35
_*RASHIN SANI.......*_
*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_
'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''
3⃣5⃣
Tamkar rugugin tsawar ruwan sama yaji kalmar ta sauka cikin dodon kunnenshi,
ta daki zuciyarshi da kwakwalwarshi,
komai dake cikin duniyar tsayar mishi yayi cak,
kwakwalwarshi tayi hooking na d'an lokaci,
shiru yayi yana jin abin kamar a mafarki,
tunanin abinda ya faru ya fara yi,
had'i da k'ok'arin san tuna abinda ya farun,
cikin kid'ima da firgici Sir Moli ya mik'e tsaye,
had'i da cewa " say it again!,
shiru yaji tayi bata yi magana ba, hannunshi na kerrrma,
while duk ilahirin jikinshi na tsuma ya cire wayar daga kunnenshi ya kalli screen d'in wayar,
yaga batayi dropping ba, da sauri ya mayar da wayar kunnenshi,
jikinshi na rawa yace " please say it again,
I want hear it in millions time's from you,
kamar mahaukaci ya cire wayar daga kunnenshi yana dukan screen d'in yana cewa " say it again please!,
ki k'ara fad'a say you love me dan Allah,
amma ina ita bama tasan ta fad'i na farkon ba balle ta kuma fad'a a karo na biyu,
kanshi ya rik'e da hannu d'aya ,
d'ayan hannun kuma ya cusa cikin gashin kanshi,
bakin shi yak'i rufawa sai murmushi yake yana cewa " Alhamdulillah! ya Rabbi thank you,
nagode ma Allah finally yau Sanah ta furta man abinda na d'auki tsayin lokaci,
shekara da shekaru ina jira,
dariya ya saka had'i da fad'awa kan bed,
" wai anya kuwa ba mafarki nake yi ba?
D'an marin kanshi yayi had'i da cewa " tashi Aryan,
pillow ya rungume tsam yana dariya yace " ba mafarki nake yi ba it was real!,
am not deeming, thank God,
haka yayi ta sambatu yana juye-juye yana jiran gari ya waye,
dan ya nunawa Allah godiyarshi,
ya kuma nunawa mutane da duniya tsantsar farin cikin da yake ciki,
kwana yayi bai runtsa ba yadda yaga rana haka yaga dare,
sai da aka kira sallar asuba ya shiga bathroom yayi alwala ya fita masallaci.
Tun daga masallacin ya fara rabon bandir na 100k,
ranar duk wanda yaje ya samu sai da ya bawa kowa,
bayan ya dawo haka yayi ta bin ma'aikatan gidan yana yi musu b'arin kud'i,
duk da gaba d'aya ma'aikatan gidan they're soldiers,
cikin farin ciki ya koma bedroom d'inshi ya zube saman bed,
idanshi na kallan ceiling kyakkyawar fuskarshi d'auke da murmushi,
I'm done......!
"Alhamdulillah Allah abin godiya,
juyawa yayi ya gyara kwanciyarshi,
" Sanah ta zama Mrs Aryan Rayyan Moli,
" masha Allah nice name and match name,
idanshi ya lumshi yana hango irin kwawawan yaran da zasu haifa,
yana cikin wannan hali bacci yayi awon gaba dashi,
kasancewar bai samu bacci da dare ba,
bai farka ba sai 11:00am a hankali ya bud'e idanshi ya kalli agogon bango,
kanshi ya dafe da hannunshi yana mik'ewa zaune,
yakai 5 minutes a haka kana ya mik'e ya shiga bathroom,
shower ya sakarwa kanshi, runwa ya dad'e yana sauka jikinshi,
kana yayi wanka ya fito direct wajen wayarshi ya nufa,
ya d'auka yayi mata sending text,
_kin sanya ni cikin farin cikin daban tab'a tsintar kai na ciki ba I love you MRS ARYAN MOLI_ ,
wayar ya jefa saman bed kana ya shirya cikin d'anyan material na maza,
white color ya saka takalmi da hula & agogo silver color,
yayi masifar kyau tamkar wata daren sha hud'u,
fuskarshi cike da annuri ya nufi part d'in Nailah,
gaba d'aya ya iske su saman dinning suna breakfast,
fuska ya gwab'e cikin shagwab'a yace " shine ko a taso ni!,
hannu Hilwa ya mik'e mishi yana dariya,
yace " you look so handsome and classic my son,
ina zuwa haka?
Fuskarshi d'auke da murmushi an sosa mishi inda yake yi mishi k'aik'ayi yace " finally Hilwa she said it,
cikin fara'a Nailah tace " what! ?
" She said she love me!
dariya duk sukayi kana Hilwa yace " I she must said it dan yaro na ba banzan namiji bane,
irinsu dubban nan mata suke nema ido rufe,
Haidar yace " kai dai Hilwa banda cika baki ta dawo tace ta fasa,
kaga b'arin hawaye da ragonta,
matar Haidar tace " ai ko yanzu data amsa dai taja shi k'asa ta nuna mishi ita mai tsada da aji ce,
tunda har kuka mutum yayi wiwi,
cikin shagwab'a yace " Hilwa......!
yana kallan Haidar da matarshi,
Hilwa yace " kai rabu dasu kaji kai ma ka kusa kawo mai shigar maka,
murmushi yayi yace " wallahi kam dan akwaita da tsiwa,
Haidar yace " ba wani ka fito kace bata da kunya mafad'aciya ce,
ka tsaya kana yiwa haram kwaskwarima,
murmushi yayi yana kai coffee bakinshi,
yace " today is happy day in my life,
dan haka ban bari ka b'ata man ita,
idan ma so kake ka tsoka ne ni ko ka tun zura ni,
Nailah tace " yauwa my good boy,
yi breakfast d'inka ka kyale su kaji,
" yauwa my happiness!,
yana gama breakfast d'in gidan marayu ya nufa yakai musu taimako mai yawa,
yaran sukayi tayi misha addu'a suna yi mishi godiya haka ma manyan, kana yayi government hospital nan ma yaje yayi musu b'arin kud'i,
sosai yayi ta kai taimako guraran da suka dace suka kuma cancanci taimakon,
ko a hanya yaga almajiri da nakasashshe sai yayi parking yayi mishi kyautar dashi da bara har abada,
sai da ya gama tsaf kana yayi hanyar gida,
dan shi ba mutum bane mai yawo,
dan ko abokai bai da su.
Bata tashi ba sai wajen 10:20am na safe,
da sauri ta mik'e ta fad'a bathroom tayi wanka da sauri ta fito ta shirya,
cikin riga da normal zani na lace,
ta d'anyi heavy make up, wayarta ta d'auka danta tabbatar ya kirata ko ya turo mata text,
sororo tayi a tsaye bayan ta gama karant text d'in,
cike da mamaki tace " menayi masa?
" Allah dai yasa ba wani abun nayi kona fad'a cikin bacci batare dana sani ba,
cikin 'yar fad'uwar gaba tayi dialing number shi,
sai kuma ta fasa ta zura wayar cikin hand bag d'inta tayi parlor,
a parlor ta iske Mamu zaune tana kallo,
" ina kwana?
" Lafiya Alhamdulillah ina zaki na ganki da jaka?
" Kai Mamu badai har kin manta ba?
" Na manta, sai kin tuna min,
" gidan Khulud mana, jiya fa na fad'a maki har kika ce kina sak'on da zaki ban na kai mata,
"Oh! na shafa'a ne,
har kin shirya sai tafiya yanzu?
" Eh! fitowar nan ma danayi tafiyar zanyi,
Mamu tace " aiko na manta da zakije gidan Khulud yau har tarko abinci mai wuya,
" uhnnnn ki kira Juju ko wad'an can tsofaffin su tayaki mana,
" wad'anne tsufi?
" Ga su can suna zaune meye amfanin su, in ba su rink'a tayaku aikin ba,
ku rink'a danna musu aiki suna yi maku ke da Juju,
kuma kinga suna da yawa har su hud'u fa,
hannu Mamu ta tafa had'i da zaro ido tace " uwaki Sanah yanzu iyayen namu ne tsofi?
Baki ta turo tace " to basu tsufan ba?
" Dak'uwa Mamu tayi mata tace " zanci gidanku wallahi Sanah idan baki fita daga ido na,
kin kiyayar mana iyaye ba,
" kai Mamu danna ce masu tsofaffi kike fad'a?
" Wallahi idan kika b'ata man rai babu inda zaki,
cikin sigar lallashi tace " haba Mamu kakanni na ne fa ai munfi kusa yanzu da zasu ji ni zasu shigarwa suce ina ruwanki,
" idan zaki musu kiyi musu can idan babu idon mu,
" tom naji na daina, ta fad'a dan kar a hana ta fita,
mik'ewa Mamu tayi ta nufi bedroom d'inta tana mita,
magungunan mata ta d'auko ta bawa Sanah,
tace " ki kai mata kice maganin basir da shawara ne tasha da fresh milk ko peak milk,
dariyar dake shirin kufce mata ta danne,
jin Mamu ta mayar da ita yarinyar goye,
ko ta manta a jami'a take ne oho?
Kuma ko ba jami'a ai yanzu akwai social media,
amsa tayi while tana danne dariyar tace " aiko akwai peak milk bari na d'auko ni ma nasha dan basir da shawara na damuna,
cikin dakewa Mamu tace " a'a wannan nata ne dan ita tayi magana,
ita kad'ai na amsowa ke miyasa da can bakiyi magana an amso miki ba,
" ai naga magungunan na da yawa zasu isha nima nasha tunda ba wani da yawa zan sha ba,
" a'a karki sha wannan ki kai mata,
idan kin dawo ina da saura sai na baki cikin nawa,
" ok badamuwa nasha a can idan naje gidan nasan ai bazata hana ni ba,
d'aure fuska Mamu tayi tace " wai ni sa'arki ce Sanah ko kuma wasa nake dake?
" Da ina magana kina yi min gardama,
" yi hak'uri my sweet Mom bazan sha ba idan na dawo kya bani nakin,
nakin ma sai ya fi man dad'i,
" ato ya dai fi maki, maza tashi ki tafi, a dawo lafiya Allah ya tsare,
" Amin ya Allah my sweet......!
wayarta dake cikin jaka ta soma ringing,
da sauri ta zuge hand bag d'in ta d'ako wayar,
bata san sanda ta saki murmushi ba,
ganin shine, jakarta da mayafinta ta bari nan tayi bedroom d'inta da gudu tana dariya,
saboda yadda Mamu ta kafe ta da ido,
sai da ta saita kanta kana tayi picking,
bakinta d'auke da sallama,
ido ya lumshe had'i da amsa sallamarta yana kishingid'a kan sofa,
" ina wuni?
tace tana kwanciya rigingine saman bed,
Alhamdulillah dear, ya kike?
" Lafiya lau, kai fa?
Idanshi ya lumshi yana sauke ajiyar zuciya,
yace " ni yau ai ina cikin matsanancin farin ciki da annushuwa,
yau komai mutum zayyi man bai tab'a man rai,
" masha Allah meya sanya ka cikin farin ciki haka?
" You said it!
Ido ta zaro had'i da cewa " me!?
" You love me,
" what! ni d'in?
"Eh ke da kanki da bakinki,
kuma nasan koda kin ce a'a ba haka bane,
nasan kin fad'a ne kawai amma ba gaskiya bane,
saboda duk abinda mutum ya fad'a cikin bacci da maye gaskiya ne,
cikin shagwab'a ta gyara kwanciyarta,
tana cewa " ni dai Allah a'a bance ba,
kawai dai wayo kake san yi man,
yama za'ayi nace maka I love you,
" wow! kinji yadda kalmar I love you d'in ta fito daga bakinki?
Idonta ta lumshe had'i da k'ara juyawa tace " ko!?
" Yes! Sweetheart kuma ko da baki fad'a jiya ba yanzu gashi nan kin fad'a ai,
" me d'in?
" I love you d'in mana,
murmushi tayi tace " hmmm wayo ko?
" No ba wayo zanyi maki ba, seriously kin fad'a,
kuma naji dad'i sosai dan yanzu nasan ba san maso wani nake yi ba,
" hmmmm karka sa nayi yamma bari idan na k'arasa zan kira ka,
" ina zaki kuma!?
" Lah badai har ka manta ba?
" Me!?
" Ba na ce maka yau zani gidan my ulud ba?
Kanshi ya dafe had'i da cewa " ops...! Allah na manta jin dad'i yasa ni mancewa,
please ki kular man da kanki kinji?
" In sha Allah fiye ma da yadda zaka kula da ni,
ta fad'a ciki tsokana,
" wad'in never wallahi Sanah kin san yadda nake jin ki cikin rai na kuwa?
"Hmmmm tace,
yace " Wallahi idan kika d'auke Hilwa & Nainah nafi sanki fiye da kowa cikin duniyar nan,
zan iya bada rai na da rayuwata da duk abinda na mallaka akanki,
ya k'arasa maganar cikin sanyi,
" nagode sosai ,karka damu kaji my...!
shiru tayi cike da jin kunyar abinda tayi niyyar fad'a,
" no dan Allah said it karki fasa fad'a man abinda kika yi niyyar,
"hmmm ni dai zan tafi kar yamma tayi idan gamma tayi Mamu bata bari na fita,
murmushi yayi yace " ok badamuwa my happiness sai kin dawo,
please close your sexy eyes ban san ki kalli kowanne namiji,
murmushi tayi mai sauti tace " ina da kamar ka wanne irin namiji kuma zan kalla?
Saboda tsabar rawar jikin da yake yi sai da wayar ta sub'uce daga hannunshi,
da sauri ya d'auki wayar daga k'asa ya mayar kunnenshi,
had'i da lumshe idanshi yace " thank you sweetheart for make my heart happy,
I love you, ya fad'a cikin sanyin murya,
iska ta d'an busar daga hancinta kana tace " bakomai ai yiwa kai ne, bye!
da sauri ya bud'e idanshi yace " no no no please kice man I love you too,
cikin sanyin murya tace " ban iyawa,
" ok, rufe idanki, a hankali ta rufe idan kamar yadda ya umarce ta,
" ki sauke ajiyar zuciya yanzu,
ba musu tayi,
yace " ki bud'e zuciyar ki,
cikin sanyin murya tace " uhnnn,
yace " ki saurari bugun zuciyarki,
d'an shiru tayi tana sauraron bugun zuciyarta ta,
yace " now say it,
shiru tayi bata bashi amsa ba,
yace " I love you so much my sweet,
kai tsaye cikin sanyin murya tace mishi " I love you too my eyes shinning,
ta fad'a tana a yadda take batare data bud'e idan ba,
dukkansu sun kai 1 minutes shiru babu wanda yace " k'ala,
kana ya sauke nannauyar ajiyar zuciya thank you heartbeat,
dan Allah karki tab'a juya man baya a kowanne irin hali,
" karka damu Sanah taka ce har abada,
tana fad'ar haka ta kashe wayar,
ta kai 5 minutes rik'e da wayar a hannunta idanta rufe tana sauraron bugun zuciyarta,
tana jin tamkar ta tsaga zuciyar ta ciro ta,
a hankali ta bud'e idonta had'i da cewa " I love you!, I love you so much,
cikin nutsuwa ta fito parlor, ta tarar da Mamu nan yadda ta barta,
sallama ta k'ara yi mata kana ta fita,
driver yana hangota ya taso cikin rawar jiki,
" manyan gobe ina zuwa! gidan Khulud ta bashi amsa fuskarta d'auke da murmushi,
" to to muje ko...........
" a'a yi zamanka Baba driver zan kai ta,
Aarib ya fad'a yana kallanta cikin matsananciyar soyayyarta dake azabtar da rayuwarshi,
murmushi tayi mishi tace " kana ciki dama?
"Eh man yau ban fita ko'ina ba,
ya fad'a yana bud'e mata k'ofar,
zama tayi tana cewa meyasa Yaya?
Zama yayi had'i da yiwa motar key yaja suka fita،
kana yace " tunaninki ne yake hana ni sukuni,
ya fad'a yana kallanta,
rassssss! gabanta yayi muguwar fad'uwa,
amma sai ta dake ta k'ak'aro murmushin k'arfin hali tace " kamar yaya ban gane ba?
Murmushi yayi yana kallanta,
fuskarta ta d'an tsuke had'i da kawar da kanta,
babu wanda ya kuma cewa " komai har suka isa gidan Khulud,
bata tsaya yi mishi magana ba,
ta bud'e motar zata fita had'i da cewa " nagod.......!
bata k'arasa ba taji hannunshi saman nata,
a hankali ta kalle shi kana ta kalli hannun,
da sauri ya janye hannunshi ya bud'e baki yana k'ok'arin yi mata magana,
tayi ficewarta batare data tsaya ta saurari abinda zaice mata ba,
murmushi yayi yabi bayanta da kallo harta shige cikin gidan,
kanshi ya girgiza had'i da cewa " I love you!......!!,
Khulud na kwance parlor saman 3 setter taji sallamarta,
cikin rawa da kerrrrmar jiki ta mik'e har tana k'ok'arin fad'uwa ta nufi k'ofa,
jikinta na tsuma ta bud'e k'ofar ganin Sanah yasata tsayawa cak,
ido ta zuba mata na d'an lokaci kana ta fad'a jikinta had'i da fashewa da kuka,
" meye kuma na kukan?
" Allah ko kiyi shiru kona juya,
d'an dukan Sanah Khulud tayi tana cigaba da kuka tace " ba sai ki koman ba,
cikin tsokana Sanah tace " to tana k'ok'arin juyawa,
dariya Khulud tayi fuskarta d'auke da hawaye,
tace " hali dai yana nan,
cikin dariya tace " to ina zashi hali ai zanin dutse ne,
ta fad'a suna shiga cikin gidan,
saboda tsabar farin cikin ganin Sanah Khulud rud'ewa tayi ta rasa me ma zatayi,
mema zata bata, ina zata kaita,
duk ilahirin jikinta kerrrma yake,
kallanta Sanah tayi tana dariya tace " oh! ikon Allah wannan duk rawar jikin ganin Sanah ne!?
Khulud bata amsa ba ta kalli gabas tayiwa Allah sujjada,
kana ta d'ago tana cewa " Alhamdulilla,
yau dai Allah ya amshi addu'a ta ya had'a ni da Sanah ta,
ita kam ido kawai ta zuba mata tana kallanta sai sakin murmushi take yi,
Khulud tace " my Sanah me zaki ci na shiga kitchen na dafa miki yanzu?
" Kai daga zuwa na ko hira bamu yi ba sai maganar ci,
Khulud tace " eh ai ban san na barki da yunwa ne,
hannunta Sanah ta kamo ta zaunar da ita kusa da ita,
tace " zauna muyi hira kafin mu shiga kitchen d'in,
hira suka shigayi sosai sai labarai suke bawa juna,
sai da sukayi takai ta wajen 1hr kana Sanah ta dafa kafad'ar Khulud tace " my Khulud I'm in love fa!
ido Khulud ta zaro tana murmushi tace " with who!?
"Hmmmm kedai bari kawai I'm deadly fell in love,
wallahi ina jinshi har cikin rai na zuciya ta,
ji nake kamar nayi hauka ban kuma san ina san nashi ba,
sai yau, yau d'in ma yanzu yanzu da zanzo gidanki,
yau ya tabbatar man da ina sanshi,
" woow please who is that lucky man?
" *SIR ARYAN RAYYAN MOLI*
I love him, I really really love him,
ta fad'a cikin matsanancin farin cikin da shauk'i,
da sauri Khulud tace " wa!? Sir Moli kike nufi?
" Yes! My Khulud she dai,
murmushi Khulud tayi had'i da cewa " Masha Allah, Alhamdulillah gaskiya naji dad'i sosai,
ya abin ya kasance?
Ba wani b'oye-b'oye Sanah ta bawa Khulud labarin komai tun daga farko har k'arshe,
Khulud ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " dama wallahi na dad'e ina tunan sanki yake yi,
ranar da kuka zo har sukayi fad'a da Hanash ranar na k'ara tabbatarwa kai na yana sanki,
Sanah tace " hmmmm! ni ina na sani,
wallahi ban tab'a tunanin so na yake yi ba,
Khulud tace " ke ma dai ai alamomi da dama sun nuna Sir Moli sanki yake,
kuma shi so ai bai tab'a b'oyuwa,
ko gangar jiki da fusuka sun b'oye baki ya kasa furtawa,
kwayar ido da ruhi bazasu tab'a b'oyewa ba,
" hmmmm ni fa har yanzu mamaki nake yi wai I'm in love with him,
" hmmm ni kuma kin san meke ban mamaki har yanzu?
" A'a! sai kin fad'a!
"yadda ya cire girman kai, isa da tak'ama gami ji da kanshi,,
yayi kneeling down yana rok'on soyayyar mace,
wallahi in wata ta fad'a man ban tab'a yarda,
" hmmm gumu da bala'in love yaji!
duka suka sanya dariya,
cikin dariya Khulud tace " wallahi zan so naga idan Sir Moli yana shan love,
naga yadda zayyi tashi kalar soyayyar,
in ga in da dai zai kai had'e fuska da izzar da tak'amar nan tashi,
murmushi ta kuma tace " tashi mu shiga kitchen kar mijinki ya dawo na k'ara yin laifi wajen shi,
yace yau saboda nazo kika k'i dafa mishi abinci kika barshi da yunwa,
ki k'ara shafa man kashin kaji,
ta fad'a tana dariya,
dariya itama tayi kana suka mik'e suka shiga kitchen,
Khulud ta kalli Sanah tace " me zamu dafa ne?
Rolling idanta tayi kana tace " I think muyi sakwara da miyar ganye & dry fish da ganda,
" Ok Khulud tace, kana suka fara aikin,
Khulud tace " amma my Sanah anan zaki k'arasa hutunki ko?
Murmushi tayi tace " idan mijinki bai min haushi ya kore ni ba,
"au wato ma haushi yake yi miki,
saboda kin maida man miji kare ko?
" Yo in ba kare ba wake haushi,
a haka kamar na Allah yadda kasan idan aka saka mishi hannu baki bai iya cizawa,
amma idan ya fitittike yana tajira da ruwan bala'i kamar me!
duk sukayi dariya, basu fi 1hr ba suka gama abincin tsaf suka jere saman dinning,
" to je kiyi wanka kinji my Ulud,
" ban san na barki ke kad'ai ne ai,
dariya tayi tana tura ta cikin bathroom d'in, had'i da jawo mata k'ofa,
parlor ta dawo ta zauna had'i da d'aukar wayar Khulud ta shiga black list,
dan ranta da zuciyar ta sun dad'e suna bata a black list Hanash ya sanya number ta,
dan matuk'ar ba haka ba babu yadda za'ayi ace number ta ce kad'ai bata shiga koda zata shekara tana kiran juna,
tana shiga taga number ta cikin block list,
murmushi tayi had'i da cewa " shege tijararre ja'iri d'an nema,
kana ta cire wayar daga block list d'in,
Khulud bata jima ba ta fito ta gama shiryawa tsaf!,
Sanah ta kalle ta sama da k'asa tace " ke ko meya had'aki da riga da zani cikin gidanki da dare nan?
Cikin mamaki Khulud ta kalle ta tace " bangane ba!
" hmmm ai dama bazaki gane ba, please jeki cire ki saka sexy kaya,
kamata yayi ki rink'a yawo kusan tsirara cikin gidanki, ke da baki ma da yaran da zasu takura miki,
wallahi ni idan duniya na haifa bazasu hana ni sakewa da miji na ba,
nayi kwalliya, abinda yasa matan waje ke kwace maku miji kenan,
kalle ki fa ki kinganki duk kinbi komai kin rufe kamar mai shirin zuwa gidan mutuwa,
ki rink'a yadda tsiraici ciki gidanki ba haramun bane saboda kija hankalin mijinki gare ki,
sakatoto Khulud tayi tana kallan Sanah harta dasa aya,,,,
kana tace " hmmmm zan gyara in sha Allah,
baki ta tab'e had'i da cewa " ya dai kamata kam,
in ma ba ke ba mai zai had'i ki da manyan kaya cikin gidanki harda su bra,
dariya tayi had'i da cewa " gaskiya my Sanah kin waye da yawa,
kodan ai jami'a kike,
" hmmmm wallahi ba wani jami'a,
'yan mata nawa ne a JSS amma idansu tarrrr,
kuma 'yan mata nawa ne a jami'a kansu yake cikin duhu,
" hmmmm ni dai taso muje muci abinci yunwa nake ji,
" wai kina nufin baki jiran mijinki?
" Ikon Allah kuma dan zan jira shi sai na barki da yunwa kome?
" Kinga ni ki barni naci amma ke sai kin jira shi,
" please tashi muje mu ci abinci,
ta fad'a tana rik'o hannunta,
saman dinning d'in suka zauna had'i da yin serving junansu,
kana suka fara cin abincin,
basu dad'e da soma cin abincin ba ya shigo,
yana ganinta ya murtuke fuskarshi murtuk yadda kasan an aiko mishi sak'on mutuwar Mimmee,
batare daya kalle su ba, ya shigo zai wuce,
da sauri Khulud ta tare shi tana yi mishi sannu da zuwa,
fuskarshi d'auke da murmushi ya amsa,
had'i da rungume ta,
d'an kallanshi tayi tace " ina wuni?
Banza yayi da ita kamar bai ji ba,
ta kuma cewa " ina wuni,
still bai amsa na, shiru tayi bata kuma yi mishi magana ba,
Khulud tace " my sweet bakaga our Sanah bane!?
Itama shiru yayi mata,
ta kuma cewa " wai baka ji our Sanah na gaida ka bane!?
" No!, out of correction! your Sanah dai,
ta ina ta zama our, ke da wa ta zama our?
Ya fad'a fuskarshi a tsuke,
" to amma baka ji tana gaida ka bane?
"Na ji mana, in naji sai me?
" sai akayi yaya ko kuma cewa akayi kowanne kucakin yayi maka magana sai ka amsa?
Ido Khulud ta lumshe hawaye na zubowa kan kuncinta,
Sanah tace " please my Ulud karki yi kuka,
idan ba haka ba zan tafi yanzu wallahi,
a fusace yace " ke ban san iskaci da karuwanci,
abinci ne dai ya kawo ki gashi nan sai kiyi tacin mai mai dad'i shegiya kwalamammiya,
muryarta na rawa saboda k'ok'arin danne kukan da take yi,
tace " amma kasan gidan mu babu yunwa ko?
" Dan ina da tabbacin kana d'aya daga cikin wad'anda suka san mun fi k'arfin komai a rayuwarmu,
hannu ya d'agawa Khulud cikin b'acin rai had'i da cewa " enough please!
ya fad'a yana shigewa cikin bedroom d'inshi,
sakwaf Khulud ta zube kan sofa tana k'ok'arin fasa kuka,
Sanah tace " kikayi kuka ban k'ara zuwa gidanki,
ni abinda yake yi man bai damuna,
dan idan da sabo na saba,
da sauri Khulud ta goge hawayenta jin Sanah ta rantse,
a hankali ta mik'e ta dawo kusa da Khulud ta zauna had'i da dafa ta,
jakarta ta d'auko ta bud'e ta ciro magungunan matan da Mamu ta bata ta kawo mata ta bata tace " da peak milk ko fresh milk zaki rink'a,
dan ta bawa Khulud dariya tace " kin san meya faru tsakani ma da Mamu?
Cikin sanyin jiki ta girgiza mata kai,
Sanah ta bata labarin yadda sukayi kan magungunan matan,
Khulud ta kwashe da dariya harda tuntsirawa,
" kai my Sanah baki da dama wallahi,
yanzu har Mamun tamu baki kyale ta ba?
" To ji nayi tana neman mai da ni jaririya,
ganin Khulud ta sake harda dariya sosai yasa taji dad'i,
had'i da tattara nutsuwarta dan yi mata takamaiman maganar data kawo ta,
tace " Aunty Halan ce fa ta aiko ni,
" to lafiya dai ko!?
" Ke lafiya lau karki d'aga hankalinki,
idon Khulud yana kanta tace " ina jinki,
guaran murya tayi kana tace " dama akan maganar sex n........!!
"idan an cewa mutum d'an iska fasik'i ace ba haka ba,
yanzu wannan meye in na karuwanci ba?
" Budurwa dake wacce ko saka mata rana ba'a tab'a yi ba amma kina maganar sex!,,,
a fusace Khulud ta mik'e had'i da kallanshi ido cikin ido tace " dama haka kake Hanash haka halinka da d'abi'unka suke!?
Bayyi mata magana ba idanshi na kan Sanah,
tace " wai meyasa kake yiwa my Sanah haka ne?
'Hanash ka tuna ba haka mukayi dakai ba,
tun ranar daka fara zuwa waje na sai da na fad'a maka wacece Sanah a gare ni،
amma kana wasu abubuwa tamkar ka tsane ta,
idanshi ya mayar kanta yace " yahhh!,
cikin tashin hankali ta zaro idanta waje tace " meye yahhh! kana nufin ka tsane ta?
Cikin d'aga murya yace " yes I hate her! na tsane ta ban santa ban k'aunar ganinta,
tun farko saboda ke da son da nake yi miki,
yasa nake danne k'inta da k'iyayyar danake yi mata,
amma,
Khulud na tsani Sanah! so what?
A hankali Khulud ta soma ja baya tana girgiza kanta,
duk ta rud'e duk ilahirin jikinta kerrrrma yake yi,
da sauri Sanah ta mik'e ta nufe ta had'i da cewa " karki damu da duk abinda zayyi min,
dan bani yake yiwa ba kanshi yake yi...........!
tassssss!!!! tassssss!!!! Hanash ya d'auke Sanah da gigitattun marika,
a rud'e ta dafe kuncinta da hannunta,
yayinda jinta da ganinta sukayi d'aukewar wucin gadi,
a razane Khulud ta kalli Sanah kana ta mayar da kallanta kanshi,
muryarta na rawa tace " what! marin Sanah kayi!?
"Ok yayi kyau ni bazan rama mata da kai na ba,
saboda albarkacin igiyoyin aurenka da ke kai na,
a hankali ta mayar kallanta ga Sanah tace " ni kikayiwa alk'awarin cewa duk abinda yayi maki baki k'ara ramawa har abada ko!?
" Ni kika yiwa alk'awarin duk abinda zayyi miki zaki shanye ko!?
" To daga yau kuma yanzu na yafe wannan alk'awarin naki,
ya yafe duniya da lahira Allah yana shaida,
a yanzu nace ki rama marin da yayi maki,
tun da shi baiga darajata a matsayi na,
na matarshi ta sunna ba, bai ga darajar su Abbu da Dide ba,
yake duk wad'annan abubuwan har ya iya d'aga hannu ya mare ki,
dan Allah dan Annabi Sanah idan har so da soyayyar da kike man gaskiya ne,
a yanzu a nan take ina san ki rama marin da Hanash yayi miki.......................
MOMYN ZARAH