CHAPTER SEVEN 7
by @misshajo
🧸 *KHADIJATUL SABREEN* 🧸
```MALLAKAR```
*HAJARA L SADEQ*
Arewabook👉@Miss Hajo✍️
🅿️.............*15 & 16*
"Saida bayanin nata ya so bawa Anwar dariya ya fusge ya ce"waye zai gane kwatancen Nan naki,,ki fad'amun yanda Zan gane kina batamun time".
Shagwabe fuska tayi kamar zatayi kuka ta ce "To nima Bansan sunan unguwarba Yaya beauty Amma muje zangane bi hanyar chan ta fad'a ta na nuna Masa bayansu"
Duk yanda Anwar yaso fisgewa Saida ya danyi murmushi sosai yanayin yarinyar da yanda take magana ya basa Dariya ,kafin yabi hanyar da ta fad'a ,.
Hanyoyi ya dinga bi da ita sai sunyi nisa ta ce ba Nan bane a sauya sosai Anwar ya Fara gajiya ya lura shiriritar dashi yarinyar keson yi Parking Yayi tare da juyowa ya kalleta fuska ba wasa ya ce.
"Saukarmun a Mota tunda bakisan Inda zakiba Ina da aikinyine."Sabren najin haka ta fashe da kuka tare da Fara Masa diddire_diddiren kafarta a Mota Tana kukan sangarta ta ce.
" Allah bazan saukaba saika maidani gidanmu so Kake a saceni a yankani ayiwa mom Dina da dad asara nidai saika kaini gida".
sakato Anwar Ya yi Ya na Kallon ikon Allah ,Ya na ganin sangartattun Yara Amma tunda yake bai taba ga Mai sangartar wannan yarinyar ba tsaki Yaja a ranshi Dan ya tsani yaga Yara na sangarta"To Ni sani na kikayi,idan fa nidinma D'an yankan Kaine haka kawai kin makalemun to Bari na kaiki wajen yankan Kan ba shikenanba"
Ta tsinkayi muryarshi Lokaci guda ta hadiye kukan kallonshi tayi sosai ta Kare Masa kallo kafin ta turo Baki gaba ta ce.
"Ai nasan Kai ba D'an yankan Kai bane bakayi Kama dasu ba "ohh Daman har Kama garesu"ya Fada Yana tada Mota ya bi wata hanyar ko Allah zaisa a dace"Eh Mana Ni ai Dana gansu Ina ganesu ".
shiru Yayi Mata Jin hakan ya sanyata itama yin shirun"tsit motar ta dauka bakajin Komai sai sautin Gidan radio kallonshi ta dingayi haka kawai saita dinga ganin Yana yanayi da mom d'inta musamman idanunsa chocolate skin dinsa kasayin shiru tayi a hankali ta ce ".
"Yaya Beauty kaima D'an Nan garin Ne?Eh"ya Bata Amsa a takaice"To Kai inane gidanku?"duniyar sama"ya sake Bata amsa"kenan Yanzu Samar zaka koma?"Eh ko kina zuwa?Mak'e kaf'ad'a tayi ta ce "Umm umm injema ko Kai aljani ne "ya sunan mamanka wlh kanamun yanayi da mom d'ita ?
ta Kara jefo Masa tambaya"Dan tsaki yaja ya ce "kin fiya surutu parrot "harara ta galla Masa Tere da juya Dara daran idanuwanta "daidai ya juyo wara idanu yayi ya ce"Ni kike harara"Kauda Kai gefe tayi ta ce "Ni bada Kai nake ba "cigaba yayi da driving dinsa Daidai zai gitta ta wajen wasu masu gashin kaza idonta ya Kai wajen cikin d'aga murya ta ce.
""wayyo Yaya Beauty Dan Allah kaza ka sayamun "ganin Yana Shirin wucewa ya sanyata rirriko hannunsa Kadan ya Hana ta chaza musu accident ba shiri ya taka birki cikin d'aga murya ya ce "Waike Baki da da hankali,da Kika kadamu fa"ya Fada Yana sakar mata Tsawa "Kuka ta fashe dashi kamar ya daketa ta ce "To ba Saida nace ka tsaya ka sayamun kaza ba"tsaki yaja ya ce.
"ba a saya Ajiyar kud'in Kika bani,wlh idan bakiyi wasa ba Zan saukeki a tsohon Daren Nan daga haduwa dake kin likemun saikace na had'a dangi dake Duk kin chazamun Kai sai gararamba kike sanyani inayi a gari".
"cikin shagwaba ta ce "To Daman nace Kai danginane mema zai had'ani dakai Had'uwar joint kawai Ni ka saimun kazar bashi idan mukaje ba biyanka zanyi ba daga Rance ai ba kyauta nace ka sayamun ba?.
",Oh haka kikace to bazan ranta ba Kuma daga wajen Nan indai har Baki gano Gidanku ba Zan saukeki ki nema ke kadai"naji Yaya Beauty wlh indai ka saimun kazar sannan Zan gano Gidan sannan ma Rance Ne zakaban da munje gida Zan amsa wajen Mom d'ina na baka".
Banza Anwar yayi Mata Tare da fita ba ayi minti ukku ba ya dawo tare da leda batare da ya kalleta ba ya aje Mata Kan Cinya cike da murna ta ce.
"Thnks Yaya Beauty"cigaba da driving yayi ya nufi wata hanyar ko Allah zaisa a dace Yana tuna sunan da ta lakaba Masa Yaya beauty ko gidanwa ya Zama yayanta in Banda kawaii macece idan Ya sauketa baisan wani Hannu zata fad'a ba da tuni ya sauketa shawara ya Yanke in har Bata gano ba gidan ganin 11pm harta wuce gwara kawai ya kaita Gidan Radio.
Sabren bude kazarta tayi tahau ci sosai naman yayi Mata dadi har wani lumshe Ido take ta gefen Ido Anwar ya kalleta ya GirGiza Kai Yana jinjina wautar yarinyar kawai batasanshi ba ta makale masa to da ace shidin mugu Ne fa ya tabbata da Bata fada hannu ba gari ba da komai zai iya faruwa,.
Tana cikin ci taga zasu wuce wajen da ake Saida Fruits da juice marairaicewa tayi ta na kallonshi ta ce "Uhm Yaya beauty Dan Allah ga fruits Nan ka sake rantamun sai ayi lissafi"wata harara ya banka Mata ganin haka ya sanyata Fashewa da kuka ta Fara diddira kafa "tsaki yaja baisan Lokacin da ya sakar Mata tsawa ba Wanda haka ya Kara rudar da ita ta Kara Fashewa da kuka ".
.OMG ya Fada Yana dafe saitin kansa tare da duba agogo yaga karfe Sha Biyu saura tsaki yaja ya fita ya sayo Mata tare da cilla Mata cikin sauri ta amshe tare da aje naman kazar fakar idonsa tayi tare da yi Masa gwalo,tunani yayi kawai gwara ya kaita Gidan radio Dan ya gaji da gararanba da ita a gari karta jaza Masa masifa,wani tunani ne ya fad'o Masa kallonta yayi ya ce "Baki da number wani naki da kika hardace a Kira".?
Tana Shan gwanda ta ce "umm na haddace ta mom" ta Fada muryarta Bata ma fita sosai sakamakon cika Mata Baki gwanda da tayi,".
"Daman kinsan Akwai number a kanki kikayi ta sanyani gararanba sai kace kin samu driver"mancewa nayi fa Yaya beauty "ta Fada hankalinta kwance tuni damuwarta ta gushe tunda ta samu abunda takeso"karki Kara cemun wani Yaya beauty "ya Fada Yana Had'e girar sama da ta kasa tare da Mika Mata wayarsa ya ce Sanya ki Kira ki tambayeta unguwar".
Amsa tayi ta Sanya numbobin mom ringing biyu mom ta daga lokacin ta gaji da kuka Dan har Gidan radio an tafi badawa cigiyarta "Hello mom baby ce "Lokaci guda mom ta zabura ta Mike ta ce "Baby Ina kikaje ,kika tayarmana da hankali kina Ina"Bata bawa mom amsa ba sai Cewa tayi "Ya sunan unguwarku mom"Cikin sauri mom ta ce "Layout"layout"ta Fada Masa Masa kafin ta katse wayar ta goge number mom ta Mika masa.
Cigaba da ciye ciyenta tayi har batasan sunzo unguwarba ,kina iya gane gidan Yanzu ko sai an kirata tunda na Kula kwalwar Taki chunkushe take bakya ganewa daga gani ko a class"Harara Sabren ta balla Masa tare da turo Baki gaba wara idanu yayi Yana nuna kanshi ya ce.
"Ni"?
To menayi a cikin Daren Nan harma idonka yagane maka"
ta Fada Tana turo Baki tare da karewa unguwar kallo Kasancewar akwai hasken glove ya sanyata gano k'ofar Gidan su Mom wata Nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauke gabanta ne ya fad'i tuno bashin da taci na uban sayayyar da yayi Mata kayanta ta Had'e a leda guda Tare da bude murfin motar ta fita da gudu kafin ta juyo da karfi ta ce.
"Yaya beauty Daman wayau nayi maka naci banza ,na koshi,sannan kayi yawo Dani a gari Daman so nake Naga gari kuma Kayimun sayayya da kudinka nagode saimun had'u a lahira Dan bazaka Kara gani na ba har abada ba garin nake ba "Tana Gama fadar haka ta Kara kwasawa a guje.
Anwar ya rasa Dariya zaiyi ko haushi ,baitaba haduwa da wacce tayi wasa da hankakinshi ba irin wannan yarinyar babban haushinshi na dagangan ta Bari ya dinga yawo da ita,Wanda baisan ta fada Masa ne kawaii saboda tsabar shakiyanci,sannan maganarta ta taci banza ita ma taso bashi Dariya ga haushin shi na ashe layin su Hajja ne ma tun farko Rashin sani juya Kan motarshi yayi Ya wuce Kai tsaye spare Gidansa Dan baya shiga cikin masarauta muddin dare yayi.
Sosai mom sukayi mamakin ganin Sabren Ita hankalinta kwance Su kuma gaba Daya ta tayar musu da hankali Dan maman katsina ko gida Bata tafi ba koda suka tambayeta Bata boye musu komai ba sosai maman katsina ta Kara jinjina wautar da rashin ji irin na Sabren kawai ta makalewa wani batasanshiba danma Allah ya taimaka mutumin kirki ne da ta hadu da na banza ya lalata Mata rayuwa fa Fada sosai maman katsina tayi Mata akan yawo,da Kuma yarda da wadanda Bata saniba kafin mom ta Dora nata Tana ganin haka ta shigewarta daki ta kwanta ta jima Tana dariyar wayan da tayiwa mutumin Nan yayi Mata sayayya Tana ta Dariya har bacci yayi awon gaba da ita.
Washegari Anwar ya wuce Lagos wajen aikinsa bayan yasamu Sanya albarka daga wajen iyayensa Bangaren hajiya talatu ko bataso hakan ya faru ba saboda Akwai maganin da Boka ya Bata akan tilas ya cisa a abinci kafin mako guda maganin zai daina aiki to gashinan Kuma ya tafi Dan ko bankwana baije yayi Mata ba sai text yayi Mata saboda Kiran gaggawa Daya samu daga wajen aikinsa.
Mom rage kwanakin da zasuyi tayi Dan ba k'aramun tsorata tayi da b'atan Sabren ba tasan ba saduda take ba hakan yasa kwanansu shida ko gidan Yan uwanta Bata zagaya ba tayi musu bankwana driver' da Daman Yana Nan ya wuce dasu Wanda murna wajen Sabren har baka suna Isa gida ko ciki bata shige ba ta ruga Gidan su Affan sosai suka hau murnar ganin Juna suna rungume juna Affan Yana Fada Mata yanda yayi missing d'inta Shi ya rakota har gida bayan yayiwa mom Sannu da zuwa dashi ya Taya mom ta gyara Gidan da ya danyi datti abun Tafiya da sukayi Dan Sabren Cewa tayi ta gaji.
Wannan karinma da dad yazo satinshi biyu haka yakoma ba abunda ya shiga tsakaninsu da matar tasa sai Dan wasanni Dan Sabren ta k'asa ta tsare babu ta yanda zasu kebe sannan ko bacci take indai sukayi niyyar wani Abu sai ta farka cikin satin Ne mom ta Fara rashin lafiyar zazzabi da ciwon ciki.
Yauma kwance take sosai ciwon cikin nata ya matsa Mata gashi Taki fad'awa dad Sabren da ta hado Mata tea ta zauna gefenta cike da kulawa ta rungumota ta tadata zaune ta ce
"Sannu mom ga tea din "GirGiza Mata Kai tayi Ta ce "jira ya Dan lafa"Aje tea din tayi ta ce "Wai mom ciwon cikin me kike kwana biyun Nan sannan jikin kima da zafi fa ko dai ciki gareki kani zakiyimun Daman Ina sane tun ina karama idan nace kiyimun Kane kikecewa zakimun Allahsa Kanin ne zakimun mom shine ko?"
"Saida ciwon cikin ya lafa mom ta Gama had'a zufa kafin ta dauki ruwan tea din Tasha "Kwabe fuska Sabren tayi ta ce "Mom Baki bani Amsa ba "Dan Allah yimun shiru Sabren please banason surutu".cewar mom.
"Sannu to?yawwa Baby"momy Saura wata nawa ki haihun Dan na Fara shirya dinner da zamuyi da friends dina"dafe Kai mom tayi ta ce "Zaki dameni baby cemiki nayi haihuwa zanyi"turo Baki gaba tayi ta ce"Ai nasani Mana bakyason ki fadane Kuma Bari naje nayiwa dad albishir ta Fada Tana rugawa tare da janyo wayarta Ta dannawa dad Kira.
Yana Dauka cikin d'oki ta ce "Dad Albishirin ka"Goro babyn dad"Mom nada ciki zata haifamun k'ani "Wara idanu dad yayi sosai cike da farinciki ya ce "da gaske baby wannan babban albishir ai kin chanchanci tukuici Mai tsoka Ina mom din Taki maza Kai Mata wayar '"Tana Dariya ta ce.
"Ai dad tukuicina kawai shine ka kaini Dubai da England da Paris tare da India mu hadu da aditi sharma saboda ita ce best actress d'ita "ta Fada Tana mikawa mom wayar daga Bangaren dad ya ce "Sweetheart Daman Akwai wannan babban albishir din Baki fad'amun ba ,wannan abun farinciki haka".
"Mom ji tayi kamar me wani gamin saita rasa Wanda yafi wani tsakanin sabren da dad "Hmmmmm ya wajen aikin".
kawai tace "Kamarya hmm ya Zaki chanza magana please wata nawa,kinje hospital an dubamun lafiyarki kuwa?waiko baka karya ba dadyn Sabren Kai Yanzu ko ce maka akayi Ina da ciki saika yarda ,ana haihuwa ba mahaifa Daman?Sannan kodai a Ruwa akeshan cikin ban sani ba kamanta shekara biyu da wani abu rabona dakai?".
Lokaci guda murnar dad ta koma ciki A sanyaye ya ce"sorry na Manta hakane sweetheart Gaskiya Nima Hakuri na yazo karshe Jibi ki shirya tarbar mijinki Ina Nan zuwa jibi saimu shirya yanda zamuyi da daughter".
Sosai mom Taji wani Dadi a ranta suna Gama waya da dad ta mikawa sabren wayarta.
kamar yanda dad ya Fada ranar ya dawo Sabren da mom sosai sukaci kwalliyarsu kamar ko yaushe idan zai dawo an shirya Masa lafiyayyun abinciccika Sabren na lik'e jikinsa Tana da dokin ganinsa Yana shafa kanta suna ta hirar y'a da uba mummy tayi serving dinsu wanda a Baki ya dinga feeding din Sabren harta Koshi kafin itama tayi feeding dinshi mom ce ta ce.
"Nima ban yarda ba to oya ayi feeding Dina "Dariya sukayi Sabren ta ce "To Mom Bari mijinki yayi feeding dinki".
dakuwa mom tayi Mata yayinda dad da ita suka sa Dariya cikin farinciki suka Gama dinner dinsu kafin Dad ya kalli agogo Karfe Tara na dare ya gani da Ido yayiwa mom sign ta ankare Kallon Sabren tayi ta ce.
"Babyna Muje na kaiki Gidan Su Affan Samira tayi maki kitso saiki kwana a chan"Jin zata kwana gidansu affan ya sanyata murna haada tsalle ta ce.
"To mom muje"Ajiyar zuciya mom ta sauke har dad dad ya ce Bari na rakata ke zauna "Dad ya rakata har gidansu Affan kafiin yayi hug d'inta tayi mishi bye bye tare da Saida safe ta shige cikin Gidansu Affan .
Affan shine matsayin sallamarta Tana shiga suka Taba ta ce "Albishirka besty yau gidanku Zan kwana zamu jima muna game a tab yau saina gwada maka kwarewata "Dariya yayi ya ce.
"Wayarki dai Akwai charge ko "Ehmana tun safe na cikata "Maman su Affan ce ta ce "Au ba kitson da mamanki tace a Miki ba zakiyi ba kenan ta game ma kike"Dariya tayi ta ce "Mama kitso da Daren Nan saidai gobe Tana Gama fadar haka taja hannun Affan suka zauna a k'asa suka Fara buga game Hankalinsu kwance ,girgiza Kai mamansu Affan tayi Tana jinjina wannan kawancen tun yarinta zataga ranar da aure zai raba tasan dai ansha kuka.,
Kashe wayoyinsu mom sukayi saboda gudun wata matsala......bayan komai ya lafa kamar sarar mom Koda yaushe Bata kwanciya ba tsarki wanka ta maza taje tayi tare da dauro alwala dad ko Wani baccin dadine da ya Jima baiyi irinsa ba ya kwashesa ba irin yanda mom bata tasheshiba Akan ko alwala ce ya Tashi yayi Amma ya k'iya haka dai ta hakura suka kwance like da juna.
Bangaren Sabren harsun kwanta karfe Sha Daya ita da samira Taji ta kurma wani uban ihu yayyun affan manya Dakyal suka rirriketa zabura kawaii take Tana wasu maganganu da basusanma wani yare ne ba gashin kanta gabaki d'aya ya warware zabura take sosai Tana neman fusgewa mamansu affan da Ihun ya tasheta da ita aka hadu aka dinga tofa Mata adduoi tare da Sanya Karatun alkur'ani wani irin gunjin kuka take Tana jujjuya Kai Tana hawaye adduoi sosai aka shiga tofa Mata Dakyal suka samu wajen 1:00am abun ya lafa ta Fara sauke ajiyar zuciya kafin ta lafe jikin Maman Affan ta koma bacci kamar ba itace ta Gama fisge fisgen Nan ba".
____Da wani irin masifaffen zazzabi Mai zafin gaske dad ya Tashi Gaba Daya hankalin mom Duk ya Tashi baitaba ciwon da ya hanashi yin sallar asuba ba sai wannan sosai jikinshi yad'au kerma,Yana kakkarwa ya ce.
"Rufamun bargo Amina sanyi nakeji,"Hankali tashe mom ta ce"To Dadyn sabren please ka Tashi Muje asibiti "Ki Rufamun zan samu sauki "Tana rufa Mai ya Kara cewa ta rufa Masa wani Saida ta rufa Masa bargo har ukku chan Cikin muryarshi da Bata fita ya ce "yayemun bargon Nan Amina zafi nakeji har Cikin Kashi na ji nake kamar ana huramun wuta a Cikin jikina zafi Aminaaaaa"ya fadada Cikin dauriya Yana Jan Aminaaaaa da karfi".
Iya rikicewa mom ta rude batasan sanda ta fashe da wani irin kuka ba ta ce "innalillahi wa Inna ilaihiraji'un meke faruwa dakai Mustapha?.........✍️
*Domin magana da marubuciyar kai tsaye ****
_Ummu Maheer_
*DINYAR MAKAHO*
_Miss Hajo_
*KHADIJATUL SABREEN*
_Mrs Bukhari_
*ANGULU DAKAN ZABO*
_Ummu Affan_
*SANDAR MAKAUNIYA*
_Mom Islam_
*TSAUTSAYIN TAUNA*
*Ga tsarin yanda biyan yake*
_Guda d'aya 300_
_Guda biyu 500_
_Guda Ukku 700_
_Guda hudu 800_
_Guda Biyar 1k_
Kai tsaye zaku iya turo kuɗinku ta wannan hanya.
0037219728
FATIMA RABIU SUNUSI
StanbicIBTC BANK
Shaidar biya ta nan
***
Masu turo kati MTN ta wannan number.
***
Ƴan Niger zaku turo da naku kai tsaye ta wanna number.
***
*Mun gode da kasancewa da gawurtattu biyar taku na biyu* 🤘🏿
_*Miss Hajo ce*_ 🤙