A CIKIN DUHU

35

by @kitty

A CIKIN DUHU


BONUS PAGE😋😋

35

***


Ahmad yana sauka kai tsaye office ya nufa ya fad’a aiki, gajiya ce a jikinsa sosai saidai aiki da ‘kasashen waje ba kamar aiki da nigeria bane kowane lokacinka cikin kud’inka yake, kwanakin da yayi baya nan saida aka zaftare awannin a albashinsa saboda haka ba zaiyi sanya ba.


Saida dare ya gama aikinsa ko tunanin komawa gida baiyi ba ya fita ya sayo abinci yaci ya shiga toilet d’insa na cikin office ya kwanta kan kujera baccin gajiya yayi awon gaba dashi, kiran sallar asuba ne ya tadashi yayi sallarsa a office d’in domin yana da tabbacin kamfanin nasu a rufe yake, mamaki yayi ma da babu wanda ya nemeshi.


Yana idar da sallah ya sake komawa bacci bai tashi ba saida yaji bugun ‘kofa. A gajiye ya tashi dukda baccin da yayi ya kalli agogo yaga 9:30 na safe, zumbur ya mi’ke ya bud’e ‘kofa ya samu manager d’insu ne.


“Ahmad you’re sleeping?” Managee ya tambaya yana nufar teburin Ahmad, sosa ‘keya Ahmad yayi yace “sorry sir i was working till late I didn’t know i slept here, but I’m done with the files here they are”. Ya mi’kawa Manager d’insu da ake kira da Hakeem files d’in, dubawa hakeem yayi yace “nicely done, sannu da
‘ko’kari ko?”


Murmushi Ahmad yayi ya mishi alamar eh da kai domin tun zuwansa nigeria ya damu ya iya hausa kuma a hankali yana iyawa. Kallon office d’in Hakeem yayi yace “I think you can rest today we don’t have much to do, but we have a meeting tomorrow with some of our clients so be here early”.


Dad’i ne ya ziyarci Ahmad yace “thank you sir, i will insha Allah”. Hakeem na fita Ahmad ya d’auki kayansa ya fice shima, mashin d’insa ya d’auka har ya kunna zai tafi yaga fitowar Abbu, tsayawa yayi suka gaisa Abbu yace “ya hanya? Naga shigowarka jiya ina shirin fita”.


“Lafiya lau alhamdulillah, ai anan na kwana ma yanzu babu aiki na kammala jiya zanje na huta ne, na bar Inna a can”.


“Okay..um
ya kariman?” 

“Tana lafiya lau”. Ahmad ya furta a ta’kaice domin sam a yanzu baya so yana maganar karima da Alhaji Ismail musamman yanzu da yaje yaga new karima ba wadda ya saba gani ba.


“Babu wani matsala dai ko?” Abbu ya sake tambaya, Ahmad danne zuciyarsa kawai yayi ga gajiya ga kishi yace “babu”.


Sallama sukayi ya wuce gida Abbu kuma ya koma office yana tunanin hanyar da zaibi yaji daga bakin karima ko kuma ya ganta. Tun tafiyar Ahmad yake tunani akan maganar da yayi a station wadda itace kad’ai mafita idan yana so ya mallaki karima ya dawo da ita kusa dashi, aurenta kawai zaije nema a bashi kuma a yanzu ya shirya aurenta idan yaso ko me zai faru daga baya sai su san hanyar warwareshi.


Saida Ahmad yayi kwana biyar da dawowa sannan Inna ta dawo, a ranar ta sanar mishi muradin karime da mahaifiyarta sannan ta d’auki kud’in da suka bata ta dan’ka mishi tace “Ahmad mutanennan suna can wata duniya daban amma sun d’auki amana sun bamu saboda yarda, dan Allah ka kula musu da dukiyarsu kaji tsoron Allah a kan wannan amanar ka samo musu muhalli mai kyau wanda zasu sami sakewa a ciki”.


Bakinnan nashi har ‘keya saboda murna yace “insha Allahu Inna zan ri’ke amana amma bansan nawa kud’in zai kama a naira ba idan aka juyasu”.


“Sunce ya kai dubu d’ari biyu amma ka canza kaga abinda za’a samu”.


Zama yayi yace “to ai Inna d’ari biyu ba zata sayi gida ba, me zai hana a kama musu haya na shekara guda, a zuba kaya a gidan da gyare-gyare da ragowar kud’in idan suka dawo daga baya sai mugani idan akwai halin sayen”.


Zare idanu Inna tayi tace “kai Ahmad yanzu wannan uban kud’ad’en kace ba zasu sayi gida ba?” Dariya Ahmad yayi yace “Kai Inna kamar baki san tsadar rayuwa a yanzu ba? Ai yanzu ba kamar da bane. Wannan gidan namu ma sai kiji an kusan tayashi miliyan idan saidashi za’ayi. Gida a dubu d’ari biyu saye gaskiya bazai siyu ba”.


Tagumi Inna ta zuba tace “idan kuwa hakane Ahmad akwai matsala babba. Ta yaya zasu dinga d’awainiyar haya ga kuma ta yau da kullum? Ba wata tsayayyar sana’a garesu ba dukka zaman zai musu wahala fa”.


“Inna a sama musu gidan dai idan suka dawo zasu iya samun sana’ar da ko ma menene amma bana son zaman karime a wannan garin, da ace inada daban bazan dawo ba tareda ita ba, yanzu kuwa tunda ga sau’ki ya samu ai duk yanda zanyi naga ta dawo gareni zanyi”.


Inna kawai jinsa takeyi amma a ranta tana tsoron zamansu a kano da wannan ‘karma-‘karmar. Tunani take yanda zata sanar musu da abinda ake ciki saidai babu damar waya, kaf timiya babu sabis sai ka fito farkon bagzane wanda tafiya ce mai nisa ta kusa awa guda, gashi karime babu caji wurinta babu alamun caji ita kuma ba zata iya komawa Timiya nan kusa ba saboda yanayin jikin tsufa.


Kwana biyu da dawowarta tana zaune da yamma taji sallama, cikin sauri ta fita domin tace Ahmad ya turo mata mai ruwa fanfon gidanta ya d’auke, Alhaji Ismail ta gani a jikin motarsa wanda ya sanyata fad’ad’a murmushin ta tace “sannu da zuwa Alhaji bismillah”.


Cikin gidan ya shiga ta shimfid’a mishi tabarma ta kawo mishi ruwa sannan ta d’auko dabino ta ajiye mishi tace “wannan tsarabar mutanen Timiya ce dama inata cewa zan baiwa Ahmad ya kawo maka”.


“Masha Allah sannu da ‘ko’kari fa Inna ana ta d’awainiya Allah ya saka da alkhairi”. Abbu ya furta yana shan ruwan da ta kawo, wannan na d’aya daga cikin abubuwan dake ‘kara mishi girma a idanun Inna saboda bai ta’ba zuwa ta kawo mishi abinci ko ruwa ya’ki amsa ba, ruwa ne ta d’ebo daga randarta a kofi Abbu bai nuna ‘kyan’kyami ba ya d’aga ya sha abinsa sannan yaci dabino yace “dama nazo ne naji yarinyarnan tana lafiya dai ko?”


“Lafiyarta ‘kalau wallahi tana tareda da uwarta ai hankalinta ya kwanta, saidai dake garin ‘kauye ne kuma kasan ‘kauyen can ‘kasar da namu akwai banbanci tace bata jin dad’in zaman garin, yanzu haka ma mahaifiyarta ta bada kud’i tace a nema musu gida a nan ko da haya ne su dawo saboda karatun ita kariman da sauran abubuwa”.


Gyad’a kai Abbu yayi yace “okay, amma shi Ahmad bai fad’a min hakan ba koyaushe na tambayeshi ita zaice lafiya take kawa”. Shiru Inna tayi bata amsa mishi ba yace “kuma ai haya abu ne mai wahala gaskiya, zaifi kyau ace sun mallaki gidan kansu”.


“To nima haka nake musu kwad’ayi amma abinda ke hannunsu ne ba lallai ya kai ba, yanzu haka dubu d’ari biyu suka bayar Ahmad na ta fafutuka a sami haya mai sau’ki a ma gidan kwaskwarima a saka musu abinda ya samu kafin su ‘karaso”. Inna ta ‘karashe maganar tana kallon Abbu da ya bata dukka hankalinsa.


Amsa mata yayi da “okay” sannan yace “gaskiya haya bazai yiwu ba, zanga abinda za’ayi akan gidan insha Allah amma kafin wannan akwai magana mai muhimmanci da ta kawoni ina neman alfarma da kuma izni”.


Inna tamkar ta sauko daga kujera tace “umarni daga garemu Alhaji?” Murmushi Abbu yayi harda Sunkuyar da kai yace “eh Inna tunda kusan dai anan kece kamar uwa a wurin
ita
yarinyar wato karima. Ina neman Izni a bani damar aurenta kuma ina neman alfarmar a shige min gaba
wurin..umm
su nata iyayen”.


Jim Inna tayi dukda ta jima da sanin maganar sannan tace “To Alhaji ba wai na’ki bane domin duk wanda yace yana son naka ai ya gama maka komai ga kuma d’awainiya da aka sha da ita wadda da ace da mu ka barta ba zamu iya ba, saidai yarinyarnan yanzu tana hannun iyayenta sannan tana da abubuwa da dama a gabanta, shigewa gaba zan iya shige maka amma idan har karime ta amince da kai a matsayin miji”.


Wani murmushi Abbu yayi ya du’kar da kai wai shi suruki sannan yace “Hakane Inna ai nima babu dole a ciki idan ta amince zanfi kowa jin dad’i idan kuma bata amince ba ma duk babu matsala abinda nayi niyya zanyi musu insha Allah, dama ina tunanin zuwa can garin nasu na gabatar da kaina ne amma nace sai na fara neman izni gareki tukuna”.


“Babu komai hakan da kayi yayi kyau sosai ya nuna kai d’in mutumin arzi’ki ne, Allah ya tabbatar da alkhairinsa duk abinda tace zan goyi bayanta d’ari bisa d’ari amma yanzu bazan maka al’kawarin komai ba”.


Godiya Abbu yayi ya fita daga gidan cikin murna, yana fita ya kira ‘kaninsa da yake harkar gidaje ya sanar dashi yana neman gida na sayarwa.


“Ismail me zakayi da gida kuma?” ‘Kanin nasa ya tambaya, Abbu bai amsa mishi ba yace “dama akwai tsarin amsa tambayoyi irin d wad’annan idan mutum zai sayi gida? Kaga gida kawai nakeso madaidaici na mutum biyu ginin zamani wanda akwai ruwa da wuta babu matsala”.


“Akwai, miliyan d’aya da dubu dari biyu”. ‘Kanin Abbu ya furta, shiru Abbu yayi ya gama lissafi sannan yace “okay ka turo mun shi a waya nagani”.


Abbu yana isa gida videon gidan da aka fad’a mishi ya shigo wayarsa. Gida ne ‘karami ginin zamani da madaidaicin gate da ‘karamin tsakar gida sai band’aki d’aya a tsakar gidan. Babban palo ne daga gefen band’akin wanda yake d’auke da d’akuna uku a ciki da kitchen. ‘Dakuna biyu suna kallon juna da band’aki a tsakiyarsu sai d’aki d’aya daga gefe. Gaba d’aya gidan an mishi sabon fenti milk and yellow yayi kyau sosai.


Abbu kiran ‘kaninsa yayi yace “naga gida amma wacce unguwa ce? Banason nesa sosai”.


“Ba nesa bane a cikin sharad’a gidan yake ai, idan ka samu lokaci kazo muje ka gani”.


“Okay zanzo amma yanzu zan maka wiring kud’in ka kular min da gidan na wani d’an lokaci wanda zasu tare basu kusa”. ‘Kanin Abbu dai tambayoyi ne fal ransa amma baida damar fito dasu domin ya san halin yayan nasa indai ba niyyar fad’in abu yayi ba bazai fad’a ba, tsoronsa d’aya Allah yasa ba aure Abbu zaiyi ba domin sarai ya san halin Amina ba zata ta’ba amincewa ba.


Abbu yana tura ma ‘kaninsa kud’in gidan yayi murmushi a ransa yace “na gama da wannan saura next kuma”.


Zuciyarsa ce ta tunasar dashi ‘iyalinka fa?’ Saidai Abbu yayi saurin kawar da wannan tunanin daga ransa, zaiyi dealing da wannan daga baya amma a yanzu zaiyi ‘ko’kari yaga ya mallaki karime kafin wani ya mishi shigar sauri.


Duk wasu ayyukansa dake gabansa ya had’a ya ‘karashesu a cikin kwanaki uku sannan yayi canceling duk wani meeting ya d’aga su zuwa lokacin da zai dawo daga timiya, masu muhimmanci kuma ya matso dasu kusa. Bayan ya tabbatar da ya zama free ya kuma bar komai a kan secretary d’insa da sauran departments ya nufi gida da niyyar fad’a ma Amina tafiya ta kamashi, saidai a rayuwarsa ya tsani ‘karya musamman da girman amma kuma gaskiyar a yanzu zata fi kawo mishi matsala, ta ina zai fara?”


Yana zuwa gida ya tarar da Zee da hammad suna coloring a parlor, da gudu suka nufeshi suna mishi oyoyo bayan sun gaisa yace “ina Mumynku?”


“Tana d’akin Yaya Fatima”. Hammad ya furta yana nuna d’akin tareda komawa kan littafinaa da yake coloring, da murmushi Abbu ya amsa mishi da okay sannan ya nufi d’akinsa. Yana ajiye jakarsa yaji sallamar Aminatu saidai yana kallonta yaji gaba d’aya shirin da yayi a waje na tunkararta ya wargaje