EDD
by @realsmasher
đź’ đź’ đź’ đź’ đź’
©®AS-2023.
*♡DAUƊAR GORA¸.•💥*
(Cɪᴋɪ ᴋᴀ sʜᴀ ᴛᴀ)
Ná´€
*HAWWA__B__KUMO.*
(Rᴇᴀʟ Sᴍᴀꜱʜᴇʀ).💕
*WATTPAD:REAL-SMASHER.*
*AREWABOOKS:REALSMASHER.*
••••••••••
*It's all about:#Vesicovarginalfistula,#VVF,#Desined,#Stepmom,#Family-Saga,#Rural-Urban,#Nigerians,#Halfcast,#Arabian-Fulbe,#Arrogance,#Hated & #Romance..*
20
#EDD!
Kallon Ummii kawai take zuciyarta na mata ƙaiƙayi,Allah ya sani har ranta take jin ba ta son tafiyar nata,sai dai ba ta da bakin cewa komai,kasancewar jirgin dare Ummii za ta bi,Iyami kuma za ta kwana nan gidan Aya,sai washe gari sannan ta kama hanyar komawa gida,yinin ranar haka nan Aya taita hidima da su har yamma suna ta hira da Tayyibah akan tafiyar ta Ummii,kou da Amado ya dawo daga aiki ya tarar da su a gidan,bai nuna damuwa ba tunda sun saba zuwa,ya tsaya tare da gaishe da su Iyami respectfully kafin ya wuce ɗakinshi,Aya ta tashi tabishi tai masa sannu da zuwa ya amsa,kasancewar yau ya ɗan so yin dare yasa a hankali tace "a kawo abincin yanzu kou sai ka dawo daga masjeed?" Yana ɗan yamutsa sumar kanshi mara yawa yace "no! Zan yi sallah first sai na ci" tace "okay!" Tare da gyaɗa kanta,har ta juya za ta fita ta dawo tana cewa "ohh! Na manta ban sanar maka zuwansu Ummii ba" ya gyaɗa kansa yana rage kayan jikinshi yace "no worries! Ai na gansu mun gaisa yanzu kafin na shigo" tace "ehh! Hakane,amma Iyami za ta kwana nan ne tare da mu,gobe in sha Allah tace za ta wuce" juyowa yayi yana kallonta a gajiye yace "and then?" Tace "a'a babu komai,dama na manta ne bamu yi maganar tafiyar Ummii ba" wani irin kallo yai mata yace "wani gurin za taje?" Aya tace "ehh! Yau da dare jirginsu zai ɗaga" yace "as in? Zuwa ina?" Jikinta a sanyaye tace "za ta koma Saudiyya ne" kallonta ya dunga yi har na tsawon minti uku,kafin yace "Saudiyya?" Ta gyaɗa mashi kai tana ta ƙoƙarin mayar da hawayen da suke son saukowa fuskarta,kasa cewa komai Amado yayi,kawai sai ya wuce ya nufi bathroom,a hankali Aya ta ɗago kanta tare da sa hannu ta share hawaye sannan ta juya ta fita ɗakin. Har Amado yai wanka ya fito ya shirya cikin ƙananan kaya ya fita masallaci sallar ishaa maganar da Aya tayi bai bar yi masa yawo a cikin kai da zuciya ba,sam bai ga dalili kou amfanin ace Ummii za ta koma Saudiyya da zama ba,tou amma shi meye nashi? Tunda har mahaifiyarta ta amince mata,ina ruwansa da saka kanshi cikin matsalar da bai shafeshi ba? Tou amma kuma ai ya ga kamar Aya ba ta son tafiyar nata,wani zuciyar yace "dan ba ta so kou ta nuna maka haka,mene ne ribar ka idan ka shiga tunda ba fasawa za tayi ba?" Taɓe baki yayi tare da shigewa masjeed,bayan an idar da sallah ya taso tare da nufo gida,sai dai wannan karon bai tarar da su a parlour ba,kai tsaye shima ya wuce ɗakinsa cikin halin kou in kula da wancan maganar,yana shiga ya samu guri gefen katifarsa yai zamansa yana wani tunanin daban akan matsalar gidansu,Aya da taji shigowarsa ta fito bedroom inda suke tare da su Iyami bayan sun idar da sallah,kitchen ta isa ta haɗa masa abinci sannan ta ɗauko tana tafiya a hankali ta nufi ɗakinsa tare da yin knocking,yana jinta amma kou tari bai yi niyyar yi wanda zaisa ta fahimci kou yana wani uzurin ne shi yasa bai amsa ta ba,da yake ta saba da wasu cikin halayensa dan kanta ta buɗe a hankali tare da yin sallama ta shiga,bai ɗago ba har ta isa gabansa ta ajiye tray ɗin sannan ta miƙe tana sakin numfashi me kama da haki tace "kana son wani abu kuma?" Ya ɗago idanunsa ya kalleta,ba tare da ya ce komai ba ya kalli warmers ɗin abincin,kamar bazai buɗe baki yai magana ba,cike da izza yace "ina son tea" gyaɗa mashi kai tayi sannan ta juya ta fita,ruwan tea ɗin ta ɗaura mashi tasa kayan ƙamshi sannan ta haɗawa su Iyami abinci ta fito ta nufi ɗakinta,tana yin sallama Iyami ta tashi ta tareta tana cewa "sannu Shalele.. Allah ya raba ku lafiya,kina ta ƙoƙari da mu tunda muka zo" sanyayyan murmushi tayi kafin tace "Iyami bari na kai masa tea na dawo,ku fara cin abincin kada ku jirani" Iyami tace "tou ki samu ki ci abincin mana tukun" Aya tai mata murmushi cike da son ɓoye damuwarta tace "zan ci Iyami,bari na kai masa na dawo" Iyami ta gyaɗa mata kai a hankali tace "tou shi kenan" juyawa Aya tayi ta fita,Ummii ta bita da kallo cike da so da tausayinta,sai ta tuno lokacin da take ɗauke da cikinta kamar haka,mahaifinta sam bai bari tai hidima da shi kamar yanda ƴarta ke fafutuka da nata mijin,tun yamma take ta zarya tsakanin kitchen da parlour,haka kou yanzu ma tunda tai sallah take ta hidima da su da kuma mijinta,ita lokacinta duk abunda za tayi Bukar ke tayata,haka za aita tsaiguminta ana mata habaici ta shanye shi,shi kuma ana ce masa mijin tace,sai yai murmushi yace "ni mijin kafin tace ne,baza ku gane adadin soyayyar da nake ma Maryama ba,kou dan baku yi dace da miji kamar nata bane shi yasa kuke adawa? Ni ɗan zamani ne,kuma na san soyayya,duk abunda nake mata ina yi ne saboda sunnah,ina koyi da Annabin rahama (S.A.W),kuma kuce da mazajenku suje su koyo yanda ake soyayya" da irin maganganun nan yake kashe bakinsu,sai kaji shiru baza'a samu wanda zai sake cewa komai ba,ajiyar zuciya Ummii ta sauke tare da jinjina ƙoƙarin Aya da dauriyarta. Aya na fitowa kitchen ta sake nufa,nan ra tarar ruwan yai zafi sosai yana neman tafasa,tsayawa tayi gefe har ya juya,kamar baza ta sauke ba ta barshi yaita tafasa,sanin ya fi son a haɗa masa tea yana sha yana ƙona baki,idan ma yasha yaji bai masa yanda yake so ba,zai iya cewa ta koma kou ya ajiye mata abunta yace tasan yanda za tayi da shi,sai can kafin tasa karamin rariya na tatar shayi ta tace,sannan ta haɗa ta ɗauko ta nufi ɗakinsa,tana shigowa ta sameshi kishingiɗe yana operating wayarshi,tai sallama tare da ƙarasawa ta ajiye masa tea ɗin a cikin mug,tashi yayi yana kallon yanda ruwan ke tiriri ya kai hannu ya fara taɓa jikin mug ɗin kafin ya ɗauka,ita kuma Aya ta samu guri nan saman carpet ta zauna jiran ya gama ta kwashe kayan kamar yanda ta saba dare da safiya,ruwan tea ɗin na ƙona masa baki ya dunga sha a haka har ya kammala sannan tayi serving ɗinsa abinci,babu mai magana cikinsu ya kama cin abincinsa,sanda ya gama ta tattara komai ta ɗauka,za ta fita yace "idan kin gama abunda kike kizo ina son ganinki" gyaɗa mashi kai tayi tare da juyawa ta fita,sai da ta fara kai kayan kitchen sannan ta koma ɗakinta,tana shigowa Iyami ta fara yi mata sannu,tai murmushi ta ƙarasa tare da zama tana sauke ajiyar zuciya,sai sannan ta ɗebi abinci ta fara ci,dan already su Iyami su har sunci tunda ta ce kada su jirata,so they thought can gurinsa za ta ci,sai suka ga saɓanin haka,sai dai babu wanda ya tambayeta tsakanin Iyami da Ummii suka zub mata idanu kawai,tana gamawa ta kwashe kayan ta fita da su,sanin ba ɗan tayin aiki gareta ba yasa take dabara tayi wanke² tun dare,da safe kuma sai dai taji da shirya breakfast da gyaran gida,ba ita ta baro kitchen ba sai da ta wanke komai ta mayar da shi muhallinsa,tana gamawa ta dawo ɗakinta ta shiga tai wanka,sanda ta fito sai da ta gama komai har sallar shafa'i da wutr kafin tace masu za taje yana kiranta,Ummii tai mata murmushi tace "tou ni dai sai muyi sallama dake tun yanzu kou?" Aya ta girgiza mata kai tace "a'a Ummii ai zan dawo,kuma ina son zuwa nai maki rakiya airport" Ummii tai mata murmushi tace "tou shi kenan,sai ki sanar masa idan kin je,in ya barki sai muje ɗin kwa dawo daga baya" gyaɗa mata kai tayi sannan ta juya ta fita,knocking ƙofar ɗakin ta fara yi then ta tura ta shiga da ƴar siririyar muryarta tai masa sallama ya amsa,ta yi zaton wani abu yasa shi kiranta,da ta shigo ta ɗan tsaya tare da cewa "ga ni kace nazo idan na gama" bai ɗago ba haka nan fuskarshi babu fara'a kou kaɗan yace "samu guri ki zauna" kamar yanda ya buƙata ta zauna a hankali,tana wasa da yatsun hannunta tai shiru tana jiran yai magana,bai bi ta kanta ba sai da ya gama abunda yake a wayarshi kafin ya ajiye tare da miƙewa yaje ya kashe bulbs ɗin ɗakin,duhun da ta gani ya mamaye ko ina,da sauri ta ɗago kanta tana kalle²,kamar wacce bata saba da yanayin ba,haka nan tsoro ya cikata ta dunga ƙyafta idanunta har sanda ya iso gurinta,a hankali ya kai hannu ya cire hijab ɗin dake jikinta,ita kam tana ganin ikon Allah,dan batai zaton wannan al'amarin yanzu ba,kou dan su Iyami da Ummiinta da suke gidan,har ya gama budurinshi ya koma gefe ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya bai ce komai ba,ta laluba a hankali tare da janyo rigarta kafin ta sauka tare da wucewa bathroom ta gyara jikinta,tana wanka tana sauke ajiyar zuciya tare da kallon cikinta dake motsawa lokaci²,har ta gama ta fito ta tsaya tare da tsane gashin kanta sannan ta ɗauki hijab ɗinta za ta fita,sai sannan ya ɗago kansa a hankali yace "ina za kije?" Juyowa tayi tace "zan koma gurinsu ne" yana mayar da kanshi saman pillow yace "kada ki sake ki bar ɗakin nan" ba ta da zaɓi bayan tabi umarninsa,jikinta a sanyaye ta dawo tare da komawa ta kwanta tayi shiru tana tunani har bayan wani lokaci,ɗan juyowa tayi tana kallon gurin da yake kwance,cikin sanyin lafazi tace "Mmmm! Yaya!" Da sauri ya buɗe ido sosai yana kallonta,sai tai shiru kuma ta rasa me za tace,da wani murya yace "ina jinki" cikin wani trembling voice tace "dan Allah ina son zuwa raka Ummii" kai tsaye muryarshi babu alamun wasa yace "zuwa ina?" A hankali tace "airport!" Wani irin kallo ya dunga yiwa inuwarta kafin ya miƙe,ba tare da yace komai ba yai wucewarshi bathroom,sanda yayo wankan tsarki ya dawo,ya canja kayansa zuwa na bacci yai kwanciyarsa tare da juya mata baya ya kulle idanunsa,Aya da batai zuciya ba cikin sanyin jiki ta sake cewa "dan Allah.." Bai juyo ba yace "ki yi bacci" kamar za tayi kuka tace "ai idan na kwanta lokacin tafiyarta yai bazan sani ba" da wani kakkausar murya kamar suna faɗa kou kuma dama yana jin haushinta yace "and so fucking what? Malama kin dameni da maganar tafiyar nan,ta tafi mana sai me? Ni mene ne nawa a ciki,zan hanata yin abunda zuciyarta ke so ne?" Wani irin kuka taji yana neman ƙwace mata ta daure muryarta na rawa alamun kukan yana daf da zuwa tace "amma bamu yi sallama ba ai" so pissed off yace "will u please shut ur mouth up? Nace baza kije ba,kou akwai wanda ya isa sawa na barki?" Da sauri ta rufe bakinta hawaye suna ɓallewa idanunta ta fashe da wani irin kuka me cin rai,yaja tsaki ba tare da ya juyo ba yace "ki mutu!" Sosai taci kukanta ita ɗaya,duk tayi shiru tana tuna maganganunsa sai taji hawaye sun sake ɓallewa idanunta,tsayin lokaci ta ɗauka kafin wahalallen bacci ya sace ta,duk yanda taso kada tai bacci saboda tayi sallama da Ummiinta,amma ina ciwon da kanta yaita yi saboda kuka da kuma gajiyar da ya tara mata,banda na aikin da taita faman yi,nan suka taru suka danneta,sam ta kasa hana kanta faruwar hakan. Around 1am Ummii suka fito parlour ita da Iyami,ƙasa² Iyami take cewa "Aya kam ina jin ta yi bacci can gurin mijinta,gashi kuma baku yi sallama ba har lokacin tafiyar naki ya yi" Ummii tai ɗan murmushi tana kallon hanyar ɗakin Amado tace "babu komai Iyami,ina ga gajiya tasa ta yin bacci" Iyami tace "ai fa ta yi fama kam ta sha aikace²,Allah dai ya basu zaman lafiya" Ummii tace "ameen.. Iyami bari na wuce,idan ta tashi da safe kya sanar mata na tafi,tayi min addu'ah na sauka lafiya" Iyami ta gyaɗa mata kai a hankali tace "tou! Kou dai aiwa shi Ahmadin magana ne ya taso ta?" Ummii tai saurin girgiza mata kai tace "a'a Iyami gara ki barta,yanzu idan ta fito kin san halin rigimarta,gara ace sai bayan na tafi sannan ta samu labarin,na san kukan da za tayi bazai kai wanda idan ace a gabanta zan tafi ba" Iyami ta sake gyaɗa kanta tace "tou shi kenan.. Allah ya tsare Maryama,ubangiji ya kaiku lafiya,dan Allah ki kula kin ji,ki kama mutuncin kanki.." Ummii tace "in sha Allah Iyami,na gode sosai Allah ya saka da alkhairi.. Yanda zan barku lafiya,Allah yasa na dawo na sameku lafiya.." Rungume Ummii Iyami tayi tana goge ƴan ƙwallar data taru gefen idanunta tace "dan Allah ki dunga bugo waya kina jin halin da muke ciki ni da ƴarki" Ummii tace "in sha Allah Iyami" horn ɗin da suka jiyo,yasa ta saurin ɗaukan jakarta ta rataya sannan ta ɗauki ta kayanta tana cewa "Iyami me motar ya iso" Iyami tace "tou muje na rakaki bakin ƙofa na dawo" tare suka fito da Iyami ta rakota har bakin get inda me motar da zai kai Ummii airport yake tsaye yana jiranta da yin horn,yana ganin fitowarta ya sauko motar tare da karɓar kayanta yasa a booth,Ummii kuma ta buɗe gaba ta shiga,bayan ya rufe sannan ya zagaya ya shiga shima ya tada motar,Iyami na tsaye get ɗin gidan su Ummii kuma suna shirin tafiya sai ga Tayyibah da Usman sun fito,da ɗan gudunta Tayyibah ta isa gaban motar tana faɗin "Ummii! Allah ya tsare ya sauke ku lafiya" murmushin ƙarfin hali Ummii tayi idanunta akan get ɗin gidan zuciyarta na mata babu daɗi saboda rashin ganin Aya ba tare da sunyi sallama ba,ta amsa mata tana cewa "kuyi haƙuri mun tasheku daga bacci" Tayyibah tace "laaa! Ummii babu komai wallahi,ai gashi har na fito mun yi sallama" sai ta miƙawa Ummii wani roba me ɗan girma tace "Ummii ga shi babu yawa,Allah ya sauke ku lafiya" kallon robar dake cikin leda Ummii tayi kafin ta ɗago kanta ta kalli Tayyibah tace "na gode sosai Tayyibah,Allah yayi albarka,ya kawo babban rabo" Tayyibah tai dariya sannan ta ɗan koma baya tana ɗagawa Ummii hannu,Usman yai mata addu'ar sauka lafiya tare da bata ƴan kuɗi yace ta sha ruwa a hanya,ita kuma tana tai masu godiya har me motar yaja suka tafi,sanda suka dena gano motarsu kafin su koma ciki,Usman ya rufe get tare da yiwa Iyami sai da safe,Tayyibah ta kalli yanda jikin Iyami yai sanyi lokaci ɗaya,kafin a hankali ta juya tabi windows ɗinsu Aya da kallo kamar yanda taga Iyami na kallon gurin,kou da ba'a faɗa mata ba zuciyarta ta sanar mata Iyami bata ji daɗi ba,haka nan itama sai take tuhumar kanta dalilin rashin ganin Aya da Oga Ahmad,kou dai ace basu raka Ummii airport ba a matsayinta na surukarshi,amma ai ya kamata ace sun fito kou iya bakin get ma suga tafiyarta,wannan tunanin sai yasa ta saka alamar zargi cikin abunda ya faru,da ƙyar ta iya yiwa Iyami sai da safe kafin tabi bayan Usman zuwa ɓangarensu,Iyami ma haka nan taja jikinta ta koma ciki ta rufe ta isa ɗakin Aya,sai dai tuda ta dawo ta kasa bacci saboda tunanin dalilin rashin fitowar Aya da Amado,tabbas ta san ba nauyin bacci ne da Aya ba kou da can,sai dai in akwai abunda yake faruwa ne kawai,tunani iri² haka yaita zuwa zuciyarta sai dai ba ta son ta yanke hukunci,dole yasa ta kawar da tunanin ta shiga banɗaki tai alwala tazo tayi nafila daga nan ta koma saman gadon ta kwanta har bacci ya ɗauketa. Kiran assalatu ya tayar da Aya,ta miƙe a ɗan hanzarce kamar kuma wanda ke jin tsoron rasa wani abu,cikin ɗan sauri ta sauke ƙafarta ƙasa kafin ta tashi ta fita ɗakin tana faɗin "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.." Yana jin sanda ta rufe ƙofar ɗakin ya miƙe zaune yana jan siririn tsaki,komai da ya faru tun daga fitowar su Ummii,maganar da suka yi da Iyami,har zuwa fitarsu daga gidan,da horn ɗin da me taxi da yazo ɗaukar Ummii yayi ta yi,fitowar su Tayyibah da maganganunsu duk yana ji,kuma har sauka yayi daga saman katifar yaje ya tsaya bakin window yana kallonsu,duk akan idanunsa da kunnensa komai ya faru,sai dai tun lokacin da yaji maganar tafiyar,haka nan ya dunga jin zuciyarshi tana zafi,kuma yake jin haushin Ummii akan tafiyar da za tayi,though bai ga dalilin kanshi na jin haushin ba,amma kuma sai zuciyarshi ta dunga saƙa masa kar ya bar Aya suyi sallama da mahaifiyarta,saboda wannan ne hanyar da kamar zai amfani da power ɗinshi a matsayin mijinta ya ƙuntatawa Ummii. Aya na fitowa ta shiga ɗakinta,sai ta tsaya turus tana kallon ɗakin da Iyami dake ƙoƙarin tada sallah,hawaye suna ciccikowa idanunta jikinta na sakewa cikin wani murya me rauni tace "Iyami ina Ummiina? Kada kice min ta tafi banyi sallama da ita ba?" Juyowa Iyami da bata riga ta tada sallah ba tayi tana gyaɗa mata kai tace "ta tafi tuni Aya.. Sai dai kiyi mata fatan sauka lafiya" wani irin kuka ne ya ƙwace mata tace "amma Iyami me yasa baki tasheni ba?" Iyami ta taho tare da riƙo hannunta ta zaunar da ita gefen gado tace "kiyi haƙuri Aya,Ummiinki ita ta hana na buga maku ƙofa,naje dai na rakata bakin ƙofar gida,har su Tayyibah ma suka fito sukai mata sallama" kallon Iyami ta ɗago tana yi hawaye wasu na korar wasu a fuskarta tace "shi ya fito yai mata sallama ne?" Iyami ta girgiza mata kai a hankali tana jin kamar da sannunshi yayi haka,Aya ta dunga kallon Iyami ta kasa dena kuka,can ta gyaɗa kanta tare da miƙewa ta nufi banɗaki,har tai alwala tazo ta tada sallah kuka take,zuciyarta na mata wani irin ciwo saboda baƙin ciki,sai dai kou da take yarinya amma ai ta san me take,kuma tana da hankalin da za ta gane fari da baƙi,tas ta fahimci inda ya dosa,bayan ta idar tai azkar ɗinta,ta miƙe tana dafe cikinta ta haura saman gadonta tare da kwanciya tayi shiru sai ajiyar zuciya take saukewa,Iyami ma data idar tazo ta ɗan kwanta kaɗan tana bata haƙuri,sai ta lumshe idanunta taƙi cewa komai,ganin kamar ta yi bacci yasa Iyami yin shiru nan bacci ya ɗauketa,har gari ya gama wayewa Aya bata iya komawa bacci ba,duk sanda ta tuno Ummiinta ta tafi basu yi sallama ba,sai hawaye sun gangaro idanunta. Can guraren 8am saura ya gama shirin tafiya aiki ya fito daga ɗakinsa,sai dai abun da ya bashi mamaki shi ne,yanda yaji gidan shiru babu alamun motsinta,ya gama kallon parlon kafin ya wuce hanyar kitchen,yau kam kou ƙofar ma a rufe yake,ya buɗe tare da shiga ciki,duk da shigowarsa bai fi a ƙirga ba,amma ya karanci komai yana zaune ne a muhallinsa,babu alamar an taɓa wani abu kou an ɗaura,tas ya ƙaraci observation ɗinsa ya fito tare da rufewa,ƙofar ɗakinta ya isa yai knocking a hankali,tana jinsa itama ta shareshi,saboda yanda ta sha alwashin komai zai faru sai ta nuna masa kuskurensa,tunda sukai aure dai² da sau ɗaya bata taɓa ɗaga kai tai masa kou da kallon banza ba duk tsayin zamansu,shi ne har kuma har zai samu damar taka ta,idan yana taƙamar haɗashi akai da ita,ai itama ba ita tace tana sonsa ba,da zai dunga mata abubuwa kamar basu haɗa jini ba,ita fa sai yanzu ne ma da zama ya haɗa su guri ɗaya ta fara gane halayenshi,da can lokacin da yake mata kirki ne take masa kallon mutumin arziki,ashe mugun halinsa a ɓoye suke,ai kuwa ya yi da ita dan itama side ɗinta ɗaya ya sani na,shi ne gefen haƙurinta da kawaici,aita mata abu tana shanyewa,ba ta kou kallon mutane bare ta nuna masu ta san me suke nufi,bai ga her other side ba idan tai fushi. Tana jinsa haka tai banza da shi,Iyami data farka ta kai hannu tana taɓata da kiran sunanta "Shalele! Tashi maza kije mijinki na kira" sake kulle idanunta tayi tace "Iyami ba na jin daɗi ki barni dan Allah" Iyami tace "a'a tashi kije sai ki sanar masa,ai zai maki uzuri idan kuma za kuje asibiti nema tou" ba dan taso ba ta tashi,lokacin shi kuma yana sake knocking da kiranta "Aya please!" Buɗe ƙofar tai fuskarta ɗaure tace "ga ni!" Ya dunga kallon yanda fuskarta yai ja idanunta a kumbure,lokaci ɗaya kamar bai san me ya faru ba yace "breakfast fa?" Janyo ƙofar tayi tana wucewa parlour tace "ban yi ba" ya dunga kallonta kafin ya biyo bayanta,ya tsaya da wani irin fuska yace "kamar ya baki yi ba?" Tace "ehh! Ba na jin daɗi ne" tsaiwa yai ya kasa ce mata komai,ita kuma ta ƙi kallonshi sam,gyaɗa kansa yai kafin a gajarce yace "okay!" Daga haka ya juya ba tare da ya sake ce mata komai ba,ya koma ya ɗauko jakarshi ya fito,bai kalli inda take ba yace "na wuce office" ta sake ɗauke kanta kamar bata ji ba tana dafe ƙasan mararta dake ɗan mata ciwo tana yatsina fuska,har ya kai bakin ƙofa ƙala bata ce masa ba,ya buɗe ya fita yana jin wani irin ɓacin rai na cika masa zuciya,taɓe baki Aya tayi bayan ta tabbatar ya wuce kafin ta tashi da ɗan sauri ta shiga kitchen,abunda za ta iya girkawa Iyami ta duba ta ɗaura,har ga Allah kou da tace bata jin daɗi ba ƙarya take ba saboda kukan da ta kwana yi kuma ta sake tashi da shi,amma ganin yanda ya nuna mata halin ko in kula nan ya ƙara tunzurota,tai ƙwafa da faɗin "za ka san ka yi da me yi" da ƙyar ta daure tai aikace²n da za ta iya,sannan ta nemi guri ta kwanta,kou abincin bata iya ci ba haka taita bin Iyami da kallo,Iyami kam tana gama yin breakfast ta fara shirin tafiya,10am ta kammala kayanta guri ɗaya ta fito tana cewa "Tou! Shalele ni zan wuce" Aya ta buɗe idanunta da har sannan basu gama komawa dai² ba,da sanyayyan murya tace "Iyami ki bari sai anjima dan Allah" Iyami ta girgiza mata kai tace "a'a Shalele barni dai na tafi yanzun,kinga ni kaɗai ce kuma zan koma na kama aikin gida nima,sai dai nace sai kun zo ɗin" Aya dake jin kuka yana taho mata tace "shi kenan! Allah ya tsare hanya ya saukeki lafiya" Iyami ta amsa sannan ta ɗauki buhun kayanta,a hankali Aya ta tashi ta ɗauki hijab ɗinta tace "bari na rakaki na dawo" Iyami bata hanata ba ta amsa mata,suna shirin fitowa sai ga Tayyibah da uban warmers ɗinta ta yowa Iyami girki,tana fiddo idanuwanta take cewa "Iyami ba dai har tafiya za kiyi ba da safen nan?" Iyami tai mata murmushi tace "in sha Allahu yau sai kwanan gida,kuma yanzu ba da ɓata lokaci ba" Tayyibah tace "Iyami ai na yi zaton kin zo kenan fa sai Sister ta haihu" Iyami ta girgiza mata kai tace "a'ahh! Na dai yi magana da ita,idan mijinta ya barta ta dawo gida ta haihu" kallon Aya Tayyibah tayi lokaci ɗaya ta matso tana cewa "Sis amma dai baki da lafiya?" Murmushin ƙarfin hali ta yiwa Tayyibah ta gyaɗa mata kai a hankali tace "Mmmm!" Tayyibah tace "eyyahh! Sannu dear Allah ya ƙara lafiya" Iyami da Aya suka amsa,babu irin roƙon da Tayyibah bata yiwa Iyami akan ta zauna ba Iyami tace a'a,haka ta ajiye warmers ɗin cikin parlon Aya suka fita rakata tare,kafin Iyami ta tafi haka tai ta jaddadawa Aya maganar zuwanta gida haihuwa,sannan tai masu sallama suna tsaye me tricycle yaja suka ɗauki hanya. Tunda suka dawo Aya ta samu guri ta kwanta ta rasa me yake mata daɗi,da ƙyar Tayyibah tasa ta cin abinci kafin ta kwanta,nan bacci ya ɗauketa Tayyibah kuma ta zauna gadinta har yamma,kou sallah ranar sai haɗawa tayi,Tayyibah na tai mata sannu,tai mata murmushin ƙarfin hali tace "thank u Sister.. Ba dan Allah ya haɗa ni dake ba da ban san yau ya zanyi ba" tana maganar zuciyarta a karye,hawaye suka fara biyo fuskarta,rikicewa Tayyibah tayi ta fara bata haƙuri tana tambayarta kou jikin ne suje asibiti,Aya ta girgiza mata kai tace "a'a lafiya ta ƙalau,ba na jin ciwon komai yanzu.. Kawai dai ina jin zuciyata na zafi ne" Tayyibah tace "wani abu yana damunki kenan,amma kin san condition ɗinki fa,kin fi kowa sanin ba'a son kina zama da damuwa,dan Allah ki sanar min me yake faruwa,domin tun dare na fahimci kamar akwai wani abu" murmushi me ciwo Aya tayi tana share hawayen da suka zubo mata,sannan ta shiga bawa Tayyibah labarin komai,Tayyibah ta dunga kallonta tana jin ranta na ɓaci for no reason,dama ta fahimci haka tunda taga basu fito ba daga ira har shi kanshi Oga Ahmad ɗin,tace "amma me yasa zai yi haka? Mahaifiyarki ce fa,kuma inda kara ai shima ta haifeshi tunda ta bashi ƴarta ya aura,fisabilillah ya kamata ace har ta zo gidanki kuma ta tafi bai barki kuyi sallama ba,shi yasa mana naga Iyami ma ta dage tafiya za tayi,ashe abunda ya faru kenan" faɗa sosai Tayyibah taita yi kamar za ta aro baki kou kuma kamar ance mata ga Amado a gabanta,Aya tace "ai babu komai hankali ya koyamin nima.." Haka sukai ta tattaunawa kan maganar,ƙarshe ma Tayyibah taji haushi kou jira ya dawo batai ba ta fita,dan ta rantse baza ta gaisheshi ba. Yau ma ɗin bai dawo da wuri ba,dan sai can bayan ishaa sosai sannan ya shigo,Aya dake kwance ita kaɗai shiru ta amsa underneath her breath sai dai bata ɗago kanta ta kalli inda yake ba,shima bai ce mata ba ya wuce ɗakinsa,bayan ya gama uzurorinsa da yaga bata shigo ba,ya fito tare da buɗe ɗakinta ya tsaya daga bakin ƙofar yana kallonta,sanda ya gaji dan kansa yace "na kasa fahimtar abunda kike nufi,idan wani abu akai maki ai sai ki fito fili ki faɗa,ba wai ki kama fushi mara dalili ba" idan ta ɗago ta kalleshi kou ta nuna da ita yake,tou ƙofar da yake kusa da ita ta tanka masa,ganin ba ta da niyyar kulashi ya daɗa sawa ya shaƙa,kawai sai ya fice ya bar mata daɗin,duk yanda wani gefe na zuciyarta yaso tanƙwarata,fushin da take ciki da shi yasa ta rufe ido ta shareshi,a haka kwanaki suka ci gaba da wucewa,tsakaninsu babu me yiwa wani magana,kullum damuwarta tunda Ummii ta tafi bai wuce ta san yaya take ba,sai dai babu wanda ta sani da zai ara mata waya ta kirata,kou da ma ta samu ɗin ita kanta ba ta da lambar Ummii ɗin,shi kaɗai ta sani da yake da waya,amma duk da yana matsayin mijinta,sam taji bazs ta iya cewa ya ba ta aro ba kou dan gudun kada ya wulaƙanta ta,musamman kuma data tuno asalin faruwar matsalar ma duk a dalilin Ummii ɗin ne,hakan sai yasa ta kama mutuncinta,sai dai yanzu ba kamar da farko ba,dan ta ɗan sauko har tana masa abinci da sauran hidimomi,kawai abunda ta rage kou ma ace ta daina shi ne doguwar magana da shi,za tai masa komai har ta gaisheshi,amma dariyarta gaba ɗaya ta daina bari yana gani a sadaka,Iyami ma kuma tunda ta tafi,sau biyu kaɗai ta leƙota shima duka bata daɗe ba,a bakinta ne ma ta samu labarin Ummiinta har da saƙon gaisuwa,ba ta jira har ya dawo daga gurin aiki ya sameta za tai tafiyarta,duk dan gudun afkuwar wani matsalar,cikin wannan yanayin suka fara wani irin zama mara daɗi tsakaninsu,Tayyibah kullum za ta shigo kou ita taje su yini suna hira da wasa da dariya,sai dai kou itama Aya bata bari ta fuskanci irin zaman da suke ba,duk fara'arta da zaran dare ya yi ta ganta ita kaɗai,kou ta duba taga lokacin dawowarsa ya kusa za ta fara ɗaure fuska kou tai shigewarta ɗakinta,sam ta daina shiga harkarsa akan abubuwa da yawa,shima kuma da yake soko ne ya biye mata ya fita sabgarta,gaba ɗaya ya ɗebeta ya bawa banza ajiyarta,ƙarƙari idan tashi ta kawoshi nan zaita ɓarin jiki da son yı mata magana,data gama ganoshi sai dai ta kalleshi kawai,da zaran ya gama samun biyan buƙatarsa shi kenan za su koma gidan jiya,a cewarshi fushinta da rashin magana ba damuwarshi bace,sanda suka kusan share sati uku a haka,ya gaji dan kansa ya fara saukowa tare da nemwn sulhu,ita kuma ta nuna masa ai yanzu ta fara nata fushin,duk yanda yai zaton al'amarinta sanda ya wuce nan,har gida yaje yai kwanakinsa ya barta ita kaɗai,da ya dawo ya yi zaton zuwa lokacin ta sauko,amma har sannan tana kan dokin zuciya,ƙarshe da yaga shi ne yake azabtuwa kou kuma dai huɗubar Innarshi ya ɗauko ohon masa,nan yace ta shirya ya mayar da ita gida ya san matsalarta,bayan ta haihu komai zai dawo dai² tsakaninsu,cikin zaƙuwa kuwa ta shirya da yake lokacin cikinta ya kama hanyar shiga wata na tara,ta yi zaton idan sunje gida zai kaita gurin Iyami,sai dai suna zuwa yace shima sam sai dai ta zauna nan gidan,duk kukanta da roƙo baisa ya saurareta ba yai wucewarshi Kano bayan ya kafa mata mugayen sharuɗanshi na bai yarda da fita ba kou da gidansu za ta,kuma bai yarda Iyami tazo ta zauna da ita ba tunda gidan ga mutane nan,idan ma wani abu ne ya taso ta nemi wani ta sanar masa a kirashi,iya takura da damuwa ta shigesu,domin gidan sam babu wanda ke shiga harkarta banda Baba Wada,a haka taita zaman haƙuri har kwanakin EDD ɗinta suka wuce babu batun haihuwa kwata²...
*MAZAN FAMA GLOBAL COMMUNICATION..*
```Muna farin cikin sanar da ƴan uwa tare da masoya cewa,wannan Company namu yana siyar da data akan farashi me sauƙi na networks da muke da su a Nigeria kamar haka:```
*MTN*
500MB—₦150
1G—₦300
2G—₦550
3G—₦850
5G—1,450
10G—₦2,750.
FOR DATA BALANCE
DIAL:*460*260# or *461*4#
*AIRTEL*
500MB—₦150
1G—₦300 2G—₦550
5G—₦1,4000
6G—1,650.
DATA BALANCE *140#
*GLO*
1.35G—₦550
2.9G—₦1,050
5.8G—₦1,500
7.7G—2,050.
DATA BALANCE *127*0#
*9MOBILE*
2G—₦1,200
3G—₦1,650
4G—1,950
6G—₦2,600
7G—₦2,900.
DATA BALANCE *228#
contacts:***
Account â„–:6074981401
Account name:Aliyu Muhammad Usman
Bank name:9 Payment Service Bank.
#Follow
#Vote
#Comment
#Share
#Asli Smasher.