41
_*RASHIN SANI.......*_
*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_
'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''
~DEDICATED TO~
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
'''(GARKUWAR JIDDARH)'''
4⃣1⃣
Tashin hankali wanda ba'a sa maka rana....!,
ji tayi tamkar an buga mata gudumar k'arfe cikin kanta,
dan wata irin k'ara taji " gannnnnnn...!,
cikin k'ok'on kanta, take ji da ganinta sukayi d'aukewar wucin gadi,
zuciyarta tayi bak'i k'irin mak'ogwaranta ya bushe rak'ayau,
k'irjinta ya soma yi mata zafi yana soya had'i da tuk'uk'in bak'in ciki,
sakwaf jiki ba kwari Sanah ta zame k'asa saman tails tayi zaman dirshan,
komai tsaya mata cak yayi, brain d'inta tayi hooking,
ta daina ji da ganin komai, ta d'auki tsayin lokaci a haka,
cikin kuka Khulud ta durk'usa gabanta,
gami da sanya hannunta tana jijjiga ta tare da kiran sunnata,
" Sanah...! Sanah..!
wani irin kallo Sanah keyiwa Khulud tamkar mai tab'in hankali,
bakinta na rawa tace " na cuci kai na,
bazan tab'a yafewa kai na ba,
hannu da k'afarta ta kalla had'i da cewa " ni da hannu na da k'afarta, da kai na illata my Ulud,
lalle *_RASHIN SANI...!_* yafi dare duhu,
ta fad'a tana kallan Khulud,
kamar zararriya tayi zumbur ta mik'e had'i sakin tijararran kuku mai cin rai,
gami da d'ora hannunta a ka tana ihuuun kuka,
tamkar wacce aka cewa uwarta, ubanta dama ahalinta gaba d'aya sun mutu,
sosai take kukan tana ihuuuu had'i da dukan kanta,
" wayyo na shiga uku na lallace,
innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
wayyo Allah na ni Sanah wayyo rayuwa ta,
ganin yadda take ihuuu tana buge-buge yasa Aarib da Zafran saurin mik'ewa suka rik'e ta,
amma duk da sun rik'eta bata daina ihunnn da turje-turje ba,
sosai ta rink'a kokowar kwacewe tana ihuuuu,
" dan Allah ku barni na mutu ku barni na kashe kai na,
wallahi koda na rayu bazan tab'a rayuwa cikin farin ciki da jin dad'in duniya ba,
zan rayune cikin k'unci da k'unar rai,
ta fad'a tana kukan, sosai itama Khulud take kukan had'i da durk'ushewa a k'asa,
duk ilahirin jikinta kerrrrma da tsuma yake,
gashin kanta yayi buzu-buzu ta koma mahaukaciya tuburan muraran,
cikin kuka Khulud ta mik'e ta nufi inda Sanah keta saman yunk'oran kwacewa,
rungumeta tsam Khulud tayi a jikinta,
tun tana k'ok'arin kwacewa Khulud tak'i bata damar hakan ta rik'e ta gammm,
har ta gaji ta saki jikinta cikin na Khulud itama ta runngume dukkansu suna kuka,
cike da tsantsar bak'in ciki abin tausayi...!
Duk wanda ke wajen sai da yaji zuciyarshi ta karye,
" kiyi hak'uri my Ulud wallahi ban tab'a sanin hakan zata faru ba..!
" bani da masaniya, wallahi bada gayya nayi miki hakan ba,
ban san hakan zata faru ba, dana sani kin san ban tab'a yi miki haka,
dan Allah kiyi hak'uri my Ulud,
ta fad'a cikin matsanancin kuka,
" bakomai my Sanah nafi kowa sanin haka a duniya,
nasan bazaki tab'a yin abinda zai cutar da ni ba,
please ki bar maganar abinda zai faru ya rigada ya faru,
bamu san abinda abinda ya b'oye ba,
bamu san manufar Ubangiji nayin hakan ba,
sai dai muyi ta addu'a,
ta fad'a tana goge mata hawayen dake kan fuskarta,
" mai yasa ni abin bai fad'a kai ba...!?
" Mai yasa ni Allah bai jarrabe ni ba...!?
" Mai yasa ni k'addarar da jarabawar basu fad'a man instead of you ba...!?
" Mai yasa sai ke abin ya fad'a kanki...!?
" Mai yasa duk tarin students d'in dake wajen abun bai same su ba sai mu my Ulud...!?
" Why always us, why..! why...! my Ulud...!?
Ta fad'a cikin matsanancin kuka mai cin zuciya,
murmushi k'arfin hali Khulud tayi tana k'ok'arin danne damuwarta,
tace " karkice haka please, karkiyi sab'o mana, su sauran students d'in kin san kalar tasu jarabawar...!?
Cike da tsantsar tausayawa Dide ya rungume su had'i da shafa kansu,
cikin nutsuwa ya zame su daga cikin jikin shi gami dayin gyaran murya,
yace " wannan abu daya faru babu ruwan Sanah,
ba kuma itace ta d'orawa Khulud ciwo ba, ba itace ta hana Khulud haihuwa ba,
domin lokacin da akayi abun dukkan su suna yara k'anana,
a cikin su babu wanda ya haura shekara goma,
lokacin babu mai cikekken hankali ko wayo,
suna cikin d'anyar k'uruciya, ko ita Khulud d'in ce Allah ya k'addara tana iyayiwa Sanah haka,
idan ma da sanadi ko k'arar kwana tana iya mutuwa,
mu ahalinmu (Hard'o families) mun san k'addara, dangana, tawakkali da kuma hak'uri,
idan abu ya same mu bamu tab'a yin blaming wani muce shine sila,
domin muna da tauhidi, had'i da ilimi dai-dai gwargwado,
jahili ko mushiriki shine idan abu ya same shi bazai danganta al'amari ga Allah ba,
sai ya danganta abun ga wanin Allah,
bayan kowa yasan dai-dai da kwayar zarra bata da ikon motsawa face sai da izinin Ubangijin al'arshe,
tun farko Allah ya riga da ya tsara haka a cikin k'addarar Khulud,
babu kuma wanda ya isa ya kankare hakan daga cikin littafin k'addarar ta,
abinda ya kamacemu anan shine mu taya ta da addu'a bawai mu tsaya muna jimami ba,
idan rashin haihuwar shine alkhairi da kwanciyar hankaki a gare ta fa?
" Yaran yanzu wasu da haihuwar su gwara babu,
sosai Dide yayi musu nasiha mai ratsa jiki da ruhi gami da zuciya,
wanda har ita kanta Khulud da Sanah suka ji ransu da zuciyoyinsu sunyi musu d'an sanyi,
cikin sanyin jiki Sanah taje gaban Hanash ta duk'a while hawaye bai bar zuba daga cikin idonta ba,
tace " I'm sorry Brother kayi hak'uri nasan kaima na sanya ka cikin tarin bak'in ciki da takaici had'i da damuwa,
nasan zuciyarka tayi maka k'unci, zafi gami da rad'ad'i duk a dalilina,
please for gv me, I promise you nima bazan tab'a haihuwa a rayuwa ta ba,
ta fad'a cikin kuka,
take Hanash ya ji jikinshi yayi mugun yin sanyi,
zuciyarshi tayi sanyi, lokaci d'aya ya nemi duk wata k'una da rad'ad'in dayake ji akanta ya rasa,
karo na farko da yaji tayi abinda ya burgeshi,
cikin nutsuwa yayi mata murmushi tare da cewa " ba laifinki bane haka Allah ya tsara tun farko,
tun kan a haliccin duniya da abinda ke cikinta,
" thank you..!, thank you so much,
Mamu ta rungume Khulud tana share hawaye,
a hankali Khulud ta d'ago kanta had'i da mik'awa Sanah hannu alamar ta tazo,
jikinta na rawa ta mik'e ta fad'a jikin Khulud da Mamu,
dakyar Mamu ta lallab'i Khulud da Sanah suka ci abinci,
haka ma Hanash, daya tashi tafiya gida Khulud cewa tayi bata binshi ya barta anan,
dan tana san su d'eb'ewa juna kewa da damuwar da suke ciki..!
murmushi kawai yayi musu kana yayi tafiyarshi ya barta nan da sunan after 3days zata koma gida,
cikin ikon Allah da k'ok'arin Mamu, Juju Abbu da Dide suka fara mantawa da abun,
haka ma Halan ta dake tana kawar musu da abun daga cikin ransu,
aka kuma dage dayi musu addu'a da rok'on Allah akan Allah ya mantar dasu,
dayake Allah maji rok'on bayinsa ne ya amshi addu'arsu,
yasa suka manta suka shiga harkokin gabansu
yayinda yayyansu ma ba'a barsu a baya ba, kullum cikin d'aukar su suke yi suna fita dasu yawo,
sai da Khulud tayi 1 week kana ta koma gidanta.
2 weeks later
Tayi ta faman kiran wayarshi harta gaji, baya picking,
haka ma ko text ta tura mishi bayyi mata reply sosai hankalinta yayi mugun tashi,
haka ma a makaranta baya bari su had'u ko office d'inshi taje bai barinta ta shiga,
haka zatayi ta jiranshi bakin k'ofa amma yak'i bud'ewa sai ta gaji da jiranshi ta tafi,
kana ya bud'e,
yau kasancewar Saturday ce basu da lectures sosai,
da wuri suka gama, tun around 1:50pm na rana suka fito,
suna fitowa ta nufi office d'inshi directly,
batayi knocking ta rab'e daga gefe yadda bazai ganta ba,
tana jiran MD ya fito saboda taga sanda ya shiga,
batafi 10 minutes tana jira ba taji MD na cewa " ok to shikenan ba damuwa sai mun had'u goben,
da sauri ta fito daga inda take lab'e taje jikin k'ofar ta tsaya,
dai-dai lokacin MD ya fito, ganinta tana k'ok'arin shiga yasa MD bai rufe k'ofar ba ya fito ita kuma ta shiga,
kishingid'e ta same shi saman sofa idanshi lumshe jikinshi sanye da cot sai dai ya cire ta saman ya rataye ta,
daga saman bottles d'in gaban rigarshi b'alle kwantaccen gashin k'irjinshi ya fito luf-luf dashi abun sha'awa,
kwata-kwata bai san ta shigo ba, saboda lokacin da MD ya fita ta shigo,
so koda yaji motsin k'ofa ya d'auka na fitar MD ne,
ta d'auki tsayin lokaci tana kallanshi,
kafin ta taka zuwa inda yake ta zauna gefenshi,
a hankali ta sanya hannunta saman fuskarshi tana shafa sajenshi,
da sauri ya bud'e idanshi a d'an tsorace,
murmushi tayi mishi tace " na baka tsoro ko..!?
Sosai yayi murtuk da fuskarshi ya tsuke face, had'i da cewa " waya baki izinin shigo man office kai tsaye..!?
" Yadda akayi na shiga cikin zuciyarka kai tsaye batare daka sani ba, ka kuma shiga cikin tawa zuciyar batare da dana sani ba, ta haka na shigo,
ta fad'a hannunta saman face d'inshi,
hannunta ya ture had'i da nuna mata k'ofa yace " get out..!
" wai meyasa kake haka ne..!?
" Nafa baka hak'uri, please ka hak'ura mana,
" tashi ki fita, ban san magana dake please...!
bakinta ta rik'e had'i da cewa " nashiga uku yau Sir Moli ya kure ni wai bai san magana dani,
ta fad'a in a funny way,
" yes..! I said it again ban san magana dake get out,
" waii! in bi ina inga haske idan ka kore ni...!?
Ta fad'a tana k'ok'arin cusa hannunta cikin k'irjinshi,
da sauri ya rik'e hannun dan ya lura neman burkita mishi lissafi take yi,
" uhmmm idan na kula neman lalata ni kike yi, so kike yi ki lalata man tarbiyyarta,
shiyasa kika k'i yarda muyi auren ko..!?
Sosai abin ya bata dariya " wai neman lalata shi take yi ,
"Eh so kike yi ki iskanta ni ki...!,
" ok haka kace ..!?
"Eh...! hak.....!
jin ta had'e bakinsu yasashi yin shiru dole, had'i da zaro idanshi waje,
sai da ta tsotsi bakinshi sosai hana ta saki bakin,
ta d'ago ta kalle shi tace " uhmmm na lalata kan yanzu ko da saura....!?
"Ah inaga dai da saura..! ya fad'a yana sa hannunshi ya zame d'an kwalinta had'i da cire reborn d'in data d'aure gashinta dashi,
ya cusa hannunshi cikin gashin kanta,
ya karkata kanta had'i da had'e bakinsu,
idanuwansu duka lumshe duka suna sauke numfashi da sauri da sauri,
ta k'asa ya zura hannunshi cikin rigarta yana shafa bayanta,
while suna tsotsar bakin juna cikin shauk'i,
a hankali ya zagayo da hannunshi cikinta,
yana shafa cikinta da cibiyarta,
cikin dabara ya fara yin sama da hannunshi yana nufar boobs d'inta,
da sauri ta zame bakinta daga nashi had'i da saurin mik'ewa ta koma jikin bango ta jingina,
idanta lumshe tana fitar da numfashi a gaggauce,
ganin yadda k'irjinta ke yin sama da k'asa ya k'ara d'imauta shi,
a hankali ya mik'e ya nufi ta hannunshi ya saka ya dafe bangon ya sanya ta tsakiyarshi,
had'i da zuba matata jajayen idanuwanshi,
cikin salo yasa k'irjinshi saman nata,
ya matse ta da jikinshi sosai da bangon yadda bazata iya kwacewa ba,
sumar kanta data zubo ta rufe mata fuska ya sanya hannunshi ya mayar da ita baya,
had'i da zubawa k'irjinta saman boobs d'inta ido,
idanshi ya runtse da k'arfi kana ya sunkuyo da kanshi saitin kunnenta,
muryarshi na sark'ewa yace " why Sanah..!?
" Me yasa kike san jefa mu cikin hakala da tab'ewa had'i da fushin Ubangiji...!?
" Meyasa baki bari muyi aure muji dad'in duniyar ma'aurata ba...!?
" Why Sanah..!?
Ya fad'a yana lasar kunnenta,
a hankali ya shiga lasar kunnenta had'i da hura mata iska cikin kunnen,
idanta ta kuma runtsewa da k'arfi k'irjinta yana up and down,
cikin salo ya gangaro da bakinshi zuwa wuyanta yana lasar wuyanta,
zuwa saman boobs d'inta, hannunshi ya sanya yana shafa bayanta zuwa cikinta da cibiyarta,
cikin k'ank'anin lokaci suka rud'e hankalinsu yabar gangar jiki da ruhinsu,
jikinsu ya d'auki rawa, hannunta ta cusa cikin k'irjinshi tana shafa kwantaccen gashin k'irjinshi,
zuwa cikinshi da cikin kwarmin cibiyarshi,
take ya fara fitar da numfashi mai sauti,
cak ya d'auke ya mayar da ita saman sofa ya kwantar da ita saman 3 sitter had'i dayi mata runfa da jikinshi,
while bakinsu na manne cikin na juna suna ta faman shan lips da harshen junansu,
ta bayanta ya zura hannunshi yana b'alle bra d'inta ya sanya hannu cikin kwarmin bayan yana shafawa had'i da yin tafiyar tsutsa a gadan bayanta,
gaba d'aya sun gama rud'ewa sun kai k'ololuwa wajen buk'atuwa da juna,
sai aikin shafa k'irjinshi take yi,
tana k'ara ruk'unk'ume shi,
sun dad'e da tafiya cikin wata duniya ta daban,
sama-sama taji ana knocking k'ofar,
knocking d'in da aka cigaba da yine da yawo da ita cikin hayyacinta,
da sauri ta fara k'ok'arin tureshi,
had'i da k'ok'arin tashi, amma ina maza bisa kanta,
dan k'irjinshi ya sanya ya tokare ta sosai yadda bazata iya tashi ba,
while yana cigaba da abinda yake yi,
a hankali ya sanya harshe yana lasar saman boobs d'inta batare daya tab'a su ko fiddo su daga cikin riga ba,
cikin kunnanshi tace " please ka barni..!
ta fad'a maganarta na sark'ewa,
" ban iyawa yace while bai bar abinda yake yi ba,
" please ka bari ban so ana knocking k'ofa..!
" ban iya bari, idan na bari ina iya mutuwa,
ganin yadda duk ilahirin jikinshi yake kerrrrma,
yana k'ok'arin rabata da kayan jikinta,
yasa gabanta muguwar fad'uwa,
tasan kwata-kwata baya cikin hayyacinshi komai yana faruwa muddin tayi sake,
ga ta kasa yin koda kwakkwaran motsi,
cikin tashin hankali ta soma yin kuka k'asa-k'asa gudun kar wanda ke knocking yaji,
ta shiga yi mishi magiya had'i da bashi hak'uri,
amma ina yadda kasan cikin kunnen kurma take magana haka Sir Aryan ya koma,
ya birkice mata ya koma tamkar mayunwacin zaki daya shekara babu abinci,
sosai ta fara kokawa dashi tana k'ok'arin kwatar kanta,
danta lura muddin tayi sake yau sai buzunta hannunshi,
gaba d'aya k'arfinta ta tattaro ta sanya hannunta da gwiwarta ta hankad'a shi baya,
ya fad'a saman carpet tana ganin ya fad'i tayi saurin mik'ewa,
jikinta na tsuma ta koma can gefe ta rakub'e had'i da had'e kanta da gwiwa,
yakai 5 minutes zaune jikinshi ya mutu murus bai iya koda motsi,
ya d'an d'auki lokaci,
" Sanah gaskiya bazan iya wannan wulak'antaciyar kuma tab'abb'iyar rayuwar ba,
muddin kina so na ki bani chance na fito na aure ki,
idan kuma baki so na ki barni please,
Allah ya sani na gaji I'm very tired,
ban iyawa, kwata-kwata bana san zina, ban k'aunar koda kusantarta ne,
amma saboda wani banzan ra'ayinki na karatu kina neman jefa rayuwarmu cikin had'ari da bala'i,
ya fad'a muryarshi na creaking,
kanta k'asa tace " yanzu dana barka da sex zaka yi dani...!?
" Ka keta man haddi..! ashe zaka iyayin Zina...!?
" Waya ja..!, duk wad'annan abubuwan waye ya ja su....!?
" Wallahi Allah ko sex nayi dake kece kika ja mana,
" maiyasa bazaki tallafi rayuwarmu ba...!?
" Maiyasa bazaki barmu muyi aure ba please...!?
A hankali ta mik'e taje gabanshi ta zauna had'i da sanya hannunta ta shafo kumatunsa,
tayi murmushi tace " na baka dama ka tura gidan mu,
ina so a d'aura auren mu cikin satin nan wannan Friday mai zuwa,
nan da six days,
ta fad'a tana murmushi,
wani irin sanyin dad'i yaji ya lullub'e shi,
ya ziyarci dukkan jikinshi da zuciyarshi,
cike da tsantsar farin ciki ya mik'e da ita a hannunshi yana zagaya office d'in da ita,
thank you sweetheart..!, thank you so much K'albi I love you moreeee,
ya fad'a yana kissing goshinta,
I love you most, ya fad'a yana kissing kumatunta,
I love you madly and deadly ya fad'a yana kissing hab'arta,
dariya tayi tace " I love you too Hub..!,
muje na aje ki gida yau zan tafi Maiduguri gobe su Hilwa suzo,
idan ta kama ma a d'aura auren a goben,
ya fad'a yana d'aukar key d'inshi,
while tana rik'e a hannunshi,
da sauri Sanah ta ido tana k'ok'arin direwa,
" dani zaka fita a haka...!?
Murmushi yayi yace " to meye na tsorata..!?
"Bakomai ni dai aje ni ka shirya tsaf,
ji fa ko bottles d'in gaban rigarka baka rufe ba,
" kina jin tsoro kar a gane kinzo kinyi man fyad'e......!
ya fad'a had'i da kashe mata ido d'aya,
baki ta turo tace " nayi me..!?
Dariya yayi had'i da direta ya sanya 'yar saman cot d'inshi,
Sanah ta b'anle mishi bottle d'inshi,
kana ya kwashe wayoyinshi da key suka fita,
a bakin k'ofa suka iske labourer zaune yana jiranshi,
da alama shine yayi knocking,
da sauri ya mik'e yace " Yallab'ai dama nazo gyaran office ne,
murmushi yayi mishi gami da cewa " no karka damu bakomai ka barshi,
har ya juya zai tafi ya juyo ya sanya hannu cikin aljihunshi ya d'auk'o bandir d'in 1k gudu biyu na 200k ya bashi,
jiki na rawa labourer ya amsa had'i da zubewa k'asa yana godiya,
basu tsaya jin abinda yake cewa ba suka wuce, suka shiga mota,
sai da suka fita daga cikin makaranta,
kana tace " I'm sorry na manta ban fad'a maka ba,
gidan Khulud zaka kaini fa,
cikin mamaki ya kalleta yace " gidan Khulud kuma...!?
"Eh..!, zanje na dubo ta ne,
" lafiya dai ko..!?
"Oh...! ashe fa baka san meya faru ba,
d'an kallanta yayi yace " meya faru..!?
Cikin sanyin jiki muryarta na rawa ta bashi labarin abinda ya faru batare data b'oye mishi komai ba,
tamkar yayi kuka shima dan yaji abun har cikin ranshi,
sosai ya tausayawa Khulud had'i da kwantarwa da Sanah hankali da bata baki,
dayake sun sake sabon mai gadi,
dan waccan tun ranar da Sir Moli ya bashi 5m ya bar gidan ya kawo mak'ocinsa ya cigaba da aikin,
lek'owa mai gadin yayi had'i da cewa " waye..!?
Cikin nutsuwa Sanah tace ita yayar matar gidance,
batare daya kuma cewa komai ba ya bud'e musu get suka shiga,
murmushi Sir Moli yayi yace " hmmm uwar san girma ba rana d'aya aka haife ku ba,
kike cewa yayarta ce,
" eh man ai na bata 1hr kaga ko ai yayarta ce,
tunda na rigata shak'ar iskar duniya,
" eh lalle ke yayace ya fad'a yana dariya lokacin da yayi parking cikin gidan,
kallanta yayi yace " na jira ki ..!?
"A'a kaima kasan Khulud bazata barni na tafi yanzu ba,
" tom Maiduguri zan tafi ni,
a'a dan Allah ba sai kaje ba, kayi musu waya sai suzu nan su same ka,
idan ka tafi wa zai rako su gidan...!?
Ta fad'a tana langwab'e kai,
" hmmm ke dai kawai kice baki san na tafi,
" eh Allah ban san ka tafi, please kayi musu waya suzo kawai,
"tom naji na fasa bari zanyi musu wayar, as you said,
idan kin gama kiyi man magana nazo d'aukeki,
" Ok tace had'i da mishi light kiss ta shafa fuskarshi tace " I love you and I will never ever hurt you Hub..!,
kiss yayi mata yace " I know,
har ya fita tana tsaye harabar gidan tana d'aga mishi hannu,
sai da ya fita kana ya nufi cikin gidan,
tun daga waje ta soma jiyo tijarar Jaddah, tana ruwan bala'i da masifa,
da sauri ta k'arasa shiga cikin gidan,
tsaye ta iske Jaddah Hanash rungume da Khulud tsaye a gabanta,
Khulud nata faman kuka, Khulud na ganin Sanah tace " ya Salam!,
innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
dan tasan Sanah dai-dai take da Jaddah,
jin salatin Khulud yasa Hanash mayar da kallanshi inda yaga tana kallo,
shi kanshi sai da yaji gabanshi ya fad'i,
da sauri Khulud ta zame jikinta daga na Hanash ta nufi Sanah ta fad'a jikinta,
" wacece..!?
abinda Sanah ta iya furtawa kenan,
" dan Allah karkiyi mata magana Jaddah ce mahaifiyar Papu Baban Hanash,
ido Hanash ya zubawa Sanah yana kallan abinda zatayi,
idanta ta runtse da k'arfi kana ta bud'e su,
ta sauke su kan Jaddah, abinda ya bawa Hanash mamaki yadda lokaci d'aya idanta ya canja kala,
" lalle yarinyar nan masifaffiyace,
ya fad'a cikin ranshi,
" hmmm munafuka ke mai 'yar uwa,
shine tsabar munafurci kika lallab'a kika kira ta,
to da tazo mezatayi min..!?
Jaddah ta fad'a tana hucin bala'i,
idanshi na kanta danya san hali,
da sauri Khulud tace " please for my sake dan Allah don't say anything,
" oho dai Jaddah tace tana mayar da kallanta ga Hanash tace " kai dakai nake nace alk'aminka baya motsi ne..!?
" Ko kuwa karanka ne bai isa tsaiko bo..!?
Ido Hanash ya zubawa Jaddah cike tsantsar bak'in ciki yake kallanta ido cikin ido,
" ka wani tsare ni da ido tunninka bazan iya magana bane, dan tsareni da wad'annan shayayyan idanun naka masu kama dana mashaya?
" Ka bani amsa juya ka auro wacce bata haihuwa data kasa haihuwa aure shekara biyu ko kuwa kai ne baka iya kwanciya da matar ba, baka yin yadda ya kamata..!?
Shi dai bayyi mata magana ba yadai kafe ta da ido tarrr cikin nata,
" bata tashi ne, ko kuwa motsi ne bata yi...!?
Ta kuma fad'a babu kunya balle kawaici da tsoran ido,
ganin baida niyyar bata amsa yasata mayar da kallanta ga Khulud tace " ke fad'a man mijikinki bashi da cikekkiyar lafiya ne, ko kuwa kwata-kwata alk'alaminsa ne baya aiki...!?
Ganin basu da niyyar bata amsa yasata zagewa tayi ta zazzaga ruwan bala'i da tijara,
san ranta kamar wacce ke shan kwaya,
takai awa d'aya tanayi musu bala'i kana ta kalli Khulud tace " banza juya mara haihuwa sai da aci a kwanta kawai marar zuci.......!
" ya isa!!, Sanah ta fad'a idanta tarr cikin na Jaddah,
" a'a please my Sanah dan Allah karki ce mata komai,
cikin zafin rai Sanah ta cigaba,
" idan kina tantamar lafiyar jikanki ne,
d'aki zaki kai shi ki duba shi ciki da waje,
ko kuma ki had'a shi da mace ki gani zata tashin ko bazata tashi ba,
bawai kizo ki tsare matarshi da tambayoyi ba,
ke wacce irin macece da zaki tsare mace matar jikanki kina tambayarta,
abinda ya shafi kwanciyar aurensu da azzakarin mijinta,
idan ni ce ke wandonsa zan cire na duba da kai na, ba sai na ba'tawa kai na lokaci wajen tambaya ba,
kin san ance gani ya kori ji,
haihuwa bata Allah bace, ni dai a iya sanina babu kasuwar da ake siyar da yara ko haihuwa bare suje su siyo,
Idan kuma akwai muje ki raka mu, mu siyo,
dan Allah idan Zohal ko Wajnah ake yiwa haka ya zakiji...!?
Tunda Sanah ta fara magana Jaddah ta kafe ta da idanta,
haka ma Hanash,
" haba ki barsu ma da abinda ya dame su ya ishe su, amma kinzo kina tayi musu ihuu aka,
cikin mamaki Jaddah tace " yanzu ki kalli tsabar kwayar ido na kice azzakari...!?
" Ke da kika ce bata tashi da motsi fa...!?
" Mu sai muce me..!?
"Tom yayi kyau Hanash daka tsaya kana kallan yarinya k'arama tana yi man tijira da rashin kunya a gaban idanka amma ka kasa d'aukar mata,
kana ta kalli Khulud tace " wallahi wallahi wallahi Allah,
na rantse miki da girman Allah idan bakiyi ciki nan da wata uku ba,
sai na aurawa Hanash mata biyu a lokaci d'aya,
cikin tsiwa Sanah tace " to ki aura mishi mana sai me ko ce miki akayi shi kad'ai ne namiji..!?
Bata ko kalli inda Sanah take ba,
" nan da wata wallahi ko tsafi kukeyi da bak'ar jab'a sai na yi mishi aure,
ta fad'a had'i da fita da sauri,
Jaddah na fita Sanah ta durk'ushe a k'asa had'i fasa rikitaccen kuka,
" na cuci ki Khulud ni ce naja miki dukkan wannan abun,
bayyi mata magana ba ya zuba mata uwar harara had'i da cifewa,
" I'm very very sorry har abada ban tab'a gajiya da baki hak'uri,
ta fad'a tana kuka, a hankali Khulud ta mik'e ta shiga cikin kitchen ta zubo mata drink mai sanyi cikin glass cup,
ta dawo ta tsuguna a gabanta had'i da dafa ta ta mik'a mata,
kai Sanah ta kawar gefe tana cigaba da kukanta,
tace " wallahi da ina da yadda zanyi danayi danna fitar dake cikin masifar matar nan,
da ace ina da hanyar da zan taimaka miki, na share miki hawayenki danayi,
da ace zai iya yiyuwa na haihu ba baki d'an danayi,
" karb'i ki sha Khulud ta mik'a mata glass cup d'in,
hannunta na rawa ta masa ta rik'e a hannunta,
yunk'urawa tayi da niyyar mik'ewa,
amma sai karaf kalaman Sanah suka shiga dawo mata,
da sauri ta koma ta kalli Sanah tace " me kika ce yanzu..!?
"Banyi magana ba, ta fad'a muryarta a shak'e,
" no abinda kika ce last yanzu,
" cewa nayi da zai yiyu dana haifa na baki d'an,
murmushi Khulud tayi had'i da gyara zamanta,
fuskarta d'auke da wani irin murmushi mai wuyar fassarawa tace " zayyiyo..!
cikin mamaki Sanah ta kalleta,
tace " kamar yaya...! ta wacce hanya..!?
" Kisha..! Khulud tace tana murmushi,
ba musu ta karb'a takai lemun bakinta ta soma sha, ajiyar zuciya Khulud ta sauk'e tare da fesar da iska mai zafi, zamanta ta gyara, tare da fuskantar Sanah cikin fargaba da taraddadin abinda ranta ya raya mata tace,
"Idan kina san ki taimake ni ki kuma rufa min asiri to kina da damar yin hakan".
cikin zak'uwa da son jin, wane abu zatayi ta fidda Ulud d'inta cikin wannan masifar rayuwar tace,
"Me zanyi miki Ulud in taimaki rayuwarki in rufa miki asirin gaya min shi yanzu zanyi?."
auren *RASHIN SANI.…!* da shi mijin ma da kanshi bazai sani ba,
cikin mamaki Sanah tace " Auren *RASHIN SANI..!* kuma.,! ta yaya da wa kuma?
Khulud tace " *HANASH.........!!!!*
cikin rashin fahimta Sanah tace " bangane abinda kike nufi ba my Ulud?
"Please ki fito a mutum sak kiyi man bayani sosai,
murmushi Khulud ta k'arayi idanta cikin na Sanah data zak'u taji abinda Khulud ke nufi,
numfashi Khulud ta kuma saukewa kana tace " *KI AURI HANASH........!!!*
MOMYN ZARAH