9&12
*🌺DA'IMAN ABADAN🌺*
_Hot love and fate story_
Na
_YAR'MUTAN KANKIA_
_MANAZARTA WRITERS_
*Wannan page din naku ne Aunty Binta Abbale da Adda maidambu much luv🥰*
*BOOK ONE*
*PAGE 09&12*
Rintse Idanu tayi da taji ance.."yes come in." Da karfi ta rintse idanunta tana share hawayen da suke zarya a bisa kuncinta,dakewa tayi tana mai tura Office din a hankali ta bude k'aramin bakinta cikin muryarta mai sanyi da dadin saurare tayi assalama tana mai ida tura kanta a cikin office .
Aikinshi ya cigaba da yi bai nuna yasan da shigowar mutun a cikin Office din ba,cigaba da hidimar gabanshi kawai yayi.dan ko kallon kofar baiyi ba balle ya motsa yayi ma wanda ya shigo magana,duk da kuwa yasan wacece sai dai mai a halin da yake ciki baya da lokacinta.
Ta kusa Shafe minti 20 tana tsaye a wajen ko kallon inda take baiyi ba,duk'ewa tayi wajen tana mai rushewa da wani uban kuka dan d'aura hannu tayi akai ta cigaba da kukanta,dan karamin tsaki yayi yana mai d'ago kanshi daga kan aikin da yake ya daurasu a kanta tsaki yayi yana girgiza kai sannan yace.
"maza tashi kibar man Office useless."
D'ago raunannun idanuwanta tayi tana saukewa a kanshi gami da had'e hannunta wajen daya bakinta na karkarwa cikin dutsewar murya saboda da kukanta da tasha tace.
"so..r.ry..sir."
Da in'ina ta ida maganar share hawayenta tayi da gefen hannunta ta cigaba da cewa..."wallahi ba laifi na bane matsalar abun hawa na samu kuma Umma ce tace dole sai na sha koda tea ne sune sukasa ka rigani zuwa." Ta ida maganar tana mai cigaba da sauke ajiyar zuciya kanta kasa,tsab ya k'arema Zulaihat kallo duk da ita ba fara bace sosai amman ba ankirata da bak'a ba kuma ba za'a ce mata chocolate color ba ita dai wata kalar fata Allah ya wadata da ita mai shek'i da daukar hankali,ga baiwar hanci da Allah ya wadata da shi ga idanu dai dai dan ba'acewa tana da lulu eyes dan kuwa ba'a cewa tana da kananun idanu sai dai sexy eyes ,da dan karamin bakinta, sauke ajiyar zuciya yayi yana furzar da iska mai zafi a bakinshi gami da tura hannunshi cikin lunlunsar sumarshi da tasha gyara dan kallo daya zakayi ma sumar kasan ana zuba kudi a saman ta.
Da hannun yayi mata nuni yana cewa..."maza taso ki zauna."ya ida maganar yana nuna mata sit,tashi tayi ta dawo inda ya umirceta ta zauna kanta k'asa tana wasa da yatsun hannunta hawaye kuwa sai tarara suke kamar an kunna famfo haka suke shatata,girgiza kai yayi yana cewa.
"Hala kuka baya saki ciwon kai ko?Zulaihat."
D'ago kai tayi sake da baki tana kallonshi dan kuwa mamakine fal a ranta, taya akayi yasan sunanta? lura da mamakin da ke rainta sai ya tab'e baki ya cigaba da cewa.
"maiyasa kike son wasa da karatunki."
Runtse ido tayi tana mai Jin ciwo furincinshi a kanta wai tana wasa da karatunta,bayan sau daya tayi late har suka samu wannan sabani kuma a course din shine kawai take da problem duk da kuwa tafi maida hankalinta 100% a kan ko wani course da take yi kuma shine yake kadata.
Share hawaye kawai tayi ga gaskiya amman bata faduwa k'irik'iri,amman sai dai ido kawai shine nata tana ji tana gani ana neman lik'a mata sheri,maganar da yayi ce ta dawo da ita daga duniyar mamaki tana cewa.."Sir kayi hakuri akasi ne a kasamu."
D'ago kanshi yayi yana cewa.."kinji ko?baki dauki karatunki da muhimmanci ba tunda har ake samun abun da zai sa ya samu targard'a." Amman Sir sai...daura hannunshi yayi bisa bakinshi yana cewa..
"ya rage naki Zulaihat ki chanza ko karki chanza course dina 70mark ya kasance lower mark ne zaki samu. wanda maybe nayi maki favour akan haka,karki kuskura naga result dinki kasa ga 70 duka course din da kike,zuwa school akan lokaci ya zama dole.maza tashi ki barman office."
Ga magana tana son tayi amman ba hali dole ta tashi ta nufi hanyar da zata sadata da waje ta daura hannunta zata bude kofar taji yace..."dakata" waigowa tayi tana kallonshi da hannu yayi mata Singn akan tayi clear din hawayenta gogewa tayi tana ida ficewa a Office din girgiza kai yayi yana murmushi ya cigaba da aikin gabanshi.
*UKRAINE🥀*
_Kiev Estate_
"Kadir." Waigowa yayi yana kallon Ammie murmushi tayi tana cewa.."ka kula da kanka ka kuma ji tsoran Allah a duk inda kake." Langwabar da kai gefe yayi yana mai tura kofar ya ida ficewarshi yana maijin so da kaunar mahaifiyarshi yana ratsa ko wani lungu a jikinshi da bissmisllah ya bude kofar motar ya shiga sai da ya maimaita bismillah da addua sannan ya tada motar direct landscape Alley ya nufa dan yana son urgent yayi magana da Beauter.
Cikin natsuwar da ta gama bi mai jiki yake driving din yana bin suratul Al-A'raaf har lumshe ido yake dan yana jin dadin kirar Ahmad Sulaiman, idan yana jin karatun Ahmad Sulaiman har mantawa yake da kanshi, cikin ikon Allah da yardashi ya iso estate din su Beauter dai dai gidanta yayi parking din motarshi sai da ya karata addua sannan ya fito.
Tafiya yake kamar wanda baya son taka kasa, furzar da iskan bakinshi yayi yana mai É—aga kanshi yana kallon kofar gidan a hankali ya daina door bell yana mai jiran azo a bude mashi.
Tsaye take bakin mirror tana kare ma kanta kallo, tayi kyau sosai da sosai duk da ba wata kwaliya tayi ba sosai, amman tayi kyau dan karamin tsaki ta saki jin ana danna mata bell turo baki tayi gaba tana cewa.. "Waye kuma? Bayan yau banyi da kowa zamu hadu ba." cigaba da ƙarema kanta kallo tayi murmushi tayi har sai da dumple dinta suka lotsa duka size din, english wears ne jikinta gown ce dakyal ta rufe mata cinyoyinta kuma gaban rigar net ce dan kuwa breast dinta duka a waje suke, fashe jikinta da turare tayi tana mai jefa sweet mai kamshi da dadi a bikinta daukar wayoyinta tayi sannan ta sauko kasa, har ta zauna taji an sake yin nocking. dan karamin tsaki ta sake saki sannan taje dan budewa rainta a ɓace dan kuwa ko waye maganar gaskiya ya matsa mata kuma ya takura mata dan ko kadan bata da bajet din ganin kowa.
Bude kofar tayi cikin fushi ta bude baki zatayi magana kenan yasa hannu ya rufe mata baki yana mai ida shigo cikin gidan, cigaba da tafiya yayi da ita bai sake ta ba sai da suka shigo har cikin parlorn zaunar da ita ,shima zaman yayi yana mai ƙare mata kallo. kauda kanshi yayi daga kallonta yana furzar da iska mai zafi gami da lumshe idanunshi, kallonta ya sake yi ya kuma kauda kanshi... "Inalillahi." ya furta a hankali yana ƙara aro jarumta ya daura ma kanshi sannan ya dago kanshi ya kalleta yace.
"Daman baki iya karama baki ba."?
Turo baki tayi gaba tana kauda kanta gefe murmushi ya subuce mashi ya tashi ya nufi hanyar kitchen da kanshi da sauri ta tari gabanshi tana balla mashi harara... Murmushi yayi mai tsada yana ƙara raɓe ta.gefenta ya wucewarshi kitchen.ruwa ya samu mai dan saukin sanyi ya zuba a cup ya sha, a inda ya barta anan ya taddata tsaye rike da kuhu tana kallon ikon Allah, tana mamakin yanda yake mata abun da ya gadama har haka amman takan kasa yi mashi magana ko hanashi ko dan mai?
"Dan yana maiki ƙarjini."
amsar da taba kanta kenan, ƙara tamƙe girar sama da kasa tayi ta ida isa wajenshi tana cewa.
"Malan lafiya? Mai ya sake kawoka gidana."?
Tashi tsaye yayi ya kamo hannunta ya zaunar da ita yana mai shafa gefen gemunshi yana cewa.
"Sonki ne ya maidoni."
Da sauri ta tashi tsaye tana nuna mashi kofa cikin fushi tace.."wannan shine kuskurenka na karshe da zaka ce kana sona, bawan Allah ina dan ganin girmanka shiyasa nayi maka maganar lalami so karka sake ka sake furtaman wannan munainan kalma dan kuwa na tsani so na tsani duk wata kalma da zata kasance sunanta so ko makamanci."
shima tayi tsaye yayi yana mai hadata da bango kissing dinta ya farayi baya ji baya gani turashi take tana mislilinshi sai da ya tabbatar da ya gajiyar da ita ya saketa dakyal ya fisgo maganar bakinshi yana cewa.
"sake cewa baki sona, inasonki aurenki zanyi dole kuma ki soni ki bar wannan kazamar rayuwar da kika daura ma kanki."
shiru yayi yana maida numfashi sannan ya cigaba da cewa.. "Maiye ribar kinyin auren? Dadin mai kikeji idan kina zaman kanki a matsaynki na yar... "Dakata." ta tareshi tana daga mashi hannu, kukane ya subuce mata tana girgiza kai, so take tayi magana amman ta kasa, tabbas maganganunshi sunyi mata zafi kuma sunyi mata nauyi a zuciya, kalma so ta aure da ya furta mata sun tado mata da abubuwa da dama wanda kullun take kokarin ganin ta ciresu a rayuwarta ta manta da komai. ta manta da ko ita wacece tana son ta kasance fawayau tamkar jirirar da aka haifa yau bata san komai ba sai nonon uwarta, so take ta kasance haka ta manta komai ta kasance bata da komai why? Maiyasa yake son shigowa rayuwarta yake kokarin tada mata da tabon da ya fara warkewa taya ta bashi wannan fuskar har haka? jinjigata yayi da sauri yana mai yin hunging dinta da karfi dan har sai da tayi yar'ƙara kadan tare da ajiyar zuciya sakinta yayi yana cewa. "Mynull are you ok."? Goge hawayen idonta tayi tana mai kallonshi tace.
*NIGERIA🥀*
_Kano_
Tunda ta fito office dinshi take tunanin rayuwa sauke ajiyar zuciya tayi tana duba time tashi tayi jiki sake ta nufi venue din second lecture din da zasuyi, amman zuciyarta cike take da tarin tambayoyi iri iri bata da ansarsu dan kuwa bata san wa ma zatayi ma tambayar ba, ya akayi yasan sunanta? Maiyasa zaiyi mata wannan munainar shedar wai bata karatu bayan duk karatun da take kamar zata kashe kanta akan course dinshi shine kawai yake saka mata carryover a course dinshi.amman ko wane course tana kokarin ganin ta wuce dan kuwa bata cin kasa ga 60% zuwa 100% to shi maiyasa take faduwa a course dinshi har yake mata kallon jakka? Tabbas ruwa baya tsami banza ko dai itace bata fahimtar question din yakeyi a lokacin exams din? Bata da mai bata ansa shiyasa ta taitara tunanin ta watsar da shi gefe.dan ta lura kwakwalwarta gab take da tarwatsewa idan tace zata biye ta Dector Najeeb, amman tabbas zata ci maganin zama dashi duk da bata san wani irin maganin zataci ba, amman zatayi trying taga ta kaucewa ma duk abunda zai sake hada ta dashi, bashi ba ko wani malami ma da yake a cikin Buk wannan promise ne ta daukarma kanta.
Koda ta shigo lecture hall din waje ta samu ta zauna ko Zubaida ba taje nema ba dan tasan tana gaba ma ita kuwa da ta shigo yanzun a koda gidansune tasan ba zata samu gaban ba.
Bata dade da zama ba lecturer din ya shigo duk da bata cikin mood maidadi ba laifi ta gane abunda yake bukatar su fahimta daidai gargado dan har answering question tayi kuma yaji dadi sosai malamin dan yana respeating dinta a class dinshi saboda tana É—aya daga cikin masu nuna mashi sun gane É—ari bisa É—ari kuma hakan yana mashi dadi.
Bayan sun fito suka hadu da Zubaida wurga mata harara tayi tana turo baki gaba tace.
"Sis sai bai kasheni ba."
Dariya Zubaida tayi tana cewa.."ai nasan daman ba zai kasheki ba yanmatan Umma." ƙaramin tsaki tayi tana yin gaba ta gyaleta dan ta lura ƙara mata wata tempreture din take sonyi. taji da wanda take ciki ma.
*UKRAINE🥀*
Cewa Beauter tayi "Am not." Sauke ajiyar zuciya tayi a Karo na ba adadi sannan ta sauke mashi raunaunun idanunta da suka tashi daga fari suka koma ja tsabar kuka da tayi,kofa ta nuna mashi cikin tsuke fuska tana cewa.
"Fita ka barman gida tun muna fahimtar juna and daga yau karda ka sake zuwa idan nike aurene dai ko?ba zanyi ba koda zanyi banji zan iya yi dakaii ba okay"?
Girgiza kai yayi cikin zafin nama ya rike yatsen da ta nuna shi da shi. yana murd'ewa cikin tsukewar fuska da karfi ya marza hannu har sai da Beauter ta saki yar kara kadan hawaye na bin fuskarta kamar an kunna famfo,har cikin tsakiyar kai haka take jin zafin murderwar da yayi ma yatsan nata,jefar da yatsan yayi yana cewa.
"This is the first and last da zaki yi mistake din nuna ni da yatsa." Kara matseta jikin bango yayi yana hura mata iska a fuska yana manna mata kiss a saman lips dinta dan janye jikinshi yayi daga jikinta yana cewa."sonki yanzun na fara kuma zuwa wajenki ma yanzun na fara aurenki zanyi kaunarki nike. zuciya da gangar jiki mararinki suke kuma dole naba zuciya abunda take so."
Harara ta wulla mashi tana cewa. Sai muga inda akeyin dole ni kuma bani sonka ba zan aureka ka rubuta ka ajiye mtsssss." Ta buga tsaki tana nufar kitchen fisgota yayi jikinshi cikin fushi dan har kirma yake tsabar bacin rai. kama bakin yayi yana murzarwa sosai cikin fidda tausayi dan sosai ranshi yake b'ace dan yatsani tsaki a rayuwarshi da kayi mashi tsaki gwara a zaneshi kuka ta tashe da shi tana rike hannunshi fisge hannun yayi yana mai barin gidan ko kallonta baiyi ba da karfi tace.
"Ban yafe ba mugu." Shafa bakin tayi tana rintse ido dan wani irin tsuga haka take ji yana mata tashi tayi tana kallon lips din a mirror.so take ta hango jini dan tasan da wuya bai ji mata rauni ba.
Sauke ajiyar zuciya tayi tana shiga kitchen fresh milk ta dauko sai cupcake ta dawo ta fara ci Kadan ta dan ci ta ture tana kurama TV ido. tana tunanin duniya da abubuwan da suka wuce a rayuwarta hawaye ta share tana cewa.. "Na bani ni *Hauwa kulu Jidda* maiyasa na bari wannan guy din yake so maidoman da hannun agogo baya?kwafa tayi tana tashi ta nufi bedroom tana cewa.." Naga yanda za'ayi sai dai gawata amman bani ba aure.balle wata soyayyar banza ba abunda ke cikin soyayyar sai karya da yaudara." Fadawa tayi bisa gado tana rushewa da wani kuka mai cin rai ta dade ta na kuka sai taji kanta yana shirin tarwatsewa gidan biyu sannan tayi shiru tana girgiza kai gami da sauke ajiyar zuciya share hawayen tayi tana cewa.."ya isa haka nan ya wuce har abada daga yau, daga yanzun ba zan sake tunawa da komai ba,ba zan kuma yarda wani banza ya tuna man ba. ba zan bari ba har abada ya wuce kamar yanda nace ya wuce kuma ya wuce." Bathroom ta fada dan yi wanka ko ta dan ji saukin jikinta.
★★★
Kallon yanda ya shigo dakyal ya iya yin sallama ya tada hankalin Ammie da sauri ta isa wajenshi tana kamoshi ta kwantar da kanshi bisa cinyarta tana rairashin sai shafa kan shi take yana sauke ajiyar zuciya.sai da ta tabbatar da ya dawowa daidai ta kwantar da kanshi bisa cushen tana wucewa kitchen madara ta dauko mashi mai sanyi tsaka tsakiya dan gidan basu san sanyi sam,zama tayi tana kamashi ta zaunar da shi tana mai daura mashi cup din a saman lips. tsura mata ido yayi yana kaudar da kanshi gefe b'ata fuska Ammi tayi tana cewa.
"Yanzun kuwa zan b'ata maka rai KADIR zaka bude baki kasha ko sai kaga b'acin rai na? Kai dai kullun ko gajiya bakayi aita magana d'aya." Turo baki yayi yana kwantawa yace.
"Myluv." Harararshi tayi tana kara mika mashi kamar Wanda aka ba mad'aci haka ya anshi madarar yana sha yana ya mitse fuska yi tayi kamar bafa ganshi ba. ta kuma tsuke fuska da ya d'ago ya kalleta sai ya maida cup din ya cigaba da sha sai da yasha half sannan ya langwabe kai yana cewa.."am full." Kallon cup din tayi tana sauke ajiyar zuciya dan yasha da yawa ma.
Kallonshi tayi tana cewa..."Luv maike damunka?maiyafaru dakai ka shigo kamar wani zautaice kamar ba kaii ba?lafiya dai ko."?maida hankalinshi yayi wajenta yana kamo hannunta yana mirzawa a hankali cikin natsuwa yace..Ammi ina sonta Amman ita tace bata sona."kara gyara zamanta Ammi tayi tana cewa.."Kadir wacece wanann da zakace kana sonta tace bata sonka? wacece ita?yar gidan waye a kasar Ukraine? da mai take takama."?
Murmushi yayi yana girgiza kai yace.."Myluv ba kowa bace asalin ma daga gani ba yar asalin kasar nan ce ba sanann kuma."
Shuru yayi yana kallonta ya kasa magana ,dan maganar nauyin tayi mashi taya zai gayama Ammi zaman kanta take a ukraine?taya ba zai iya ba.kuma bai fatan ya fara yi mata karya akan yarinyar da ko sunanta bai ma sani ba.
Shafa kan shi tayi tana cewa..."yar wace kasa ce to Son gayaman yar wata kasace mai kuma tazo yi a kasar nan."?
Girgixa kai yayi yana cewa.."Myluv ban san komai ba. taki ta saurareni taki ta kulani taya zansan komai nata."? Tashi tayi tana cewa.."bani address dinta nida Dad dinka sai muje mu roketa ta soka Luv fatana kenan fa a rayuwata naji kace yau ga wanda kake so zaka aura. bani da gurin da yafi wannan Abukadir taya kuma zamuyi wasa da wannan damar? ni har duk'a mata zan iya yi in har zata soka ba faduwa bane tunda muke nema a wajenta."
Shima tashi yayi yana cewa.."Myluv ba zaki taba duk'a mata ba har abada kuma dole ne ta sone dolenta ne sai ta aureni Myluv." Kamo hannun shi tayi tana cewa."ba'ayi ma soyayya haka A kadir ba'ayin so ta tsiyatsiya lailabe so ake a riritashi kamar kwai,idan kace zakayi mata dole i ba zata taba sonka ba a hankali zamu bi har ta soka luv."
"Ai ba auren bane a gabanta." Murmushi tayi kawai tana cewa.. "Je ka kwanta ka huta kafin Dad dinka ya dawo anjima zamuyi magana okay." Daga kai kawai yayi ya wuce room dinshi daman hutawar yake bukata sosai, dan yarinyar ta chaza mashi kwakwalwa sosai.
*NIGERIA🥀*
_Kano_
"Sis." Ajiye handout din hannunta tayi tana kallon Zubaida ba tare da tace mata komai ba,sanin ba magana zatayi ba yasa Zubaida ta cigaba da maganarta dan ta saba da halinta daman.
"Daman shawara zan baki." Dan shuru tayi tana cigaba da cewa.. "A gaskiya tsoranki yayi yawa haka saurin kukanki yayi yawa ya kamata tun wuri ki chanza dan yana kawo maki chikas fah." Dan karamin tsaki Zulaihat tayi tana cewa.
"Kin cika matsala gaskiya kam Sis,tom ni ya zanyi haka Allah yayo ni bani son tsawa bani son fada keni gaba daya bani son tashin hankali Sam bani son fitina wlh."
Dariya Zubaida tayi tana cewa.."kice kina da babban aiki a gabanki kuwa."
"Kamar ya kenan."?cewar Zulaihat tana kallon Zubaida.. "Eh mana taya zaki iya zama da Dr Najib kina da wannan dan banzan tsoro wahala zaki sha a wajenshi kuwa."
Tsaki kawai tayi bata sake cewa komaii ba ,ta maida hankalinta wajen karatunta dan ta lura bata lokacinta kawai zatayi idan ta tsaye biyema shashancin Zubaida, itama Zubaida dariya kawai tayi ta cigaba da karatunta dan gobe test din Dr Moha zasuyi early 8 ma kuwa.
Washe gari tun 6am su Zulaihat suka shriya suka kama hanyar school dan bata son abunda zai ja mata matsala da Dr Najib duk da ba test din shi zasuyi ba Amman ai Dr Moha close friend din shi ne dole kuwa ta kiyaye duk wasu dokoki da ya shimfida mata mundun tana son kanta da arziki kuwa,zuwa 7 suna cikin school,venue suka nemo suka samu waje suka zauna kara dubawa sukayi tans nuna ma Zubaida idan bata gane ba, sai ga Dr Moha ya shigo shi da wasu malamai da zasu taya shi invigilation din test din,dukansu ya fidda waje ya saka su saka layi sai ya kira mace ta shiga sannan namiji two seat per intable haka ya gama arranging dinsu sannan aka rubuta question aka bada umirnin farawa tsit haka hall din ya dauka dan tsautsaran tsoro aka dauka ko motsi mai karfi baya tashi a hall din. kuma kowa nashi yake babu damar tambaya balle har ka tambaya wani abunda ka sani shi zaka rubuta.
Shigowarshi kenan hall din cikin tsuke fuska as usual haka Dr Najib yake murmushi bayi yake ba. balle dariya miskiline na karshe haka Allah ya halliceshi kuma bai daukar raini daga wajen kowa dan a aganinshi bai raina ba tom ba zai yarda a raina shi ba,saman step din ya hau yana hangen kowa da kuma motsin kowa kara nastuwa student din sukayi fiye da da.wasu ma fara dabarbarcewa sukayi sakamakon shigowar tashi.
Ita kuwa Zully tunda ta d'ago kanta sau d'aya ta kalleshi ta maida kanta kan papper din ta.ta cigaba da answering questions duk da gabanta sai faduwa yake gami da karmar jiki ,dan jikinta ya bata ita yake kallo dan ajiye pen din hannunta tayi tana d'ago kanta carab idunuwansu suka sarke da juna da sauri ta maida kanta kasa gami da rintse idonunta fatfatfat haka zuciyarta take bugawa sai kace Wanda tayi tseren gudu.
Cikin takun nan nashi na kasaita yake saukowa daga kan step din yana bin round by round yana kuma duba pappers Wanda yaji za ya iya haka har yazo seat din da Zubaida take dauka yayi ya karanta full name dinta yana mai duba question din da tayi answering ajiye mata yayi yana mai karawa gaba. yana duba na sauran yana zuwa seat Zulaihat ya dan tsaya ya dauki paper dinta ya duba kallonta yayi yana cewa.
"Be fast."
A hankali yayi maganar kuma ba wanda yaga motsawar bakinshi,rintse ido tayi tana budewa gami da daga mashi kai,dan maganar tashi har cikin jinin jiki haka ta shigeta gaba yayi yana cewa..
"gud girl."
Ficewa yayi daga hall din yana mai wurgama Dr Moha harara dan ya lura da irin kallon da yake mashi yana mashi murmushin raini,bayan fitarshi da five minute aka fara ansa sanann suma suka kama gabansu.
Cafeteria suka nufa bayan sun fito daga test din sai da tasha ruwa mai sanyi one bottle sanann ta lumshe idonta ta bude tana sauke ajiyar zuciya sau ukku a jere tana cema Zubaida..
"Sis bakiji yanda zuciyata take tsale ba har yanzun bata daina ba."
Dariya Zubaida tayi tana dan kurbe lumun chivita dake gabanta tace.."farar kura mai ya saka maki tsalen zuciya har haka."? Harararta tayi tana cewa.."ban sani ba je ki nemo farar kura ta baki ansa,ki fa fita idona in kulle naga kina son rainani bayan kuma na girmaiki."
Dariya kawai Zubaida tayi tana cewa.."to Umma ki yafenman karda kiyi man baki na koma tafa ko hirji." Tsaki tayi tana tashi tace.."kinji da shi tashi mu tafi saura 20min karda ki ki ja mana masifa kinsan dai Dr Najib ne yanzun 12-2 ko."?itama tashi tayi tana. Cewa.."Ina sane Mrs Najib taya zan manta."
Wani dogon tsaki Zulaihat tayi tana fisger back bag din ta. ta goya ta kama gabanta,dan zuciyarta har tafasa take idan Zubaida na hadata da Dr Najib ita ta rasa ya zatayi mata ,ta ma rasa da wa zata hadata sai Dr Najib mutumin da jininsu bai hadu ba ,ita ko shi kadai ya rage a duniya ba zata taba aurenshi ba,balle ma tasan har abada ba zai taba sonta ba shima,dan ita ba kallarshi bace ,sosai take cikin fushi dan har fuskarta ta nuna.tana shigowa class ta samu front seat ta zaune tana mai kara tamke fuska dan ta kasa control din fushinta ji take kamar ta kurma ihu ta rasa mai tayi ma Zubaida take mata haka. amman dole yau tayi maganinta ta kawo karshen rainin nan na Zubaida.dole ta tuna mata tafa girmaita ta bata shekara a duniya zata tuna mata shekara daya ba kwana daya bane,jin shiru da class din ya dauka yasa ta fahimce da shigowarshi d'ago kanta tayi sai idonta ya sauka cikin nashi dan tsaye yake ya kafeta da ido,dauke idonta tayi tana goge hawayen da suka fito mata a saman fuska,girgiza kai kawai yayi,ya fara abunda ya tarasu amman rabin hankalinshi yana wajenta dan ya lura da bata cikin happy kamar ranta a bace yake ,mai yasa ta kuka?tambayar da yake ma kanshi kenan.take yaji komai ya fice mashi a rai shima sai ya tsince kan shi a situations din da take ciki,dakyal ya samu ya danyi masu abunda ya sawaka ya sallamaisu yana fita ko office dinshi bai koma ba direct motarshi ya nufa yana shiga yayi mata key ya kama gabanshi.
Suma suna fitowa suka fara traking dan babu abun hawa babu bus kuma babu naped Zubaida na kallonta take ta zubga mata uwar harara harda karamin tsaki, itama sai ta kama kanta. idan ta harareta sai ta rama suna cikin haka sukaji mota ta tsaya gabansu da sauri taja baya tana jan tsaki dan sauran kadan a take mata kafafu.itama Zubaida ja da baya tayi cikin masifa tace.
"Maiye haka?waye wannan yake kokarin kashemu k..makalewa maganar tayi tana fiddo ido waje gami da rufe bakinta da hannu,ita kuwa Zulaihat k'ara ja da baya tayi tana neman rugawa da gudu, lura da hakan da Dr Najib yayi ya buga mata tsawa yana cewa.
"kika kuskura kika motsa daga inda kike sai ranki ya b'aci stupid."
Cak ta tsaye tana dafe zuciyarta dake kokari fitowa kasa tsabar firgici da tsoro.haka ma Zubaida da take taji cikinta na juyawa babu abunda take bukata sama da ta ganta toilet dan zawo zawo taji tanaji take,tsaki ya buga yana cewa..
*AMATULLAH DATA SERVICES*
*MTN*
500MB-140
1GB-270
2GB-540
3GB-810
4GB-1080
5GB-1350
6GB-1620
7GB-1890
8GB-2160
9GB-2430
10GB-2700
*AIRTEL*
500MB-180
1GB-350
2GB-700
3GB-1050
4GB-1400
5GB-1750
6GB-2100
7GB-2450
8GB-2800
9GB-3150
10GB-3500
*GLO*
500MB-180
1GB-350
2GB-700
3GB-1050
4GB-1400
5GB-1750
6GB-2100
7GB-2450
8GB-2800
9GB-3150
10GB-3500
9MOBILE
500MB-150
1GB-300
2GB-600
3GB-900
4GB-1200
5GB-1500
6GB-1800
7GB-2100
8GB-2400
9GB-2700
10GB-3000
VIA✓8160508316
Jamila Bello Abubakar
Opay bank
VIA✓0777512438
Jamila Abubakar Bello
Access bank
*** for call or whatsapp
Share
Comment