Chapter 26
*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*
*Sadaukawa ga Halima yusuf gwarzo Besty Alherin Allah ya kai miki a dukkan inda kike Ameen*
*🅿️26*
Ranar Hajiya Uwani keda Shashen Mallam shiyasa ta chaba ado tana tashin kamshi ta ko"ina,Ta shigo da Fara"arta sai dai kuma ya mamaye hakan da bakincikin ganin Amina gaban Mallam suna hira saboda Takaici ji tayi kamar ta koma da baya sai dai sun riga sun ganta bata da yarda zatayi sai ta Saki Fuskarta ta Kakaro Dariya da Mirmishi ta Dora Saman Fuskarta..!
Baba Mallam ya dago kansa Daga kan Amina ya sauke kan Hajiya uwa data Tsaro kwalliyanta cikin Doguwar rigar shaddanta Nan da nan ya saki Fuska yana kallonta acikin matansa kaf ko Anty Amarya bzata gwadama Uwani Kwalliya da kamshi ba Duk da Ta kwana Biyu a duniya bata yarda ta zauna ba gyara ba ita din yar Kwalliya ce kowa ya sani.!
Cikin Fara"arsa da Sautinsa yace"Lale da zuwa Hajiya uwa..Uwanin Alheri uwanin Yunusa daman yanzu nake Fadi araina ko an tsaya yanga ne yanmatancin ne ya tashi!
Kanta sai ya kara girma ta kariso Cikin takun mata har ta kariso gefensa ta zauna sai Amina ta matsa gefe Tana gaisheta ta amsa Tana Fadin"Ka fahimci abunda ya Tsaidani ko Mallam..?
Yana kallon Fuskarta yace"Na fahimta..Uwani uwayen kwalliya da ado..!
Dariya tayi Tana kallon Amina da kanta ke kasa tana wasa da Gefen Hijabinta cikin Fara"a tace"Allah yasa ban katse Hirar surukanta ba. !
Sai da ya kalli Amina kafin yace"Ko da Sakina bana Surukanta Uwani..Ballatana Amina..Itadin Uwatace..Hira muke ta Tsakanin Uwa da abunda ta haifa kin kum san bamai iya raba wannan soyayyar..!
Tana Mirmishi tace"Ba shakka kam.Ko na koma sai kun gama ne Mallam..?
Kai ya girgiza kafin yace"A"a ai bazata kare ba..sai dai mu barsa zuwa gaba..Mamana tashi kije shashen Hajiya ki kwana zuwa safe Dare yayi su Akilu sun kwanta ballatana na Taso shi ya rakaki..!
Amina batayi gaddama ba ta mike tana musu sallama ta fice zuwa shashen Hajiya babba tana jin sukuni aranta da bata Furta abunda Mamanmu da tsarata mata da batasan ina zata kai kunya ba..!
Sai da Amina ta fice sannan Hajiya uwa ta gyara zama tana fadin"Mallan kayi mgana da shamsu kuwa..?
Kai Tsaye yace"bai kirani ba meya faru..?
Cikin kwantar dakai tace"Kudin hannunsa ne duk suka kare wajen Registration,yace min yana son aturamai wasu kudin..!
Dayake shamsu ya samu gurbin karatu a Federal Universty Dutse ne har ya tafi..!
Baba mallam kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Nayi mgana da Aliyu abokin Umaru yace min har Daki ya samu nan Kusa da makarantar bai ce Komai ba..Ammh zan kira shi Shamsu naji kinsan ba kasafai zaka rika sakarma yara kudi domin sun Tsallake gaban zuwa karatu ka rika saka ido kada watarana sakewarka ta saka su jawo maka wani abun mgana zan yi mgana dashi kuma zan saka shi Aliyun ya Bincikamin inda bukatar wani Abu zam ma Sa"idu mgana zai Turamai Insha Allahu..!
Hajiya uwani gabadaya takaici ya Rufeta,kamar ta saki kuka haka take ji sai dai bata nuna ba sai ma kai data Rausayar tace"Shikenan hakan yana da kyau Mallam ka bincika din..!
Daga haka ta tsuke bakinta tana wani Nazari har yaushe ne ya"yanta zasu zama na Farko wajen Mallam bayan ya"yan Hajiya Babba da Sa"idu Burinta na shekaru bazai cika da wuri ba kenan.
Shi ya katse mata tunani da Fadin"Ya jikin Umaima ina Fatan ta daina Ihun nan cikin Dare..?
Ya famo mata inda ke mata kaikayi Cikin Karin Damuwa tace"To yayi sauki za"a ce Mallam..Anya ba mganar malamin nan gaskiya bane..?
Cikin Kallon sama sama yace"Dayace mene..?
Sannan wajen wani malami kika kai min yata ban sani ba..?
Sai alokacin tasan tayi barambarama ai baisan sunje har Niger kan matsalan Umaima ita da Batula ba..!
Cikin Inda inda ta fara mgana da sauri ya katseta cikin Kaushinsa yace"Ina kika kaita kuma me malamin da kika bashi yarda Fiye da Ubangijinki yace..?in kikamin karya wlh zan ci Mutumcinki in nayi bincike na gano gaskiyan mgana..!
Sai Jikinta ya fara rawa tasan Halin Mallam in bata Fadamai ba bazaman Lafiya ita kuwa dake cikin Kishiyoyi har uku mezai sa ta dinga Fada da Miji..!
Da hanzari tace"Wlh ba da son raina naje ba labarinsa naji ance yana bada mganin Aljanu..k..
"Ki amsamin Tambayata..!
Katseta yayi cikin bacin rai bakinta na rawa tace"Niger ne..Mukaje kuma..kuma yace ne wai Ture ne akayimin bai sameni ba ya Fadama Umaima..!
Wani wawan Tsaki yaja kafin yace"Wa ya rakaki wajen..?
Kai Tsaye tace"Kanwata Batula ce..!
Yana kallonta cikin bacin rai yace"Ba tun yau ba na lura da Batula ta yarda da Bin malaman nan makaryata makiyan Allah kema shine ta jaki kikai min ya gaban wani mushuriki da sunan neman mgani akwai abunda zai baku wanda Allah bazai baku bane..?Meyasa wani Lokacin baku da Tunani ne Uwani..!
Da sauri ta tareshi ganin yadda Ransa ya baci tace"Wlh ni da batula muka je..Ban je da Umaima ba..!
Cikin bacin rai yace"Ko baki je da ita ba kin kai laluranta gabansa kin Tallatamai shi kuma ya cikaku da karyansa..Banda Hada fada da karya waye zai miki sihirin da har zai koma kanta..?To ban yarda da wannan ba Ni ya'ta Lalurarta daga Indalahi ne kuma garesa nake nema mata waraka in ta warke wannan ikonsa ne in bata warke bama wannan ikonsa ne..Kada na Sake ji koda wasa wata mgana irin wannan in haka ta sake faruwa komai ma zai yi faruwa zan dauki mataki mummana akanki kin ji na Fadamiki..!
Ya karishe faada cikin bayyana bacin ransa da sauri ta Sulale kan Gwiwoyinta tana fadin"Kayi hakuri mallam..Insha Allahu haka bazata kara faruwa ba..!
Bai kalleta ba yace"Bana son Rabuwar kai kan mata na da yara na..Nayi shekaru ina hada kan iyalaina Waje Daya..Nan duniya bayan ku da Iyalan Sa"idu bani da wani Ahali da zan kallah nace nawa ne sai ku..To ki sani in kina Biyema mganar malaman karyan nan zaki haifarmin da Gaba cikin Gidana kuma in hakan ta faru Uwani zaki sha mamakin hukuncin da zan yanke akanki Wlh..!
Gabanta ya fadi taya ya komai zai kwace mata Burinta bai cika ba yasa ta kwantar dakai tana ta basa Hakuri sai da taga ya Hakura sannan ta Sauke Numfashi ta koma ta zauna tana kokuwa da bacin ran dake taso mata..!
Ba domin ta kasa galaba akansa ba da Tuni Mama ta samo mata kan mallam ya zama sai yarda tayi dashi sai dai ina ta gaji da kashe kudi akansa ta Hakura Allah yana tare dashi kuma ya kare bawansa wani abu bai isa ya Cutar dashi ba sai dai ko in ya so..!
Ganin yadan sauko har suna Hira yasa ta Sako mganar dake cin ranta"Mallam ya mganar Amina da Danmallam ne..!?
Naji bakace komai ba haryanzu..?
Kai tsaye yace mata"Har gobe sunanan a matsayin miji da mata..wani abu kike son sani kuma..?!
Ya kalleta cikin son Tabbatar da abunda yake Tunanin take son ji game da lamarin.
Da sauri ta sauya mganarta da cewa"Maallam mganar tarewa fa..?ai tunda angama mai wahalar itama sai yayi mata Visa da Shedar zama achan kamar yadda yayi ma Sakina ya Tafi da matarsa ni aganina zai fi mallam..!
Ya dade bai yi mgana ba har ta Fidda rai kafin taji ya sauke numfashi Lokaci Daya yana fadin"Bazan yi haka ba..zan bama Mamana daman da bana ma kowacensu..Bazata tare a matsayin matar Umaru ba sai ta gama makaranta ma"ana in sunyi Candy in Hadata da yan"uwanta in aurar dasu..!
Hajiya uwani da Farimciki ya cika sai ta kanne cikin wani yanayi tace"Nan da shekara nawa kenan Mallam..?
Kai Tsaye yace"Hajiya tace alissafi Shekara Daya da wani abu in bai kai Biyu bama..!
Ranta Fari tas kafin Lokacin nata Burin ya cika wato ma ta kwantar da Hankalinta Amina bata cikin Tsarinta yanzu tunda mijin ma baisan da ita ba kuma tarewar ma ba yanzu ba hakan ya Bala"in yi mata Dadi har sai da Fuskarta ta Nuna cikin dan yanayinta tace"Gaskiya kuma fa hakane..Ko Sa"idu kada yaga anyi mata Rashin Adalci..!
Wani banzan kallo yayi mata Kafin yace"ko Sa"idu ina da iko da Kansa ballatana abunda ya Haifa..Ko cutar dashi zanyi bazai taba mgana ba..Ballatana ba wannan Tsakani na dashi.Kauna ce da Biyayya Tsakanin Uba da abunda ya Haifa..Kada ma na Sake jin wannan mganar Sa"idu namin Biyayyar da ko ya"yan dana Haifa basa min yana wahala dani da Dukiyata batare da na yankamai albashi ba gayamin cikin Tarin mazan da na Haifa akwai wanda ya zauna Dani yake wahala dani kamar Sa"idu..?
Kai ta girgiza ta kasa mgana Miyan bakinta ya kafe cikin Dattakonsa yace"To ki saka aranki Sa"idu Shakikana ne..Kafin na same su shi na Sama kuma ina masa kwatakwacin kaunar da Uba zai yima abunda ya Haifa..Ki saka wannan aranki..!
Daga haka bai jira cewarta ba ya mike Dauke da Littafinsa ya Nufi Cikin Bedroom dinsa yana Fadin"Ni na shiga ciki sai kin shigo..!
Da kallon Takaici ta bisa kamar tatashi ta Makesa haka take ji Sa"idu rai Daya ya hana Burinta cika agabanta Mallam ke fadin yafi yemai ya"yan daya haifa Dariya tayi acikin Ranta Saboda itace silar rashin zaman Umar da Nazir agaban Ubansu ballatana su taimakamai bata so su sha gaban ya"yanta Yanzu kuwa Burinta yana gabda cika Nazeem ya kusa gama makaranta sannan Tsumi da Tanadi ya karanta wato Economics sannan yayi Degrre dinsa na Biyu kan abunda ya shafi Kasuwanci yana Dawowa zata san yadda zatayi Sa"idu ya matsa ya bama mai waje wajensa ya kasance shine kan duka Dukiyar Mallam din Kafin Uzairu shima ya gama yazo su hada hannu hango kanta Take shekara Biyar masu zuwa ita Amtsayin Hajiya babba..Ya"yanta ne masu gidan ita ce mai Bada Umarni da mgana da yawun mallam wannan Tunanin yasa ta farinciki ta tashi Cikin Takunta ta nufi Bedroom din mallan tana cigaba da Tsara wasu abubuwan acikin ranta..!
Amina kuwa sai washegari Hajiya ta ganta saboda sanda ta shigo gabadayansu sun yi barci Ya Abida ce kadai idonta Biyu tana karatu hanne ma ta Dade da yin barci.
Da safe ko gida bata koma ba kayan Hanne ta saka da hijabinta na Hadda Tunda guda Biyu hannen gareta.
Suka tafi Hadda Hamida bata je ba bata da Lafiya ciwon mara Ya zeenatu ke fadama da Amina taga bata ga Hamidan ba..!
Sai da yammah da suka Dawo Amina ta Dawo gida ita Da hanne suka Duba Hamida taji sauki ma,Hanne bata jima ba tayi musu sallama ta wuce gida Mamanmu daman jiran Amina take yi taji ya ake ciki tun Safe Aanty Amarya ta Kirata taji Labari mai Dadi ba wani bayani shiyasa Hanne na Tafiya taja Amina kuryan Dakinta Tana Fadin"Ya kuka yi da Mallam din..?
Amina ta Sadda kanta kasa kafin tace"Mammanmu na kasa..Bazan iya kallon Baba mallam nace bana son jininsa ba..Bai kamata na rama Tarin Alherinsa da sharri ba..Sannan in Aba yaji Wlh sai ya kusa kasheni agidanan..!
Ta karishe kamar tayi kuka ba Domin mamanmu ta kai zuciyarta nesa ba da sai ta kaima Amina Duka yadda Wani Takaicinta ya kamata ammh duk da Haka sai da ta Tureta tana Fadin"To Shikenan tunda kin kasa..sai kije..Sakina ta gasaki don Ubanki..bakuma zaki taba Daraja ba Tunda baya Sonki..Kuma matar Cushe bata Daraja .!
Yadda ta Zageta ta kuma Tureta yasa tasan ranta ya baci da Sauri ta riko Hannayenta tana fadin"Ba haka bane mamanmu..Wlh na kasa ne bazan yi kallon Baba mallam nace mai bana son auran nan ba..!
Mamanmu da kanta har ya fara ciwo Saboda takaici tace"Shikenan na fita Acikin mganar nan..Ba ruwana daman yancinki zan kwatan miki..!
Amina taji kanar tayi kuka kafin tace"To ke kije mana ki fadamai mamanmu..!
Hararanta tayi kafin tace"Saboda ni ce nake son rabuwa da shi ko..?ba inda zani ke kika sani ni sakamar min hannu Ke ji chan ki karata Wlh Amarya da Sakina bazasu barki ki zauna Lafiya ba.!
Amina tace"Tab..Sai dai ni ce bazan bar su zauna Lafiya ba Mamanmu..!
Ta razana gabanta na Fadi tace"Bangane ba..?
Amina tayi dariya kafin tace"To ai ba Tsoronsu nake ji ba..mamanmu ai Amina nake kirarina badai ta Mutum ba sai ta Allah su din banza!
Basu isa suyimin Abunda Allah bai min ba..!
Ta dade tana kallon Amina sai taga kamar Shagube tayi mata shiyasa cikin son tabbatarwa tace"ko kin fara son Danmllan din ne..?
Ta fada cikin Hararanta Amina ta Zaro Ido kafin tace"Ni..?Allah ya kyauta..ni Aminu kadai nake so..!
Ta Karishe Fada cikin wani yanayi Mamanmu ta sauke Numfashi kafin tace"Na Dauka kin fara son shi ne nace Ke kika sani..Domin Danmallam dai ya fara Tsufa auran wuri ne bai yi da kuma Haihuwar da bai samu ba..Kadan ne Aba din ku fa ya Girmesa..
Amina ta zaro idanuwanta suna shekk tace"Kai Mamanmu ko Aba fa bai Tsufa ba ballatana ya Danmllam..!
Mamanmu tace"Eyee..Kina son shi kenan Tunda ke baki ga tsufansa ba..?
Tafada tana Dungure mata kai Amina ta Dafe wajen tana fadin"Allah ya Tsari Amina..wannan ne zan so..Ya taba fa cemin banda natsuwa kuma ni wai kazama ce..!
Ta fada kamar alokacin yake fada mata Takaicin abun na Dawo mata Mamanmu ta kwace hannunta tana Fadin"ni sakeni..Kekika sani..Ba ina neman hanyar kwatan miki yanci ba kina bani kunya ba..Na barki dashi..Kin dai ji kazama yake ce miki Allah kadai yasan kuma wata kalma zai kara Jifanki dashi in ya ganki agidansa an riga an Tusamai ke..!
Amina ta Tura baki kafin tace"Sai na rama wlh..!
Mamanmu ta kalleta cikin Tunanin mafita ko mgana batayi ba ta Tura Kofar Tiolet din Dakinta tana Fadin"An kira sallah..!
Amina fita tayi ranta yadan yi sanyi ganin kamar mamanmu ta Dauki Zafi da Farko ammh Taji Dadi taga Daga baya ta saki ranta ajiyar rai ta sauke Tana jin kaso mafi yawa daga cikin Damuwarta suna yayewa Samun uwa irin Mamannu is a Bleessing..!
Mamanmu kuwa har Aba ya Dawo ta kasa samun wata mafita tana ganin ta bangaran Amina ba nasara Dole zata Jaraba ta bangaran Sa"idu ta Latsa ta gani ko zata ga Jini..!
Shiyasa koda ya dawo tayi wanka ta Shirya cikin riga da zani na Atamfa Hamida ta saka ta gyara Shashen nasa Dazu dataji Saukin jikinta Kayan abincinsa kuma tun kafin ya Dawo akai kai komai ciki.
Sanda ta fito duk suna Tsakar gida kan Tabarma suna Hira an kunna Gen akwai haske shiyasa basu shiga sun kwanta ba..!
Ganin bata ga Jawad ba yasa ta kalli Zeenatu Dake fama da karatu tace"Ina Jawaad..?
Hamida ce tace"Aba na shigowa ya makale masa..!
Mamanmu kamar ta saki Tsaki yaron nan zai zame mata ciwon ido sai ta rabashi da Uban taga ya zai yi shege kawai..!
Mirmishi ta saki kafin tace"Ni ina Dakin Abban ku. Ku kwanta da wuri ke Zeenatu saboda makaranta Gobe..!
Da toh suka amsa mata har ta wuce suka cigaba da Hiransu Amina da Hamida suke ta uban gaddama sai da Zeenatu ta Daka musu Tsawa tace sun dameta.!
Koda ta shiga Shashen Aba ta iskesa zaune shi da Jawaad suna cin Tuwom Shimkafa Miyar shuwakan data Girka Dazu da yammah Saboda Aba din Ranta ya kara baci ganinsa Dare Dare kan cinyar sa yana bashi Tuwon abaki Dakyar ta iya shigowa cikin Dakin tana kokuwa da yanayinta..!
Kan kujera ta zauna Tana fadin"Sannu da zuwa..Ka shigo ina wanka..!
Da yauwa ya amsa mata yana fadin"Haka yaran suka ce..!
Kafin ya cigaba da cin Tuwonsa yana Tambayan ko Jawad ya koshi ya Dagamai kai alamun eh Mamanmu tace"Daman Gulma ce irinta Jawad..Bai dade da gama cin nasa ba .!
Aba yace"Kinsan yaro..Ballatana ko abaya Jawad dani yake cin abinci ko da riga yaci nasa ne..!
Takaici bai barta tayi mgana ba Tana kallonsa har ya gama cin abimcin tatashi ta Dauki Faranti ta Fito dashi Ta mikama Amina tana fadin"Saka shi a Kitchen Amina..!
Da Sauri ta zo ta karba ita kuma ta koma ciki ta ga Jawaad ya gyara zama kan cinyarsa yasa ranta ya kara baci ta kalli Jawad tana Fadin"Jawad tashi kaje dakina ka kwanta..!
Tunda tun bayan rasuwar yay wani Lokacin in ya saka Rigima wajen Aba yake kwana ita kuma bazata iya Daukan wannan ba ta gama da Uwarsa kuma shi yazo ya rika sakata Damuwa ba..!
Aikuwa make Kafada yayi alamun bazai je ba Aba ya kalleta yana Fadin"Kyalesa in yayi barci sai ki kaisa..!
Takaici bai kara sa tayi mgana ba ta koma kan Daya daga cikin kujerun falon ta lafe ta maida hankalinta kan Tibin Dake falon cikin tashan Larabawa tana ji Aba ya maida hankalinsa kan jawaad yana Biyamai karatun da sukayi yau a makaranta Tun tana jinsu tana Gumduma ma Jawaad zaki aranta har ta fara barci Sama sama taji Aba na Kiran sunanta ta Bude ido tana kallonsa cikin Mamaki yace"wai har kin yi barci..?
Har jawad yayi barci na mika shi wajen Zeenatu nace yayi Fitsari kafin ya kwanta..!
Mikewa zaune tayi Dakyau tana sosa idonta kafin tace"bansan sanda barcin ya kwasheni bane..!
Kai ya gyada kafin ya wuce ciki yana Fadin"Bari nayi wanka..!
Da toh ta Bisa kafin tatashi tabi bayansa Yana shiga wankan ta Fitomai da jallabiya da gajeran wando ta koma ta zauna tana jiran fitowarsa Daya fito ya ganta sai da yayi mamaki cikin mamakin yace"Baki kwanta ba..?
Kai Tsaye tace"Eh ina son mgana Dakai ne..!
Bai damu ba yace"Bari nayi shafa"i da wuturi ke kin yi ko.?
Da sauri tace"Eh saboda bata so yace sai tayi alhalin ba Damunta yayi ba Khamsul salatin ma dole take yinsu.
Sai da ya saka Jallabiyan ya Shimfida Darduma ya tada salla har ya idar tana zaune ganin haka yasa bai Tsawaita addu"a ba ya juyo yana kallonta kafin yace"Ina Sauraranki..!
Gyara zama tayi tana Tattaro Jarumta da wani Kalan Tsausayi tace"Abban Jawad daman kam mganar Amina ce..!
Cikin dan Fargaba yace"Amina..?me Aminan ta sake yi kuma..?
Da sauri tace"Kwantar da Hankalinka batayi komai ba..Kawai ni ke son mgana Dakai kam Auran da mallam ya hada Tsakaninta da Danmallam na wajem Hajiya..!
Kallonta yake yi ko Kiftawa bai yi ba cikin mamakinta yace"Ina jinki..Sai me ya faru kuma..?
Mamanmu ta gyara zama tana Fadin"Tsakani ga Allah Abbansu baka ganin an kwari yarinyar nan..?
Cikin kosawa yace"Ina jinki..jeki kai Tsaye kan mganarki..!
Mamanmu bata Lura da yanayin kallonta da yake yi ba ta cigaba da Fadin"To gani nayi shi ba sa"anta ba In fa aka duba ya kusa haihuwanta in da auran kauye yayi..Ina Amina zata kai shi..?Sannan ga tarin Kishiyoyi har Biyu Abbansu a shekarun Amina batasan Dubarun zama da Kishiya ba,Shiyasa naga bari nayi maka mgana gaskiya aduba wannan al"amarin..!
Kallonta yake yi yana kokuwa da bacin Ransa kafin cikin Kaushin Murya yace"Ita Aminar ne tace miki bata son Dubarun zama da kishiyoyi ba..?To don Ubanta agidan nan Tsakanin mata Biyu ta taso..Gidan Baba Mallam kuma Hudu garesa reras gayamin wani karatu ne ya Ragemata bayan na wadannan gidajen..?
Sai mamanmu ta Daburce cikin Inda inda ta fara fadin"Ai kasan yarinya ce..Allah na Tuba ko hamida girman jiki ne..Ammh sai wannan shekaran ne suka shiga sha shida fa..Ina zata kai Umar..?
Akwai zalunci gaskiya..!
Kai Tsaye yace"Naji an zalunceta..Yanzu me kike so ayi..!?
Ta zata ya yarda da mganarta ne yasa Cikin Fara"a tace"Yauwa..Mallam kawai zaka je ka fadamawa baka son wannan Hadin na tabbata zai saka Danmallam ya saketa..!
"KE BALARABA..!
Aba ya Daka mata Tsawa da sai da ta Tsorata cikin Bacin rai mai Tsanani yace"Ita Aminar ne ta aiko ki kizo ki Fadamin naje na samu Mallam na Fadamai bata son auran Umar..?Tana so ya saketa..?
Mamanmu Sai taji ta kasa mgana Mikewa yayi cikim bacin rai yana Fadin"Dake nake mgana..!
Cikin kwantar da Murya tace"ba yadda ka Dauka bane..Wlh basu dac..!
"daman waya ce sun dace..!
Ya katseta cikin Tsawa kafin ya Cigaba da fadin" A yanayin Rayuwar Umar Kwata kwata Amina bata Dace dashi ba..Ita din ba ajinsa bane..Kinsan waye Umar kuwa..?Kyakyawan Asali Ubansa Malami ne, da ba iya Nageria ba kasashen Duniya sun san da zamansa Umaru nada shaidar Degree guda Biyu akan abunda ya shafi Qur"ani da Hadisai Balaraba tashin Madina karatun Madina garin ma"aiiki Kinsan adadin iliminsa..?Koyarwa yake a Babbar Jami"ar Musulunci ta Madina Shine kike fadin an zalunci Amina domin an aura mata Mutum nagari mai kamala da nagarta..Mai Sanyi mai biyayya da gudun mgana Shine kike fadin an zalunceta..?To bari kiji ba ita aka cuta ba Shi aka Cuta..Shi aka Tauye Balaraba ammh bai Bude baki yayi mgana basai ku..!?to ni Ubanta banda Sanadin Ubansa da ko Filin jirgin sama bazan taba Tsallakewa ba..!
Ya karishe fada cikin bayyana bacin ransa har jijiyon kansa na mikewa.
Mamanmu kuma ta Daskare Rashin Sukuni ya shigeta tasan ba Nasara wannan gabar bata ci nasara ba sai dai bata sare ba cikin Lallashi tace"Kayi hakuri abun bai kai harda gori ba..!
Dakatar da ita yayi yana fadin"Ko ni Sa"idu ban isa Mallam yayi Umarni akaina na Tsallake ba ballatana abunda na Haifa ki Fadamin gaskiya Aminar ce ta aiko ki ko..?
Mamanmu ranta ya gama baci shiyasa tace"Yarinya ta fadi Ra"ayinta ne Abbansu kada kaga Laifinta..!
Bai jira cewarta ba Fuuu ya fice yana kwala Kiran Sunan Amina Tun daga Cikin Dakin har ya fito Tsakar gidan Mamanmu ta rufamai baya gabanta na Fadi.
Amina da suke hira da Hamida da taji kiran Aba sai da gabanta ya fadi kuma sai suka ganshi agabansu kwatsam cikin Tsoro ta mike tana fadin"Gani Aba..!
Yadda idanuwanta sukayi ne saboda Tsoro sai ya ganta kamar Hadiza Shiyasa sai ya Sauke Murya yana Fadin"Zo nan..!
Lokaci daya ya juya ya Raba gefen Mamanmu ya koma Falonsa Amina ta koma Daki gabanta na Fadi ta Dauko Hijabinta ta saka tabi bayansu Hamida da Zeenatu sukayi Tsuru Tsuru suna Tunanin me ya faru kuma..!
Dukkansu a tsaye ta gansu Aba da Mamanmu sai ta kara Rikicewa yasa ta Zube gabansa cikin Rawan baki tace"Gani Aba..!
Cikin rawan murya sai yaji Fushinsa ya Sauka sai yaji Tsausayinta komawa yayi ya zauna yana Sauke Numfashi kafin yace"Amina..Ni waye a wajenki..?
Sai da ta kallesa sannan tace"Kai Baba na ne..Mahaifina..!
Cikin Jinjina kai cikin wani irin Sauti yace"Indai ni mahaifinki ne Amina..Ki sani ko bayan raina kika bijirema Auran Jinin Baba Mallam ban yafe miki ba Amina..!
Ba Amina kadai ba hatta Mamanmu ta firgita cikin wani yanayi Amina ta Dago ta na kallon Aba cikin Taruwan Hawaye aidanuwanta.
Ganin haka yasa ya Daga mata kai yana Fadin"Eh haka nace..Ban yafe miki ba Amina..Sannan zan sallama ki acikin ya"yana..Bazan jure ganin Abunda na Haifa ya Bijirema Mutumin da ya zama gata na ba..Mutumin da ya Lullube Rayuwata da Duka Alheransa..ki Tuna da wannan..!
Da haka ya mike ya shige ciki ya bar su nan Amina ta kalli mamanmu sai hawaye sharr.
Mamanmu tayi saurin cewa"Tashi kije zamu yi mgana da safe..!
Ba musu ta mike ta fice bayan ta share hawayenta tana fita su hamida suka fara Tambayanta Lafiya Mirmishin Daya fi kuka ciwo tayi kafin tace"Bakomai..!
Daga haka ta shige daki kokarin Daidaita kanta take yi domin tayi alkwarin daina bayyana rauninta kan wasu abubuwan..!
Ko washegari kasa ce mata komai tayi mamanmu ta tuna yadda suka kwana Aba bai kalleta ba tasan kwabarta tayi Ruwa da Safe ta Fadama Madina komai ita kuma tace bama zai sabu ba auran nan bazai Daure ba koda ya Tabbata din.!
Amina kuma ko hanne bata fadamata abunda Aba ya fadamata ba,sai dai ta Dauki nauyin mganar acikin ranta tana jin kamar abu ne mai wahala.!
Haka Rayuwar ta cigaba da Tafiya su Zeenatu suna cigaba da Jarabawarsu sun gama Weac sun fara Neco gefe Daya kuma ana cigaba ana cigaba da Shirin Bikinsu wanda Baba mallam yace nan da wani Lokaci za"ayi Auran nasu kamar yadda Tsarin yake..!
*Janafty*