RASHIN SANI…

28

by @hauwaausmanjiddarh

_*RASHIN SANI.......*_





*HAUWA A USMAN*

    _JIDDARH_




'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''



_DIDECATED TO_

*MY AUNTY AYSHA ALIYU GARKUWA*

('''GARKUWAR MARUBUTA''')

~MY UWAR ROOM~




2⃣8⃣




Khulud ba ko takalmi ta k'arasa harabar gidan,

shi kuma dai-dai lokacin ya juyo yana niyyar shiga cikin gidan,

a tsakiyar compound suka had'u,

kallanta yayi kana yace " lafiya?


" Lafiya ta bashi amsa tana hangawa bayansa,

bayan nasa shima ya juya ya kalla kana ya mayar da idansa kanta,

yace " me kike dubawa?


" My Sanah ta bashi amsa,

" oh!, yace yana rik'o hannunta,

da nufin shigar da ita cikin gidan,

k'in binsa tayi ta tsaya cak, tana kallansa a marairaice,

yace " me kuma?


" Ina My Sanah ta tambaye shi,

wata muguwar fad'uwa gabansa yayi,

amma ya dake kamar babu komai yace " kamar ya?


Tace " bada ita na ganku yanzu kuna magana ba?


Murmushi yayi had'i da sungumarta cak,

yayi cikin gidan da ita, cikin sanyin murya tace " please my Sanah!,

murmushi ya kuma yi yace " oh! wannan duk d'okin ganin our Sanah ne?


Zata kuma yin magana yayi saurin had'e bakinsu,

yana cewa muje na gaisa da baby na,

dan nasan idan our Sanah tazo ba'a da lokaci na,

ya fad'a yana tura k'ofar bedroom da k'afarsa,

dole tasa Khulud yin shiru amma badan taso ba,

dan gaba d'aya hankalinta yana kan Sanahrta,

kwantar da ita yayi a kan bed yana cigaba da shan bakinta,

had'i da shafa jikinta, a hankali ya rabata da kayan jikinta,

kana ya kashe arna, Hanash bai wani samu yadda yake so ba,

dan Khulud bata sakar mishi jikinta yadda ya kamata ba,

bata kuma taimaka mishi wajen bashi hakk'in nasa ba,

dan kwata-kwata bata cikin hankali da nutsuwarta,

dama ko ba yanzu ba,

yana fuskantar irin wannan matsalar daga wajen Khulud,

dan kwata-kwata bata da wayewa a wajen sex,

kwanciya takeyi kamar ruwa sai dai shi ya sarrafa ta,

amma even romance Khulud bata iya yi mishi,

farko-farko ya d'auka kunya da rashin sanin, da kuma rashin sabo da abun ne ke damunta,

amma yanzu gashi kusan 3 months da auren su,

amma still bata san komai ba,

gashi shi ba abokanai ba balle ya kaita wajen matan su suyi mata bayani,

kuma shi kunyarta yake ji bai iya yi mata bayani da kansa,

dan gani yake kamar cin fuska da wulak'anci ne,

 shi yadda ake fad'ar ana mugun jin dad'in sex shi bai wani ji,

dan wani lokacin ma sai yayi da gaske yake yin releasing,

tun abun bai damunshi har abun ya fara damunshi sosai,

wani lokacin koda yana cikin buk'ata hak'ura yake yi,

dan bai san shan wahala a banza,

bayan komai ya lafa tsakanin Hanash da Khulud ya jawo ta jikinsa ya rungume ta tsam a k'irjinsa.



Yana shafa kanta, deep down kuma yana sak'e-sak'e a ransa,

yana jin inama zai iya fitowa ya fad'a mata gaskiyar abinda ke ranshi,

sun kai 15 minutes a haka kana ta mik'e ta shiga bathroom,

tayi wankan tsarki ta shirya,

wayarta ta d'auka da nufin kiran number Sanah,

Hanash yayi saurin cewa " my love yunwa nake ji bani abinci naci,

ido ta zaro waje tace " yanzu fa kaci abincin,

yayi kyakkyawan murmushinsa kana yace " bakiga uban aikin danayi yanzu ba?


" Ai dole naji yunwa tunda kin zuk'e abincin dana ci,

bata kuma cewa komai ba saboda kunyar abinda ya fad'a,

ta juya da sauri ta nufi kitchen,

tana fita yayi saurin d'aukar wayarta ya sanya number Sanah a black list,

bata jima da fita ba ta dawo d'auke da tray,

sai da yaci abincin sosai kana ya shiga wanka.


Sai da Sanah ta tsaya a bakin get d'in da Hanash ya hankad'o ta,

taci uban kukanta sosai, kana ta share hawayenta,

ta mik'e ta nufi bakin titi,

tana tafe hawayen bak'in ciki na sake zubo mata,

Allah ya taimake ta tun kafin ta k'arasa bakin titin ta samu mai napep,

da sauri ta tsaida shi ta shiga ta zauna,

sai da ta zauna kana ta fad'a masa inda zai kaita,

sai da ta tsaya a bakin get d'in shiga gidan su,

ta saita kanta kana ta shiga, dan bata san kowa ya fuskanci abinda ke faruwa tsakaninta da Hanash,

bata tsaya shiga part d'in Halan ba tayi shigewarta part d'in Mamu kai tsaye,

a parlor ta iske Mamu tana jera abinci a dinning,

kallo d'aya Mamu tayi mata ta fuskanci da akwai matsala,

da sauri Mamu ta nufe ta tana cewa " ke lafiyarki?


Murmushin k'arfin hali Sanah ta k'ak'aro kana tace " meye Mamu?


Mamu ta kalle ta cike da mamaki tace " ban gane me ba?


" Bayan ga fuskarki nan da idanki sun nuna kinyi kuka,

rolling sexy eyes d'inta tayi kana tace " kuka kuma Mamu?


Mamu tace " ke ban san rainin hankali,

zanci ubanki wallahi, ni kike san yiwa yawo da hankali dan gidan ku?


Sanah ta zumb'uro baki kana tace " ni fa babu komai Mamu,

Mamu tace " wai tsaya ma, ba gidan Khulud kika tafi ba?


Sanah tace " ni kuma?


Ta fad'a tana zaro idanta waje,

" ni bance zani gidan Khulud ba,

Mamu tace " kan uba!, ke ni kike san maidawa mahaukaciya ko me?


" Idan ba gidan Khulud kika ce zaki ba, gidan ubanki kika ce zaki?


Sanah tace " a'a ni test naje nayi,

Mamu tace " oh! ni Allah na, Ubangiji ya kawo mu wannan lokacin,

yanzu Sanah ni zaki yiwa yawo da hankali dan ubanki yanzu kina nufin har kinje BUK,

kinyi test kin dawo ko me kike nufi?


Ta fad'a tana kallan Sanah a k'ufule,

Sanah tace " kai Mamu dan Allah kiyi hak'uri ki kwantar da hankalinki mana,

cikin fad'a Mamu tace " a gidan ubanki zan kwantar da hankalin nawa,

kin fita kin kuma dawo min gida kina kuka,

sannan kina neman raina man hankali,

amma ina zuwa,

ta fad'a tana nufar inda ta ajeye wayarta,

ta d'auka had'i dayin dialing number Khulud,

da sauri Sanah ta k'arasa inda Mamu ke tsaye fuskarta d'auke da tsoro tace " me zakiyi Mamu?


Mamu bata kula ta ba,

ta maida hankalinta ga abinda take yi,

Khulud na zaune kusa da Hanash taji wayarta na ringing,

bai wani damu ba saboda ya san ya saka number Sanah a black list,

da sauri Khulud tayi picking ganin number Mamu,

cikin girmamawa Khulud ta gaida Mamu,

Mamu ta amsa kana tace " Khulud ba gidanki Sanah tazo yanzu ba?


Sanah najin Khulud Mamu ta kira tayi saurin zaro ido,

Khulud tayi shiru ta rasa amsar da zata bayar,

a hankali tace " lafiya Mamu?


Mamu tace " 30 minutes back tayi man sallama tace " ta tafi gidanki,

amma yanzu ta dawo cikin damuwa kuma da gani taci uban kuka sosai,

ido Sanah tayi rolling,

itako Khulud idanta ta zaro tana yiwa Hanash kallan zargi،

kana ta cewa Mamu bani Sanahr,

Mamu tace " kamar ya na baki Sanah?



" Karku had'u kuyi min yawo da hankali,

tambayarki nayi dan haka ki bani amsa,

cikin sanyin murya Khulud tace " eh nan tazo,

Mamu tace " meya faru da har tayi kuka?


Khulud tayi shiru na d'an wani lokaci kana tace " wai cikinta ke ciwo,

Mamu tayi tsaki kana tace " Allah ya shiryeku,

cikin sanyin Khulud tace " Mamu bani ita please,

Mamu tace " ai kina da phone number ta ki kira ta mana,

Khulud zata kuma yin magana Mamu ta kashe wayarta,

bata k'ara bi takansu ba ta cigaba da subgoginta,

cikin sanyin jiki Khulud tabi wayar da kallo na wani d'an lokaci,

kana ta k'urawa Hanash ido tana karantar yanayinsa,

" me!?


Yace, yana kallanta, yayinda gabansa ke fad'uwa,

idanta na kansa tace " me kayiwa My Sanah?


Da sauri ya mik'e zaune kana yace " kamar ya menayi mata?


Idan Khulud na kansa still tana karantarsa tace " please me kayi mata?


" Wani abun tace nayi mata?


Ido ta kafe shi dashi batare data kuma cewa komai ba, shima shirun yayi bai ce komai ba,

 wayarta ta d'auka,

tayi dialing number Sanah amma sai taji not reachable,

bata kawo komai a ranta ba ta aje wayar,

itama Sanah nacan na faman neman layin Khulud amma busy yake nuna mata.



Tunda Sir Moli ya lura matuk'ar ya keb'e da Sanah yana loosing control,

yasa shi yin nesa sosai da ita,

ya gujewa duk wani abu da zai keb'anta shi da ita,

dan shi kansa yana mugun mamakin kansa,

ya rasa meyasa yake shiga wani yanayi idan yana tare da ita,

ya rasa meyasa yake mance kansa idan yana tare da ita,

shi dai yasan a iya tsayin rayuwarsa bai tab'a kusantar zina ba,

ya zauna da turawa, larabawa, indiya da sauran jinsunan duniya,

amma bai tab'a tsintar kansa da irin haka ba,

sai akanta, 

sosai ya dage da yin azumin nafila da istigfari,

saboda neman tsira dan gani yake kamar ya aikata babban laifi.



Yauma bayan sun gama attending lectures,

bata fito ba sai gab da magariba,

ganin yanayin garin na damuna ga kuma dare na neman kawo kai,

yasa Sanah yin sauri sosai, 

tun daga nesa ya hangota,

yayinda dashi ke zaune cikin motarsa k'irar ferrari,

yana driving,

idansa ya lumshe lokacin dayazo zai wuce ta dai-dai ita,

yana san taimaka mata ya d'auke ta,

amma baijin zai iya yin haka,

dan gudu da kaucewa duk abinda zai kai shi ga keb'ewa da ita,

balle har a samu sab'anin da zai iya kawo shigar wani abun a tsakaninsu,

motar Sanah tabi da kallo had'i da tab'a bakinta tace " kai dai ka sani.



Hanash kwance akan k'ayataccen royal bed d'insa,

ya fad'a duniyar tunani,

idan da abunda yafi damunsa yanzu a duniya bai wuce na rashin gamsuwa da jin dad'in sex da bayayi ba,

saboda kwata-kwata baya samun ishashshiyar gamsuwa,

ba wai dad'i ko ruwan ni'ima ne Khulud bata dashi ba,

tana da ni'ima sosai kamar me,

dan ruwan ni'imarta har mamaki yake bashi wani lokacin idan yaga yadda take b'ulb'ulo da ruwa daga k'asanta,


shi abinda ke damunsa

kwata-kwata bata iya sex ba,

bama tasan yadda zata yi sex d'in ba,

ga rashin samun had'in kanta wajen sex,

da rashin taya shi, kwata-kwata bata iya komai ba,

ba kuma tasan komai,

shi kad'ai yake kid'ansa yake rawarsa,

ko romance bata iya ba, gashi bata iya sex styles and irin kukan kissa da nuna irin tana enjoying sosai ba,

sai dai ta kwanta kawai kamar ruwa,

shi zayyi komai ya sauka,

wannan abun yana matuk'ar damunsa,

dan tun abin baya damunsa yanzu har abun yazo ya zame mishi babban matsala,

dan wasu lokutan ma yana bala'in jin haushinta,

dan ji yake kamar ya rufe ta da duka,

ita ko irin shigewa jikin miji, da nanik'ar miji batayi,

ko irin zama akan cinyarsa batayi,

kwata-kwata ba romantic girl bace,

shi kuma gashi so hot romantic,

yana bala'in san irin rayuwa da soyayyar turawa,

yana san koyaushe ya kasance matarsa tana nanik'e dashi,

yana bala'in san mace mai san jiki,

da iya love, & romancing,

sosai yake cikin damuwa, ya rasa ta inda zai b'ullo mata,

ya rasa ta hanyar da zai bi yayi mata bayani,

yana tsaka da tunaninsa ta shigo,

zama tayi a bakin bed d'in fuskarta d'auke da murmushi tace " breakfast is ready Sir,

idanshi na kanta yace " ji babu ko d'an sexy abu balle romantic,

babu even kiss, just breakfast is ready,

ya fad'a cikin ransa,

a fili kuma yayi mata guntun murmushi,

kana ya mik'e ya shiga bathroom batare dayace mata komai ba,

mik'ewa tayi ta fita ta koma parlor,

yana jin fitarta ya tab'e baki had'i da cewa " even wanka da miji bazata iya ba,

dan duk wad'annan abubuwa babu yadda bayyi ya koya mata ba amma tak'i ta d'auka,

sai da yayi wanka ya shirya kana ya fita parlor'n,

a parlor ya same ta zaune, tana ganinshi tayi saurin mik'ewa tana murmushi,

shima murmushin yayi mata kana suka zauna a dinning table,

serving d'inshi farfesun kayan ciki da soyayyar doya da miyar kwai tayi,

sama-sama ya d'an tsakuri abincin ya mik'e,

da sauri ta kalle shi ta kalli abincin tace " wai kana nufin har kayi me?


Murmushi yayi mata yace " Alhamdulillah na k'oshi,

bata kuma yin magana ba ta mik'e rik'e da brief case d'insa,

" ba ko tarairayar miji, ko irin ta saka ni gaba tana yi man shagwab'a tana tarairayata akan dole sai naci abincin babu,

ina cewa nak'o shi shikenan, bayan tasan ba iya abinda na saba ci kenan ba,

ya fad'a cikin ranshi,

har bakin mota Khulud ta raka shi ya shiga kana ta koma cikin gida.



Kullum sai Khulud tayi ta 

faman kiran number Sanah amma not reachable,

haka itama Sanah kullum cikin kiran number Khulud take amma busy,

dukkansu basu kawo komai a ransu,

dan haka suka cigaba da harkokinsu,

haka ma sau uku Sanah na zuwa gidan Khulud mai gadi yana hanata shiga,

daga k'arshe ma rok'arta yayi akan dan Allah karta k'ara zuwa saboda mai gidan yace zayyi asarar aikinsa,

dole Sanah ta hak'ura ta daina zuwa gidan Khulud,

haka duk sanda Hanash zai kai Khulud gida,

sai ya tabbatar da Sanah bata gidan,

sannan zai kaita, kafin ta dawo kuma sun bar gida,

haka suka cigaba da rayuwa lokaci na tafiya har Khulud tayi wata hud'u da aure,

amma ko sau d'aya basu tab'a had'uwa da Sanah ba,

tun bayan aurenta,

su dukkansu basu tab'a tsammanin zasuyi kwana d'aya a rayuwarsu batare da sunga juna ba.



Su Khulud na zaune a parlor'n Mimmee ita dasu Zohal,

Mimmee ma na zaune gefensu,

Zohal ta kalli agogo tace " kinga har 3:30pm na rana tayi,

muyi sauri mu fita kafin Yaya ya dawo,

yanzu daya dawo sai yace yamma tayi babu inda zamu mu bari sai gobe,

Khulud tace " gaskiya kam muyi sauri dan nima ina san zuwa saloon d'in nan wallahi,

Mimmee tace " ta ku tashi kuyi sauri ku shirya mana, 

kun tsaya kuna surutu, Khulud tace " mu ai mun shirya Wajnah kawai muke jira,

Mimmee tace " ina Wajnah nan?


Zohal tace " tana bedroom tana ta faman k'ak'ale-k'ak'ale kema ai kinsan halin shirinta,

Mimmee tace " ikon Allah ta kuje ku kirata mana,

kafin suyi magana Wajnah ta fito tana cewa " gani ma na fito ai,

babu wanda yayi magana duk suka mik'e Mimmee ta bisu da kallo d'aya bayan d'aya,

suna k'ok'arin fita Jaddah ta shigo,

tana binsu da kallo, kana tace " ina zuwa?


"Saloon cewar Zohal,

kallan Khulud Jaddah tayi kana tace " wajenki fa nazo,

Mimmee ta kalli Jaddah cikin mamaki batare da tace komai ba,

Khulud ta durk'usa har k'asa tace " ina yini?


Jaddah bata amsa gaisuwarta ba,

tace " ke wai har yanzu ba wani labari ne?


Khulud ta kalleta cikin rashin fahimta,

tace " me Jaddah!?


Jaddah tace " watan ku hud'u kenan da aure amma har yanzu banji kin fara 'yan amaye-amaye,

da rashin lafiyar laulayi ba,

ko har yanzu babu komai,

ni fa kin san babu abinda nafi so sama da ganin yaran Hanash ato kima dage,

Khulud durk'ushe agaban Jaddah kanta na k'asa,

daga Mimmee har su Wajnah babu wanda yace k'ala,

dan sanin halin Jaddah sarai,

Papu dake sakkowa daga samansa yace " Jaddah ba sai Allah ya kawo ba tukunna,

ai basu isa su bawa kansu ba, 

sai idan Allah yaga dama ya basu tukunna,

kallan Papu tayi cike da mamaki dan hakan bata tab'a faruwa ba,

tunda take dashi bai tab'a mayar mata da magana ba sai yau akan Khulud,

Khulud ta kalla kana ta juya zata fita,

harta kai bakin k'ofar fita ta kuma juyowa tace " ni dai na fad'a miki,

kana tasa kai tayi ficewarta,

Papu ya k'arasa shigowa cikin parlor'n,

a hankali Khulud ta juya tana gaida Papu,

cike da fara'a ya amsa kana yace " kiyi hak'uri kinji?


Murmushi tayi tace " lah bakomai Papu,

yayi murmushi shima,

kana suka fita.



Washe gari Sanah bata shiga makaranta ba sai around 10:30am na safe,

saboda bata da lafiya zazzab'i da ciwon kai ke damunta sosai,

a hankali take tafiya dan ji take kamar zata fad'i saboda jirin dake d'ibarta,

in banda suna da test da Sir Moli babu abinda zai kawo ta makarantar,

tana shiga class Rose ta nufo ta da sauri ganin yanayin datake ciki,

dan tun da suka samu d'an sab'anin nan suke shiri,

Rose tace " meke damunki,

murmushi Sanah tayi kana tace fever & headache,

cike da tausaywa Rose tace " ayya sorry,

gashi har anyi test baki nan,

da sauri Sanah ta d'ago kanta tace " Sir Aryan har yayi test d'in!!?


Rose tace " yes! tun around 9:30am na safe,

kai Sanah ta dafe had'i da cewa " ya salam!

shiru tayi na wani lokaci kana ta kalli Rose tace " please ki raka ni office d'insa,

Rose ta zaro ido waje cike da tsoro tace " am sorry sister babu abinda zaki tambaye ni na kasa yi maki,

amma ban iya rakaki office d'insa,

shiru Sanah ta kuma yi,

batare data kuma cewa Rose komai ba,

ta nufi office d'insa,

sallama tayi ya bata izinin shigo,

a hankali ta tura k'ofar ta shiga,

yana kishingid'e akan sofa,

idanuwansa lumshe,

ta durk'usa a gabansa,

saboda ji take kamar zata fad'i,

cikin muryar marasa lafiya tace " Sir!,

bai ko motsa ba balle ya bud'e idansa ko yayi mata magana,

muryarta na rawa ta kuma cewa " Sir!

a dak'ile yace " fad'i,

"Sir banyi test ba,

" sai akayi yaya?


Ya fad'a bai motsa daga inda yake ba,

" bani da lafiya ne, ta fad'a muryarta ba creaking,

" me zanyi miki to?


Ya kuma fad'a bai motsa ba,

"dan Allah kayi man tawa!

ta fad'a tana kallanshi,

shiru yayi baice komai ba,

Khulud na kwance a parlor Hanash na gefenta zaune,

tayi saurin mik'ewa ta,

a hankali Hanash ya d'ago kansa ya kalleta,

yace " lafiya naga kin zabura!?


"Ki rink'a bi a hankali saboda unborn d'ina,

dariya tayi tace " kai komai Baby,

shima dariyar yayi kana yace " shine babban buri na a duniya,

wallahi komai za'a bani bai kai na samu Baby ba,

bani da wani sauran buri ko muradi daya wuce na ganni da d'a ko 'ya nawa na kaina,

idan naga Baby na bani da sauran buk'ata a duniya,

murmushi tayi had'i da cewa " Allah ya bamu basu albarka,

ta fad'a tana nufar bedroom d'inta,

wayarta ta d'auko ta dawo parlor ta zauna had'i da kunna data ta shiga WhatsApp,

ta shiga sunan Sanah jikinta na rawa dan basirar yi mata voice note bai tab'a zo mata ba sai yau,

muryarta na rawa tace " My Sanah kina kusa please?


"Idan kina kusa kiyi man magana,

Sanah na durk'ushe gaban Sir Moli taji notification na WhatsApp,

kamar bazata duba ba, sai kuma ta duba,

ganin Khulud ce yasa ta saurin kunnawa a speaker,

Sanah tayi murmushi kana tace " ina kusa my Khulud,

Khulud na rik'e da waya tana jiran amsa,

taji k'arar shigowar sak'o, da sauri ta duba,

kuka Khulud ta saka had'i cewa " me nayi miki My Sanah?


Sanah tayi playing, a hankali ta lumshe idanta jin Khulud tana kuka,

kana tace " meye my Ulud?


Khulud tace " au meye ko?


Sanah tace " eh mana,

 cikin kuka Khulud tace " haba my Sanah yanzu fa na shiga 5 months da aure amma baki tab'a zuwa inda nake ba,

tunda nayi aure bamu sake had'uwa ba,

wallahi ko a mafarki aka fad'a min zamuyi 5 months bamu had'u ba ban yarda,

matuk'ar muna raye a duniya,

musamman ma a cikin gari d'aya,

dan Allah idan wani laifin nayi miki ki fito ki sanar dani sai na gyara,

na kuma baki hak'uri,

idan kuma akwai abinda ke faruwa please ki sanar da ni,

dan Allah hukuncin nan yayi man tsauri,

Sanah na danne kukanta tace " kiyi hak'uri kinji my ulud,

komai na duniya muk'addari ne kuma yana da iyaka,

Khulud tace " dan Allah kizo yau please,

Sanah ta lumshe idonta hawaye na zuba,

tace " kiyi hak'uri my Ulud ban iya zuwa dan bani da lafiya,

Khulud ta tura mata amsa cikin tashin hanakali " subhanallah meke damunki?


Sanah tace" fever & headache,

Khulud tace " kina ina yanzu?


Sanah tace " ina makaranta,

Khulud tace " yaushe zaki dawo gida?


" Sai dare, Sanah ta fad'a while hawayen bai bar fita ba,

Khulud tace " to dan Allah gobe karki je ko'ina zanzo,

Sanah tace " tom zan jira ki in sha Allah,

sai da sukayi hira kana sukayi sallama,

Hanash na jinsu, suna gama wayar ya jawo ta jikinsa ya rungume batare dayace komai ba,

suna gama chart d'in Sanah ta saka kukan da take dannewa,

Sir Moli yana nan yadda yake baiko matsa ba, idanuwanshi lumshe,

sai da taci kukanta ta k'oshi kana ta mik'e zata fita,

har takai bakin k'ofar fita,

yace " meke faruwa tsaninku ku ukun?


Cak ta tsaya had'i da juyowa a hankali,

red eyes d'inta ta d'aga ta kalle shi,

taga yana nan yadda yake,

batayi niyyar b'oye masa komai ba,

dan haka ta fad'a masa tun daga zuwanta na farko gidan har zuwanta na k'arshe bata b'oye masa komai ba,

idansa rufe yace " yanzu kina san zuwa ganin Khulud d'in?


Ido ta k'ura masa batare datace komai ba,

a hankali ya bud'e idansa had'i da mik'ewa zaune,

yana kallanta yace " tambayarki nake,

cikin sanyin jiki ta d'aga masa kai,

yace " amma kin san ban san nodding kai ko?


Cikin sanyin murya tace " sorry،

ya kuma cewa " kina san zuwa ganin Khulud?


"Eh! tace tana kallanshi,

a hankali ya mik'e batare daya kuma kallanta ba,

ya zura talmi da hularsa,

kana yace " muje,

da sauri ta kalle shi tace " ina?


" Ban sani ba, yace yana fita daga office d'in,

bayansa tabi a hankali kasancewar jikinta babu kwari,

office d'in ya rufe kana yayi gaba batare daya kalle ta ba،

binsa tayi a baya har suka isa motarsa,

bayyi mata magana ba ya bud'e ya shiga,

tsaye tayi bakin motar tana kallanshi,

harara ya watsa mata,

ganin hararar dayiyi mata yasa ta zumb'urar baki kana ta bud'e motar ta shiga,

Sir Moli bai tsaya ko'ina ba sai a unguwar su Khulud,

dai-dai inda yaga Sanah da daddare,

batare daya kalle ta ba yace " ina ne gidan?


Nuna masa ta shiga yi har suka k'arasa bakin get,

sosai gaban Sanah ke muguwar fad'uwa saboda bata san abinda zai jawowa Khulud matsala a zamantakewar aurenta,

dandai babu yadda zatayi da Sir Moli ne,

yasa ta biyo shi, musamman ma da irin zargin da Hanash yake yi musu,

horn yayi mai gadin ya lek'o, kasancewar motar tine tac ce yasa bai ga Sanah ba,

kuma daya ga motar babbar motace d'auke da private number yasa shi,

tsayawa yana tunani dan shi ba'a sanar dashi akwai bak'i ba,

ganin haka yasa Sir Moli zuge glass d'in motar a hankali,

ya lek'o da kansa yace " bud'e,

ya fad'a a tak'aice,

ba musu mai gadin ya hangame get d'in,

Sir Moli ya danna motarsa cikin gidan kanshi tsaye,

lura da yadda Sanah take yasa shi cewa " fita،

fuska ta kwab'e kamar zatayi kuka tace " please mu koma,

bai kalle ta ba, yace " nace ki fita ko!?


Yayi maganar a d'an hasale,

a hankali Sanah ta kwab'e fuska had'i da cewa " to dan Allah karka tafi ka jira ni,

bai amsa bata ba, ya kawar da kanshi gefe,

a hankali Sanah ta bud'e motar ta fito,

mai gadi na ganin Sanah, ya nufo ta da sauri,

jikinsa na kerrma, yace " Hajiya dan girman Allah ki taimaka min karki shiga,

Yallab'ai yana nan, kuma a gabanki yayi min gargad'i,

Sanah zatayi magana Sir Moli ya bud'e motar ya fito,

ya jingina da jikin motar had'i da hard'e hannayensa a k'irjinsa,

yace " gargad'in me yayi maka?


Muryar mai gadin na rawa yace " Yallab'ai ne yace muddin na kuma barinta ta shiga cikin gidan a bakin aiki na,

"Ok Sir Moli yace kana ya mayar da kallansa ga Sanah yace " shiga,

fuska ta kwab'e kamar zatayi kuka tace " please!

mai gadin yayi saurin cewa " dan Allah ku taimaka min،

ina da yara k'anana,

da mata, sannan ga iyaye na,

ga yaran d'an uwana daya mutu,

 duk a k'ark'ashi na suke,

ni kuma da wannan aikin kad'ai na dogara,

Sir Moli yace " idan ya koreka kazo zan baka aiki mai kyau,

ya fad'a batare daya kalli inda mai gadin yake ba,

mai gadin yace " ni dai dan Al.........,

hannu Sir Moli ya d'aga masa,

yace " please Baba kayi shiru nace idan ya kure ka zan baka aiki,

kuma dama matsalarka bata aikin bace,

idan kuma aikin ne baka so zan baka jari mai kyau,

shiru mai gadin yayi saboda kwarjinin da Sir Moli yayi masa,

karaf idan Sir Moli ya sauka akan Hanash dake nufar d'aya daga cikin motocin dake jere a harabar gidan,

da alama bai lura da su ba,

daga Sanah har mai gadin babu wanda ya lura dashi,

Sir Moli ya kalle ta yace " karna sake miki magana,

da sauri ta nufi hanyar shiga part d'in,

Sir Moli ya tsaya jikin motarsa had'i da hard'e hannuwansa a k'irjinsa,

ya zubawa Hanash ido,

yana nazarinsa,

shi dai a fuska baiga wani mugun hali ko alamar munana d'abi'u a tattare dashi ba,

sai nutsuwa da kalama had'i da suffar nagartattun mutane,

 daya gani tattare da Hanash d'in,

abinda da marar lafiya Sanah na fara takawa tayi taku na uku,

k'afarta ta gurd'e kasancewar takalmin k'afarta mai tudu ne,

 jiri ya d'ebeta tayi baya luuuuuu zata fad'i,

cikin matsanancin zafin nama Sir Moli yayi saurin tare ta,

ta fad'a jikinsa,

a tsorace Sanah ta saki 'yar k'ara,

saboda ta gama sadak'arwa ta fad'i,

k'arar da Sanah tayi ce tajawo hankalin Hanash kansu,

 ya sauke idansa a kansu dai-dai lokacin da Sanah ta fad'a jikin Sir Moli.



A hasale Hanash ya juyo yana kallansu cikin matsanancin b'akin rai yace " hey! nan ba hotel ko club bane,

ba kuma gidan karuwai da 'yan iska bane,

idan zakuyi iskancinku kuje can kuyi,

tsabar rainin hankali kuzo man har cikin gidana kuna iskancin da kuka sabo yi, 

ko an gaya maku nan gidan 'yan iska ne?


Da sauri Sanah ta fara k'oka'rin kwace jikinta daga na Sir Moli,

amma Sir Moli ya k'ara manneta da jikinsa,

idansa akan Hanash yana kallan cikin kwayar idansa,

yana karantar yanayinsa,

had'i da san fassara abinda yake hangowa cikin kwayar idan nasa,

ran Hanash ya kuma mugun b'aci cikin mugun takaici yace " get out from my house,

kwaratan banza, 'yan iska fasik'ai kawai,

guntun murmushi Sir Moli yayi yana k'ara shigewa jikin Sanah,

had'i da shinshinar wuyanta yana goga hancinsa a kumatunta,

ita ko Sanah sai k'ok'arin kwace kanta take yi,

amma ta kasa sai nuk'u-nuk'u take, 

tana k'ifk'ifta idanuwa,

ido Hanash ya runtse cike da tsantsar bak'in cikin ganin abinda Sir Moli yake da mace kuma har cikin gidansa,

cikin b'acin rai Hanash yace " I said get out from my house,

nan ba hotel bane, gidan ma'aurata ne,

Sir Moli yayi dariya kana ya saki Sanah ya maida kallansa ga Hanash yacewa Sanah " jeki shiga,

tsayawa Sanah tayi bata ko iya d'aga k'afarta ba,

idan Sir Moli nakan Hanash ya had'e rai sosai,

yadda kasan bai tab'a yin dariya ba yace " nace ki shige ko,

Hanash tsaiwarsa ya gyara yana kallan Sanah,

yace " tazo ta wucen inta isa ita tacacciyar mara kunya ce,

cikin kuka Sanah ta kalli Sir Moli tace " please mu koma na hak'ura da ganin Khulud d'in,

gigitacciyar tsawa Sir Moli ya daka mata cikin b'acin rai yace " nace ki shiga ko!?


Jikin Sanah na kerrrrma saboda tsawar da Sir Moli ya daka mata

bawai saboda tsoran Hanash ba,

 ta nufi hanyar shiga gidan,

Khulud dake zaune a parlor ta mik'e ta fito da sauri kasancewar gigitacciyar tsawar dataji Sir Moli ya daka,

dama tun d'azu take jiyo maganganu k'asa-k'asa,

Khulud na fitowa harabar gidan dai-dai lokacin Sanah ta rab'a ta gefen Hanash zata wuce,

a k'ufule Hanash ya maka mata kyawawan marika gudu biyu a jere,

wad'anda sukata zubewa k'asa ba shiri,

karaf akan idan Khulud........

cikin tsananin b'acin rai da zafin zuciya Sir Moli ya.........




Ya azumi da ibada?


Ubangiji ya amshi ibadun mu,

Allah yayi mana rahama da rahamarsa,

yaji k'anmu da jin k'ansa,

Allah yasa muna daga cikin wad'anda za'a yafewa a wannan watan mai albarka.






MOMYN ZARAH