15
by @kitty
A CIKIN DUHU
Kittyđ
Wattpad @mssmeemah
15
âDukda bamu son baâko amma ka taâba ganin wani ya nemi taimakonmu mun hanashi? Tunda har ta ratso shingenmu tabbas batada abin cutarwa a tattare da ita abinda ke wuyanta ne ma ya dâauki hankalinaâ.
Zuba ma wuyanta idanu sukayi tayi saurin damâke sarâkarta a hannu, sai a lokacin gajiya ta dirar mata jiri ya kwasheta tayi âkasa saidai kafin ta kai âkasa sukayi saurin taro ta su biyu. Kwantar da ita sukayi ganin batada wani kataâbus wanda ya fara ganinta ya dâauko wuâka zai yanke zaren dake riâke da sarâkar wuyanta.
âKarku kuskura ku mata komai idan ba haka ba ranku zaiyi mummunan âbaciâ. Wani dattijo ya nufosu cikin sauri yana nunasu da sandarsa, ja baya sukayi suka dâaga hannayensu dâaya yace âLamidâo ba wani abu zamu mata ba zaren wuyanta zamu cire, shigowa tayi tace tana neman taimakoâ.
Shima dattijon da aka kira da Lamidâo kallon zaren wuyan nata yayi sannan ya durâkusa cikin harshen hausa yace âdaga ina kike? Me kikeso?â
âTaimako nake nemaâ. Ta furta tana lumshe idanunta, tura samarin yayi su kira mata cikin âkanâkanin lokaci wasu âyanmata biyu suka iso, umarni yayi musu da su kama taishu su shiga da ita suka kamata ta tashi suka nufi cikin bukkokin da ita. A kan tabarma aka shimfidâeta, âkwala kira yayi yace âdabo jauro!â
Wata dattijuwa ce ta fito da bazata gaza shekaru 45 a duniya ba, cikin biyayya ta durâkusa kadâan, magana sukayi a hankali ta tashi ta koma ta fito da âkwarya da ganye a ciki ta zuba ruwan dâumi ta miâka ma Lamidâo.
Ganyen ya cire yace ta dâaga kan Taishu ya danna ganyen a ciwon dake bayan kanta dabo jauro ta dâauko farin dâankwai ta dâaure ganyen a jikin ciwon sannan aka shafawa taishu ruwan a jikinta, cikin âkanâkanin lokaci bacci ya kwasheta saida tayi bacci sannan modibbo yace âki kula da ita zamu fitaâ.
Amsa mishi tayi da to ta tashi ta cigaba da aikace-aikacenta na gida har ta dâora ma yaranta tallan nono suka fice Taishu bata farka ba, lokaci-lokaci ta kan zagayo ta dubata domin ta tabbatar tana numfashi har saida rana ta riski taishu sannan ta farka daga baccin da take. Tashi tayi ta zauna tana kallon harabar gidan. A hankali ta miâke tsaye wanda ya sanya dabo jauro nufota da sauri tace âki zauna karki fadâiâ.
Murmushi taishu tayi tace âbana jin komai nagode sosai Allah ya saka muku da alkhairi ya biya muku buâkatunkuâ. Juye-juye taishu keyi tana neman lulluâbinta Dabo jauro tace âina zaki?â
âTafiya zanyi bansan yanayin da âyata ke ciki baâ.
âNa fahimta amma ki zauna ki sake hutawa tukuna. Daga wani gari kike?â
âDaga tamaru nake, bazan iya zama ba nagode da taimakonku amma dole na koma na bar karime ita kadâaiâ. Murmushi dabo jauro tayi tace âki zauna ki bari modibbo ya dawo daga nan zuwa tamaru akwai âyar tafiya kuma hanya babu kyau. Idan suka dawo cikin yaran sai wani ya rakaki a yanayin da kike bazan barki ki tafi ba ko ruwa baki sha baâ.
Dagewa Taishu tayi sai ta tafi itama Dabo jauro ta dage ba zata barta ta tafi ba sai modibbo ya dawo. Tunani taishu tayi taga bai dace ta tafi ba tareda ta ma modibbo godiya ba hakan yasa ta zauna saidai gaba dâaya hankalinta na wajen karime. Meyasa ta gudu bata koma ta dâauko karime ba? Meyasa bata jira ta a hanya ba tayi gaba? Me yake faruwa da karime? Shin tana raye? Ta mutu? Ta tsira? Tana garin ko bata nan?
Tana wannan tunanin Dabo jauro ta kawo mata tuwo da miyar kuka da man shanu. Sai ruwan dâumi saboda ta dâumama cikinta. Godiya taishu tayi taci abincin sannan ta tashi domin tayi sallah. Cire dâaurin dake kanta Dabo jauro tayi Taishu ta taâba inda ciwon yake taji babu alamun jini sannan zafin ciwon ma ya ragu sosai, godiya ta sake ma dabo jauro sannan ta dâaura alwala tayi sallar magrib, isha, da sallar asubahi.
Sai a lokacin ta âkarewa rugar kallo. Bukkoki ne guda takwas a cikinta sai tsakiyar bukkokin da aka shafe da siminti. Tana bin bukkokin da kallo ne dabo jauro ta dawo ta fara mata bayanin yanda gidan nasu yake.
Bukkar da take kwance a âkofarta itace bukkar Dabo jauro, sai ta gefenta kuma ta lamidâo da matarsa wadda taje gida mahaifinta ya rasu, sai ta kusa da ita ta bamanga matarsa amarya ce da tsohon ciki, dukkansu âkannen modibbo ne sai kuma bukka dâaya ta âyaâyan dabo jauro mata su uku baddo, danejo da Hauwa. Sai bukkar âkarshe kuma ta bawuro dâa dâaya namiji ga dabo jauro wanda ya rasu shekarar da ta wuce sai kuma bandâakinsu dake can gefe guda. Bukkoki biyu dake gefe kuma dâaya ta iyayen modibbo ce da suka tafi ziyara dâayar kuma ta matar da modibbo zai auro.
Tana zaune a wannan rugar har yamma ta doso, saida duhu ya fara
Shiga sannan modibbo suka dawo daga kiwo shi da yaransa da sauran âyan uwansa dake kewayen. Suna shigowa taishu ta tashi tace tafiya zatayi. âKi bari idan gari ya waye sai ki tafiâ. Dabo jauro ta furta ganin yamma ta shiga. Dagewa taishu tayi tace âkarime âyata tana cikin matsala zasu iya kasheta, ku barni naje na dâaukota na gode da taimakonku da inada abinda zan biyaku dashi zan bayar amma banida komaiâ.
âKi fadâa mana menene ke faruwa dake? Waye zai kashe âyarki? Idan kikayi mana bayani mu kuma zamu taimaka miki na hadâaki da wadâanda zasu rakaki ki dâauko âyarkiâ.
Bayani tayi musu daga mutuwar sani zuwa kasheta da akayi âkoâkarin yi Modibbo ya umurci yaransa biyu su raka Taishu ta dâauko âyarta. Fita sukayi saida sukayi tafiya mai dâan tsayi sannan suka fita titi. Mashina biyu sukayi suka hau dâaya Taishu ta hau dâaya suka nufi tamaru.
Suna zuwa suka ce ta tsaya su shiga su gano meke faruwa. Wurin da samari ke zaune suka nufa sukayi basaja anan sukaji anan hirar karime da ta âbace lokacin da akaje kamota har wani yana cewa ânifa na riâko hijabinta zan janyota kenan kawai naji kamar an fizgeta babu ita, ai na fadâa muku babu shiri na ja da baya na shafawa kaina lafiya. Kuna gani dai itama gawar Hauwa haka aka nemeta aka rasa. Da alamu ma dai banda maita a lamarin nasu akwai shedâanci ko babban tsafiâ.
Sun jima suna jin hirar mutanen wurin sannan suka nufi inda suka bar Taishu (hauwa) suka sanar mata abinda suka jiyo. Kuka sosai tayi ta dage lallai su barta taje ta ganowa idanunta inda karime take suka hanata suka lallasheta suka koma gida.
Saida hauwa ta dâauki tsawon sati biyu a kullum zata fita neman karime ta dawo babu ko labarinta. Wasu lokutan tana saâa ta shiga tamaru ba tareda an ganta ba har gidan da suka zauna taje ta ganshi an âkoneshi âkurmus.
Wata shiga da tayi tamaru ne ta hadâu da âyammatan âkauyen a hanya, suna ganinta suka tsala ihu suka watse suka koma gari suna shelar sunga kurwar Hauwa. Tun daga ranar aka sanya idanu aga shigowar itama daga lokacin bata sake zuwa tamaru ba.
Zamanta a rugar su modibbo a dâarare take yinsa a kullum jira take wani mugun abu ya faru su dâaura mata laifi saidai babu abinda ke faruwa a rugar su modibbo sai alkhairi. Taishu ta zama âyar gida domin tare suke tatsar nonon shanu ita da dabo jauro har kadâi ta koya mata sannan wasu lokutan ita ke girki a gidan. âDakin amaryar modibbo aka bata domin auren da sauran lokaci.
Suna zaune a bukkar dabo jauro modibbo ya kirata yace yana son magana da ita. Fitowa tayi ta tsaya ya shimfidâa tabarma yace â ya batun âyarki kuwa?â
âBabu labarinta har yanzu domin na zaga sosai ban sameta ba, ina shirin dai naje garinsu mahaifinta na duba ko tana canâ.
âAllah ya bayyana ta, dama tambayarki nazo yi saboda zaren dake wuyanki. Zaren ya tabbarmin da maganarki ko dai âkarya ce ko kuma akwai abinda kike âboyewaâ.
Kallon sarâkar tayi ta riâke kan kan sarâkar da hannun tana mamakin maganar modibbo. Babu wani abu a jikin sarâkar zare ne irin na saâkin da a jikin sarâkar sai wani abu round tamkar agogo amma ruwan gwal. Cigaba da magana modibbo yayi yace âduk mutumin da zai rataya wannan a wuyansa to tabbas ba âkaramin mutum bane domin a cikin buzaye ma dâaidâaiku ne ke iya mallakar abinda ke cikin wannan sarâkar. Ki fadâa min dalilin zuwanki garemu me kike nema?â
âBanida wata manufa ta zuwa gareku modibbo face taimakon da na nema. Wannan sarâkar itace abu na âkarshe da mahaifina ya barmin gado ina rataye da ita ne saboda tunawa dashiâ.
âMu ganiâ. Modibbo ya furta yana miâka mata hannu, kunce zaren tayi ta danâka mishi ya budâe gidan sarâkar ya ciro wani dunâkulallen abu ya miâka mata gidan sarâkar yace âmutum dâaya ba taâba gani da irin wannan abun sai ke. Mahaifina yana da irinsa wanda aka bashi kyauta a wani can âkauye mai nisaâ.
âMenene shi?â Taishu ta tambaya, murmushi yayi yace âsanin amfaninsa da sarrafashi sai wanda ke shiga jeji. Idan har zaki bani wannan zan fansheshi da shanu biyuâ.
Mamaki ne ya kama Taishu domin tasan darajar shanu a wurin fulani amma zai fanshi wannan âkanâkanin abun da shanu har biyu? Idan har ta saida shanu biyu tana da tabbacin zata samu kudâin da zai iya kaita cikin asalinta timiya. Har ta budâe baki Modibbo yace âkar kiyi gaggawar amsawa kiyi tunani. Sannan wannan marufin zinaren gaske ne kar kiyi wasa dashi. Ki rage bayyana shi domin kika shiga cikin mutane zaki iya rasa ranki sanadiyyar saâ.
A ranar kwana taishu tayi tana tunani saidai tunaninta na kan abu dâaya ta baiwa modibbo abinda yakeso ta karâbi shanu ta sayar ta tafi neman âyarta. Juya sarâkar wuyanta take cikin mamaki, ashe tana da dukiya a hannunta take zaune cikin talauci da wahala na tsawon lokaci?
Washegari da sassafe kafin fitar su Modibbo kiwo sukayi baâki daga wata rugar, tunda aka sanar ma Modibbo manga maudâo yazo yanayinsa ya sauya, dabo jauro ma saida ta sauya fuskarsu ta nuna alamun dâacin rai. Tambayarta Taishu tayi lafiya meke faruwa? Dabo jauro tace âdâansa ya kashe yarona shekarar da ta wuce a wannan shekarar gidâadâo yaci alwashin dâaukar mishi fansa, ina tunanin dalilin da yasa yazo kenanâ.
âAllah sarki Allah yayi mishi rahma, amma dabo jauro da dai kunyi haâkuri mahaâkurci mawadaci, ta yiwu tsautsayi ne ya gifta wancan ya kashe yaronku idan gidâadâo ya kasheshi da gayya zai iya zama fitina a nan gaba, kuma ran yaron zai rataya a wuyan gidâadâo. Kuyi haâkuri Allah yana tare da masu haâkuriâ.
âAbinda yasa gidâadâo yayi haka shine tunda aka kashe bawuro babu wata magana da tazo daga garesu, da ace sun bada haâkuri abun zai iya wucewa amma sai sukayi tamkar babu abinda ya faruâ.
Suna maganar Modibbo ya shigo da sauri ya kira dabo jauro gefe yace mata cikin harshensu na fulatanci âmanga maudâo yazo ya bani haâkuri har ya taho da shanu ashirin a matsayin yarjejeniyar zaman lafiya. Dabo jauro ina ganin mu Karâba kawai tunda ko fitinar muka tada sun fimu mutane, banaso a sake rasa wani ran dalilin fansaâ.
âAshirin modibbo? Ban taâba tunanin ruga mai girman ta su manga maudâo zasu zo su bamu haâkuri baâ.
âNi kaina nayi mamaki, yanzu yace muyi magana dake ki fito zai baki haâkuri kemaâ.
Mayafi Dabo jauro ta yafa ta fita inda suka zauna cikin yarensu na fulani ya cika ta da kalamai masu dadâi, suna washe baki suka haâkura aka kora musu shanunsu suka dâaure. Kwana biyu tsakani dâaya daga cikin âkannen manga maudâo ya nemi auren danejo, harka ta girma shima saida ya bada shanu goma a matsayin na gani inaso.
Farin ciki wurin modibbo baya misaltuwa domin shanunsa sunyi ciwuka watannin da suka wuce ya rasa wajen shanu goma dalilin wata cuta da baisan dalilinta ba, bayan ya natsa ya kira taishu yace âzuwanki kin zo min da alkhairi taishu, alkhairin da nayi shekaru ban sameshi ba. Ina neman alfarmar ki cigaba da zama damu taishu, idan har kin amince ina miki tayin aureâ.
Free page
Free pages sun kusa qarewa, a hanzarta a siya đđ
Littafina na kud'i ne 500 kacalđ„°đ„°ku nuna min solidarity ni kuma zanyi 'ko'kari na baku abinda zu'katanku suke sođđ
Akwai VIP 700 ga wadâanda ba zasu iya jira ba, 3 pages a kullumđđ
Account details
0472624453
Musa maryam Aminu
Gtbank
Ki a tuntu'beni ta wannan number
***