DA'IMAN ABADAN

1&2

by @jameelarhsadiq6388

*🌺DA'IMAN ABADAN🌺*

_Hot love and fate sorry_


 By


_YAR'MUTAN KANKIA_


_MANAZARTA WRITER'S_



*BOOK ONE*


*WANNAN PAGE DIN SADAUKARWA NE GA REKI MAMANA,ALLAH YA K'ARA TSAWANCIN KWANA MAMANA INA KAUNARKI SOSAI..ALLAH YA BAR MANA KE🥰*


*PAGE 01&02*



***


*KYIV UKRAINE🥀*




_Grand Club_



Rungumota yayi yana manna mata kiss a kumatu,gami da shafa mata gefen fuska murmushi shimfiɗe bisa fuskarshi manna kanshi yayi a tsakankanin wuyanta yana shaƙar kamshin _DAISY_ lumshe idonshi yayi yana lasar wuyan nata ,sai ta bakinshi yayi dai dai shetin kunnenta yana cewa.


“Beauter ilove you too,kinyi kyau sosai.” murmushi tayi tana tura hannuwanta cikin sumar kanshi,maida kallonta wajen da yanmata da samari suke ta rawarsu ko wane yana rungume da partener dinshi,zare jikinta tayi daga rungumar da yayi mata,shiga tayi cikin filin rawar ta fara juya albarkatun jikinta,tana wata irin rawa kaf wajen sai da hankalin kowa ya dawo kanta,take aka fara yi mata barin kudi ko wani saurayi so yake beauter ta kulashi,yanmata wajen kuwa haushinta da kishinta suke,saboda ganin suke suna yan kasa amman wata yar'africa tazo ta fisu kasuwa.


    Suhaib shima shigowa filin yayi ya fara yi mata barin kudi,sai dai ya balle bindir din _1000 hryvnia_ take wajen ya kara rudewa ,sosai Suhaib ya zage ya barnata kudin da koshi baisan adadinsu ba,Beauter ta sai ta kwashe kusan one hour tana rawa a fili,sai da ta gaji dan kanta sannan ta fito.


Biyota Suhaib yayi sai murmushi yake,yana zaunar da ita bisa cinyoyinshi kallon juna sukayi suka kasarma juna Murmushi,_WIN_ ya balle mai sanyi ya kwafa mata a baki take ta ansa ta fara korawa har lumshe ido take dan dadi ,shima balle murfin tashi yayi ya fara korawa sai da suka sha kusan kwalbar biyu ta giya,sanann kuma suka kara da hodar ibilis sai da sukayi mankas,sannan suka shiga cikin hotel dan hutawa.


    Rungume da juna suka shigo cikin room din,a tare suka baje bisa gado suna kallon juna,fara shafata yayi yana kissing dinta ta ko ina,lumshe ido kawai tayi tana amsar sakonshi sun juma suna romantic din juna,dan har sunyi nisa sun fita haiyacinsu,ganin yana kokarin wuce gona da iri tayi saurin riƙe hannunshi.


Dakyal ta bude narkarkun idanunta kallo daya zakayi mata,kasan a bige take sai dai mai abunda tasha bai gusar mata da hankali ba,saboda sun zamamai mata jiki,motsa karamin pitch lips dinta tayi tana kallonshi tace.


   "Sau nawa zan gaya maka ba zan taba yin sex ba."?narke mata yayi yana kissing din lips dinta sannan yace. "Sorry Beauter sonki ne ya janyo haka,please i beg you ki barni nayi ko da sau daya ne." ya ida maganar yana kokarin tura kanshi a kasanta,tureshi tayi tana nuna mashi kofa tace. Get out of my side Suhaib." kamo hannunta yayi cikin yanayin bukatuwa yace. "Am sorry ba zan sake ba." tureshi tayi tana shigawa toilet ta barshi kwance bisa gado sai juyi yake hannunshi rike da mararshi,ya rasa dalilin da yasa Beauter take mashi haka,kodai shi daya take ma haka a cikin samarinta?to maiye aibunshi da har taki bashi kanta bayan kuma baida guri da ya wuce ya ganshi tare da ita suna making real love,koda ta fito wanka zama tayi ta shirya cikin T-Shirt;flipflop dai dai giwwa sannan ta daura turkiya jacket ta gyara gashinta ta bajeshi bisa bayanta ta fashe turarenta take kamshin _KAY ALI_ ya bude room din. wayoyinta ta dauka sanann ta kalli Suhaib tace.


"Byee sai kuma mun sake haduwa." kallonta kawai yake har ta fice yana son ya dakatar da ta ita,yaji yaushe kuma ta yanke mashi da zasu sake haduwa,amman gani yake mudun ya kuskura yayi magana to numfashinshi zai iya fita daga jikinshi.



     ★★★



*NIGERIA🥀*



_Jigawa dutse_



Gently yake saukowa daga upstairs,yana maigyara rolar's din dake manne a hannunshi yana mai kuma duba time,dan karamin tsaki yayi ganin ya kusa yin late,kamar baisan taka kasa haka ya ida saukowa rungume Ammie yayi yana mata pick a kumatu yana cewa.


"Morng Myluv."shafa gefen fuskarshi tayi tana mai zaunar dashi bisa kujera,sannan itama ta zauna tana mai ansa gaisuwarshi tashi tayi tana kokarin zuba mashi breakfast,da sauri ya dakatar da ita yana mai kwabe fuska yace. "Ammie.." harararshi tayi tana cewa. "What."? Tayi tamau da fuska babu alamar wasa ,ganin babu fuska yasa yayi saurin kasa da kanshi yana cewa. "Sorry." ya maida kanshi kasa bai sake cewa komae haka itama har ta gama abunda take ta tura mashi plate din abincin a gabanshi tana cewa. "Maza ka ciyenshi tas kafin naje na dawo." rairai yayi da fuska yana kallon abincin yana kallon Ammie kamar wanda akayi ma dole ya bude baki yace.


"To,but Ammie abincin yayi man yawaa ba zan..."enough A-Kaɗir." yanda ta ɗaga mashi hannun ta kuma kira sunanshi yasa ya shiga taitayinshi ,ya fara tsakular abincin yana kuma duba agogon hannunshi ganin har 8:15 tayi,kuma yayi alkwarin zai hadu da abokan kasuwancinshi by 9am ,kallon yawan abincin yayi yaga kafin ya ida cinyeshi maybe sai 12pm tayi bai gama ba,ganin wakin hula na neman kai shi dare,ya fara ci yana danna waya dakyal ya samu yaci rabi yasha drink bai sake gigin kara cin ko da spoon daya ba,dan gani yake ya kuskure ya ƙara to cikinshi zai iya fashewa.


Tunda ta sauko take kallonshi ita dai tana mamakin hali irin na A-Kaɗir,ace mutu baida abokin gaba sama da abinci ,samun waje tayi ta zauna tana kallon plate din gabanshi sanann kuma ta maida idonta a kanshi,da sauri yayi kasa da kanshi yana wasa da hannunshi ,dan karamin tsaki Ammie tayi tana cewa. 


"Nidai ai ba daukarka zanyi ba nace zanyi maka dure Love,tunda kaki ci tashi ka tafi,ka tabbatar da ka gama sallamar duk wanda zaka sallama a campanynka dan this wednesday zamu tafi ukraine." kamar ta soka mashi wuƙa a ƙahon zuciya haka yaji maganarta,baisan ko kadan yana wannan yan tafiye tafiye ,bayan kuma yana da harkokin business din shi ,yana son ya nemi na kanshi duk da idan kudi ne to yana dasu wanda har taitab'a kunnenshi ba zasu iya cinyesu ba dan Dad dinshi ya tara mashi,a'a shima yana son yaji yanda akeji wajen nema,kallon Ammie yayi yana haɗe hannunshi waje ɗaya yace.


"Ammie please kuyi tafiyarku keda Dad nidai ku barni nan na kula da campany nina." harararshi tayi tana cewa. "Kasan wata nawa zamuyi acan har kake cewa haka."?dafe kanshi yayi yana furzar da iska mai zafi a bakinshi yace. "Oh my God,yanzun har wata zakuyi."?


Murmushi Ammie tayi tana cewa. "Bama wata ba,wata hudu zamuyi dan Dad dinka zai duba campany's dinshi kaga dai abunda ya faru a kasar dole yaje ya duba yaga inda akayi mashi barna ko?kaga kenan tafiya ta wuce ace mata sati dan haka ba zan barka nan ba,kafata kafarka understand." 


Bai sake cewa komai ba ya matsa kusa da ita ya dukar da kanshi kasa ,daura hannunta tayi bisa kanshi tace. "Allah ubangiji yayi maka albarka Abu-kaɗir yasa ka gama da duniya lafiya ya tsareka da tsarewarshi ya rabaka da sherin zamani ya baka mace ta gari kamili mumuna ka aura ya kuma baka zuri'a daiyi ba." rungumeta yayi yana cewa. "Amin myluv." ya tafiyarshi,amman kasan zuciyar shi tana mashi ba dadi,idan ya tuna wanann larabar ukraine zasu tafi,shi dai baya son kasar baya son ko sunanta baison yaji.


    Koda ya isa wajen aiki bai wani saki jikinshi da abokan aikin nashi ba,ya dai duba yaga yanda komae ke tafiya sanann sukayi meeting da wasu baki da yayi daga jahar katsina kan zuba hannun jari sai da yayi sallahr azahar sannan ya wuce wajen da yake saida motoci A-kaɗir moto's nan ma sai da yayi kusan two hour sai da yayi sallah sannan ya wuto gida duk ya gaji.



*KYIV UKRAINE🥀*


Dan karamin tsaki tayi,tana mai ajiye glass cup din dake hannuta,maida kallonta akan wayarta tayi take ta ƙara turnike fuska dan ta tsani tana hutawa a damaita da kiran waya,ganin tayi baida niyar daina kiranta yasa ta dauka a zuciye ta kanga wayar a kunne,ajiyar zuciya ya sauke yana mai huro mata iskan kiss a kunne yace.


"Why Beauter?mayasa kike azabatar da zuciyata da yawa haka"?murmushi tayi tana korawa da lemun dake gabanta gami da lumshe kyawawan idanunta,ajiyar zuciya ya sauke yana mai marairace fuska ya cigaba da cewa. "Yanzun ko nazo mu hadu ina bukatar ganin kyawkyawar fuskarki dan nayi missing dinki sosai." 


Girgiza kai tayi kamar yana gabanta gami da yatsine fuska tace. "A'a karda kazo.".....Zunbur ya tashi daga kwanciyar da yake yana fiddo ido waje yace. "No Beauter karda muyi haka dake mana ki tausayama zuciyar da take cike da kauna da bige mana."


"Kamal,nagama magana yau ba zaka samu damar ganina ba,ina buƙatar hutu,bansan takura and daga yau idan ka kirani sau ɗaya banyi picking ba ka sake na biyu bance ka ƙara na ukku ba,hakan zai iya yanke alaqarmu understand." kashe wayar tayi tana mai wurgi da ita a tsakiyar parlor ta mai lumshe idonta.


  *NIGERIA🥀*


_Kano State_



Zulaihat waikukan bai isa haka ba."? Cewar Zubaida da ta kurama Zulaihat ido sae kuka take.share hawayenta Zulaihat tayi tana kallon Zubaida sanann tace. "Haba ae abun da ciwo wallahi bansan abunda nayi ma Doctor Najeeb ba,amman nidai ya tsaneni jibi fa wae saven naci over fourty da wannan ae kara yasa man zero nasan na fada baki daya." ta ida maganar tana share hawayen idonta ,girgiza kai Zubaida tayi sannan tace . "babu abunda kikayi mashi,maima zakiyi mashi keda ba sabgar kowa kike shiga ba,shima kanshi bai shiga hidimar kowa abunda ya kawoshi yakeyi ya kama gabanshi koda captain bai cika magana ba,balle wani can dabam nidae ina mamakin yanda yake kadaki a course dinshi tun muna level one gamu a level two baki taba CO ba sae akan course din shi kina fama da gyara yana kokarin kara kadaki da wani. kuma nima abun yana bani mamaki Zulaihat kodai kinsan Dr Najeeb a wani waje amman baki gaya man ba,koda wani abu a tsakaninku."?


Kama hannun Zubaida tayi suka samu waje suka zauna sannan tace. "Wallahi Zubaida tunda uwar da ta haifeni ban taba ganinshi ba sae anan makarantar,sanann kuma magana ko ta fatar baki bata taba hadani dashi ba wallahi asalima inaga bai sanni ba by face may be sunanane baiyi mashi dadi shiyasa yake kadani a course dinshi nidai ki tayani da addua Allah ya rabamu lafiya dashi kawae na huta." Murmushi itama Zubaida tayi tana cewa. "Kedai kice Allah ya shiga tsakaninki dashi kawae,amman muna tare dashi har level four dan haka ki cigaba da addu'a nima zan tayaki tashi muje marda Dr Moha ya shiga ya kuma yanamu shiga kinsan shi kuma bai dauki hana mutun shiga Lecture dinshi ba a bakin komae." tashi Zulaihat tayi tana cewa . "hakane kuma dan na lura malaman nan ba wani wadataicen mutunci bane dasu." tare suka jera suka shiga Lecture hall dan saurarar Lecturer din gaba.


Basu wani jima da shiga ba Dr Moha ya shigo fuskar nan tashi murtuke babu ko annurin murmushi bisa fuskarshi dan shima kamar Dr Najeeb yake basu ma dalibansu fara'a ko kadan babu abunda yake hadasu da student sae dai karatu dan ko office dinsu dalibi bai isa ya shiga ba,basu shiga harkar kowa ko malamai ba da kowa suke ma'amala ba,idan suka lura da malan baida natsuwa da kanmu kai to sun kulleshi sun gama magana dashi ba ruwansu dashi haka suke rayuwarsu.


Sosae kowa ya natsu yana saurarar Lecture din Dr Moha baka jin motsin komae sae karar fan din da ke aiki cikin theater din sosae suke ganewa masu joting na joting sae da sukayi awa biyu harda minti talatin sanann ya sakesu ,daman shi Dr Moha haka yake ba dai kara time ba idan yana class a gajiye sosae suka fito gashi marece yayi dan shidda harda rabi,kowa ka kalla sae ya baka tausayi yanda suke dauke da gajiya gashi sunje Bus Stop babu Bus sun tashi kuma nakep duk sunyi karanci saboda sun dauki pasenging sunyi cikin gari ,masu tafiya hostel kuwa sun kama hanyar gabansu ,kallon Zulaihat Zubaida tayi tana cewa.


"Mu danyi tracking mana,may be mu samu naped sae muyi droping dinta kawae mu tafi dan wallahi na gaji da tsuyuwar nan karda na fadi dan yunwa nike ji sosae wallahi." ya mutse fuska itama Zulaihat tayi sannan tace. "Nima wallahi agajiye nike sosae ,ba zan iya tafiya ba wallahi faduwa zanyi mu kara hakuri har Allah ya kawo naped din please Sis."


Kwabe fuska Zubaida tayi tana turo baki tace. "Kinji matsalarki ko?ki daure mana munayi muna hutawa har mu samu naped wallahi tsiyuwarmu wajen nan duk bata lokacine saboda dubi iyayen mutanan da suke jiran naped fa." kaɗa kai kawae Zulaihat tayi sanann ta tashi ta dauki hand bag dinta suka fara tracking suna hutawa har suka danyi nisa,cikin ikon Allah suka samu naped ya juya dasu sosae kuwa sukaji dadi.


Da sallama dauke a bakinsu suka shiga gida sae wash suke ,kallonsu Umma tayi tana cewa. "Sannunku yanbiyu kyautar Allah." Murmushi kawae sukayi suka samu waje suka zauna ,Zulaihat ce ta kwabe fuska tana cewa. "Wae Umma kullun kin kama hadani da yarinya bayan na bata kusan shekara" dariya Umma tayi tana cewa. "Kyaji dashi uwar son girma ,yanzun wanka zaku farayi ko kuwa abinci zaku ci."? A kusan tare suka ce. "Abinci."


Dariya Umma tayi dan ta lura daman yaran nata yunwa tana ɗawainiya dasu dan haka kitchen tashiga ta dauko masu abinci ta ajiye masu a gabansu sannan ta dauko kwano da ruwa a kofi ta zuba masu suka wanke hannunsu sanann suka zuba suka fara ci,ita kuma taje dan cigaba da hidimar gabanta su kuma suka sa abinci gaba suna ci dan a ƙa'idar gidansu idan ana cin abinci ba'a magana har sae angama.


 ★★★


Wash! Wallahi duk na gaji sosai yau dai ,sae kace yau na fara shiga Lecture hall." mtss yayi tsaki yana mai zaunawa gefen gado ya fara cire takalminshi ,tsakin da yaji anyi mashi ya sashi waigawa yana kallonshi sae yayi Murmushi dan yasan halin abokin nashi komae nashi yana tsare akan lokaci baya wasa da lokaci kuma baya bata lokacinsa wajen aikin banza,turare ya ida fashe ma jikinshi sanann ya waigo ya kalli Moha yace.


"Ae duk tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa kan doka,kai da zaka shiga Lecture four ka fito six amman dan naci sae da ka ƙara har 30min ina amfani yanzun ka fara gajiya ae." kallon Najeeb Moha ya tsaya yi yanda yayi mashi magana mai yatsawo har haka,yana iya cewa wannan shine karo na farko da Najeeb yayi mashi magana mai tsawo tabbas yau za'ayi ruwan sama ,san miskilancinshi ke hanashi bude baki yayi magana indan har yayi magana mai tsawo to Lecture ce ya shiga itama yasan dan baya da Zabi da ba zaiyi ba .


Bisa kujerar dake a bedroom dinsu ya koma ya zauna sannan ya dauko wayarshi ya bude data dan duba sakon da aka turo mashi tunda ya shiga yake ganin sakonin new nember kala kala ,dan karamin tsaki yayi sanann ya fito daga whatsapp ya koma IG nan dai DM ne ya gani iri daban daban rabi da kwata na mata ne girgiza kai kawae yayi sannan yaje ya duba BBC da sauran shafinka yaɗa labarai ya gama karanta sannan ya kashe datar yana ajiye wayar gefenshi ,lumshe idanuwanshi yayi yana mamakin yanda yanmatan yanzun ko kadan basu da aji ,ace mace ke cewa tana son namiji tana yarda girmanta da ajinta akan so tsaki ya kuma yi ,lokacin Moha ya fito daga wanka yana shiryawa kallonshi yayi bayan ya dawo kusa dashi ya zauna tea ya hada yasha sannan ya kara kallonshi ya ɗaga mashi gira yayi sannan yace. "Yau ma anyi maka sakon ana sonka ko."?


Murtuke fuska yayi sannan ya hada tea shima ya fara kurbe kamar baya so ya bude baki yace. 



"Eh."  


Girgiza kai Moha yayi sannan ya tashi ya shiga kitchen ya girka masu indomie ya dawo zaunawa sukayi suka fara ci sai da suka gama Najeeb ya tashi ya wanke plate din da tukunya ,dawowa yayi yana Murmushi kallonshi Moha yayi yace.



"Idan ina aiki har abunda mamaki yake bani,haka kawae mun daura ma kanmu aiki da gatanmu." harararshi Najeeb yayi sai kuma yace. "Nikuwa inason haka." tashi Moha yayi ya dawo gabanshi yace. "Weldone kayi kokari ni kuwa na gaji transper zan nema na koma Abuja da aiki gaskiua na gaji da zama kanon nan gaskiya." 


Ɗaga kafaɗa yayi yana ya kalleshi yace. "Go ahead ban hanaka ba ae." yana nagama fadin haka ya juya ya fita bin bayanshi Moha yayi suka wuce sallahar mangrid sae da sukayi isha'i sannan suka dawo basu wani jima ba kowa ya kwanta bacci dan ba wata firar dare suke ba sosae,saboda suna tashi da wuri dan zuwa wajen aiki.



   ★★★



Dafata Umma tayi tana cewa. "Karda ki damu Zulaihat dan yana kadaki ki manta da hakan ki cigaba da karatunki zan cigaba da tayaki da addua ,kema ki dage da addua Allah zai shiga tsakaninki dashi tashi kije kiyi wanka ko kinyi bacci karda kuma ki makara gobe." kaɗa kai kawae tayi taje tayi wanka ta shirya ko waya bata dauka ba ta kwanta.ba bacci take ba ,tunani take yanda ake take faduwa a Course din Dr Najeeb bayan komae ya tambaya tana bashi dai dai bata yarda tayi kuskure ,tafi maida hankali akan Course dinshi ,amman shi take faduwa a fili tace. 


"Nidai ko sanin fuskata nasan bakayi ba,sannan kuma Ko kalmar tak bata taba hadani dashi ba ,maybe dai sunane yake bashi hushi shiyasa yake kadani." tsaki tayi sannan tayi adduar bacci ta kwnata dan ten gareta kuma Dr Najeeb zaiyi masu Lecture din...



**AMATULLAH RAHUSA DATA*


*DATA SERVICES AT APPORDABLE PRICES*


*MTN*        

500MB-150      

1GB-280

2GB-560

3GB-840

4GB-1120

5GB-1300

10GB-2700


 *AIRTEL*

500MB-200

1GB-400

2GB-800

3GB-1200

4GB-1550

5GB-1950

10GB-3850


*GLO*

500MB-200

1GB-400

2GB-800

3GB-1200

4Gb-1550

5GB-1950

10GB-3850


*9MOBILE*

500MB-500

1.5GB-1300

2GB-1500

3GB-1800


*Validity 30days*

Checkbalance codes

*MTN* *460*260#

*AIRTEL* *140#

*GLO* *127*0#

*9MOBILE* *228#


*VIA THIS ACCOUNT*

8160508316. Jamila Bello Abubakar. Opay bank


*** for call or whatsapp


#Vote

#Comment

#Share pls