TA FITA ZAKKA..!

Chapter 22

by @jamilaumarjanafty

*TA FITA ZAKKA..!*

_(Aminene)_

*BOOK 1*



*Wattpad:JamilaUmar351*

*Mallakar:Janafty❤️*


_Wannan shafin jinjina ce da godiya gareku masoyana a duk inda kuke masu Sharhi da masu fatan Alheri musamman yan Group dina na TA FITA ZAKKA COMMENTS SECTION da ku yan JANAF NOVELLA Tare da duka sauran gidajen marubuta da ake yin sharhin wannan Littafin nagani kuma na yaba naji dadi Allah ya bar zumunci gaisuwa ta musamman zuwa gare ku yan wattppdians kuma kuna kokari sosai nagode Allah ya bar zumunci.._



*🅿️22*


Zuwa dare duk wanda ya kamata yaji Labarin Auran Amina da Danmallam yaji,kowa mamaki kamasa yake yi in yaji Domin agabadaya da Dubawa ta mahanga ta Dan adam Amina bata Dace da Rayuwar Danmallam ba sai dai Ina Allah shi ke Tsara dukkan Lamuran sannan kuma ya zartar ya riga ya Dora alkalamin kuma ya Bushe akan Amina da Umarun dan bazanga..!

Aba yana asibiti ya jafar ya kirasa ya sanar dashi maimakon ya shiga bakinciki da takaici kamar yadda ransa ya darsu da Tunanin Baba Mallan yayi gaggawa domin Amina bata dace da Rayuwa irin ta kamili Natsattse Irin danmallam ba sai kuma sai yaji kamar zuciyarsa tayi son kai yaga kamar ita diyar tasa irin Mijin Daya dace da ita kenan baisan Lokacin Daya Daidaici gabas ba ya Fadi yayi sujudul Shukur ga Allah ya Dago yana Hawayen Farincikin da bai taba Zaton Daga jiya zuwa Dazu zai iya Fuskarta haka ba yadai ce zai aurar da Amina ammh acikin ransa yanajin kamar bai kyautu ba yana ji kamar wani al"amari zai faru ashe wannan al"amarin ne mai Daraja tuni kimar Baba Mallam ta kara Hauhawa acikin Zuciyarsa ya tabbata ko mahaifinsa Aminu gusai na Raye iyakar kaunar da zai bayyana masa kenan..!

Bangaran Amina kuma tun Lokacin Dataji labari data fara kukan nan bata Daina ba,Har Hajiya Babba da mamanmu sai da suka taru akanta suna ta bata baki bayan sun Fatattaki su Hamida Dake tayata kuka,Agabansu sai tayi kamar taji Duka Nasihansu ta daina Abu Daya ke mata yawo Aminu ta kasa gane wannan wata irin kaddarace da zata Raba ta da masoyinta ta kaita inda Har Abada baza"a taba sonta ba..Wannan wata irin kaddarace haka take ta Tambayan kanta..!

Hajiya Babba na tafiya Amina ta cigaba da gunjin kukanta har ta su Hamida sun daina sun koma suna Lallashinta,Ammh taki daina kuka Mamanmu kuma gajiya tayi ta rabu da ita ya Zeena ce ke kitchen tana samar da abunda zasu ci da wanda za"a kaima Aba Dake chan Asibiti suna Tunanin yasan abunda ke faruwa Tunda Baba Mallam baya Zartar da wani abu sai da saninsa shi da Hajiya Babba basu san wannan karon duka bai nemesu ba shi kadai dagashi sai Allah Daya barma Zabi bayaso yayi mgana da wani ko wata su ce ba haka ba shi yasa wannan karon ko Hajiya babba batasan me ya yanke ba Sai Daga baya..!

Tun Mganar da Yaya tayi ma Hajiya Babba ta koma Daki ko motsinta ba wanda ya sake ji,Sai Lokacin da iskancin kukan Amina ya isheta sannan ta fito ba wanda yaji Shigowarta illah Dundun data Dirkama Amina agadon bayanta wacce ke zaune kasa ta Hade kai da Gwiwa tana gunjin kuka alwala ta Dauro Dakyar shima sai da Hanne da Hamida sukayi ta magiya shine ita batayi sallar ba ta koma tana kuka..!

Dukkansu sai karan Dukan sukaji Amina ta bankare baya wannan Hannu shi kadai ne bata saba dashi ba Hannun Yaya ne..!


Cikin bacin rai ta kalli Amina tana Fadin"Ai bake bace da kuka ba Amina..Umaru ne da kuka domin shi aka Gurbanta ma Rayuwa..Mutum kamili kamarsa an Hadasa da wacce bata Dace dashi ba Amina kamar ki ace kin san Namiji..?Daman nasan wannan Firiritan nan naki watarana sai yakai ga haka har kina mana wani kukan banza to wlh ki kama bakin ki ko na sake Dana miki Dukan da sai kin Raina kanki Sakarya wawiya mara Tunani kawai..!

Ta karishe Fada Cikin Huci Amina na kuka tana Fadin"Wlh bana bin Maza..Ni ba yar iska bace..!

Yaya tace"Shi Jafarun zai miki karya ne..?yaron da yace ya ganki Rumgume dashi Ubanki ne shi..?wlh in bakin ki bai Mutu ba,zaki sha wahala ke baki ji kunya da Tsausayin kanki ba..?Mahaifnki nachan kwance asibiti taa Dalilinki Tir da Halinki Amina Tir wlh..!

Tafada Tana nuna ta da Hannu Cikin wani yanayi Hanne ce ta Dukar dakai Cikin wani yanayi tana Fadin"Don Allah yaya kiyi hakuri..Nasan Wacece Amina sai dai in kuskure akayi wlh bazata aikata abunda akace ba..!

Yaya bata samu bakin mgana ba Mamanmu Data Daga Labule tun dazu Tana jin yaya tace"Hanne ku kyalesu..Duk abunda zasu fada sun Dade basu fada ba..Abu Daya na sani Amina ba Haka take ba..Amina bazata Watsar da Tarbiyanta ba..Akwai abunda ba Daidai ba..!

Yaya tayi mirmishin Takaici kafin ta Juyo tana kallon Mamanmu Cikin Sanyin Muryanta tace"Yaushe ne Ranar da Amina zatayi kuskure ki nuna mata tayi ba Daidai ba..?

Yaushe ne Ranar da zaki bi bayam gaskiya ba bayan Amina ba..?

Mamanmu tace"Sai Ranar da na Tabbatar da gaskiyan kuke fada yaya..Ammh ayanzu har gaban Abada bazan bar Tsagin Amina ba..Amina Diyatace da nake mata soyayyar da ko ya'yan dana Haifa da cikina ban musu shi ba,Har abada bazan Daina Fadin kunyi kuskure Amina ba haka take ba..!

Yaya Batace komai ba kawai ta girgiza ta raba ta gefen mamanmu ta fice Mamanmu ta bita da kallo kafin ta maida kallonta kan su Hamida tana Fadin"Ku bata baki..Bari akawo abinci taci tasha mgani..!

Daga haka ta saki Labulen Dakin ta koma to a wannan gabar sai kukan Aminan ya tsaya cak kamar an Dauke ruwa Zuciyarta ta Bushe bata jira Lallashin kowa ba ta Gyara zama Daga zaune ta tada sallah domin jikinta har yanzu atsame yake bata iya Tsayuwa waje daya ta Gudanar da sallar ba..!

Wajen karfe Tara na Dare sai ga Ya Jafar da ya Nasir sun zo Amina na Daki taji Ya Jafar na fadin"Ina ita mara kunyar Aminar .?

Yaya Data Fito daga Daki tana gyara zaman Hijabin jikinta Da zasu tafi asibiti tace"Tana ciki..Tun dazu da taji Labarin abunda ya faru take kuka..!

Yaya Jafar sai da ya Lailaya ashar kafin yace"Yar iskace bata Daku bane..Ai wannan auran Baba mallam ya Daurasa ne ba domin ya dace ba wlh..!

Ya Nasir yace"Uhmm.Ni kuma ina ganin Daidai ne Jafar..Amina sai irin su ya Danmallan ne daidai dasu..!

Ya Jafar yace"Kamanta ne shi fa ba irin mu bane bai da Hayaniya bai kuma kaimu Zafi ba..!

Ya Nasir yace"Duk na yarda..Ammh kuma ya fimu Shekaru sannan cikin Ruwan sanyu yake Ladabtar da Mutum..Wlh ina ji ajikina Wannan al"amarin ba Tsarin Mallam bane Tsarin Daga Allah ne..Abu ne da Hasashe ko Tunanin mu bai taba kawo ba yanzu muka gama mgana da Ya Nazir shima haka yace..!

Ya Jafar yace"Nima ya Kirani yana Tambayana sai dai ina mamakin waya fadamai..?

Ya Nasir yace"Tab to har su Nazeem Dake Zaria sun ji Labari..Ya Danmallan din ne ban da masaniya ko ya sani..?

Mamanmu na zaune saman Tabarma cikin baranda tace"Nima yaran nan sai kirana suke Zulahait dai tace min Aisha ta Kirata ta fadamata itama tace Abida ta sanar da ita da wayar Hajiya..Suma mamaki suke suna son ji ko gaskiya ne nace musu gaskiya ne..!

Ya jafar yayi ajiyar rai kafin yace"Dawa dawa zamu koma asibitin..?

Mamanmu tace"Da yaya zaku je ni bazani ba zan zauna wajen Amina..!

Ya zeenatu tayi karaf tace"Ya Jafar don Allah zani..!

Tana rufe baki Hamida da Hanne suka Fito suna Fadin"Muma zamu don Allah..!

Sai da ya Hararesu kana yace"Bazaku ba..gobe da safanan za"a sallamesa..!

Mamanmu ce tace"Kaje dasu don Allah Jafar..Oh na manta ina mai ciwon kunni..?

Ya jafar yace"Yayi sauki sosai kin ma Tunamin ban karbi mganin da Baba Mallam yace nazo na karba ba..bari mu dawo..kuzo mu tafi Dare yayi kuma bana son rawan jiki yarinya ta natsu..!

Ba musu suka shiga Taitayinsu Ya Zeenatu ce ta Dauko kwandon data Zuba abinci yaya daman da hijabinta Jawad na gefenta sai su Hamida sallama suka ma mamanmu suka Fice,ya zeenatu da Hamida Motar Ya Nasir suka shiga ashe matarsa na gaba Anty Fadila da ita za"aje..!

Yaya kuma da Hanne suna Motar ya Jafar

Koda sukaje Aba yaji Sauki sosai sun samesa yana cin kayan marmari ga Ferfesun kayan ciki ne,da suka tambayesa wa ya kawo masa..?

Yace Hajiya Babba da Hajiya uwani yanzu suka fita Idi Direba ya kawosu ya riga ya koshi shiyasa suka ijiye abunda suka zo dashi Aba ya amsa gaisuwan Hamida da Hanne ya Kallesu Cikin kulawa yana Fadin"Ina Amina..?

Hamida tace"Tana gida Baba..!

Daman ta sani Amina na ransa ita din yarinya ce mai shiga rai kaunar da iyayanta Biyu suke mata Allah ne kadai yasanta sai dai baza su bayyanata ba Saboda kawaici da kuma Tunanin ba ita kadai suka Haifa ba

Daganan bai kara mgana ba Jawad yaja kan jikinsa yana Tambayansa ya makaranta yana bashi amsa basu Dade da zuwa ba sai ga Baba mallam ya shigo Cikin shigar Alkyabbansa da Rawaninsan nan suka Ramkwafa suna gaishesa ya amsa cikin Sakin Fuska yana kallon Su Nasir kafin yace"Ashe nan kuka zo..?

Kan Nasir na kasa yace"Eh Baba..Na kawo Fadila ne ganin bata zo ba..!

Yana zama saman kujeran Dake gefen gadon Aba da Ya jafar ya tashi ya bashi yace Lokaci daya"Yayi kyau..Kun kyauta Allah yayi muku albarka..!

Su hamida ya kallah ita da Hanne kafin yace"Naga zara ban ga wata ba..Ina mamana..?

Wannan karon Hanne tace"Tana gida Ita da Mamanmu Baba..!

Kai ya gyada kafin yace"In ta warware zamu daidaito ni da uwata insha Allahu..!

Ba wanda yayi mgana sai Su ya Jafar ne suka Murmusa kawai,Baba Sa"idu ya kallah yana Fadin"Kai ai ka warke tunda naga har kana iya Daukan Jawaad..!

Baba Sa"idu yace"Da sauki Baba..nacema ce su sallame ni yau sukace sai da safe in Likita yazo..!

Baba Mallam yace"Gwara ka kara samun karfin jikin ka kafin ka koma gida..!

Ganin suna gaisawa da Aba yasa su ya jafar sukayi shirin tafiya sai alokacin Baba Mallam ya kalli yaya yana Fadin"Hadiza bana son ganin wannan Damuwar afuskarki Daga gani kin ta kuka..Sa"idu ne babban banza shi ga inda ya kawomu ke kuma kina chan kina kuka har wata Cuta ta kamaki ta Miki illah ina amfaninta..?Ina ce Amina ce Matsalarku..?to ta fita Daga Hannunku ta koma karkashin ikon Umaru sai ku daina Damuwa..Ina ce ba Shikenan ba..?

Yafada yana kallon Aba da kunya yasa ya Sunkuyar da kansa Yaya kuwa kanta na kasa batayi mgana ba har sukayi musu sallama suka fice suka bar Baba Mallam anan da Jawad daya makale ma Aba yaki tafiya Baba Mallam yace a kyalesa in zai taho zasu taho tare. !


******


Tun bayan Fitarsu daga gidan ta Mike ta Leka Amina abinci ta Debomata Farar Shinkafa da Miya Kadan Amina taci don ma Mamanmu tana bata baki Tana Hadawa da Lallashinta Fadi take yi"Ki daina damun kanki ni nasan babu abunda kika aikata..Kuma mganar auran in baki so batare da kowa ya sani ba zan kira shi Danmallan din na Rokesa ya Sauwake miki..Ina Zaki iya da Sakina..?Matansa fa Biyu Kina yarinya Dake duka duka Shekarunki nawa Amina..?Sha Shidda fa Ko sha bakwai din Baki cika ba Har yanzu..Gaskiya akwai kwa ruwa acikin Hukuncin Mallam..!

Take fada cikin bayyana bacin ranta Amina kallonta kawai take batayi mgana ba to me zatace..?Tayi mgana ai bai da amfani komai ya riga ya kare ta rasa Aminu ta gama rasa komai Mganar Rabuwa da Ya Danmallam kuma bata isa ba har gaban Abada bazata watsama Baba Mallam kasa a ido ba kamar yadda bazata watsama Mamanmu ba uwa uba gasu Aba da yaya bata Fatan wani abu ya kara Giftawa,Ta riga ta sani Kaddara ta,kaita wani bingiren da Har yanzu ta kasa dora kanta a inda kaddaran ta jata ta kaita in tana tunawa ma sai wani Rauni da Faduwar gaba su Lulleta waje ne da har Abada zatayi Daraja ba ta sani..!

Har mamanmu ta gama bata tana ta Mita panadol ta bata tasha sai kuma ta shafa mata man zafi ajikinta Da Amina taji Dadinsa kwarai hawaye take yi da kukan zucci acikin ranta tana kara Ninka kaunar dake yi ma Mamanmu tana Fadin dama dama ana Sauya wani abu da Tuni ita Amina ta Dade da Sauya Yaya da Mamanmu amtsayin uwa..!

Amina bata sani ba Allah yana Boyemana wani abun ne kafin mu sani saboda kila alokacin in ya bayyana mana bamu da karfin gwiwan da zuciyan da zamu iya Dauka..!

Boyayyin Fuskokin wani Lokacin Alheri ne garemu kila sanda zasu bayyana Mun Tsaya da kafafunmu Raunin da zai bayyana garemu kadan ne..!

Sai da ta tabbatar da barci ya fara Daukan Amina kana ta bar dakin Dakinta ta koma bata Dangana ako"ina ba sai Cikin Bedroom dinta tana shigowa wayarta Dake kan gadonta ta sake Daukan kuwwa alamun kira ya shigo Da hanzari ta karisa ta Dauki Wayar sunan wacce ke kiran yasa bata Tsaya bata Lokaci ba ta Daga Daman ta sani zata kirata itama din Jiran kiran nata take yin bayan Tabbattuwaar abunda basu taba Tsammani ba..!


"Dayyaba Da saninki komai nawa ya Rushe..Dayyaba da saninki akamin wannan yankar bayan..Da Saninki kika bari yarinyar da ta Ratso cikin gabar aikina alokacin danake Hasashen ina gabda cin nasara..Na sani hakan zata faru shiyasa nake ta Kiranki tun dazu baki Daga Kirana ba..!


Tunda ta fara mgana wannan kamilar Fuska mai cike da Annuri da Tsausayi ta rine ta koma Bakar fuska mai Cike da mugunta da rashin Imani Cikin Wata Murya mai cike da Amon Takaici da Bakinciki tace"Da sanina Bazan bari haka ta faru ba Madina..!

Wlh ban sani ba..Kamar yadda kikaji abun Daga sama nima haka najisa..Shammatan mu Mallam yayi..Shammata mai girman da bamu Taba Tsammani ba Madina..!

Dagachan bangaran Agidan Baba Mallam ashashen Anty Amarya itama Cikin Tsakiyar Bedroom dinta tana Tsaye gaban makeken madubin Dakin nata tana kallon Fuskarta Data wani yarkace na Wunin yau kawai tun bayan Samun Labarin Daurin auran Amina da Umar..!


Cikin Muryanta mai Fadi da ba kowa ya santa da ita ba tace'"Lalle ko ya shammaceni Dayyaba..Sai da na Riga na gama Tsara komai..na gama Tunanin matsala tadaina shigomana cikin Aikinmu ashe suna chan suna Shirya ganina akasa..To basu isa ba..In a zaune suka kwana Ni Madina a tafe na kwana nayi alkawarin yadda bansamu Mallam ba ta bangaran Sakina Da Umar sai na Juya ragamar Mallam da duka abunda ya mallaka..Karya ne..Bayan sakina ba wacce ta isa Umar ya sota har ya Hada Jini da ita Sakina kadai keda Alhakin Haihuwa da Umar ita kadai ce Zata Haifama Mallam Yunus Bazanga Jika,Abaya nayi Sakacin da Har Ya"ya Biyu suka fara Fitowa daga Tsatson Nazir nayi sakaci Dayyaba..Sai dai kinsan aikin da mukayi ya"yan Nazir baza su taba Tasiri a wajen Mallam ba..Kacokan Burina na wajen Abunda Sakina zata Haifane..Sai da nace miki Mu kauda yarinyar nan Dayyaba kika ki bani goyon baya ta rasto cikin Aikin mu batare da Mun gayyaceta ba gashi nan yau Rana Daya ta Fadomin cikin Tsarina Tsarin da bazan taba bari ya Rushe ba Koda hakan na Nufin za"a rasa rai ne..Na kasa gane miki ko kin fara Sauya Ra"ayi ne na Sauya Duka Tsarina Dake..Kila kin hakura da Abunda Sa"idu yayi shekaru yana Kunsamiki ne shi da wannan Munafukar matar tasa..Ko kuma kin shagala kin Fara Kaunar wannan Hatsabibiyar yarinya Dake nemam batamin Shirina..!


Fuskar MAMANMU nake gani ta koma Jawur idanuwanta sun kala sun sauya Launi jijiyoyin kanta har sun Daga Saboda Bala"i cikin wata gigitaciyar Tsawa tace"Dakata Madina..!

Har Abada ni Dayyaba bazan manta Da Bakimcikin da Sa"idu shi da Hadiza suka Dade suna kunsamin ba..Wannan Kaunar wannan Tsausayin da Soyayyar da nake gani acikin Idanuwan Sa"idu kan Hadiza saura kadan su kaini kushewata Har Gaban Abada bazan yafe musu wannan ba..Sai sun Dandanan gudarsu bana yafiya.. ni din nafi Rama Sharri da Alheri..kamarni Sa"idu zai kallah gaban Ya"yana da Matarsa ya SAKENI madina kan wannan Shegiyar yar tasu..?Yarinyar da duk cikin ya"yan Hadiza nafi Tsananta saboda iyayanta sun fi sonta..Sa"idu ya Dade yana kunsamin Bakinciki ya fifita soyayyar Hadiza Fiye da tawa sannan yazo ya fifita ya"yan Hadiza Fiye da ya"yana Saboda Ban Haifi namiji ba ko..?akoda yaushe in na Bude ido na ga Jafar sai naji kamar na kashe kaina..Meyasa na barsa araye ban saka malamin mu ya Kashesa ba..Da yanzu ba haka ba Madina Da yanzu na Dade da kunsa ma Sa"idu da Hadiza bakin cikin da Har su koma ga Allah bazasu manta ba..Duk Saboda Cikar Burina na aro Fuskar da ba tawa ba Madina..Ina zaune cikin wadanda nafi Tsana ina Fifita ya"yam makiyiyata Fiye da ya"yana ina Faman kare ma wanchan yarinyar da bata da wani amfani a wajena...Madina Dukkanmu mafita muke nema saboda haka koma menene ki Fadeshi zan yarda zan amince zuciyata zafi take madina Amsa kuwar Sa"idu nake ji yana Fadamin ya Sake ni Saboda wannan Shegiyar yarinyar ina so suma su Dandana ina so suji yadda na daukii shekaru ina ji acikin raina..!


Anty Amarya tayi Mirmishin Dayafi kuka ciwo kafin tace"Sakacin ki ne Dayyaba..Tun Lokacin da aikin malam ya Tsallake Jafaru ya koma kan Amina nace a kaudashi kika yi yarda..Da yau baya Raye Da wane d'a Sa"iidu zai yi takama..?yau gashi dan Zaki ya Girma harda albarka Haihuwan wani karamin Zakin Dayyaba anya ke naki Tsarin ba Doguwar Tafiya bace..?

Da Sauri Mamanmu tace"Bana kallonshi a Faduwa Madina..Jafar da Abunda ya Haifa ba su da wani amfani kadan nake jira na karar da su..Yanzu ni Sa"idu zan fara mgani Tukunnah so nake naga bakimciki da Rauni acikin Idanuwansa Madina..!


Kai Tsaye Anty Amarya tace"Za"a rasa rai...YAYA ZATA MUTU...!


Mamanmu tace"TABBAS YA KAMATA TA MUTU..sai dai naso sai ta gama shakan bakincikin da na Dade ina Tanadama mata madina..!

Anty Amarya tace"Yanzu Lokacin Daya kamata ta Mutu ne Dayyaba..Mutuwar ta ne kadai zai sa kiga wannan Bakincikim acikin Idanuwan Sa"idu..Mutuwarta ne zai sai nima naga Sa"idu ya koma abun Tsausayi ya dade yana min katsalanda Shi da Hajiya Babba..Zamu fara ta kansa ne kafin mu dawo ta kanta da Saninsa aka Aurama Umar Amina..Da saninsa ta shigo Tsarina nima wannan Damar nake jira da Zan Dandana ma Sa'idu koda Rabin abunda nakeji ne game dashi..Komai na ke kokarin samu Shi da Hajiya babba sai sun tare ni Dayyaba..!

Cikin wata irin Dariya tace"TABBAS yakamata ta Mutu...!

Zata mutu..!

Anty Amarya tace"Zan kira mallamin mu Dayyaba zan sanar dashi ya yanke mata wa"adinta kafin wayewar gari bazan jira ba..bana son wannan karon asamu matsala..!

Mamanmu tace"Nima haka..Wayewar garin gobe Ranar mu ce..Na kosa na kosa naga wannan bakimciki akallon da zan ma Sa"idu..Babban kuskuransa shine ya Fifita komai na Hadiza akaina..Babban Raunina Ina SON SA'IDU..!

Anty Amarya tace"Shikenan kada ki damu ki Dauka an gama..Mganar kudi akwai wani abu a hannunki..?

Mamanmu tace"ki kamallah komai in mun hadu zamu warware komai..!

Anty Amarya tace"Shikenan..Mganar yarinyar nan baki ce wani Tsari zan kaita ba..?

Mamanmu ta saki Dariyan Nishadi kafin tace"Ban damu ba Madina..Ni Kaina na sani Dagani sai ya"yana..Ki kaita Duk Tsarin da kika ga Dama..Koda Tsarin na MUTUWA NE..!

Anty Amarya tace"Tsarin bana Mutuwa bane..Zata sha wahala ne kawai sai daga baya mu kaudata..Tsarin da na kai Balarabiyar nan Tsarin zan kaita Dayyaba..Hotuna zasu zama wajen Umar har Abada Sakina ce Zata Cigaba da amsa matsayin mata awajensa..Wannan alkawarin ne..!


Mamanmu ta jinjina kai tana Fadin"Hakan yayi daidai..Daga gobe komai ya Dawo hannuna..Daga Sa"idun har ya"yan nasa..basu san Wacece Dayyaba ba..Balaraba Ita suka sani..!

Dukkamsu Dariyan suka sheke da ita Dariyan cin nasara da samun Duniya lokaci daya suna yanke kiran atare..!

Abunda basu sani ba wani abun Allah ya Riga ya kaddaran Faruwansa bakin Alkalami ya Riga ya Bushe..!

Tabbas za"a rasa rai..Sai dai basu isa su Dauki ran wani ba..Daman chan ita ran Lokacinta yayi ne..!

Suna gama wayar ta Wurgar da wayar saman gado ta fara Zagaya Dakinta Cikin kaushin murya take fadin"Allah Sarki Yaya..Yau za"a amsa kiran Allah..!

Wayyo wayyo..!

Haka take ta fadi sai kuma ta kece da Dariya kamar mahaukaciya kafin ta koma ta Duke kuma sai ta saki kuka Lokaci Daya tana Fadin"Ba haka naso na zama ba..Sa"idu kai ne sila..Na soka Tun kafin ka fara son Hadiza..Me na rasa baka taba sona ba..?Kasha bansan auran biyayya kayi dani ba..?

Kasha bansan ka Tattara Zuciyarka ka bama Hdiaza ba..Wannan son shi ya ja maka kai da ita..Wannan Tsausayin shi zai kasheta Sa"idu..Ba Laifina bane..Laifin SOYAYYARKA CE..Bantaba son wani Namiji yadda na SOKA BA

Koda bazaka soni ba nayi alkawarin baka isa ka so wani ba..Komai na ya"yanta ya zarce nawa..Duk yadda naso hakan bata Faru ba sai da na zama koma baya agidanka..Kasha bansani bane.?bakayi karya ba nasan Amina ta fara soyayya da wani..bakayi karya ba..Nasani naki fadamaka Saboda Daman ina son damar da zata kara Ruguza rayuwar Hadiza..ban so abunda ya faru ya Tsaya nan ba na so ne Tayi Cikin shege na Tsawartsaku gabadaya..ba Laifina bane..Yaya ki yafemin Sa"idu ya ja miki MUTUWA..!


Take fada tana Hawaye Lokaci Daya Dadariya tana Tuna ranar data fara kama Amina tana waya da Aminu acikin bayinta bata nuna ta ganta ba..Hakan ya mata Dadi Domin bata kaunar cigaba Daga bangaran Hadiza ita da ya"yanta Tundaga Lokacin Da gangan take ijiye wayarta Har Aminan take samun Daman Dauka ta kuma fara Bibiyan Motsinta abunda kowa baisani ba Hatta Haduwar da take yi dashi duk tana sane..Taso ta shirya wani abu ne..Taso ta yi amfani da Amina ta Tsarwatsa Yaya da ahalinta sai dai Mallam ya shammesu matuka shammatam da basu taba Tsammani ba..!

Abunda bata sani ba..Ba Mallam bane Allah ne ya Rubuta abunda ya Faru Daki Daki..Su basu isa su Hana Al"amarin Allah ya Faru ba..Zanen kaddaran ya zama kuma bawa bai isa ya goge shi ba..!


Achan asibiti kuwa bayan fitan su ya Jafar Baba mallam bai kara cema Aba komai ba sai shine da kunya ta kamaasa yace"Nagode Baba..Allah ya kara Girma..Naji zabin da kayi ma Amina badomin kada nayi sonkai fa sai nace nafi kowa Murna da hakan..!

Baba Mallam ya yi mirmishi cikin wani yanayi yace"Sai da ga baya naga kamar nayi gaggawa Sa"idu.Abunda kuka zata ba haka bane..Jikina yayi sanyi naji kamar na so kaina nima dana aurama uwata Umaru a karancin Shekarunta na yarinta..Da ace na sani da na jira..Kadan da na aura mata wanda ke sonta Tsakani ga Allah ya kuma dace da ita..!

Yafada yana jin Tsausayin Aminu na kamasa yana Tuna yadda iyayansa suka nuna jimamin Lamarin bayan sun gayama mallan duk abunda Aminu ya fadamusu kan Amina ce ta Dakatar dashi na bayyana kansa sun yi sallama Cikin wani yanayi ya Rakosu har waje suka iske Aminu Cikin wani yanayi wanda Dole bawa ya Tsausaya masa..!

Baba Mallam yaji Dama ace ya Jirakadan..Da duk haka bata Faru ba..Sai da ga baya yaga kamar yayi gaggawa..Da ace Nazeem ya aura mata..sai daga baya yace dama Nasir ne..Umar yayi ma Amina girma Tazaran Dake Tsakaninsu kamar tazaran kasa da sama ne..!

Yaji da ace Aminu zai karbi Tayinsa Daya Aura masa Hanne ko Hamida Domin ya wanke kansa Daga wannan zargin sai dai ina Agaban idonsa suka sakashi a mota cikin wani yanayi suka Dauki Hanyar Yola..!

Shi kanshi Aba jikinsa yayi sanyi da bayanin Baba Mallam tun ma Daya bude baki yana fadamai abunda ya Faru bayan zuwansu Aminu..!

Dukkansu shuru sukayi sun kasa mgana sai chan Aba yace"Baba Komai fa Da kaga ya faru yau..tsarin Allah ne..Mu yi fatan wannan Auran ya zama Sillar warwarewan duka abubuwansu Allah ya amintar da zuciyoyinsu waje daya..!

Da Amen Baba Mallam ya amsa abunda basu sani ba sun yi addu"an akan gaba ammh Allah ya Riga ya amintar da Ruhin Amina da Umar waje Daya Alkaalamin kaddaransu ya Riga ya Bushe!

Sun dade suna kara Tattaunawa sai da Shamsu yazo shi da zai kwana da Aba ranar sannan Baba Mallam yayi mai Sallama ya koma gida Cikin Damuwa da Tunanin yayi gaggawa..!

Abunda ya Dade bai Faru ba yau ya Faru Baba Mallam bai isa shashensa ba kai Tsaye shashen Hajiya Babba ya Sauka kuma aidon matansa duk da Ba ita ke dashi ba Hajiya Nasara ne..!

Yana cikin Damuwar da ita kadai zata iya kwantar da mai hankali.

Haka yaje mata yana Fadin"Zainabu anya banyi gaggawa ba..?

Ina ji kamar na zalunci uwata..!

Hajiya bata Fahimci mganarsa ba sai da ya warware mata na zuwan iyayan Aminu ya karishe da Fadin"Meyasa na Zabi Umaru..?Meyasa ban zabi Nazeem ko Nasir ba..?Uwata tayi kankanta Umaru ba Tsaranta bane..ba zata iya zama cikin mata Biyu ba Hajiya..Nayi gaggawa..!

Yake fada lokaci Daya yana Cire rawanin kansa..!

Hajiya taji jikinta yayi sanyi itama Sai kawai ta Riko Kafadan Mallam tana maimaita Hasbunallahi cikin ikon Allah shima ya shiga amsa mata har ya samu natsuwa zaunar dashi tayi kan gado taje ta Debo masa ruwa mai Sanyi yasha yayi hamdala sannan ta kallesa tace"Bakayi gaggawa ba mallam...Daman chan Amina bata da miji sai Danmallam..Ba Tsarinka bane naa Allah ne..Ina ji ajikina wannan aueran Alheri ne zamu ji Dadinsa Watarana..shi kuma yaron Allah ya basa wacce ta fi Amina haka Allah yaso..!

Kalamanta sun kwantar mai da Hankali Cikin natsuwar daya samu yace"Ameen ya Allah zainabu Abu mai Tawagayen suna..Bani abinci in ci inji dadin saka miki albarka..!

Dariya kawai tayi tana Ficewa Daga Dakin ya Bita da kallo aransa yana Tunanin Har Abada bazai taba samun macen kwarai irin zainabu ba..!


Sai da ta dawo da farantin abinci ta Sauke agabansa sannan tace"Muna da bakuwa fa..?

Yana Saukowa saman Cafet din Daya malale Dakin yace"Bakuwa kuma..?

Tana kokarin zama gefensa tace"Eh Hajiya BATULA ce kanwar Uwani Tazo Dazu da yammah nan daga Tsafe..!

Bai ce komai ba illah kai daya gyada ita kuma sai ta fara kokarin zubamai Tuwon shinkafa miyar ogun din da akayi..!


*******

2:30pm na Dare..!


Acikin Tsakiyar Falon Hajiya Uwani Zaune suke ita da yar"uwanta kwara Daya da suka fito ciki Daya su ka kuma Taso acikin jerin ya"yan da Alhaji hamza mahaifinsu ya Haifa..!

Tayi aure mijinta ya rasu da Dadewa sai dai bata taba Haihuwa ba..Kuma tundaga Lokacin bata sake aure ba kasuwanci take yi..!

Haj.uwani Dakin da Umaimatu ke ciki ta kallah kafin ta sauke numfsshi Lokaci Daya tana Fadin"Anya Batula kina ganin ba Zunubaina ke shafan Umai ba..?

Duba kiga irin wahalar da mukeyi akanta har yanzu taki Lafiya Sa"o"inta duka Mallam ya aurar dasu ita ba Boko ba ba aure ba gani cikin kishiyoyi bana so aga gazawata..!

Wacce aka kira da Batula ta gyara zama suna kama da Hajiya uwani sosai..!

Cikin Yar dariya tace"Bai kamata ki karaya ba tun yanzu Uwani..Matsalan Umaima Daga Allah ne kin sani duk inda mukaje haka ake fadamana..Na Fada miki zata samu lafiya..Yanzu dai mu ijiye mganar Umaima agefe mu yi wacce Itace Dalilin zuwana..!

Haj.uwani ta gyara zama tana Fadin"Uhmm..Acikin Abunda muke so mu kauda Batula wani abun yazo ya kara shan gabanmu..Yakin ba yanzu zai kare ba Batula..Mallam yau da azahar ya Daurama Umar aure da Diyar Sa"idu Amina..!

Batula ta zari ido kafin tace"Aure kuma..?

Haj.Uwani tayi dariya takaichi kafin tace"Eh ba wanda ya sani sai da aka Daura mukaji..Kuma bai yimana bayani ba..Kina gani yazo ya shige shashen giwa bai nemi kowa ba..!

Batula ta karkace kai kafin tace"Shine yasa kika Tadoni tundaga Tsafe zuwa Gumel Uwani..?

Kai ta gyada mata karamin Tsaki taja kafin tace"Da kin fadamin tun awaya wlh da ban zo ba

Wannan ai karamin aiki ne..Me zai gagaremu Yarinyar wai me take takama dashi data baki tsoro..?

Haj.uwani tace"Ba komai yarinya ce karama Sa"ar Sadautun Amarya..Yanzu suke SS1 MA..!

Batula ta karaa sakin Tsaki kafin tace"Abu mai sauki..Ai tunda muka iya kai Sakina kasa kowa ma ta auri Umar sai mun kaita kasa..Hajiya babba ta samu Mallam da duka komai nasa to ta bar shi haka bata isa ta bangaran ya"ya kuma ta miki Zarra ba..Kada ki manta mu mukasa akayimana aiki kan manyan ya"yansa da sukaki zama kusa da Hajiyan da Mallam din mu ka Tura kurciyan Umar Madina yadda bazai ji sha"awan Dawowa gida ba kuma muka Tura Kurciyan Nazir Lagos yadda Har Abada zai iya zaman Gumel ba..Abu kadan ya ragemana Nazeem da Uzairu su gama karatu su Dawo gida Lokacin sai mu maida Sa"idu mara amfani alokacin Mallam bai da wata mafita sai ta ya"yanki sune Jagora Uwani!

Haj.Uwani Ta saki kayattacen Mirmishi tace"Kin manta baki Tunanin Jikokin ya"ya na ne kadai Mallam zai kallah yaji Dadi ba..Tunda Mama ta fadamana Mallam yana matukaar son ganin kwam Umar aduniya na Mike Tsaye,Duk Shigen Shigen Marliya sai da nasha gabanta Bata sani ba ko gobe Sakina ta samu Ciki sai ya Lalace Mama ta tabbatarmin Umar haka zai zo ya koma bazai taba ganin kwamsa aduniya ba..!

Batula tayi dariya kafin tace"Wai itama balarabiyar madina din kin gama mata aikin..?

Haj.Uwani tace"Tun yaushe..Tare suka sha mganin Mama cikin Ruwan Tea din da suka tako har Fadona na Hada musu sun koma ba Dadewa..Sakinar tayi bari har Umarun yaxo karban mata mgani da Marliya ta karbi mata na Hausa..Araina nace kyayi ki gama..Wannan gidan na Uwani ne da ya"yaanta..!

Atare suka saka Dariya kafin Batula tace"To wani mataki zamu Dora sabuwar zuwan namu..?

Haj uwani tace"Tsarin da na Dora na gabanta zan dorata..Duk da nasan ma Umar b abunda zai ci da wannan mara kunyar yarinyar sai dai kinsan Namiji baka rainasa..Awajena bata da wani amfani kamar yadda na Maida yaron nan NASIR mara amfani a wajen Mallam in ba ya gansa bama mantawa yake yi dashi..!

Wata Dariya suka saka har da Tafawa kafin Batula tace"Don Mallam din da Giwar suna Tsaye ne..Ai da tuni burin mu ya cika..!

Haj.uwani tace"Abu daya na kasa..Kai Maallam kasa shi da Hajiya..Mama tace har Abada bazan ci galaba akansu ba sai dai kan yaran

Basa wasa da ibada sannan azkar kamar ya zama jikinsu in ba ikon Allah ba Sihiri bazai taba kamasu ba..!

Batula tace"Shiyasa nace ki bar asaran kudinki..Mu koma inda Mama tace sai muga riba..!

Haj.Uwani ta saki kayayyatacen Mirmishi kafin ta koma ta kishingida kan kujera Lokaci daya tana Fadin"Aikuwa naga Riba Batula...!


Ashe ashe basu sani ba..Suna Tufka ne..Daga gefe wata Boyayiyar Fuskar tana Faman warwara..!








*Janafty*