Chapter 21
*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*
*🅿️21*
Suna idar da Sallar Asuba Baba Mallam bai Tsaya ba Ya Nasir ya Tukasa zuwa asibitin Tunda shima nan ya sallaci sallar asuba Ya jafar tun Daran jiya ya kirashi ya fadamai kafin su tafi sai da Baba Mallam ya Umarci Shamsu daya kira Mallan ya"u mai Dori yazo ya Duba Amina..!
Haka kuwa akayi gari na waye bakwai na safe Ya shamsu yazo da mai Dorin,Koda yaje Hajiya Babba tana gidan Amina jiki yayi Tsami sai faman kuka take ashe kadan tayi Domin wajen gyaran Targade da Goshewar data samu sai da ta raina kanta sai da su Hajiya da Mamanmu suka Riketa Hamida da Hanne suna ta kuka Ranar ko shirin zuwa Hadda ba wanda yayi acikin gidan sai dai chan su Sa"adatu ne Idi Direba zai kaisu..!
Yaya kuwa Hada hadar abun karin da zata kai asibiti take yi ko afuska bata bayyana wata damuwa game da Amina ba Ita ta Aba take yi,ammh sai dai karkashin Ranta Damuwa ne Dankare wanda Tsabar kawaicinta yasa bata bari a Fahimceta ba, sai dai fa Uwa uwa ce kuma bazata Haifi abu da Cikinta tace kuma bata kaunarsa ba sai dai kawaici da wasu abubuwan da kansa Uwa ta kauda kai kan abunda ta haifa sanin Halinta ma ba wanda yabi ta kanta Domin kowa yasan Yaya bata taba Shiga Sha"anin Amina sai abun yaci Tura yakai mata makuran da zata tanka..!
Ya bada mgani an shafa mata Cikin kwana Daya ammh Amina ta Fita Hayyacinta ta rame sai ido,Tasha wuya cikin kwanakin Wuyan da bazata taba mantawa da ita ba Hamida da Hanne sun fi kowa sanin Amina tafi kusa dasu shiyasa lamarinta yafi Damunsu gabadayansu suma Suku suku suke kamar basu da Lafiya sun tasa Amina da Tagumi tana kallonsu sai dai yau karon Farkon Bakin Amina ya Mutu bata mgana sai ido sai kuka acikin Ranta wani abu ne mai Girma Tana ji ajikinta komai yazo karshe ta rasa Aminu shima ya rasata sannan abu mafi girma tana jin kamar wata Kaddarace zata faru da ita yasa abubuwa suka kwabe mata Lokaci Daya sai dai koma menene Tayi alkawarin bazatace komai ba Tunda mai Faruwa ta Riga ta Faru babu Tsumi babu Dubara..!
Dakyar Hajiya ta Lallasheta tasha Tea da Panadol Saboda Zazzabin Jikinta sai ta samu barci sai alokacin suka samu Daman karyawa Mamanmu da Yaya suna shirin Tafiya asibiti duk da sunyi waya da Ya Jafar yace ya Dawo gida Ammh Baba Mallan nachan suka barsa tunda safe Ruwan zafi ma Nasir ya koma gida ya Taho dashi Da kayan Tea..!
Ya Abida ta shigo ta Duba Amina kafin su wuce Hadda ya zeena ma bataje ba su Sa"adatu ne suka tafi dasu ya Akilu sai Umaimatu,Misalin karfe Tara na Safe Hajiya Babba da Yaya da Mamanmu da Anty Shamsiya matar ya Jafar suka tafi asibitin da aka kwantar da Aba domin su Dubasa shi kowa kagani rai da zuciya ba Dadi.
Wani private Hoptal ne Daki na Musamman Aba ke ciki Vip.
Suna shiga Baba Mallam kadai suka Iske awajensa Aba din yana ta barci su Mamanmu suka gaisheshi Cikin girmamawa ya amsa yana Fadin"Mungodema Allah..Ya jikin uwar tawa?Nace shamsu yazo da Mallam ya"u sun zo kuwa..?
Wannan karon Hajiya ce tace"Eh har ya gyaramata ya bada mgani an shafa mata tasha mgani koda muka fito ta samu barci..
Ya shi Sa"idun..Ya farka kuwa..?
Baba Mallam yace"Eh ya farka da Safe jikinsa da sauki sosai bai dade da komawa barci ba koda Nasir ya bar nan muna ta Hira dashi..!
Gabadaya suka amsa da Alhamdulillah mai sunan Mallam ne Dake bayan Shamsiya ya fara kuka Mallam yace Hajiya ta karbo shi ,ta kwatoshi daga baya Ta mikama Hajiya ita kuma ta mikoma Mallam ya saka Hannu Biyu ya karbesa yayi wayau Yayi girma kansa ya dafa yana Tofamai addu"a sai da ya gama sannan yace"Ciwon kunnin nasa fa.?
Kan Anty Shamsiya na kasa tace''Yayi sauki..yadaina kukan tun jiya daddare..!
Baba Mallam ya gyada kai yana Fadin"In muka koma gida zan bama Jafar wani mgani ku rika Digamai Daga Saudiya nazo dashi..!
Kai ta gyada kafin tace"Jiyan ma Da daddaren wajen Mamanmu yacemin zai zo ya karbo masa wani mgani shine baidawo ba sai waya naji yana Fadamin yana Tare da Aba a asibiti..!
Baba Mallam yace"Wlh kuwa..Ammh ai da sauki yana ta cewa ma a sallameshi ya koma gida..!
Mamanmu tace"Daman ai baisan zaman asibiti..!
Hajiya tace"Sai hakuri ya bari ko zuwa gobe ne in ya kara jin Sauki..!
Suna cikin mganar ne Aba ya Farka Daga barcin daya kwasheshi suka fara Rige rigen mai sannu Mamanmu tana kokarin Taremai Filo Sai Yaya ta rigata sai ta sakarmata Ya jingina da Filo sannan ya tashi yana amsa gaisuwansu Lokaci Daya yana Binsu da kallo cikin Tsausayinsa Yaya tace"Ga Ferfesun kayan ciki nayo maka..In zubo maka zakaci..?
Mirmishi ya saki kafin yace"Zubomin Hadiza..Nagode Allah yayi miki albarka..!
Akunyace ta amsa ta Duka tana Zubamai Cikin Filet din da tazo dashi,Kadan yace ta zubamai ta mikamai ya karba Baba Mallan na Fadin"Ashe girkinta kake jira shiyasa bayan Ruwan Tea kaki cin komai..Duka abincin da matan yaran nan sukayi bai taba komai ba Hajiya..!
Dariya tayi tana Fadin"Sa'idu ne fa..Tun farkon auransu Girkin Hadiza yasa ya faramin yajin cin abinci kaga Tunda yayimin yaji nasan Hadiza ta Curi Tuta..har yayi aure adakina Sa"idu ke cin abinci Mallam har haushi yake ji na kwace masa yaro..
Gabadayansu Dariya sukayi Saboda yanayin yadda sukayi mganar Aba ma sai da ya Murmusa bai ce komai ba yana kallon Yaya basu sani bane aduniya ita kadai ce macen da yake Fatan Har aljannah ta zama matarsa Saboda kyawawan Hallayarta Tunda suka zama miji da mata shekaru aruaru bai taba ganin Ranar data Daga Muryansa sama da tashi ba..Yana kokarin Boyewa ne Sai Hadiza matsayinta Daga Allah ne ko ya Boye Kaunarta bazai taba Boyuwa ba Tana da wani irin girma acikim Idonsa da Rayuwarsa da ba wanda ya sani ita yake kallo yana jin zuciyarsa na Sauka Duk da cikin Halin Dayake ciki ita kuma kanta na kasa tana da kunya ballatana gaban Hajiya da Baba Mallam..!
Yaci kuma Ferfesun duka ya Cinye ya Dora da kayan marmari sai gashi garas dashi sai dai kallo Daya zakayimai kasan yana cikin Damuwa,Ya Jafar daman bai shigo ba sai gasu shi da Nasir sun shigo suka kara gaida Aba daganan su Mamanmu sukayi sallama dasu Jafar zai maidasu Gabda zasu fita Hajiya ta dawo wajen Baba Mallam daya mikama Jafar takwaransa yana jadaddamai yazo zai bashi wani mgani Jafar din ya Juya kenan Hajiya ta kalli Baba Mallam tana Fadin"Mallam naji bakace komai ba Har yanzu..?
Kallonta yayi yana Mirmishi kafin yace"Nazir ya Kirani da Safan nan yace yana ta kiran wayarki baki Dauka ba..Sai daga baya Abida ta Daga kiran tace baki nan kina gidam Sa"idun..!
Kauda mganar yayi ta sani tace"Ina na sani..Gida na bar wayar..Suna Lafiya ko..?
Yace"Lafiya lau..Shehin ne dai ba Lafiya yacemin kwanansu Biyu asibiti Ciwon ciki ammh sun dawo gida shine nake fadamai nima ina asibiti ga yayansu Sa"idu ba Lafiya..!
Hajiya tace"Assh..Allah ya Sauwake in na koma na natsu zam kirasa..!
Kai ya gyada mata bai ce komai ba,sai ta kalli Aba da hankalinsa baya kansu ya Lula Tunanin Halin da Amina ta Jefasa Cikin Damuwa Hajiya tace"Sa"aidu wannan Tunanin babu Riba cikinta..Ka kwantar da Hankalinka ba wata mtsala insha Allahu..!
Aba ya sauke Numfashi kafim yace"Hajiya in ban aurar da Amina yanzu ba..Watarana Jidalinta zai iya ajalina..Kinga Hadiza bata mgana ko..?
Na rantse tafini jin Dacin Amina tafini Sanin Ciwonta Domin itace uwa gareta ina Tsoron yadda take shanye abubuwa watarana Amina ta Dauko abunda zai yi sanadiyar zuciyarmu ta Buga Dukkanmu mu fadi mu mutu..!
Hajiya ta kama baki tana Fadin"Assh..Haba Sa"idu bama zai taba Faruwa ba..!
Tari ya farayi sai kuma jikinsa ya fara rawa Da Sauri Hajiya tace"Mallam yace komai zai daidaita ko ba Haka ba..?
Tafada tana kallon Mallam din wanda ke kallonsu bai ce komai ba Rawanin kansa ya gyara kafin yace"Insha Allahu..Zan Daura ma Amina aure in an idar da Sallar azahar da yardan Allah..!
Baba Sa"idu da Hajiya suka kallesa da mamaki Aba ya rausayar dakai yana Fadin"Ina fata da bada wannan Lalattacen yaron da suka gama Lalacewa bane ko..?
Baba Mallam ya yi mirmishin su na manya kafin yace"Bashi bane Sa"idu..!
Hajiya tace"To waye ne Mallam..?
Sai da ya kara Murmusawa kafin yace"Da wanda Allah ya kaddara..Shine dai wanda Allah daman ya Rubuta Mijinta ne dashi za"ayi..!
Hajiya daman tasan bazai fada ba Tunda bai iya fadamata ba kuma bai Fadama Sa"idu ba to Tattabata bazai Taba Fadama kowa ba..!
Aba ne yace"Kada ka Tursasama Mutumin Kirki sai ya aureta Mallam..Ka hadata da irinta sannan ka Sanar da kowaye halinta Baba..Kuma ina so aje a gwada Amina kada yazo wajen Lalacewarta ta Samo wata cuta..!
"SA"IDU..!
Baba Mallam ya katsesa Cikin Tsawa da Bacin rai kafin yace"Kul na Sakejin wannan mganar daga bakin ka..ina da yakinin Har Abada acikin zuru"ata baza"a samu bara Gurbi ba...Duk da Allah na Jarrabatan bayinsa ta kowani Fanni Ammh ta wannan gabar ban yarda ba..Amina bazata taba Rusa Tarbiyarmu ba Sa"idu ba abunda zan ce ma wanda zai aureta illah ya Rikemin ita Amana kuma in Cucuta koda abayan Idanmu ne Ban yafe MASA BA..!
cikin kaushinsa ya karishe mganar da ta ja Hankalin Aba da Hajiya suka kalli juna bai kuma basu zarafin mgana ba ya kalli Hajiya yana Fadin"Kinsan suna jiran ki ko?
Kai ta gyada kafin tace"Shikenan Allah ya kara afuwa..!
Har ta juya zata tafi Baba Mallam ya Kira sunanta ta juyo Cikin bacin ran da bai barsa ba yace"Ki fadama su Balaraba kada wata cikinsu ta kira yaran nan dake gidan auransu tace zata Daga musu hankali ko Husai ban yarda afadamata ba..!bana so a adaga musu Hankali..!
Hajiya tace"Insha Allahu ba wacce zata ji..!
Kai ya gyadaa mata ta juya ta cigaba da Tafiya har takai kofa zata fita ya Kira sunanta wannan karon a Taushashe ta juyo tana Fadin"Mallam..!
Kai Tsaye yace"Umaru ya kiraki kuwa..?
Cikin mamaki tace"A"a rabona dashi Tun shekaranjiya da safe..! lafiya kuwa.?
Mirmishi yayi kafin yace"Bakomai..Allah ya kaiku gida Lafiya sai na dawo.!
Hajiya ta jinjina kai kafin ta Fice ya bita da kallo Daman ai yasan bazai taba Kiranta ba Shi ya Haifi Umar ammh yana Daraja kyakyawan Dabi"ansa..!
Aba ne yace cikin Raunin Murya"Kayi hakuri Baba..!
Hannu ya dagamai kafin yace"Nace ne kada na sake jin irin mganar makamancin wannan abakin ka..Ba hakuri nace ka bani ba..!
Cikin Sauri Aba yace"Insha Allahu..
Sai alokacin Baba Mallam ya saki Fuska yana Fadin"Allah yayi maka albarka kaida zuru"arka Sa"idu.Har Abada ban taba Nadamar samunka Cikin zuru"ata ba..Ka warke da wuri ban shirya rasa Da"a na farko ba..!
Ya karishe Cikin barkwamci Da sai da Aba ya Murmusa Lokaci Daya Hawaye suka cika kwarmin idonsa yake Fadin"Nagode Baba..Nagode Ban taba jin kai ba Uba kake gareni ba..Ina Alfahari dakai..!
Baba Mallan yayi wani kayattacen Mirmishi kafin yace"Nima ina Matukar alfahari dakai Sa"idu..!
*******
Tana cikin Tiolet din Bedroom dinta taji Ringing din wayarta Allah yasa ta Gama wankan ta Dauro babban zaninta ta fito wayar tana kan Mirror dinta ne Jikinta yana digan ruwa takai Hannunta saman wayar wanda taga yana kiran nata ne yasa taji gabanta ya Fadi..!
"MALLAM..!
haka kurum mallam awannan Lokacin bazai kirata ba,Dazu Shamsu ke fadin yana asibiti wajen Sa"idu Har wayar ta kusa yankewa bata Daga ba sai Daga baya ta Daga kiran tana Fadin"Assalamu Alaikum Mallam..!
Dagachan Haraban asibitin Baba Mallam yace"Marliya kina ina ne..?
Cikin mamakinsa tace"Ina gida mana Mallam..!
Kai Tsaye yace"Marliya abunda ya faru jiya gidan Sa"idu kuskure ne da Rashin Fahimta ko..?
Cikin Mamakinsa da Tunanin inda ya Dosa tace"Hakane..!
Cikim Dattakonsa yace"To mu barsa ahaka..Kada na sake naji mganar nan ta fita..In har najita a waje Nasan kece..Bana son surutu da mgana Hajiya kinsani bata da wannan Halin Saboda haka ki kiyaye..!
Anty Amarya taji ta Muzanta Ranta ya baci wato Hajiya ba ruwanta itace mai Surutu ko lalle ne Mallan dinnan.!
Danne bacin ranta tayi tana Fadin"Ah..Wlh ban fadama kowa ba Mallam..yanzu dai nake shirin shiryawa na shiga gidan na Duba Amina ya jikin Sa"adun..?
Fata ya samu Sauki..!
Cikin son Dakile mganar yace"Yaji Sauki..Kada ki fita ko"ina nima ganinan zuwa. !
Bai jira cewarta ba ya Datse kiran yana wani nazari yasanta da kananun mgana sarai shiyasa ya taka mata Burgi in ba haka ba,kafin wani Lokaci ta gama Fesama ya"yanta su kuma su fara yawo dashi mgana har ta fita wacce bata da wani amfani..
Ita kuwa Anty Amarya Sororo tayi da waya a Hannunta mamaki bakin ciki da Kishi sun Turniketa wayar ta Dangwar nan saman gado tana Fadin"Aikin banza..Abunda kake son ka Rufe mallan bazai taba Rufuwa ba..Ko ba"a bakina ba Lalacewar Amina sai ya fita Duniya..!
Abunda bai sani ba ta Fadama ya"yanta Sa'adatu da Jidda da Sadiya Jidda ce kawai bata Dauki mganar ba Ammh Sa"adatu har tana Fadin daman idanuwan Amina na rashin gaskiya ne sannan abakinta Anty Amarya tasan Amina na karancen karancen Littafan hausa Sadiya dai da Uwar ta fadamata batace komai ba Domin bata cika Hayaniya ba.
Wayar Sakina tayi ta nema ta Tsegunta mata bata sameta ba Shiyasa da Tuni Labari ya isa Saudiya Arabia..!
Tana shiryawa tana Tsaki ita kadai ta rasa me Hajiya Babba tafi su da Mallam yake Fifitata akansu ta manta tun Tale tale Take tare da Mallam din kwafa tayi afili tace"Daga ita har Sa"idun duk sai nayi mganinsu Algumgumai duk su ke zuga Mallam..Da basu da Tuni nice Tauraruwa awajensa da gidan gabadaya..!
Abunda bata sani ba,ba irin Mallan ake ma haka ba ko ta manta Malami ne wanda bai zauna ba,kariyar Allah Tana Tare dashi kuma ilkonsa bazai bari acutar da bawansa ba..!
Baba Mallam na asibiti kafin ya baro ya Kira ya Jafar yace ya siyamai Dabono da Goro mai yawa zai yi amfani dashi bai damu ba sanin kila Mallam din zai yi wani abu dashi sai dai abu daya ya bashi mamaki Dayace su samu sallar azahar anan masallacin gida shima gashinan zuwa..!
Koda ya tafi Aba na barci Nurse tazo tamai allura kila tana saka barci ne shi kuma sai bai tashesa ba Idi Direba ya Kira yazo ya Daukesa zuwa gida Kai Tsaye Shashensa ya wuce domin ya Shirya Tunda azahar din ta kusa Shi kadai kawai yake jin karfin Gwiwa da alhafarin wani abu akaron Farko zai cika wani Burin Daya Dade acikin ransa bai Mutu ba kuma da Ransa..!
Wanka yayi ya shirya Cikin Shadda Fara harda babban Riga dataji aikin Hannu ya Dora rawaninsa sai ya Fito Tar dashi Farin gemunsa na kyalli yana tashin kamshinsa kamar koda yaushe adaidai Lokacin ya samu wayar Jafar yana Fadamai ya siyo abunda yace asiya din Baba Mallan yace yana cikin gida gashinan Fitowa..!
Bai Fadama kowa komai ba acikin gida yayi alwalansa ya fito Mutane basu wani mamaki ba in yana gari dashi ake yin sallah duk da akwai Limamin masallacin Mallam Muhammad Dayyab in Baba Mallam bai nna shi ke kula da masallacin har ya jafar da Ya Nasir suna bada Sallah da Mangariba haka ko isha"i Mallam din ke sakasu saboda gaba in watarana ya fadi ya Mutu ace akwai masu bin bayansa Koda Umar da Nazir basa kusa akwai Jafar da Nasir manyan dake bin bayansu..!
Kowa ya zata Baba Mallam din zai bada sallah sai dai ana shiga masallacin yace Mallam Muhammad yajasu Sallar,to sai mamakin bai yi yawa Tunda yana haka sau tari dadama.
Mallam Muhammad ya bada salla ana Idarwa Baba Mallam dake sahun gaba ya matsa gabansa sukayi kuskus kafin Mallam Muhammad din ya sanar da Daurin aure da za"a Daura shi yanzu Baba Mallam sai annuri yake yi Ya Jafar da Nasir Dake layi na Biyu ya yafito da Hannu Sai Shamsu Dake gefe duk suka taso suka kariso gabansa gaban Liman Mallan Muhammad..!
Suna karisowa yace su zazzauna suka zauna nan gefensa Cikin Dattakonsa yace"Jafaru dauko sakon nan..!
Ba Musu ya mike ya fita daman acikin Motarsa ya bar Huhun goron da Ledan Dabibon yaje ya Dauko ya kawo ya Mikama Mallam ya karba ya Mikama Mallam Muhammad yana Fadin"Araba shi Liman..araba ma Jama"a..!
Ba Musu Limam ya bama Ladani Umarnin ya rabama kowa Dabino da Goronsa kamar yadda aka saba Cikin Kankanin Lokaci yabi layi layi ya bama kowa,Mutane basu yi mamaki ba sanin Daman amasallacin bazanga koda yaushe cikin kawo Daurin aure akayi shiyasa ba wanda ya damu ammh su Ya Jafar sun Tsargu ballema da suka ga yadda Baba Mallam ke ta Annushuwa kuma yana gaba gaba kan komai ko auransu Zulaihat bashi ya bada ba su ya Danmallam ne suka Zama Waliyansu..!
Basu gama mamaki ba sai da Liman yace"Allah ya gafartama Mallam an gama Raba Goron da Dabinon har yayi saura ma..!
Baba Mallam ya Jinjina kai kafin ya karkace ya zaro Bandir din kudi Sabbi yan Dubu Dubu ya ijiye gaban Liman Cikin Dattakonsa yace"Walicci zakamin Mallam Muhammad..?
Cikin mamaki yace"Waliccin wane kuma Allah gafarta mallam..?
Baba Mallan sai da ya kara Fara"ar Fuskarsa kafin yace"Waliccin Umarun Faruku zakamin aure zan kara masa ayau din nan acikin wannan masallacin..!
Liman yace"To..To..Masha Allah ai babu Laifi Allah gafartama Mallam sai Waliyan ita yarinyan su matso afara siga..!
Baba Mallam ya Murmusa kafin yace"Nine Waliyan Amarya..Ga Sauran yan"uwanta nan..!
Ya nuna su ya jafar da suke zaune mamakin kalaman Baba Mallam ya cika su.
Cikin karin mamaki Liman yace"Au kace Abun duk na gida ne..To masha Allahu..Ba bu laifi sai mu fara gabatar da siga ya sunan Amaryan..?
Sai da Baba Mallam ya gyara zama kafin yace"Sunanta AMINA..AMINA SA"IDU..!
Jafar da Nasir suka kalli juna kafin su juya suna kallon Baba Mallam Shamsu kuwa Kunni ya saki yana jin abun kamar almara..!
Liman ya washe baki yana Fadin"To..To..Masha Allahu wannan abu yayi kyau..Allah yasa a kulla alheri..!
Zamu fara gabatar da siga..Ladan ya Ciremana Lasifika..!
Da Sauri Baba Mallan yace"A"a abarta Liman..!
Liman cikin mamaki yace"Dokarka ce Allah gafarta Mallam ba"a Daura kowani aure cikin Lasifika..!
Baba Mallam cikin Annuri yace"Na yau kadai na Sauke Dokar liman..So nake naji Sautin Tattabatuwar auran Uwata da Umaru so nake na ji Sosai acikin kunnuwana Liman..!
Liman bai yi gaddama yace abar Lasifika,cikin Abunda bai fi mintina goma sha Biyar ba aka gabatar da siga aka kuma Tabbatar da Daurin auran AMINATU SA"IDU GUSAI da angonta Mijinta UMAR YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA akan Sadaki Naira Dubu Dari Cif..!
Adaidai Sanda Muryan Ladan ta Karade Lasifikan yana kara Jaddada Daurin auran Amina da Umar din Akan Sadakin da uban Amarya kuma Uban ango ya Biya Mallam Yunus Abdurrahaman bazanga..!
Awannan gabar Alkawarin Allah ne ya cika..!
Zanen kaddara ya tabbata..!
Auran ya Dauru.!
"fallasa wasu sirruka ne..!
Dalilin wannan auran za"a rasa rai..!
Fuskokin wasu amintattu zata bayyana..!
Zuciyoyin wadanda basu taba Tsammani ba zata girgiza..!
Abunda basu taba zato ba ya faru alokacin da basu shiryama hakan ba..!
Wasu sun makara..Saboda Alkalamin ya riga daya Bushe ko sunzo kafin Lokacin Allah bazai sauya wannan kaddaran ba SABODA RUBUTTACIYA CE..!
Daurin auran daya Faru a kunnuwan mutane Dadama da suka cika da Dimbin mamaki wadanda da basu yarda ba Sa"idu ba dan Mallam bane yau suka kara yarda da mganar wasu Mutanen yadda Baba Mallan ke Hannu da Mutane kawai zaka Fahimci yana cikin Farimcikin da bai Taba tsintar kansa aciki ba shi ya Hana Jafar ko Nasir cewa wani abu suma sai sukabi ayarin yan gaisawa da Mutane suna faman amsa Fatan Alherai daga kowani bangare..!
Baba Mallam Dakyar ya samu ya Fito daga masallaci su Jafar ya kallah yana Fadin"Ku scigaba gda amsan Fatan Alheri jama"a bari nayi wata waya..!
Daga haka yayi nesa da Masallacin ya Fiddo wayarsa ya Kira Danmallam..!
Tana gabda Katsewa ya Daga Kiran Cikin Mutuwar Jikin da Baba Mallam ya Saukarmai Tun Safe daya Kirasa yana Fadamai zai aura masa Kazamar yarinyar nan..!
Cikin Farimciki Baba Mallam yace"Umaru..!
Dagachan bangaram Muryansa a shake yace"Na"am Baba..!
Bai jira cewarsa ba ko yanayinsa ba yace"Yanzu nan aka Daura auranka Da Uwata..Ayanzu din nan AMINA ta zama Amanarka Umaru..daidai da Rana Daya in kaci Amanarta ko ka Dannen Hakkinta Allah na kallonka sanna amatsayina na Mahaifinka ban YAFE maka ba Umar daidai da Rana Daya in ka Zalunci AMINA.!
ya karishe Fada Cikin kaushin Murya
Gabadaya sai yaji kamar Duniyar na Juyawa dashi wannan shine gaba kura baya Damisa..!
Baba Mallam bai Damu da amsar ba ya Cigaba da Fadin"Ina Alfahari dakai..Yau ka cikamin Burina Umar..albarkata da addu"an Allah ya baka Zuru"ata tagari bazata yanke Daga bakina ba..Ina Rokon Allah yasa Amina ce Sillar Arzikinka da Daukanka..Ina ji ajikina Uwata ce Farincikinka watarana ko bana Raye alokacin nasan zaka Tuna dani Umar..!
Jin Mallam kawai yake ta ina wannan kwailar yarinya zata zama Farincikinsa watarana..?
An dai hadasa da aiki Yarinya kazama ga rashin Natsuwa da Taurin kai da rashin ji yana zaman zamansa Mallan ya Debo masa aiki Sai dai shi Yaro ne mai Biyayya har abada baya Fatan Ranar da zai Sabama Iyayansa..!
Shiyasa Cikin karfin hali yace"Nagode Baba..Allah ya kara girma..Insha Allahu zaka sameni mai biyayya..!
Baba Mallam cikin jin dadi yace"Nasani..nasan bazaka watsamin kasa a ido ba..Allah yayi maka albarka..!
Ya amsa da Ameen Daganan sukayi sallama bayan ya tambayi jikin Aba yace da Sauki sannan suka rabu da juna da cewar shi Danmallan din zai kira wayar Baba Sa"idun Baba mallam yace ya Kirasa Jafar ya Tahomai da wayarsa da Safe..!
Abunda kowa bai sani ba Tun Da Asuban nan da Danmallam ya Kira Baba Mallam yaji aransa wannan mafitan ne Allah ya nuna masa.
Bai yi shawara da kowa ba kafin ya tafi asibiti wajen Aba ya kirasa suka Tattauna Komai Daga farko har karshe sai da ya Fadamai duk abunda ya Faru kwanaki da na jiya Daddare da kalaman Baba Sa"idu da Rokonsa garesa ya kuma Roki Danmallam Daya auri Amina ba domin Umarni ba sai domin daman Yana da Burin Hada Dansa ko yarsa da Ahalin Sa"idu..!
Umar bai iya cewa A"a ba..Mallam ya wuce gaddama garesa Cikin wani yanayi ya amsa masa da cewa Ya amince wannan kalaman nasa su suka Tabbatar da Kaddaransa da Amina Kaddaran zama amtsayin miji da Mata..!
****
Cikin wadanda Daurin Auran Amina da Danmallam ya shiga kunnensu yaya na ciki ita da Hajiya da Mamanmu kai kaf wadanda ke gidan sun ji hadda Amina uwar gayyar Domin tatashi alokacin Hamida ta taimaka mata tayi wanka tayi alwala tana Rama Salolinta ta idar kenan tana Zaune Saman Darduma alokacin ma Tunanin Aminu take da Tunanin Halin Dayake ciki.
Kamar mafarki Taji muryan Ladanin nan yana bayyana sunanta da na Ya Danmallam amtsayin mijinta da aka Daurama taaure yanzu nan.
Ta Rude kanta kamar ya Kulle domin bata gane komai ba Sama sama take jin Muryan Mamanmu Daga Tsakar gida inda suka zauna tun bayan Dawowarsu daga asibitu tana Fadin"Kunji Abunda naji kuwa..?
Kamar Naji ana Fadin an Daura ma Amina aure da Danmallam..ku Saurara,kuji..!
Suma sun ji din sai dai sun kara kasa,kunni Saboda su gasgata,Hajiya kuwa tun jinta na Farko ta tabbatar da Duk abunda taji gaskiya ne..Mallan ne fa tasani Daman shurunsa Zai iya zama koma menene..!
To duk abunda akeyi a masallacin kamar agidansu akeyi saboda lasifukun masallacin akwai kara sosai,Radau suka sake jin wannan al"amarin Daya basu matukar mamaki Yaya Dake Dakinta Tana zaune ne sai da ta mike yayinda ya Zeena ta kwalalo ido tana Fadin"Wlh Mamanmu da gaske ne..Amina ce..!
Hamida da Hanne suka kalli juna Cikin mamaki kafin Hanne ta Rumtuma Dakinsu Hamida tana Fadin"Amina..Amiaa..Kin ji an Daura miki aure da ya Danmallam yanzu a masallaci..?
Kallonta Amina takeyi da manyan Idanuwanta da suka Zama wani irin Cikin wani yanayi tace"Naji..Naji Hanne..ammh bangane komai ba wani Danmallam din..?
Ni Umar naji an ce fa..?
Tafada cikin wani yanayi Hamida ce da ta shigo cikin wani yanayi tace"Shine Umar din Amina..Yayansu Hanne..Mijin Anty Sakina da Anty Sarood wanda ke zaune a madina..!
Cak Numfashi Amina ya Tsaya ta Fara Kokuwa dashi bata samu zarafin mgana ba taji muryan Yaya tana Fadin"Hajiya kinsani..?meyasa kikabari Mallan yayi haka..?
Amina bata dace da kamilalle irin Umar ba..Bata dace dashi ba sam..bai kamata kuyi haka ba..!
Sai kuka,acikin ranta kuma wani Sasaauci taji Tana ganin kamar Addu"anta na Shekaru ne Allah ya amsa sai dai Tana jin Tsoro tana jin tsoron An Hada Kamili kamar Umar da Amina kada ta zama mai sonkai kada taso yarta Shiyasa tayi mgana..!
Hajiya kuwa tana zaune sai Mirmishi take saki Annushuwa ta bayyana acikin ranta kafin tace"Sun Dace Hadiza..Duk abunda kikaga Mallam ya yanke mai kyau ne..Naki addu"a ne Allah yasa Alheri muka kulla..Allah yasa su aminan juna ne..!
Da karfi Mamanmu ta amsa da Ameen tana sharan kwallah tace"Yaya Amina fa y'arki ce..Tayaya zaki rika Fadin mgana mara kyau akanta ya zataji in taji abunda kike fada!
Tana mgana tana sharan kwallah..!
Amina Daga cikin Dakinsu Hawaye suka kwanyomata tace"Naji..Naji Mamanmu naji..Gaskiya ta Fada ban dace ba..Ban dace ba..!
Batasan Lokacin da wani kuka ya kwace mata ba Lokaci Daya tana Fadin"Wlh bansani ba..Bansan wannan kaddaran ke Bibiyata ba da Ban fara son ka ba Aminu..Wlh bansani ba..!
Taausayinta ya kama Hanne da Hamida suka karisa gareta suka Rumgumeta suma sai kuka Riris kamar anyi mutuwa..!
Zuwa Lokacin Wannan Daurin auran mai Cike da Bazata da mamaki ya kama Yaduwa a gidajen nan guda Biyu Anty Amarya sai da tayi suman Wucin gadi bata kara gasgata mganar ba sai Da shamsu ya shigo ya kara Tabbatar musu agabansu akayi ita da Hajiya Nasara,Haj.uwa na shashenta bata fito ba Duk da tasan abunda ya Faru domin taji..!
Alokacin da Kowacce take kiran ya"yanta masu aure na nesa tana Fada musu Anty Amarya bata cikin natsuwa ballatana ta iya kiran wani ta Fadamai awannan gabar abubuwan sun bala'in shammatanta
Abunda kowa bai sani ba alokacin Baba Mallam na cikin Falomsa na Shashensa tare da baki Daga Yola..!
Yana gama wayar nan da Umar Motoci biyu suka gyara parking kofar Gidansu kuma wajensa suka zo ya karbesu hannu Biyu ya kuma Saukesu afalonsa zuwa Lokacin mutane sun fara watsewa..!
Jikinsa yayi sanyi da yaji kamar yayi gaggawa AMINU ne saurayin Amina da iyayansa sun zo neman auran Amina da kuma ban Hakurin abubuwan da suka faru..
Ashe ashe jiya da dadaddre Aminu Daga Gumel yola ya wuce Allah ne ya kaisa Lafiya yaje gaban Baba Alhaji ya Fadamai komai yana kuka da Rokon suje Gumel suba ma iyayan Amina Hakuri su bashi auranta sai dai abunda bai sani ba sun makara..!
Mallam yaga Dattakon Alhaji Baba yaji matukar kunya alokacin Dayake Fadamasu Amina ta haramta ga Aminu yanzu taron chan na waje na Daurin auranta ne..!
Yana ganin wanda aka kira da Aminu ya tashi ya fita yana Rangaji hawaye Sunaa zuba Daga idonsa.
Sai yaji jikinsa yayi sanyi yaa ji aransa kodai yayi gaggaawa ne..?
Aminu Dakyar ya kai kansa Bakin Motocinsu da suka zo dashi Wayarsa ya Dauko biyu biyu yake gani da haka ya Kira Nenne..!
Tana ganin kiransa gabanta ya Fadi Daman kiran nasa take jira tana Dauka tace"Aminu ya ake ciki..?
Cikin karyewar murya yace"Na rasata Nenne..Nasara MEENATA..
Na makara Nenne an Daura mata aure da wani bani ba..!
Yana gama fadin haka ya Datse kiran ya Sulale nan kasa Dirshen ya Hada kansa da gwiwa yana kuka kukan Rabuwa da masoyi Rabuwa ta Har Abada..!
Nenne Dake cikin gidansu na Yola gidan Alhaji Baba yayyinta da kannenta sun zagayeta suna tambayata Lafiya Cikin fitar Hawaye ta kalli Mahaifiyarsu tace"Hajjo ya rasata..Aminu ya rasa Amina....an daura mata aure da wani kafin su isa..!
Gabadaya suka hada baki wajen fadin"Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un..!
Sun sani Aminu zai samu matsala Kaddaran ta riga fata duk wani ahalin gidannan yasan yadda Aminu yake kuka yana rokon Alhaji Baba yaje yane masa auran Amina..
Ya Aminu zai yi..?
Bakin Alkali ya riga ya bushe..!
Zanen kaddaransa bata Amina bace..Kila na watace chan Dabam
Inda ya sani..Dama..Dama ace bai Hadu da Amina ba..Dama ace komai daya faru mafarki ne..!
*Janafty*