13
by @kitty
A CIKIN DUHU
Kittyđ
Wattpad @mssmeemah
13
âAâa Ahmad kar kace haka, ni nayi zaton ma ba mutum bace shiyasa nake dâari dâari da ita amma mu taimaka mata sai muma Allah ya taimakemu ta hanyar da bamuyi zato ba. Tace bata da kowa idan ta tafi ka san ina zata nufa? Wasu irin mutane zata hadâu dasu?â
âInna ki barta itama baki san wacce irin mutum bace. Yarinyar da zargin kisa ke kanta kika san idan ta zauna dake me zata miko? Zata iya cutar dake ko ta miki sata ko makamancin haka. Inna mutum fa mugun icce neâ. Ya âkare maganar yana kallon karime da tayi nesa dasu tana rufa hijabin da Inna ta bata a jikinta, tabbas a baya ya tausayawa yarinyar amma a yanzu bazai bari Inna tayi gangancin da zai janyo musu matsala ba. Alamomin tambaya ne birjik a kan yarinyar bazai bari wata alaâka ta âkullu tsakaninta da Innarsa ba.
âDa baâa taimako Ahmad da yanzu nima ina garari a tituna ina yawo ko kuma na fadâa harkar banza. Fatauci muka taho da kakanka a hanya Allah ya dâauki ransa ni kadâai na âkaraso gari da tsohon ciki, cikin ikon Allah da taimakon mutane na samu matsuguni gidan wani bawan Allah har na haifi mahaifinka a cikon gidan aka bashi auren mahaifiyarka kana sane duk da wannan. Da ace baâa taimako har na haifeshi? Har ya samu yayi auren mutunci? Halayenmu na wannan zamanin sune ke janyo mutanen cikinsa ke lalacewa. Idan baka taimakawa mutum ba lokacin da abu zai sameshi ba shi kadâai zai shafa ba harda kai, maganar mutum mugun icce bata da wani tushe a nan domin daga mai taimakon har wanda zaâa taimakawa ba ababen yarda baneâ.
Ahmad yasan ya da kakarsa babu riba hakan yasa ya ja numfashi yana kallon hanyar da karime tayi domin har tayi kwana tayi nesa dasu kasancewar unguwar cikin gari ce, ganin baya hangota yasa yace âtunda dai ta tafi maganarnan a barta kawaiâ.
âAhmad yarinyarnan fa babu inda zataje zan dâauketa na taimaka mata har Allah ya kawo lokacin da zata koma garinsu komai dadâewar lokacin kuwa. Kwanaki nawa ne suka rage min a duniya? Sai kaga ta yiwu sanadiyyar taimakon ta na shiga aljannaâ. Tana âkare maganar tabi bayan karime cikin sauri Ahmad kuwa dafe kansa yayi yace âidan baki shiga aljanna ba kya shiga hankalinkiâ.
Inna tayi saâa karime batayi nisa ba saboda yanayin jikinta, daga nesa Inna ta kirata tace âbaiwar Allah ke yarinyarnan tsayaâ.
Tsayawa karime tayi Inna cikin sakin fuska tace âmuje na taimaka miki domin Allah kinji yarinya? Amma kar ki cutar dani dalilin taimakonkiâ.
Wani dadâi ne ya mamaye zuciyar karime tace âbazan cutar dake ba insha Allahu. Ni ba macuciya bace bansanâŠâ inna bata bari ta âkarasa ba tace ânasani yanzu muje gidanaâ.
Juyawa sukayi suka fara tafiya saida suka isa gidan sannan karime ta fara wani irin haki na gajiya ga ciwukan jikinta duk sun fara tsami bansa wadâanda tuni sun fara fidda ruwa. Suna sallama Ahmad ya amsa saidai bai shigo ba goggo ta nufi dâakinsa tace âakwai kudâi ne hannunka zan kaita kemisâ.
Dubu biyu ya zaro ya bata ba tareda yace komai ba ta fita tareda kiran karime suka fita suka tafi kemis. Mai kemis dâin ya shawarcesu suje asbiti saboda yanayin ciwukan karime Inna tace âkai yaro mun fa san magungunan da suka fi naku amfani rashin saiwoyi a kusa ne yasa na kawota. Kayi abinda zaka iya ragowar sai muyi a gida amma babu asbitin da zani a âbata min lokaci a banzaâ.
âBaaba ai ba wai batun âbata lokaci bane kinga ciwukan sun fara zama infected sannan bamu da cikakkun kayan aikin da zan iya mata abinda ya daceâ. Ya âkare maganar yana duba ciwukan hannun karime domin shi kadâai ne a bayyane sai fuskarta.
âKai yaro shi imfish dâin ba zaka iya cirewa ba kenan? Banda tsurfa da zamaninnan naku a lokacinmu garin magani zan badâeta dashi kan gari ya waye ta warke. Mukayi maganin âkonuwa ma balle imfish? Ka mata abinda zaka iya na tafi gidaâ.
Bayani ya sake ma Inna a lallai fa sai sunje asbiti domin kayan aikinsa na âkananun ciwuka ne sannan a wannan lokacin ma ba a gashe suke ba zai iya âkara mata imfish (infection). Haka nan inna ta kwasheta suka koma gida tana ta mita har suka isa. Sabuwar mita ta dâora ganin Ahmad baya nan ta hadâa wuta ta dâaura ruwan zafi.
Karime na gefe a zaune tana binta da kallo lokaci-lokaci idanunta na rufewa saidai tsoron abinda zai faru idan tayi bacci ne ya hanata sakewa tayi bacci. Bin Inna takeyi da idanu tana ta kai kawo bayan ta hadâa wutar ta fara shirin abinci.
Suna zaune Ahmad ya shigo niâki niâki da buhun shinkafa ya ajiye ba tareda yace komai ba ya sake fita ya shigo da cartons na taliya da macaroni da masara, gero, alkama, da garin semo. Inna tsayawa tayi da aikin da takeyi tana kallonsa yana shige da fice bayan ya dire kayan ya sake fita ya shigo da kayan miya da kifi mai yawa sosai.
Inna a tsorace take tace âkai lafiya ina ka samo wadâannan?â Karime ya kalla yace âwasu kudâadâe na samu ne Inna. Idan akwai wani abu da babu anan sai ki fadâa minâ.
Eh kaman ka manta da mai. Amma Ahmad wani irin kudâi ka samu haka a tsakiyar watannan? Ko albashi aka maka nasan bazai kai ya siya mana wannan kayan ba kaji tsoron Allah ka fadâa min ina ka samoâ.
Hadâe ransa yayi yace âinna ki dena tuhumata gaban yarinyarnan sai ta rainani. Ba wurin wani na âkwata ba bani akayi bashi zan biya a hankaliâ. Inna dai bata amince dashi ba ta amsa mishi da to sannan tace âyauwa zaka rakani asbiti da kayanka na âyan sanda zan kai yarinyarnan a dubata munje kemis yace wai bazai iya ba ta kamu da imfish. Ni bansan imfish dâin bane da na kira âkauye wani ya kawo min maganinsaâ.
Amsawa yayi da toh sannan ya fita ya sayo sauran abubuwan da ake buâkata zuciyarsa fes babu wani tsoro. Tunda Mum ta bashi kudâadâennan ya rasa sukuni a kansu amma a yau da yaga an saki karime ya yanke shawarar kashesu tas idan ma ta dawo tace ya maida mata abinta yasan yaci rabonsa kuma babu yanda ta iya dashi. Tsoronsa ta fadâa ma DPO yasan DPO ya fishi son zuciya hadâesu zaiyi ya cinye ya bashi dubu goma ko ashirin. Amma a yanzu ya zaâbi duk hukuncin da zai biyo baya matuâkar yaci kudâadâen.
__________________________
âAbbu!!! Wayyo Allah mun shiga uku Abbu!!!â Fatima tayi ta maimaitawa a cikin wayar domin tana jin âkaran da wayar keyi da salatin Abbu tareda ihun karime. Da gudu ta fita daga dâakinta tana âkwalawa mum kira ga gida fal mutane kowa yayi cirko cirko ana jiran me zata ce.
Mum na bacci taji kiran yayi yawa ta fito tace âFatima lafiyaâ. Kuka fatima ta saki tace âMum Abbu yayi accidentâ. Tana fadâa sukaji sallama cikin wayar fatima domin a hands free take. Mum ce ta Karâbi wayar wani saurayi yace âMai wayar ne yayi hatsari muka ga wannan lambar na kai ana kira, yanzu haka an tafi dashi asbitin murtala emergencyâ. Yana gama maganar ya kashe wayar gaba dâaya.
Zubewa mum tayi a wajen ta dafe âkirjinta tana ambaton Innalillahi wa inna ilaihi rajiâunâ Fatima kuwa kuka kawai takeyi ana rarrashinta. Zee da umaima ganin fatima na kuka ga Mum itama ta fara hawaye yasa suma suka ce bari su tayasu suka zauna gefen mum suna kuka. Hammad kuwa cinyarta ya hau ya kwanta a âkirjinta yayi luf yana kallonsuâ.
Lumshe idanu mum tayi taja dogon numfashi sannan tace âFatima tashi ki shirya mu tafi asbitinâ. Kallon âkanwarta tayi tace âAisha ki zauna da su umaima a sallami kowa zamannan baida amfaniâ. Amsawa Aishan tayi da to ta dâauki hammad a hannunta taje ta samu âyan manyan dake gidan ta sanar musu zama fa ya tashi mai gida yayi accident. Nan dai masu kukan gaske da na munafurci suka fara aiki yarda masu cewa zasu bita asbiti. Cin magani mum tayi saida ta tabbatar an fara tafiya sannan taje waje suma ta sanar musu. Dake maza ne da kansu suka watse aka cire rumfa.
Suna isa emergency mum ta fadâi sunan Abbu zuciyarta na wani irin bugu, amince mata akayi ta shiga ta sameshi kan gado an nadâe mishi kai da bandage ga hannunsa da kwali an maâkale hannun a wuyansa. wuyansa ma a nadâe, hawaye ne suka zubo mata tace âAllah ya baka lafiya Abbuâ.
Fatima na daga waje da âkyar suka bari ta shiga itama tana ganinsa sai kuka amma ta danne kukan ta mishi adduâa. Muryar fatima da yaji ce ta sanya ya budâe idanunsa yana waige waige yace âkarimaâŠâ. Cak mum ta tsaya ta kalli fatima da itama ta zare idanu cikin mamaki. Muryarta na rawa tace âAbba karima ta mutu ne?â
âBan sani ba fatima ki duba min cikin wajennan kiga tana nan?â Takaici ne fal zuciyar Mum tace âbuguwar kai ta saka ka taâbu ne Abbu wacce karime kuma?â Bai amsa mata ba fatima ta fita tana ta dube-dube babu alamun karime ta dawo ta fadâa mishi, nimfashi ya sauke tareda dafe kansa dake azabar ciwo lokacin da likita ya shigo.
Gaisawa sukayi da mum yace âgaskiya ya samu buguwar kai sosai sai an mishi hoto sannan hannunsa na dama ya karye zamu maidaku theater yanzu zaâa mishi aiki. Ciwon wuyansa ba mai tsanani bane alhamdulillah an auna arziâkiâ.
Hamdala Mum da Fatima sukayi kafin likitan ya fita Abbu yace âDoctor akwai wata yarinya dake cikin motar an kawota ne itama?â
âBanida masaniya gaskiya domin ba mune muke Karâbar mutanen baâ. Yana fadâin haka ya fita. Mum bata tanka mishi ba dukda tambayoyin dake zuciyarta har aka zo aka dâaurashi kan wani gado aka nufi theater dashi. Suna zuwa Mum ta kira doctor yunusa ta sanar mishi abinda ke faruwa cikin mintina kadâan sai gashi a asbitin, shi ya shige musu gaba cikin âkanâkanin lokaci aka mishi hoton hannun da kuma gyaran karaya sannan suka tafi hoton kai. Hoton ya nuna babu wata matsala suka nemi amenity ward aka basu.
Suna Amenity ne jamaâa âyan dubiya suka fara zuwa âyan uwan Abbu da abokanansa saidai duk wanda yazo baya samun shiga Abbu yana bacci. Abinci aka kawo musu kala daban-daban sai can dare sannan aka kawo su Umaima su ganshi a lokacin ciwon kansa ya lafa sosai.
âDagashi akayi ya zauna umaima da zee suka haye gadon suna cin abinci suna bashi harda fadâansu kan wanda yafi bayarwa. Ganin suna ta raharsu hnkali kwance yasa mum ta ja Fatima waje tace âFatima kai tsaye fadâa min me ya faruâ.
âMum muna waya da Abbu yace zai kai karime asbiti ayi treating dâinta sannan ya sakata a hanyar garinsu ta tafi. Yace na kai mishi kayan da zasu ma karime asbitin dr yunusa kawai naji motar ta fara âkara sai kiran da mukaji tareâ.
Wani kallon Mum ke yiwa Fatima tace âkuma kina fadâa min ko a jikinki ko? Fatima what is wrong with you? Idan yarinyarnan ba ita ta kashe Abdul ba itace sanadiyyar mutuwarsa amma shine har Abbu ya dâauketa a motarsa zai kaita asbiti kuma kike ganin hakan abin cancanta ne ko? Fatima ki sani a ranar da Abbu ya kawo yarinyarnan gidana a matsayin kishiya zamana dashi daku ya âkare har Abadaâ.
âMum Abbu ba son karime yake ba taimakonta kawai zaiyiâ. Fatima ta furta kanta a âkasa. Murmushi Mum tayi tace âwani irin taimako ne zai saka ya sallameni daga police station saboda kawai ya dâaukota a motarsa? Taimako ne ya sanya ya ambaceta kalmarsa ta farko bayan ya farfado daga accident? Gani gaki a gabansa wa ya kira a cikinmu fatima? Ke yarinya ce Fatima ba lallai ki fahimta ba amma na lura bayansa kike goyo so ki cigaba. Idan kika rasani akan âkazamar âyar aiki zaki fahimci abinda nake fadâa mikiâ.
Free page
Littafina na kud'i ne 500 kacalđ„°đ„°ku nuna min solidarity ni kuma zanyi 'ko'kari na baku abinda zu'katanku suke sođđ
Akwai VIP 700 ga wadâanda ba zasu iya jira ba, 3 pages a kullumđđ
Account details
0472624453
Musa maryam Aminu
Gtbank
Ki a tuntu'beni ta wannan number
***