39
_*RASHIN SANI.......*_
*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_
'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''
3⃣9⃣
After 1 year
Bayan shekara d'aya
Haka rayuwa tayi ta tafiya lokaci na wucewa,
kwanaki na gudu, while Sanah an shiga first semester level 3,
yayinda soyayyar su da Sir Moli sai abinda ya k'aru,
sosai suke matuk'ar so da matsanancin k'aunar junansu,
duk ahalin Hard'o family's sun san da zaman Aryan Moli,
kowa ya sanshi sosai dan baya da burki cikin gidan,
cikin ikon Allah,
Ubangiji ya yayewa Aarib matsananciyar soyayyar Sanah,
sakamakon addu'ar daya dage yana yi ba dare ba rana,
dayake Allah maji rok'on bayinsa ne ya amsa rok'onshi,
yanzu babu komai tsakanin shi da ita sai zumunci da 'yan uwantaka.
A b'angaren su Khulud kuwa abun ba'a magana dan sosai Jaddah da sako ta gaba kan rashin haihuwa,
ta musgunawa rauuwarta sosai,
kullum cikin kuka da k'unci take,
duk ta rame ta kod'e saboda damuwa,
damma tana samun sauk'i wajen Hanash,
dan tunda suke dashi bai tab'a nuna mata damuwarshi ba,
amma tasan shima yana cikin damuwa kan rashin haihuwarta,
dan lokuta da dama tasha shigowa d'aki ta iske shi yana kuka,
ko ta jiyo shasshekar kukan shi cikin bathroom,
amma duk da halin dayake ciki yake danne nashi bak'in ciki,
ya rarrashe ta, dan ta samu sukuni,
dan yasha yin fad'a da Jaddan kanta,
while kowa na gidan su yasan matsalar datake ciki,
amma babu yadda suka iya sai dai su tayata da addu'a.
Khulud na zaune cikin parlor taji an banko k'ofar da k'arfi an shigo
a hankali ta d'aga kanta ta kalli bakin k'ofar,
ganin Jaddah yasa gabanta muguwar bugawa,
da saurin ta mik'e jikinta na kerrrma da tsuma,
har k'asa ta duk'a cikin rawar murya tace " sannu da zuwa....!,
wani irin wulak'antaccen kallo ta watsa mata batare data amsa ba,
k'asa ta k'arayi da kanta cikin girmamawa tace " ina yini?
" Ke ni tashi kije ki kira man d'aya munafukin mad'aurin gindin naki,
kin dame ni da wata banzar gaisuwarki,
kanta k'asa cikin rawar murya tace " baya nan,
" a fusace tace " wad'ancan motocin da suke waje fa?
" Eh.! da d'aya ya fita,
kallan banza ta k'ara watsa mata tace " ina yaje?
" Ban sani ba ya dai fita ne kawai bai fad'a man inda zai je ba,
" da naso na same ku gaba d'aya dan ingano ta inda matsalar take kece ko shine,
amma tunda bai nan shikenan ke bari na fara ta kanki,
cikin d'aga murya tace " to nagaji da ga fara sa har yanzu banga k'aho ba,
nagaji da zamanki cikin gidan nan haka,
batare dana ga jikoki na ba,
so nake idan na shigo in fara jiyo hayaniyar yara tun daga waje,
ina jiyo hayaya-hayaya ana guje-guje da bari-bari,
ba wai kullum nazo gida na rink'a ganin fuska d'aya tak ba,
babu abin da kika iya sai dai ki ci kwanta,
idan kinji kashi kije kiyi ko?
Ta fad'a idanta kanta,
a hankali Khulud ta sanya hannu ta goge hawayenta,
" au kuku kike yi?
"Dan munafurci dukanki nayi ko zakinki nayi?
Shiru tayi bata ko d'aga kanta ba,
rankwashi Jaddah tayi mata akanta had'i da cewa " bak'ar munafuka,
wallahi ko kiyi ciki ki haihu ko kuma inyi mishi aure,
imma shanye shi kukayi kuka hanashi k'ara auren,
tunda dama naga alamar ba'ayiwa irinku kishiya,
to ni bazan d'auka ba dan bazan tsaya ina ji ina gani a mayar man da jikana juya ba,
eheee gwara ma kisan halin da kike ciki,
imma bak'in cikin kike man dan kar naga yaran shi to wallahi baki isa ba,
haba ace aure shekara biyu yanzu amma kwata-kwata babu wani motsi,
ko sau d'aya baki tab'a yin b'ari ba,
balle mu shaida kina haihuwa,
kin zauna kullum daga kici ki kwanta shikenan,
to wallahi baki isa ba, imma shi da kanshi bai iya nemo wata,
ni ina iya nemo mishi ehee, fa fad'a tana gyara mayafinta,
" shima zai iske ni ne har gida imma bai je ba zan dawo,
tana k'arasa maganar ta fita fuuuuuu,
bayanta tabi da kallo tana kuka mai cin rai,
saboda ba'a shafe sati d'aya sai Jadda tazo har gida taci mata mutunci san ranta,
bata tuna cewa Allah ke bada haihuwar da kanshi,
bata tunanin bata isa ta bawa kanta ba,
sai wanda ke bayarwa yaga damar bayarwa,
takai 1hr tana ruzgar kuka,
kwata-kwata bata ji tsayawar motar shi,
ko motsin shi ba sai ganinshi tayi kanta,
da sauri ta fara k'ok'arin goge hawayenta dan kar ya gani,
cikin sanyin jiki ya k'arasa inda take zaune,
ya zauna kusa da ita,
cike da tsantsar tausayawa ya kalle ta yace " yauma Jadda tazo ko?
A hankali ta d'ago jajayen idanunta ta kalle shi,
rasa abinda zai ce yasa shi yawo ta jikinshi ya rungume ta,
had'i da k'ok'arin maida kwallar dake shirin zubo mishi,
" wai meyasa Jadda ke yin haka ne?
" Meyasa bazata barsu suji da abinda yake damunsu kad'ai a rayuwarsu ba?
" Meyasa take k'ok'arin k'ara musu damuwa bayan halin bak'in cikin da suke ciki?
" Meyasa take k'ok'arin shiga hurumin Ubangiji ne?
Ya fad'a cikin ranshi,
a hankali ya shiga shafa bayanta zuwa kanta,
cikin sanyin murya yace " kiyi hak'uri komai kika gani daga Ubangijin talik'ai yake,
Allah mai kowa da komai shike da ikon yin komai a yayinda yaso a kuma inda yaso,
ba wayan mu ko dabarar mu bane zai bamu,
sai wanda yayi mu yaga damar bamu,
da zarar yaga damar bamu kum fa ya kum kawai zaice ya kasance,
kuma duk inda jinkiri yake to daga Allah ne,
gaggawace daga shaid'an, muyi addu'a Allah ya bamu,
idan har haihuwar alkhairi ce a gare mu,
idan kuma ba alkhairin bace Allah ya kawo mafita,
k'ank'ame shi ta k'arayi tsam-tsam had'i da fasa kuka mai cin rai,
mai ban tausayi, " kiyi shiru please,
ya fad'a muryar shi na rawa,
a hankali ta d'ago kanta tana kallanshi,
cikin matsanancin kuka tace " dan Allah ka yarda muje asibiti please,
dan mu gano inda matsalar take,
Allah da kanshi yayi cuta ya kuma yi magani,
amma kai kwata-kwata kak'i yarda muje asibiti,
balle a gano inda matsalar take har mu magance,
ta k'arasa maganar cikin rikitaccen kuka,
jikinshi ya sake mayar da ita yana shafa kanta,
yace " yanzu abinda kike so ayi kenan?
Da sauri ta d'aga mishi kanta had'i da cewa " eh!,
guntun murmushi yayi yana goge mata hawayen,
yace " tashi muje ki shirya muje,
da sauri ta mik'e duk ilahirin jikinta na kerrrrma,
bathroom ya fara kaita ya taimaka mata,
ta wanke fuskata kana suka koma bedroom,
tana k'ok'arin saka doguwar riga,
yace " idan za'ayi scanning kuma fa?
Bata yi mishi magana ba, ta mayar ta d'auko riga da zani na atamfa ta saka,
had'i saka jihab da takalmi,
bata bi takan jaka da wayar ba ta fita,
a harabar Malam Aminu Kano Teaching Hospital yayi parking,
waya ya ciro ya kira Doctor d'in da suka zo gani,
yace su shigo ba matsala yana ciki,
wayar ya mayar cikin aljihunshi,
kana suka fita, koda suka je office d'in sai da suka tsaya bakin k'ofa sukayi knocking aka basu izinin shiga kana suka shiga,
haka nan Khulud taji gabanta na fad'uwa yana dukan uku-uku,
hannu Hanash ya mik'ewa Doctor d'in suka yi musaha,
kana Doctor yace " Bismillah ku zauna ga waje nan,
ya fad'a yana nuna musu sit,
sai da suka zauna kana Doctor ya kalle su fuskarshi d'auke da murmushi yace " Doctor Mujaheed _(Family Doctor d'in su Hanash)_ yayi man bayaninku amma ina san jin k'arin bayani daga gare ku,
a nutse Hanash yayi mishi bayanin komai,
numfasawa Doctor d'in yayi kana yace " shekararku nawa da aure?
" 2yrs kenan, Hanash ya bashi amsa,
a hankali ya mayar da kallanshi ga Khulud yace " zanyi miki wasu tambayoyi kicire kunya ki bani amsa sosai please,
dan su zasu taimake mu mu gano matsalar,
cikin sanyi ta d'aga mishi kai had'i da cewa " in sha Allah, while gabanta baibar fad'uwa ba,
" idan kuna sex kina jin zafi?
Kanta k'asa tace " a'a,
" kina zubar da wani irin ruwa mai launi daban ko wari?
"A'a,
" kafin ki fara period kin kai shekara nawa?
"16yrs,
" kina ciwon mara idan zakiyi period d'in?
"Eh..! ina yi sosai ma,
daga ina kike jin ciwon?
" Gefe cikina sai kuma k'asan mararta,
kuma ina jin ciwon harta wajen bayana da k'ugu na,
shiru yayi yana rubuce-rubuce,
kana ya d'ago kanshi ya kalli Hanash yace " kana tsagiya?
" D'an shiru yayi yana tunani kana yace " meye tsagiya,
" fitar da jini ta al'aurarka,
"a'a, Hanash yace,
" idan kuna sex kana jin zafi?
"A'a,
" kana jin wani lokacin penis d'inka na zafi, ko rad'ad'i ko kaji kamar bata aiki?
"A'a,
" bata baka matsala wajen sex, ko wani lokaci tak'i reaction?
"A'a batayin komai gaskiya,
wata 'yar k'ararrawa ya danna ba'a jima ba nurse ta shigo,
mik'ewa yayi ya nufi wajen scanning dake cikin office d'inshi,
nurse d'in na biye dashi,
" Bismillah,
Hanash da Khulud suka mik'e suka bi bayanshi,
labule yaja ya raba tsakanin gadon da scanner,
kana yacewa nurse d'in ta bud'e marar Khulud ta shafa mata scanning gel,
kamar yadda yace haka tayi,
duk iya scanning d'in da Doctor yayi baiga komai ba,
ajiyar zuciya ya sauke had'i da mik'ewa ya koma kan table d'inshi,
yayi 'yan rubuce-rubuce kana ya mik'ewa nurse
file yace " ki kaita lab,
a d'ebi jikinta, fitsarinta da sperm d'inta,
"amsa tayi kana ta kalli Khulud tace " muje,
Doctor ya kalli Hanash yace " muje ayi maka scanning,
"Ok yace yana mik'ewa,
kamar yadda Doctor baiga komai a wajen Khulud ba haka ma Hanash,
test d'in daya rubuta ayiwa Khulud haka shima ya rubuta mishi,
bayan kamar 15 minutes suka dawo office d'in bayan an gama d'aukar abinda za'a d'auka,
Doctor yace " sai kunyi d'an hak'uri dan result d'in zai kai 2hrs,
sai dai in zakuje ku dawo in kuma zaku jira ne to,
kafin Hanash yayi magana Khulud tayi saurin cewa "ok badamuwa zamu jira a waje,
dan bata jin zata iya tafiya ko'ina batare dataji result d'in ba,
murmushi Doctor yayi yace " badamuwa kuyi zamanku nan cikin office d'in,
dan nima fita zanyi yanzu, ya fad'a yana mik'ewa,
musabaha suka sake yi kana Doctor ya fita,
Hanash ya kalle ta yace " meyasa bazamu je gida mu dawo ba?
" Wallahi ban iya zuwa ko'ina a halin danake ciki yanzu,
dan Allah mu jira d'in kawai, lokaci bashi da wuya yanzu zaka ga har 2hrs d'in tayi,
ta fad'a cikin sanyinta,
murmushi yayi yana jawota jikinshi dayake akan sofa 3 sitter suke.
Cikin nutsuwa yakai kwalbar Dolomia natural mineral water,
(ruwan sayafi kowanne tsada) bakinshi ya kurb'a kana ya ajiye kwalbar saman table,
" Hub please kayi hak'uri mana,
bai kalle ta ba ya cigaba da latsa wayarshi,
a hankali takai hannunta zata shafa kwantacciyar k'asumbar dake kwance saman fuskarshi,
fuska ya tsuke had'i da buge hannunta yace " don't touch me again,
" haba my sweet Aryan na baka hak'uri fa,
Sanah ta fad'a cikin shagwab'a,
a fusace yace " ban hak'ura kuma All........! ,
da sauri ta sanya hannu ta rufe mishi bakinshi,
hannunta ya ture had'i da zafga mata uwar harara yace " ni daina tab'a, tunda na lura dama so kike yi mu lalace,
" please kayi hak'uri mana my Aryan,
hankalinshi ya tattara gaba d'aya ya mayar kanta yace " wai me kike nufi da nine Sanah?
Ido ta zaro tace " Sanah...! fa kace?
" Eh ko ba sunaki Sanah ba?
" Lalle yau ran maza ya b'aci,
bai kalle ta ba ya cigaba da latsa wayarshi,
" kayi hak'uri please..!
haba Hub..! ban sanka da dogon fushi bafa,
idanshi ya kafe ta dashi yana kallanta,
had'i da cizon lips d'inshi,
" please mana, ta fad'a tana shafa kwantaccen gashin kanshi,
" wai me kike san mayar dani ne Sanah?
" Ni na rasa me kike nufi, na rasa gane inda kika dosa,
kwata-kwata ban san me kike nufi da ni ba,
duk lokacin danyi miki maganar aure sai kiyi ta man hanya-hanya,
yanzu fa 1yr to above kenan muna dating,
kodan kinga ban tab'a attempting yin sex dake bane,
" am sorry Hub kayi hak'uri nesa ai tazo kusa,
cikin masifa yace " ban gane nesa tazo kusa ba..!?
Da sauri ta rufe mishi bakinshi tana kallan gefe da gefensu,
" kayi a hankali bamu kad'ai ne a wajen ba,
tsoki ya ja mtswwwww had'i da cewa,
" ni ban iya long relationship, ya fad'a yana mik'ewa,
da sauri itama ta mik'e ta tark gabanshi,
tana k'ok'arin rungume shi, hannunta ya rik'e idanshi cikin nata,
yace " kin san yadda nake daure sha'awata kuwa?
"Kin san taya nake iya yin controlling kai na wasu lokutan?
" Amma ke kwata-kwata baki tausayi na,
baki damu da halin danake shiga wasu lokutan ba,
ya k'arasa maganar yana shiga cikin mota,
tsayawa cak tayi tana kallanta,
motar yayiwa key batare daya kalleta ba,
yayi horn, cikin sanyin jiki ta taka ta shiga motar,
har ya isa k'ofar gidansu bayyi mata magana ba,
sai da ta sauka tana k'ok'arin shiga gida yace " daga yau bamu k'ara yin waya ko magana da juna,
balle ganin juna, duk sanda kika shirya aure na ki sanar dani,
ya fad'a batare daya kalle ta ba,
ta bud'e baki zatayi mishi magana yaja motarshi ya bar wajen,
bayan motar tabi da kallo har ya b'ace mata,
tunda ta koma gida take ta faman kiranshi a waya yana rejecting.
Doctor yayi knocking bakin k'ofar office d'inshi,
Hanash ya bashi izzinin shiga,
" kuyi hak'uri na barku kuna ta zaman jira ko?
"Ah ai ba damuwa yanayin aikin ne haka,
fuskar Doctor d'auke da murmushi ya mik'awa Hanash hannu had'i da cewa " congratulation,
duk gwaje-gwajen da akayi muku bai nuna kuna tare da wata matsala ba,
da nayi tunanin ma ko infection ne amma munyi muku test baku dashi,
ina ganin Allah ne kawai bai kawo lokaci ba,
ayi ta addu'a ana neman zab'in Allah,
murmushin jin dad'i Hanash yayi had'i da yiwa Doctor godiya sosai kana suka fita.
"Kin gani ko dama na fad'a miki babu mai matsala cikin mu Allah ne kawai bai kawo lokaci ba,
cikin sanyin murya tace " ni dai Allah ban yarda da wannan result d'in ba,
dan Allah mu canja wani hospital d'in,
" ban gane baki yarda ba...!?
" Bayan akan idanki akayi komai,
" please mu canja wani hospital d'in?
ta fad'a hawaye na zubo mata,
ido ya k'ura mata na d'an lokaci kana yace " yanzu wanne asibitin kike san muje?
" Muje Nasarawa please....!
batare da yayi mata magana ba yayiwa motar key yaja,
kasancewar a can family Doctor d'in su Hanash yake aiki yasa basu sha wata wahala ba,
akayi musu duk abinda ya dace,
amma still amsar dai d'aya ce basu da matsalar komai,
nan ma k'in yarda Khulud tayi ta marairaice mishi akan dole sai sun canja hospital,
Standard Hospital suka je nan ma akayi musu gwaje-gwaje nan ma ce musu akayi babu mai matsala cikin su,
ranar duk wani babban Hospital dake cikin garin Kano State sai da suka je,
still amma d'aya ake basu lafiyarsu lau basa tare da wata matsala,
basu koma gida ba sai around 12:25am na dare,
sosai Hanash yayi ta rarrashin Khulud yana bata baki,
had'i da k'ara tunatar da ita k'adddara da tawakkali.
A week letter
" Zohal zo ki raka ni gidan Hanash,
a hankali ta d'aga kanta ta saci kallan Mimmee,
cikin dabara Mimmee ta girgiza mata kai alamar a'a,
dan harga Allah babu wanda yake san abinda Jaddah keyiwa Khulud,
cikin sanyin murya tace " bani da lafiya Jaddah,
" baki da lafiya kike rik'e da waya..!?
Ta fad'a cikin rashin yarda da maganar ta,
" eh..! Doctor nake san kira ai,
" hmmm kedai kika sani, ta fad'a tana tab'e baki,
kallanta ta mayar kan Wajnah dake zaune kanta k'asa,
tana chart tunda Jaddah ta shigo bata ko d'aga kanta ba,
" ke..! zo ki raka to..!
yi tayi kamar bata ji abinda take cewa ba,
" Wajnah dake fa nake...!
" Au wai ni..!? me kika ce?
" Cewa nayi ki tashi muje gidan Hanash,
" ni zan raka ki gidan Hanash d'in?
" Dawa..! idan ba ke ba...!?
" Tab..! amma ai kin san ban shiga rayuwarsu da matsalar wasu ko?
" Ni bana d'orawa kai na damuwar wasu,
tawa ma ta isheni, jeki sai kin dawo,
" Wajnah ni kike fad'awa wannan maganar...!?
"Eh lalle ai kin girma kin isa aure kinga k'irjinki ya cika dole kiyi man haka,
ai dama an fad'a idan mace ta girma ta balaga ganin kanta take yi dai-dai da kowa,
to yayi yau bari na gama da wannan kafin na juyo kanku inga uban da ya d'aure muku gindi,
ta fad'a cikin masifa tana fita,
ganinta yasa gaba d'aya drivers d'in guda hud'u suka mik'e,
gudan kar suyi laifi dan sun san halin ta,
" da kuka tashi gaba d'ayanku ne zaku kai ni ko me?
"A'a suka ce,
bata kuma yin magana ba ta shige cikin mota ta zauna,
d'aya daga cikin su yayi saurin bud'e motar ya shiga ya zauna,
dukkan su shiru sukayi babu wanda yace k'ala,
ganin an d'auki lokaci yasa driver cewa " Hajiya ina zamu j.......!?
Bata bari ya k'arasa ba, tace " gidan Hanash,
batare daya kuma yin magana ba yaja motar ya fita,
bata bari ya k'arasa yin parking ba ta bud'e ta fito jikinta sai rawa yake saboda tsabar bala'i,
ganin ba kowa a parlor yasata d'aga murya tace " ke...! ina kike?
Khulud dake kwance saman bed,
jin muryar Jaddah yasata hantsulawa daga kan bed d'in,
jikinta na kerrrrma ta nufi parlor bakinta d'auke da " innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
shek'ek'e ta kalle ta had'i cewa,
" uhnnn a kwana a hantse sai manyan mata,
hanshak'iya mandiyya masu kashin gold,
an iya nanik'ewa miji akai har yanzu ana bacci amma ba'a iya d'aukar ciki ba,
kanta k'asa tace " sannu da zuwa, ina wuni..!?
"Au ashe kin san an wunin amma kike lik'e da miji kuke bacci har yanzu?
K'ara sunkuyar da kanta k'asa tayi batare datace komai ba,
" ina ma yadda nazo yanzu yaran Hanash jikoki na ne zasu tare ni da gudu,
amma dayake juya muka auro shiru har yanzu aure shekara biyu,
to yanzu zuwa nayi kuyi man bayani daga inda matsalar take kece ko shine?
" Kece ba mace ba, ko kuma shine ba cikekken namiji ba?
" Idan kuma juya muka auro sai mu sani,
in banda hawaye babu abinda ke fita daga cikin idanun Khulud,
" uhnnn ina jinki bani amsa shi ne baya yi yadda ya kamata ko kuwa?
Hannu tasa ta toshe bakinta gudun kar kukan da take yi ya kwace mata,
ta sake yin wani laifin wajen Jaddah,
" dake nake ina jinki fad'a man dalilin daya hanaki d'aukar ciki?
" Kinyi shiru, yau ban barin gidan nan sai naji amsa ta,
meya hanaki yin ciki, shine ke da matsala ko ke?
Cikin kuka Khulud ta bud'e baki zatayi magana amma kuka ya hanata,
a hasale Jaddah tace " nace ki fad'a man dalilin daya hanaki d'aukar cik....!?
"Allah'n dayake bayarwa ne bai bamu ba,
Hanash ya fad'a yana fitowa daga cikin bedroom,
" ohhhhh ashe kai ma kana ciki?
"Eh..! yace yana mik'ar da Khulud tsaye daga durk'ushen,
" nagodewa Allah dayasa na same ku gaba d'aya,
dan haka kuban amsa yau, danna gaji..!
kan sofa ya zaunar da Khulud kana ya dawo gaban Jaddah ya tsaya yana kallanta ido cikin ido,
yace " uhmmm yi tambayarki me kike san ki sani..?
Cikin muryar kuka Khulud tace " please m.......!!
hannu ya d'aga mata ya dakatar da ita batare daya kalli inda take ba,
" ehhh ina san sanin daga inda matsalar take kai ne baka da cikekkiyar lafiya ko kuma itace juya?
" Kamar ya ban gane ba..!?
Ya fad'a still idanshi cikin nata,
" ina nufin bai ba cikekken namiji mai lafiya bane,
shiyasa baka yin abinda ya kamata ka kakasa yi mata ciki,
ko ko ita ce juya?
" Har yanzu ban gane badai,
" lusarin namiji ne kai baka yin abinda ya kamata ne, shiyasa har yanzu ciki bai shiga ba, ko kuma itace lusarar..!?
Mutun murmushin gefen baki yayi,
a ranshi yana jin inama ba Jaddah ce tayi mishi wannan tambayar ba,
a fili kuma yace " Ubangiji mai kowa mai komai,
mai yin yadda yaso a inda yaso,
wanda yayi saman bakwai da k'asan bakwai,
wanda ya halicci duniya da abinda ke cikinta,
mai bawa wanda yaso ya kuma hana wanda yaso, mai kwacewa daga hannun wani ya bawa wani,
wanda ya dai-daita wuta da k'ank'ara,
wanda ya sama da k'asa, ya kuma rik'e saman,
wanda bai haifa ba, ba a kuma haifashi ba,
wai zartar da hukunci akan kowa,
wanda yake azurta fak'iri ya talauta hamshak'i,
Ubangiji wanda zaice kasance ya kasance Allah mai " Kum fa ya kum,
wanda yayi ni yayi ki yayi Khulud,
wanda ke bada haihuwa shine bai bamu ba,
ya fad'a idanshi tarrr cikin nata,
kame-kame Jaddah ta farayi had'i da cewa " Hanash ni kake ciwa mutunci akan matarka..!?
" Cin mutuci ko gaskiya Jaddah?
" To yayi kyau ka kuma kyauta,
nagode sosai Allah ya saka da alkhairi,
amma zanje na tadawa Ubanka hankali tunda shi bai isa yayi man musu da gardama ba,
balle ya sani gaba yana zani,
zanje na d'aga mishi hankali ta yadda shima zai d'aga maka naka hankalin,
shi ai baka isa kayi mishi haka ba,
tana k'arasa maganar ta fita fuuuuu,
Jaddah na fita Khulud ta fasa rikitaccen kuka,
bayanta Hanash yabi da kallo had'i da furzar da iska,
a hankali ya nufi Khulud ya zauna kusa da had'i da rungume ta,
batare dayace mata komai na,
sun dad'e a haka kana ya rabata da jikinshi yasa hannushi ya shiga goge mata hawayen ta,
cikin nutsuwa ya mik'e ya koma bedroom ya d'auko wayarshi,
kana ya dawo parlor ya kuma rungume ta yana dialing number family agent d'in su,
tana soma ringing yayi picking,
sai da suka gaisa kana Hanash yace " please zan iya samun visa America cikin kwana biyu?
D'an shiru yayi kana yace " wanne irin visa kake so yallab'ai?
" Ganin Doctor..!,
shiru ya kuka kafin yace " may be zamu iya samu cikin kwana uku,
" please kayi man k'ok'arin na samu d'in,
" haba yallab'ai idan kaga ba'ayi abuba to babu yadda za'ayi ne,
amma komai kuke so za'ayi k'ok'arin yi muku in sha Allah,
yauwa nagode sosai,
" haba yallab'ai meye na godiya kuma?
"Tsakanin mu ai ba godiya duk yiwa kai ne,
yanzu abinda ya rage ka fad'an inda zan karb'i passport d'inka?
" Oh..! Sorry na manta ban fad'a maka ni da Madam zamuyi tafiyar ba,
" amma yallab'ai idan dan wannan matsalar ce mai zai hana ku fara zuwa abuja da Lagos?
" Abuja da Lagos kuma...!?
"Eh akwai manyan asibitoci masu kyau,
wad'anda zasuyi maka tamkar kana American dan akwai asibitin wani ba'indiye daya bud'e Dr Hassan's Hospital iller crescent, 5 Katsina-Ala st Maitama, Abuja,
sannan akwai wani Primus Hospital Indian Hospital,
then..! a Lagos akwai Lagoon Hospital Apapa 8 marine road,
then...! akwai Lagoon Hospital Victoria Island 13 idejo,
sai Nicholas Hospital 7b etim crescent,
kaga wad'annan Hospitals d'in are the best hospital in Nigeria kaje ka gani daga can in baka samu abinda kake so ba,
sai ku wuce kawai ba ma sai kun dawo gida ba,
" Ok tom gobe zamu bi jirgi mu fara zuwa Abuja,
yanzu ma zanyi mana booking a Sheratoon Hotal,
" Allah yasa a dace..!
" Amin ya Allah..!
kana suka kashe wayar, kallansa ya mayar kan Khulud yace " tashi mu shirya kayan mu,
gaba d'aya daga can idan bamu gamsu ba,
sai mu wuce American kawai,
ya fad'a yana mik'a mata hannunshi,
hawayenta ta goge had'i da rik'e hannunshi,
suka shiga ciki.
Washe gari sai da suka biya suka kaiwa Agent d'in pastport d'insu kana suka wuce Abuja,
gaba d'aya hospitals d'in daya fad'a musu dake Abuja babu wanda basu je ba,
amma gwaje-gwajen da akayi musu ba'a gano wata matsala ba,
haka ma a Lagos haka sukayi ta yawon Hospitals amma duk inda suka je still dai amsar d'aya ce,
shine lafiyarsu lau basa tare da wata matsala,
bayan kwana biyu suka d'aga America,
bayan sunyi applied na ganin Doctor,
kuma an basu appointment,
k'arfe 1:43am na agogon America jirginsu yayi landing a America,
a Amsterdam Hotal suka sauka,
washe gari k'arfe 9:00am na safe suka je asibitin,
ba'a wani tsaya b'ata lokaci ba aka shiga duba su,
hmmm kayan company daban dana shago,
Nigeria anyi mana nisan nisa,
domin kayan aikin ma daban suke,
anyiwa su Hanash aune-aune,
da gwaje-gwaje an sanya su cikin machines kala-kala,
tun k'arfe goma na safe ake ta faman duba su,
ba'a gama ba sai 12:27am na dare, kana aka gama komai,
" zaku tafi masaukin ku ne ko kuma kuna san result d'in yau?
" Idan bazai d'auki lokaci ba muna san ji,
"ai yama fito, ku biyo ni, ya fad'a yana nufar cikin office d'inshi,
jikinta a sanyaye gabanta na dukan uku-uku ta mik'e,
ganin yanayinta yasa Hanash rungume cikin jikinshi kana suka bi bayanshi,
" zauna Doctor d'in yace yana nuna musu sit!,
hankalinshi ya tattara gaba d'aya kan Khulud yace " kin tab'a samun hatsari 8yrs back?
Gabanta na fad'uwa tace " a'a,
yace " baki tab'a fad'uwa daga wani waje mai nisa ko bigewa a cikin ki ba?
Sai da gabanta yayi muguwar bugawa kana cikin rawar murya tace " eh na tab'a,
ajiyar zuciya Doctor d'in yayi kana yace " a lokacin kinyi muguwar bugawa sannan abu mai nauyi ya danne miki ciki ko?
Tunowa tayi da lokacin da suke yin game a Roni,
Sanah ta buga mata ball kana ta kuma buge ta da k'afarta ta kuma taka ruwan cikinta da takalmin ball,
" eh tace duk ilahirin jikinta na kerrrrma,
" a lokacin kin suma?
"Eh..!
kuma an kaiki Hospital Doctosr sun duba ki a lokacin?
" Eh..!
sai da ya sake sauke ajiyar zuciya kana yace " I'm sorry daya kasance ni ne zan fad'a miki maganar,
numfashi ya kuma fitarwa kana yace " sakamakon wannan buguwar da kika samu a lokacin bazaki tab'a haihuwa ba har abada,
saboda an fasa miki mahaifa tun kina yarinya kafin ki balaga...................!!!!!!!
MOMYN ZARAH