12
by @kitty
A CIKIN DUHU...
Kittyđ
Wattpad @ Mssmeemah
12
Fita Mum tayi ta nufi dâakin Fatima hankali a tashi domin ta tambayeta abubuwan da ta sani tsakanin Abdul da Karime saidai ta sameta tayi bacci. Jiki na rawa ta fita ta dâauki wayarta ta kira DPO saidai ta kasa samunshi. Haka ta kwana bata runtsa ba videon da ta gani yana yawo a cikin kanta, runtse idanu takeyi saboda kawai ta kawar da hotunan saidai sun gaza fita. Hango karime take yanda ta fita hayyacinta duk a dalilin son zuciya irin. Meyasa bata fara zama ta tilastawa karime ta fadâa mata gaskiya ba? Meyasa bata bi shawarar Abbu da Fatima ba? Da irin wadâannan tambayoyin ta kwanta har bacci âbarawo yayi awon gaba da ita.
Kiran sallar asuba ne ya tasheta tana tashi ta rarumi wayarta ta kira DPO tayi saâa kuwa ya shiga, yana dâaga wayar ba tareda gaisuwa ba tace âInaso na rufe case dâin da na kawo a yau dâinnanâ.
Mamaki DPO yayi yace âHajiya ai baâa rufe case hakanan sai mun duba munga babu wasu evidence a kai, kuma case ne na kisan kai kingaâŠâ dakatar dashi tayi tace âmaganar kisan kai ta âkare likitoci sun sanar mana mutuwa yayi from natural cause kuma babu alamun yarinyarnan ce ta kasheshi. Saboda haka a saketa kawai a rufe case dâinnan ko nawa ne zan biyaâ.
âTo Hajiya mun riga mun shigar dashi fa amma ba zaâa rasa abin yi ba gobe ki kawo evidence na natural cause of death dâin mu saka a ciki sai a rufe case dâinâ.
âDuk abinda kace zaâayi amma dan Allah a sallami yarinyarnan kar ta sake kwana a cikin wannan cell dâin tunda ita ba mai laifi baceâ.
âIdan kikazo da safen duk abinda ya kamata zaâayiâ. DPO ya fadâa tareda katse wayar, sallah mum ta tashi tayi ta dâauki lokaci mai tsayi tana roâkawa Abdulyassar gafarar ubangijinsa har saida gari ya fara haske sannan ta tashi ta fita, bata damu da mutanen da zasu zo ba hankalinta yana kan dâauke nauyin karime daga wuyan Abdulyassar ta kuma nemi gafararta ko ya samu sassauci.
Abbu ta samu da umaima a parlor yana koya mata karatun âkurâani tace â Abbu zanje a rufe case dâinnanâ.
âTo Allah ya taimaka, kin dâauki isassun kudâadâe?â Amsa mishi tayi da eh ta fice cikin sauri. Binta yayi da idanu har ta fice sannan ya cigaba da biyawa umamima karatunta.
__________________________
Tashin karime daga bacci yayi daidai da shigowar Mum cikin station dâin. Wani irin tsoro ne ya ziyarci karime domin duk lokacin da Mum tazo azabar da take ciki tana sake ninkuwa. A yanzu ta sake tabbatar da dâan sanda abun tsoro ne domin basu da imani.
Jikinta duka tsami yake mata yayin da ciwukan jikinta wasu suka fara fidda ruwa, rigarta ma daudâa take sanyawa tana goge wasu ciwukan saboda yanda suke fidda ruwa marar kyau. Hannunta ta dâaga domin ta âkulle gashin kanta saidai azabar da taji a dantsen hannunta ya saka ta sauke.
Fitsari ta fara ji wanda ya sanya hawaye gangarowa fuskarta, ta tsani yin fitsari a wannan wurin saidai babu yanda zatayi, ko dai ta matsa ta tsuguna suna kallonta tayi ko kuma ta haâkura tayi a jikinta wanda wannan ba mai yiwuwa bane.
Runtse idanunta tayi tareda gyaran murya saidai har yanzu muryarta bata fita. A zuciyarta tayi adduâar neman kuâbuta sannan ta koma ta takure domin a yanzu ko ruwan tsarki babu cikin cell dâin. Batul sallah kuwa saidai ta kalli gabas a yanda take tayi domin sunâki bata hularta ta sanya.
Duk abubuwan da takeyi idanun mum na kanta har DPO yazo suka shiga office dâinsa. Nan ma sun dâauki tsawon awa guda domin dagewa yayi sai an kawo evidence âkwaâkkwara wanda zai nuna tabbas ba karime ce ta kashe abdul ba. Abbu ta kira yaje wurin doctor da kansa ya karâbo takardar da aka buga na possible cause of death likita yayi signing ya baiwa Abbu shi kuma kai tsaye ya miâka takardar station.
Tambayoyin tuhuma DPO ke musu suna âkoâkarin kaucewa saida ta bada kudâadâe masu yawa sannan ta samu shawo kansa ya amince zai rufe case dâin. Saida ya amince sannan Mum ta samu nutsuwa ta fara hammar baccin da ta rasa na daren jiya. Kallonta Abbu yayi yace âummu fadâima ki koma gida ki samu bacci ni zan âkarasa abubuwan da suka kamataâ.
Shima DPO dâin ya amince saboda gajiyar da ya gani âkarara a fuskarta ya bata wurin da zatayi signing ta tafi ta barshi da Abbu.
âAnya alhaji ba kaine ka janye raâayinta lokaci guda ta janye caae dâinnan ba?â DPO ya tambaya yana kallon Abbu, Abbu bai tanka mishi ba ya cigaba da yiwa Abbu tambayoyi a lallai sai ya âkureshi daga âkarshe Abbu yace âDPO yaronnan dâana ne, duk abinda nayi ba abinda ya shafeka bane idan ka cigaba da tuhuma ta zaka jika a gaba domin kaine abun tuhuma a yanzu. Kayi belin yarinya ka rufe case kawai idan ba zakayi ba da kaina zan dâaukaka case dâin muga ni da kai waye zai shiga problemâ.
Ganin Abbu ya mishi jan ido yasa ya hanzarta yayi closing case dâin ya kira dâaya daga cikin âyan sandan dake wurin yace âwannan yarinyar da ke cell dâin mata ku sallameta anyi closing case dâinâ.
Sara mishi dan sandan yayi ya fita ya budâe karime. Yana budâe âkofar ta razana ta ja baya tamkar zata shige bangon cell dâin, ransa a murtuke yace âfitoâ.
Tashi karime tayi da âkyar ta iya tafiya ta fito daga cell dâin tana dafa bango har ta âkarasa wurin table dâinsu. Abbu ta gani tsaye da DPO tsoronta ya âkara yawaita domin tana jin suna maganar kai case dâinta kotu, ko ranar shigarta kotun ne yazo?
Littafi aka bata DPO yace âsa hannu a nanâ. Tareda miâka mata biri, kallon biron tayi ta kalli DPO ta budâe baki domin tambayarsa ta yaya zata saka hannun saidai babu kalmar da ta fito, tsawa ya daka mata wadda ta saka ta zube a wurin tare da dafe kanta da hannayenta kuka na âkwace mata. Abbu har ya budâe baki sai kuma yayi shiru. Wancan dâan sandan ne yayi mata bayani yace âbiron zaki saka ki rubuta sunanki a nan ko baki iya ba?â
Gyadâa kanta tayi alamun eh yace ta miâka yatsanta ya goga mata biron yace ta danna hannun a wajen. Tana saka hannu yace âto shikenan dama ba wani abu kikazo dashi ba a hakanan kika zo saboda haka ga hanya nan ki tafi an sallamekiâ.
Cak tayi tana kallonsu domin bata aminta da zancensu ba gani take gwadata sukeyi suga ko zata gudu su kasheta saboda haka taâki motsawa ko kadâan. âKo kina son zaman nan dâin ne na budâe miki ki koma?â Cikin sauri ta girgiza kai yace âto fita mana me kike jira!!â
Da sauri ta fice tana tuntuâbe, gaba dâaya ta dibirbirce ta rasa inda zatayi sai yanzu take tsananin nadamar barin âkauyensu da tayi. A haka take tafiya tamkar mahaukaciya duk wanda ya wuce sai ya kalleta ya sake kallo wasu cikin tausayawa wasu kallon tuhuma.
Mota ce tayi parking a gabanta taga Abbu ya fito daga ciki, da sauri ta ja baya yace âkarki tsorata karima ba wani abu zan miki ba, ki shiga muje asbiti a dubakiâ.
Girgiza mishi kai tayi tana sake ja baya yace âzaki fadâi, bazan cutar dake ba karima taimakonki kawai nakeso nayi a duba lafiyarki kiga ciwukan jikinki, daga nan duk inda zakije bazan hanaki ba idan garinku zaki koma ma ni mai taimaka miki ne, dan Allah ki shiga mota mu tafiâ.
Bata yarda dashi ba amma ganin batada wani mafita yasa ta shiga motar domin ko gudu zatayi baifi tayi taku uku ba ya kamota. Suna fara tafiya ya dâauki wayarsa ya kira Fatima ring dâaya ta amsa tace âAbbu ya ake ciki? Mum tace an rufe case dâin Karima ko?â
âAn rufe Fatima gani ma ga karima zan kaita asbiti ne a dubata inaso ki kawo mata kayan da zata sanya a jikinta ne amma banaso Momynku ta saniâ.
âTo Abbu zan kawo ba zata sani ba amma gidannan zaâa kawota? Abba dan Allah kar ka dawo da ita gidannan ta koma gidansu kawaiâ.
âFatima ko ma wacce magana zamuyi idan mun hadâu asbiti ko kuma na dawo gida sai muyi for now ki kawo mata kayan da zata zaka zanje abitin doctor YunâŠ..â bai âkarasa ya zare ido tareda sakin wayar ganin wata yarinya da yake shirin bugewa a titin, kaucewar da yayi ne ya sanyashi dukan gefen titi motar ta fara wani irin juyi a tsakiyar titi, salati yake yana âkoâkarin saita motar saidai ya kasa Karime kuwa ihu take iyakar âkarfinta tana riâke da gefen kujerar motar.
Allah ya taimakesu babu wanda suka buge motar ta sake dukan gefen titi sannan ta tsaya. Wani irin hayaâki ne ke fita daga motar karime ta dâago goshinta na zubda jini ta kalli Abbu, yanayin da ta ganshi ne ya sanya ta firgita domin kansa na kan steering hannunsa dâaya yayi wani irin lanâkwasa ga jini shima dake zuba daga goshinsa. Mutane ta hango suna yowa wajen motar a gigice ta budâe motar ta fice kafin su âkarasa ta nufi cikin wani lungu.
Tafiya take tana kuka âkarfinta na âkarewa duk wanda ta gani sai ta roâkeshi taimako, bakinta ya budâe amma lokacin mamakin ma bata da shi saboda yanayin da take ciki. Tayi tafiya mai nisa har mutane sun fara gudunta suna tunanin mahaukaciya ce. Wata dattijuwa ce ta taho karime ta nufeta tana fadâin ta taimaka mata, kallonta matar tayi tana tunanin ko mahaukaciya ce cikin sauri karime tace âwallahi ba mahaukaciya bace ni ki taimaka min dan Allah ni ba macuciya baceâ.
Dattijuwar ta tsaya tana tunanin ta yanda zata taimakawa karime ta ciro 200 a âkaramar jakar hannunta ta baiwa karime tace âke kuwa baiwar Allah daga ina kike haka?â
âDaga âkauye nake banida kowa iyayena da âyan uwana duk sun rasu, bansan kowa a nan ba wallahi masu aikatau na biyo bansan ko ina a garinnan ba ki taimaka minâ. Tausayin karime ne ya kamata tace âba taimakonki ne banaso nayi ba baiwar Allah halin zamaninnan nake tsoro, ni kaina taimaka min akeyi muje dai na baki abinda zan iya gidana nan kusa yake sai ki tafi garinku Allah ya kawo miki mafitaâ.
Tare suka jera suka nufi gidan matar ta budâe ta shiga karime na daga waje, qirjin matar wani irin bugu yakeyi domin ta tsorata ji take tamkar aljana ce shiyasa ma ta amince ta taimaka mata domin bataso ta kasance aljana kuma tazo ta nufeta da sharri. Idan ta taimaka mata tasan ba lallai ta cutar da ita ba. Kaya ta dâauko set guda da hijabi ta fito ta danâkawa karime dake durâkushe a âkofar gidan, Karâba karime tayi tana godiya daidai lokacin da Ahmad ya nufo gidan yana âkara sauri ganin innarsa da wata yarinya a waje wadda yake kyautata zaton Karima ce ta police station dâinsu.
Tun kafin ya iso karime ta firgita tana shirin guduwa dukda ba uniform ne a jikinsa ba amma jikinta gaba dâaya ya dâauki rawa saboda tsananin tsoro. Riâke karime yayi dake shirin guduwa yace âInna me wannan takeyi anan?â
Inna itama ta tsorata ganin yanda karime ke neman guduwa zarginta ya tabbata yarinyar macuciya ce tazo ta cutar da ita, bakinta na rawa tace âwallahi Ahmad a hanya na ganta a wannan yanayin tace na taimaka mata shine nazo na bata kaya da kudâi. Ka santa ne?â
âInna itace fa nake gaya miki an kawo ta ta kashe dâan gidan da take aiki. Yau aka ce zaâa kai case dâinsu kotu inada tabbacin gudowa tayiâ.
Cikin sauri karime tace âwallahi ba guduwa nayi ba ka tambayesu sakina sukayi har aka ce na dangwala hannuâ. Yana riâke da gefen rigarta ya dâauko wayarsa ya kira abokin aikinsa domin shi bai shiga ba yana off ranar aka sanar mishi an rufe case dâinta an bada belinta. Maida wayar Aljihu yayi ya saketa yace â âbacemin da gani!! Idan na sake ganin âkafarki a hanyarnan sai na karairaya kiâ.
A razane ta matsa da shirin barin gurin Inna tace âAâa dakata guduwar tayi shine kaima zaka barta ta tafi?â Girgiza kai yayi yace âInna rabu da ita ba guduwa tayi ba an rufe case dâin ne sun gano ba itace ta kasheshi ba aka sallameta. Mu shiga daga ciki ta tafi ko ma ina zataje ko ta koma garinsu domin mutane ba abin yarda bane, ruwa baya tsami banzaâ.
Free page
Littafina na kud'i ne 500 kacalđ„°đ„°ku nuna min solidarity ni kuma zanyi 'ko'kari na baku abinda zu'katanku suke sođđ
Akwai VIP 700 ga wadâanda basu son jirađđ 3 pages ta private a kullum insha Allah.
Account details
0472624453
Musa maryam Aminu
Gtbank
Ki a tuntu'beni ta wannan number
***