu akayi kwana uku aka ‘kare zama zamu shiga kotu inaso ki bada shaida akan Karima”.


Zumbur Fatima ta tashi ta zauna tace “Mum kotu fa kikace? Shaida a kan me? Bana nan ta kasheshi bazan iya shaida akanta ba kuma ko da shaidar halayenta zanyi batada wani mummunan hali da muka gani a watanni shida da tayi damu”.


“Nasan bakya nan nima ai bana nan amma dole zamu bada shaida kuma idan munaso a d’aure yarinyarnan ko a mata hukunci mai tsanani sai mun ‘kir’kiri wani abun mun fad’a. Idan aka je kotu kice tana da kwad’ayi da son duniya da dai duk abinda zai saka a hukunta yarinyarnan. Karki manta d’an uwanki ta kashe idan har kasheta akayi ba ko d’aurin rai da rai ba zamu ta’ba samun kwanciyar hankali ba”.


Girgiza kai Fatima tayi tace “Mum duk abinda nasan gaskiya ne kan yarinyarnan zan fad’a amma bazan iya mata ‘karya ba. Mum nifa ina tunin
 karima ba itace ta kashe Abdulyassar ba”.


Wani irin kallo da mum ta jefawa Fatima tamkar ta watsa mata garwashin wuta tace “kema Abbu ya kitsa miki ko? Fatima adalci zaki bi ko son zuciyar mahaifinku?”


Hawaye ne ya gangaro fuskar Fatima tace “Mum ba son zuciya bane gaskiya ce. Nasan abinda ke faruwa tsakanin Karima da Abdul kuma ni na hana ta fad’a miki saboda nasan korarta zakiyi ki goyi bayan Abdul. Da idanuna naga abubuwa da dama kuma a waje ma ina samun complain dangane dashi from their school. Mates d’ina na fad’a min abinda yake ma ‘kannensu da sauran students. Mum kiyi ha’kuri amma bazan iya shaidar Abdul a kotu ba. Idan har case d’innan ya cigaba Mum za’a ‘baro abinda bazai ma kowa dad’i. Abdul yana bu’katar tsananin addu’a daga garemu musamman ma ke mum. Dan Allah a janye wannan case d’in ki kawo ta gida ki tambayeta da kanki abinda ya faru zata fad’a miki. Ni kuma inada shaidar da zan bayar”.


Kafe da idanu Mum tayi tace “yau kwanan d’ana d’aya a cikin ‘kasa amma ke da mahaifinki kuna nuna halin ko in kula da abinda aka aikata mishi”.


“Mum ba halin ko in kula muke nunawa ba, bansan dalilin Abbu na aikata haka ba amma ni inada dalilina. Dan Allah mum ki janye wannan ‘karar zan fad’a miki komai. Indai aka hukunta karime a kan laifin da bata aikata ba Abdul bazai samu nutsuwa a ‘kabarinsa ba dan Allah mum ki bari ya samu rahmar ubangiji ko yaya take”.


Ran Mum ya gama ‘baci ta fice a fusace bata sake zuwa d’akin Fatima ba har dare yayi. Shima Abbu bai shigo gidan ba ko sau d’aya domin zaman makokin ma gagararsa yayi, zuciyarsa ta kasa aminta da cewar karime ce ta kashe yaronsa sannan akwai wani abu na daban da yake ji a zuciyarsa, tamkar yana da alhakin kula da ita da tsaron rayuwarta haka nan ya tsinci kansa cikin damuwa saboda laifin da aka d’aura mata.


Lokacin da ya shiga gida babu kowa ya nufi d’akinsa ya watsa ruwa sannan ta d’auko waya yana duba messages da sukayi da Abdulyassar, a message d’insa na farko yake fad’a ma Abbu bazai je d’aukoshi daga airport ba saboda akwai surprise da zai shirya masa, murmushi Abbu yayi yace “Abdulyassar ashe surprise d’in mutuwarka zan samu. Wannan shine mafi munin surprise da na ta’ba samu a rayuwata. Allah yayi maka rahma yasa ka huta”.


Knocking yaji anyi ya amsa Fatima ts tura ‘kofar a hankali ta shiga, ajiye wayar yayi ganin yanayinta yace “yaya dai Fatima?” A gefen Abbu ta zauna ta d’aura kanta a kafad’arsa tace “Mum ta fita Station ita da wasu mutane”.


Shiru yayi lokaci guda ta fashe da kuka tana fad’in “Abba dan Allah kar ka bari a hukunta Karime wallahi ba ita ta kashe Abdul ba”.


Ba tareda ya kalleta ba yace “Fatima mahaifiyarku ce kawai take da wannan damar domin naje station d’in domin su bada belinta suka ce wanda ya shigar da ‘kara shi zai janye kuma ba’a janye ‘karar kisan kai. Banida hujjar da zan kareta in fact sun sakani cikin suspects ma saboda na nemi belinta”.


D’ago kanta tayi tace “to Abbu kenan idan akwai hujja da shaida mai ‘karfi za’a saki karima?”


“ ‘kwarai kuwa. Indai akwai hujja mai ‘karfi ba zasu ri’keta ba. Fatima ba wai goyon bayan yarinyarnan nake ba domin ina jin ciwon rashin d’ana, banaso muyi hukuncin da zai dinga bibiyar mutuwar Abdul saboda son zuciyarmu. A yanayin da likita yayimin bayanin mutuwar Abdul jikina ya bani akwai ‘boyayyen al’amari a ciki”.


“Abbu inada shaida, shaidar da zata tabbatar ba ita ta kashe Abdul ba. Nidai Abbu a dena maganar mutuwarnan dan Allah a bar Abdul ya runtsa a makwancinsa mu bishi da addu’a kawai”.


Kafin Abbu ya amsa ta mi’ka mishi memory card d’in hannunta ba tareda ta sake cewa komai ba ta fita daga d’akin.

__________________________

Kira Atine ta dinga surfawa Hajiya sa’a bata sameta ba, ‘karshe ‘kofar gidan Hajiya sa’a taje ta zauna domin bata nan. Ta d’auki kusan awanni uku a wajen sannan Hajiya sa’a ta dawo.


Da murmushi ta tari Atine tace “kiyi ha’kuri nasan kin kirani wallahi wayar ce ta fad’i a d’an sahu tayi daga-daga. Kin dad’e ne anan?”


“Haba Hajiya sa’a meye na tambaya tunda kika ganni a zaune ai kinsan na dad’e a wurinnan nayi kusan awa biyar”.


Murmushi Hajiya sa’a tayi tana bud’e gidan tace “to ai ko ni banyi awa biyar da fita ba. Mu shiga ciki ki samu ki sha abin sanyi kinsan nayi fridge sabo yanzu bana rabo da ‘kan’kara da ruwan sanyi”.


Yashe baki Atine tayi suka shiga saida ta take cikinta sannan ta baje tace “wallahi har na manta abinda ya kawoni. Hajiya Amina ce tace tana son ganinki wadda ta d’auki karime, ina tunanin dai yarinya tayi d’anyen aiki saboda yanda naji muryar Hajiyan”.


Cikin ko in kula Hajiya sa’a tace “babu inda zani saboda ke kinsan tsarin contract d’ina matu’kar yarinya tayi wata shida ta fita daga hannuna, sannan idan yarinya tayi laifi babu ruwana da hukuncin da za’a mata a gidan aikinta ruwansu ne wannan. Idan ta manta ne ki fad’a mata bazani ba”.


Atine batayi ‘kasa a gwiwa ba ta kira Mum ta zayyana mata batun Hajiya sa’a, tana gama magana Mum tace a baiwa Hajiya wayar. Kafin su gaisa Mum tace “Yarinyar da kika kawo min ta kashe min yaro saboda haka ko dai kizo police station ki amsa tambayoyi a kanta ko kuma kema a had’a dake. Daga ke har Atine ana bu’katarku a station zan turo muku address”.


Salati Hajiya sa’a tayi ta dafe ‘kirji ta katse wayar. Zama tayi ta zuba tagumi tace “na shiga uku, yarinya ta jamin bala’i da masifa Atine. Karime ta kashe d’an gidan Hajiya Amina shikenan kashina ya bushe”.


Idanun Atine ‘kulu-‘kulu yayi tace “na shiga uku shikenan nima tawa ta ‘kare, wallahi Hajiya indai naje police station aurena ya ‘kare kenan domin Abban Nawal saida ya min kashedi yace idan ya sake jina a police station a bakin aurena. Hajiya ki rufa min Asiri dan Allah ki fiddani daga wannan bala’in”.


“Wallahi yanda muka shiga tare haka zamu fita. Ki sani kin ma fini shiga matsala saboda kece kika kawo min karime. ‘Kafars ‘kafarki sai munje anyi komai ya ‘kare. Kuma kar kiyi tunanin zanyi amfani da kud’ina na taimakeki kowa tashi ta fissheshi. Ke Allah ya isa ma ban yafe ba kin d’auko min tashin hankali ina zaman zamana”.


Kuka Atine ta fara tace “daga taimako? Nima Allah ya isa tunda ke nake kawowa yaran kin fini samun riba dasu”. Haka suka cigaba da sukar junansu har magriba ta kawo kai, babu yanda suka iya kowacce rai a dagule suka fito suka nufi gidan Hajiya Amina.


Suna zuwa ko gaisuwa bata bari sunyi ba ta tasa ‘keyarsu zuwa police station. A hanya babu irin addu’ar da Atine bata janyo ba gashi mijinta tunda suka d’auki hanya ya addaba mata da yawa, surutan da take yasa saida hajiya Amina ta daka mata tsawa sannan ta shiga hayyacinta. Hajiya sa’a kuwa tsara ‘karairayin da zatayi a police station takeyi har suka isa.


Free page


Littafina na kud'i ne 500 kacalđŸ„°đŸ„°ku nuna min solidarity ni kuma zanyi ‘ko’kari na baku abinda zu’katanku suke so😁😁


Account details

0472624453

Musa maryam Aminu

Gtbank


Ki a tuntu'beni ta wannan number

***