GADAR ZARE…

74

by @hauwaausmanjiddarh

'''GADAR ZARE!!!'''


_(IT'S ABOUT DESTINY,HYPOCRITES, BETRAYALS, LIARS)_




      ~NA~




*HAUWA A USMAN*

    _JIDDARH_

            



*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION✍🏻*



Facebook: Hauwa A Usman Jiddarh


Gmail: ***


Wattpad: HauwaAUsmanjiddarh 




*GARGAD'I*



'''MATAN AURE KAWAI, BAN YARDA 'YAN MATA KO UNDER AGES, SU KARANTA BA''' 




~DEDICATED TO~

*AISHA A BAGUDO*




*BEST FRIEND FOREVER & EVER* 

'''ZAINAB ABDULWAHAB SHAGUMBA'''

       *~(UMMU AMAN)~*







74






Cikin matsanancin kuka yace " please.... sai kuma yayi shiru, ya kasa cewa komai, 

sosai Dady ya hasala, cikin b'acin rai Dady ya daka mishi tsawa had'iwa cewa " Mannir karka kuma bari na kuma yin magana, 

bai kalli inda Dady yake ba, ya kalli Zarah cikin ido na kamar seconds 15 sannan ya duk'ar da kansa k'asa, 

ita dai Zarah shiru tayi tana kallansa batare data ce komai ba, duk ilahirin jikinta rawa yake kamar mazari, 

k'asa da kai Mannir ya k'ara,sannan cikin rawar muryar yace " nasan duk wad'an nan abubuwan da suke samu na a rayuwa yana da nasaba da abinda nayi miki ne, 

na tabbatar iftila'in da suke fad'a min, ni da iyali nasaboda ke ne Zarah, 

dan nasan babu wani abu da nayi marar kyau a rayuwata da Allah zai azabtar dani, 

azabtarwa mai tsanani face abinda nayi miki, kuma wallahi nasan kad'an na gani, ban ga komai ba, matuk'ar ban rok'ek'i yafiya ba, 

wannan ya tabbatar min da yanzu tun a duniya ake yin hisabi ba sai anje ko'ina ba (lahira), 

idan kayi abin alkhairi tun a duniya zaka gani, haka ma idan kayi sharran, 

saboda abinda ni kad'ai nayi miki, iyalai na sai had'uwa suke da iftila, 

a gaban ido na akayiwa matata da 'yata fyad'e, kuma duk suka d'auki ciki, 

Ikram ta haifi shege kamar yadda kema kika haifa,saboda kema 'yar wani ce, kuma matar wani ce, k'anwar wani ce, 

yayar wani ce, sannan mahaifiyar wani ce, 

 sannan daga k'arshe ta mutu kamar yadda na buk'ata akan ki, 

tabbas zancen Allah baya tashi dayace " duk wanda yayi ZINA da 'yar wani, sai shima anyi da 'yarsa

idan kuma bashi da 'ya ayi da matarsa, 

idan bashi da mata ayi da mahaifiyarsa, 

idan bashi da mahaifiya sai anyi da k'anwarsa, 

saboda itama wacce yayi da ita matar wani ce, 'yar wani ce, mahaifiyar wani ce, sannan k'anwar wani ce. 



Cikin rawar muryar Zainab tace " Mannir me... me.... ka...ke....nu...fi? 



Tayi maganar idanta tarrr akansa, 

murmushi yayi wanda yafi kuka ciwo, kai da ganin murmushin kasan na tsananin b'akin ciki ne, 

mai cike da tsantsar nadamar rayuwa, 

Zainab ta bud'e baki zata kuma yin magana yayi saurin cewa " please Zainab kiyi shiru, har in kai inda nake san na kai, nasan idan nakai inda k'arshen magana ta zaki fahimci abinda nake nufi, 

cikin sanyin murya Zainab tace " amma..... bai bari ta k'arasa ba ya d'aga mata hannu had'i da cewa " please Zainab yau rana ce ta jin kunya a gare ni, rana ce ta wulank'anta!, tozarta sannan ta k'ank'anta, 

da in bari naji kunyar lahira, na kuma ci gaba da tsintar abinda na shuka gwara na fad'a koda duk duniya zasu k'i ni, 

su kuma juya min baya, Zainab kiyi hak'uri nasan nayi miki laifi mai girman gaske wanda nasan da matuk'ar wuya ki yafe min, 

cikin sanyin murya yace " na aikata laifi mai girma, mai matuk'ar munin gaske. 



A tsorace Dady yace " what Mannir, me ka aikata haka? 



K'ara k'ask'antar da kansa yayi a gaban Zarah yana kuka yace " please Zarah ki dubi girman Allah ki yafe min, 

ki tuna ko Allah ma muna yi masa laifi amma ya yafe mana, 

Zarah idan baki yafe min ba, wallahi na shiga uku na rink'a ganin bala'i kala-kala kenan har k'arshen rayuwa ta, 

cikin tsawa Dady yace " wai uban me ka aikata mata da kake rok'onta yafiya? 



Da k'arfi Mannir yace " saboda NA'EEM D'ANA NE, BA D'AN NASEER BA, 

I'm his biological father, 

gaba d'aya parlorn mik'ewa sukayi tsaye amma banda Zainab data kasa motsi saboda tsananin firgici da kid'ima, 

haka ma Zarah bata iya mik'ewa ba, saboda tashin hankalin data shiga, 

cikin rawar murya Zarah tace " Dady kasan me kake cewa kuwa?



" Eh Zarah nasan me nake cewa, kuma ni ne kad'ai nasan gaskiyar al'amari, 

da sauri Zainab ta mik'e ta nufi inda yake cikin matsanancin tashin hankali tace " Mannir baka cikin hankali ka, 

wallahi baka cikin hayyaci da nutsuwarka, kwata-kwata baka san abinda kake cewa ba, 

zafin ciwon dake jikinka ya fara tab'a maka kwakwalwa, 

ya fara haukata ka,, 

a hankali yasa hannu ya zame ruk'on data yiwa rigarsa had'i da cewa " lafiya ta lau Zainab, 

babu wani zafin ciwo ko gushewar hankali a tattare dani, 

balle lalacewar kwakwalwa, 

 ki koma ki zauna yanzu zan warware miki zare da abawa, 

ya k'arasa maganar hawaye na zuboasa, 

ya bud'e baki zai kuma yin magana yaji tauuuuuuuuuu tassssssss, 

Dady ya kifa mishi gigitattun marika, wanda sai da suka saka Mannir hantsilawa, 

cikin matsanancin b'acin rai Dady ya nuna shi da hannu yace " yaushe ka fara shaye-shaye? 

da har zaka tara mu kana yi mana maganar banza, 

a cikin mu akwai sa'anka, da zaka tara mu kana yi mana zancen banza zancen wofi, 

shege d'an iska sakarai shashasha, 

hawayen dake zuba masa yasa hannu ya goge kafin yace " Dady bana shan komai, ba kuma zancen banza nake ba, 

wallahi tallahi Dady gaskiya nake fad'a muku, 

na gwammaci karb'ar kowanne irin hukunci tun a duniya, kafin na mutu na had'u mahaliccina, 

Momy da Naseer ido kawai suka zuba masa batare da sun iya cewa komai ba, 

Abban Zarah kuwa kai ya duk'ar k'asa yana sak'a abubuwa da yawa a ransa, 

gyaran murya mahaifin Abban Zarah yayi sannan yace " kowa ya koma ya zauna, 

ba musu kowa ya koma ya zaune da yake duk ya girmewa kowa a wajen nesa ba kusa ba, 

sai da kowa ya zauna sannan ya mayar da kallansa ga Mannir yace " fad'a mana ta ya akayi Na'eem ya zama d'anka, 

d'an shiru Mannir yayi kafin yace. 



" Tun Zarah na yarinya k'arama Allah ya jarrabe ni da mugun santa, 

amma so ba irin wanda kuka san ina yi mata shi ba, so irin na masoya, so irin na aure shi nake yiwa Zarah, 

na dad'e ina dakon so da tsatsan soyayyarta, wanda ban tabbatarwa kai na da santa nake da gaske ba, 

sai lokacin da Naseer ma ya fara santa, lokacin da Zainab tazo min da maganar na shiga tashin hankali iya tashin hankaki, 

amma na danne na kuma b'oye ainahin abinda yake rai na game da ita, 

dan gudun abinda zaije ya dawo, nayi iya yina dan ganin na cire ta a raina saboda nasaba mai k'arfi dake tsakaninta da Zainab,

da farko Zainab k'anwar mahaifiyar Zarah ce uwa d'aya uba d'aya, 

kuma mahaifiyar Zarah ita ta rik'e ta, Zainab kamar 'ya take a wajen Maman Zarah, 

na biyu Zainab ita ta rik'i Zarah ta shayar da ita tare da 'ya ta, 

haka ma Zarah 'ya ce a wajen Zainab, 

 amma hakan baiyuyu ba, na kasa cire ta a raina, 

ganin babu ta yadda za'ayi aure yayi tsakani na da Zarah yasa shaid'an da zuciya suka fara k'issima min abubuwa da dama akanta.



Abinda na fara ainawa a raina shine matuk'ar bazan auri Zarah ba to kowaye zai aure ta bazai tab'a samuta cikekkiyar budurwa ba, 

dan ni nafi kowa cancanta dana amshi budurcinta, tun daga ranar danayi wannan tunanin zuciya ta da shaid'an ya fara kwad'aita min ita, 

suna fito min da zallar kyau daga na jikinta harta fuskarta, 

musamman ma surar jikinta, take idanuwa na suka rufe ruf, na daina ganin kowacce mace a matsayin mace sai Zarah, 

naji babu abinda nake so sai na kasancewa da ita, babban burina a lokacin bai wuce na kwanta da ita ba (sex),, 

lokuta da dama idan na dawo daga office saboda Zarah ta rungume ni nake tsayawa daga bakin k'ofa na bud'e musu hannu ita da Ikram, 

dan idan Zarah ta rungume ni wani irin mugun shocking nake ji a duk ilahirin jikina, 

ina jin shauk'i na shigata ta ko'ina, ta kowanne b'angare na jikina, 

idan ta rungume ni, take nake mantawa da kowa da komai ciki kuwa har da ni kai na, 

sai inji ina san na d'auki lokaci mai tsawo rungume da ita a k'irji na, 

sosai wutar sha'awar Zarah taci gaba da ruruwa a jikina shaid'an na k'ara ingiza ni, 

har nakai limit d'in da bazan iya hak'uri ba, dan har na fara loosing control a kanta lokuta da dama.



Dan haka na fara k'ok'arin neman hanyar da zan cimma burina, 

amma na rasa saboda nasan yadda Zainab ke tsananin kula da yaranta da kuma tarbiyyar su, 

tana hana kanta bacci sosai dan a dare sai ta lek'a su wajen sau uku, 

hakan ya sani k'irk'irar tafiyar k'arya zuwa Paris, 

a kid'ime Zainab ta d'ago kai ta kalle shi, 

Mannir yace " eh Zainab maganar tafiya ta Paris k'arya ne babu inda naje, 

ina nan garin kano zaune a d'aya daga cikin gidaje na, 

cikin rawar murya tace " video call d'in da muke yi fa? 



Shiru yayi na wani lokaci kafin yace " shima k'arya ne Zainab, 

wallpaper ne, nake sawa idan zamuyi video call sai nayi editing, 

shine zaku ga kamar ina Paris d'in, ranar da kuka raka ni Airport ma a nan na barku na bi ta k'ofar baya na fita, 

ina ganin ku tsaye, kafin ku dawo gidan nayi sauri na dawo na shiga gidan ta k'ofar baya shima dan kar a ganni cikin sa'a kuwa har na shiga na fito babu wanda ya ganni, 

duk wani drinks da fruits da ruwan sha nabi duk nayi musu allurar bacci, 

dan san idan ba'a sha wani ba dole za'a sha wani, 

shima kamar yadda na zata hakance ta kasance dan dana dawo gidan da dare ta b'arauniyar hanya iskewa nayi duk kunyi bacci a parlor, 

a hankali nasa hannu na d'auki Zarah nakai ta BQ, 

d'an shiru yayi na wani lokaci kafin ya sauke ajiyar zuciya.




Ya k'ara sakin rikitaccen kuka, cikin kukan yace " a ranar ne komai ya faru, 

a ranar ne na cirewa Zarah budurcinta, a ranar na kasance tun daga dare har asuba cike da tsantsar farin ciki na cikar buri na, 

da naga irin ciwon dana ji mata nayi muguwar tsorata, amma sai na daure dayake har lokacin maganin baccin bai sake ta ba, 

sai nayi amfani da wannan damar na gasa ta sosai da ruwan zafi, 

hakan yasa ta samu sauk'i, na mayar mata da kayanta jikinta, kamar yadda suke sannan na mayar da ita cikin gidan ni kuma nabar gidan, 

tun daga wannan rana kullum da Zarah nake kwana a BQ sai asuba nake mayar daita cikin gida, 

tun daga lokacin na daina jin dad'in kowaccen mace sai ita, 

ashe duk abinda ke faruwa akan idon Dauda mai gadi, kuma ashe ya kudiri niyyar ramawa Zarah, 

sosai nake samun nutsuwa da gamsuwa da ita, na rink'a jin kamar da a baya ba sex nake ba, 

sai yanzu ne nake yin sex, ina cikin wannan hali ne Dady ka kira ni ka sanar da ni maganar auren ta da Naseer,, 

iya tashin hankali da kukan bak'in ciki da takaici kam a lokacin nayi su, kamar rai na zai fita, 

haka na dawo na daure aka saka ranar bikin su, daga nan sai maganar ciki, 

inda na rink'a neman hanyar da zanbi na kawar da Zarah ko Naseer dan ta haka ne kad'ai asiri na zai rufo, 

dan nasan muddin Zarah ta haifi abinda ke cikinta na kad'e daga ni har buzu na, 

ana cikin haka sai naji Zainab tace ta tab'a kama su suna hot romance da wannan na fakaice, 

nima na dage akan shine yayiwa Zarah ciki, data haifi yaron naga yana da cindo da mark sai hankali na ya kuma tashi sosai, 

dan nasan asiri na ya tonu ya gama, sai kuma nayi wani tunanin, 

dan haka sai na cusawa Zainab tsananin k'iyayyar Naseer a ranta ta hanyar zuga ta akan shi yayiwa Zarah ciki, shine wanda ya b'ata mata tarbiyyar 'yarta, wanda nasan halin Naseer da bak'ar zuciya bazai tab'a d'aukar rai ni ba, 

da wannan nayi amfani na kawar da zargin mutane daga kai na. 



Ranar da aka d'aura auren Naseer da Zarah, wallahi ji nayi dama ai tashi duniya ranar kowa ya huta, 

haka naje d'ayan gidan da nake zama nayi ta hauka ina fashe-fashen glasses, 

sannan duk da Zarah tayi aure ban kyale taba ban hak'ura da ita ba, 

sai da nabita gidan Dady, ranar naci sa'a Naseer baya d'akin na shiga, 

na kashe duk room light, na fara hot romance da ita wanda ita a tunaninta kai ne Naseer, 

ta saki jiki sosai da ni dan ta d'auka mijinta ne, tunda a cikin duhu ne, hakan yasa bata gane ni ba ne,, 

Ina gaf da shigarta hannunta ya fad'a kan bed side lamp aiko haske ya gauraye d'akin, 

nayi saurin kawar da fuskarta ban bari ta ganni ba, na bar d'akin. 



Da Zarah ta tashi haihuwa sai Allah ya bata abinda nafi k'aunar samu a duniya sama da komai, 

wato d'a Namiji dan Allah ya sani ina matuk'ar san na haifi d'a namiji, 

amma Allah bai bani ba, tun daga ranar dana d'ora ido na akan abinda Zarah ta haifa sai Allah ya d'ora min matsanancin so da k'aunar sa, 

naji akansa babu abinda bazan iyayi ba, sosai na rink'a jinsa a raina da duk wata gaba dake jiki na, 

naji babu abinda nake so a duniya kamar kasancewa tare da yaro na, 

har gidan su Dady kawai nake zuwa dan na ganshi, 

dan haka na fara tunanin......... ya d'anyi jimmmm had'i da sauke nannauyan ajiyar zuciya. 



Sannan yaci gaba " na fara tunanin kashe Naseer ko Zarah, 

amma har Zarah ta mutu sannan Naseer ya bar k'asar ban samu na cimma buri na, 

lokacin da suka dawo naga yadda Na'eem ya koma sai naji sanshi ya k'aru a raina, 

ina shirin d'aukar mataki

Allah ya fara jarabta ta, 

ya k'arasa maganar cikin rikitaccen kuka kamar ransa zai fita.



Wannan bak'in 'kudirin nawa, da mummunar manufa ta akan Zarah yasa ni cewa a raba musu bedroom ita da Ikram, 

bayan tun da suka taso tare komai nasu d'aya ne,, 

cikin rikitaccen kuka ya k'ara zubewa a gaban Zarah yace " ki dubi girman Allah, da dajarar Annabi ki yafe min, 

nasan ban cancanci yafiya daga gare ki ba amma ki dubi..... 

bai k'asara ba yaji tauuuuu an kifa mishi mari, yana juyawa yaga Zainab tana huci kamar macijiya, 

ya bud'e baki zayyi magana ta k'ara kifa masa wani marin, 

sannan taci kwalar rigarsa da duka hanuwanta biyu 

ta zaro idanta waje da suka gama yin ja tace,, 

tsinannan Allah, munafuki fasik'i, macuci, ka cuce ni ka cuci kanka da rayuwarka, 

kayi asarar duniya da lahira, 

ashe kai ne bak'in mugun dakayiwa Zarah ciki, 

amma dan tsabar rashin imani da tsoran Allah ka zage iya k'arfin ka kayi mata dukan mutuwa har da karaya biyu kayi mata, 

dayake kai cikekken tsinanne ne, 

wallahi da Allah da mala'iku suna gajiya da tsinewa mutum kai ne mutum na farko dazasu fara gajiya da la'antarsa, 

Mannir kasa na tsani kaina da rayuwa ta, kasa ina jin kunyar kai na, 

yauce rana ta farko da uwa tayi murna da farin cikin mutuwar 'yarta ta cikinta, 

Allah ya taimaki Ikram da bata rayu taji kuma taga wannan mummunan abin kunyar ba. 



" Allah ya rufa mata asiri, dan sai ta gwamci mutuwarta da ganin wannan mummunar ranar a rayuwarta, 

ranar da zata ga ubanta mahaifi yayiwa k'anwarta da suka sha nono da ita ciki, 

mahaifiyarta da mahaifiyar ta suka sha nono d'aya, 

yarinyar datake tamkar 'ya a wajenka, wallahi tunda kayiwa Zarah haka zaka iya kusantar 'yarka ta cikinka, 

wama ya sani ko itama ka keta mata haddin tunda kai d'an akuya ne, 

ta k'arasa maganar cikin rikitaccen kuka, hannuwanta tasa ta fara dukan k'irjinsa da iya k'arfinta, 

Mannir bai hana ta ba, illa kallanta daya tsaya yana yi hawaye na zubo masa, 

sosai take dukansa tana hankad'a shi, tana cewa " ban tab'a dana sanin rayuwa ta da zuwa na duniya ba sai yau, 

yau nayi nadamar gaba d'aya rayuwa ta, nayi dana sanin saninka a rayuwa ta, 

balle har yakai dana had'a jini dakai, na kuma godewa Allah da yasa babbar alak'ar dake tsakanin mu ta yanke ta hanyar mutuwar Ikram, 

baice mata komai ba, 

a hankali cikin mutuwar jiki ya rik'e hannuwansa da take dukan k'irjinsa, 

da sauri ta kwace hannunta daga nasa ta nuna sa da yatsa tace " daga yau anan take a wannan rana a dai-dai wannan lokacin duk wata alak'a dake tsakani na da kai ta yanke har abada, 

daga nan har k'arshen rayuwa ta bana fatan ko burin sake ganinka a rayuwa,

a hankali ya sake ta ya kuma komawa gaban Zarah ya zube ya k'ara fashewa da matsanancin kuka yace " please Zarah ki yaf........ 



Ganin yadda duk jikinta yake kerrrrma da tsananin rawa yasa shi kasa k'arasawa abinda yayi niyyar fad'a, 

a matuk'ar tsorace take kallan sa dan ganin shi take tamkar wani moster, 

a razane cike da tsoro take kallansa, 

jikinta sai rawa yake yana kerrrma gami da tsuma, kamar wacce taga mutuwarta, 

cikin sanyin jiki Mannir ya matso kusa da Zarah had'i da mik'a hannu zai tab'a ta,, 

a tsorace tayi saurin ja da baya, hannu ya mik'a zai kai jikinta, tana ganin haka saki rikitacciyar k'ara, 

Naseer da tunda Mannir ya fara magana kwakwalsa tayi hook ya kasa cewa komai, 

koda motsi ma kasawa yayi mamaki, tsoro da fargaba sun gama cika shi, 

gaba d'aya baya cikin hayyacisa da nutsuwarsa, 

jin k'arar Zarah ne yasa shi dawowa cikin hayyacinsa, 

da sauri ya mik'e yaje inda Zarah ke zaune duk ta k'udundune jikinta saboda tsoro, 

Naseer ya tsungunna a gabanta had'i da rungume ta jikinsa, 

da sauri ta fad'a jikinsa had'i da k'ank'ame shi sosai, jikinta sai kerrrrma yake yana b'ari, 

ga wani uban gumi dake zubo mata, gaba d'aya ta zare, kallo d'aya zakayi mata kasan bata cikin hankalinta. 



A hankali Mannir ya kuma mik'a hannu zai tab'a ta, aiko Nasser ya zabura............ 






Don't forgot to vote & comment, follow 






MOMYN ZARAH