DA'IMAN ABADAN

71-80

by @jameelarhsadiq6388

*🌺DA'IMAN ABADAN🌺*

_Hot love and fate story_


Na

_YAR'MUTAN KANKIA_


_MANAZARTA WRITERS_


*BOOK ONE*



*PAGE 71-80*


***


So da tausayinta suka k'ara dirar mashi a cikin zuciyarshi gami da wata zaizafar kaunarta wanda baki ba zai musalta ta ta ba,furzar da iskan bakinshi yayi yana share zufar da ta keto mashi a fuska dan k'ara matsawa yayi kusa da Umma yana maida kanshi k'asa yace.."Umma dan Allah ki bani auren Zulaihat zan riketa amana zan zamai mata bango. zan sata farinciki in shaa Allah ba zan taba barinta tayi kukan maraici ba." Ya ida maganar kanshi k'asa shi kadai yasan yanda yake jin tausayinta da sonta jin labarinsu ya k'ara mashi wata kaunarta mai girma mai wuyar fassarawa.


Girgiza mashi kai Umma tayi tana share hawayenta tace.. "Najibullahi duk da a yau na fara saninku na yarda da tarbiyarku kuma na dauke ku a matsayin yarana. har shiyasa na shigo daku cikin gidan nan,sai dai maganar gaskiya ba zan boye maka ba yanda nike jin son Zulaihatu a zuciyata ko Zubaida da na dauki cikinta na haihota banma shi.dan ita Zulaihatu abun tausayice bata da uwa bata da uba sai ni.nice uwarta nice ubanta dan haka bazanso na aurar da ita idan zatayi maraici ba."


"Umma na fahimceki amman wallahi Umma zan riketa zan kula da ita zan bata kulawa ta har abada,Umma zan rayuwa da ita har *DA'IMAN ABADAN* nayi maki wannan alkwarin Umma." Dan shuru Umma tayi tana tunani can tace.."naji amman karatunta fah Najib? Kaga dai wasiyar da Yaya Aminu ya barman na sata tayi karatu mai zurfi." D'aga kai yayi yana cewa.."Umma zata cigaba da karatunta a gidana idan har tana son cigaba ma tayi master. Umma zan barta dan nima ina bukatar hakan tunda tana da kokari kinga bai kamata a tauyeta ba." Har a zuciyata Umma ta amince da Dr Najib kuma tana fatan lamarin ya tabbata duba da natsuwarshi da hankalinshi da kuma haiba da daitako tana ma Zulaihat fatan samunshi a matsayin miji, ta tabbata zai kula da ita zai bata kulawa kamar tsoka d'aya a miya ,bata da guri da fata da taga ta aurar da yaranta ga mazaje na gari masu nagarta da tausayi da amana,Murmushi tayi tana cewa.."sai kaje ka nemi so a wajen Mamana dan ba zan mata dole ba." Kasa kawai yayi da kanshi baice komai ba dan shi kunyar Umma yake ji,shima Dr Moha tambaya yayi shima a bashi dama ya nemi Zubaida numfashi Umma tayi tana cewa.


"Wannan kuma ba humurina bane Muhammadu.sai dai kaje wajen Mustapha, amman zan maka alfarmar ku fara fahimtar juna da ita sai na turaka wajen shi." Shima godiya sukayi mata sannan suka tashi dan tafiya,koda suka fito basu tadda kowa a tsakar gida ba suna cikin room din su.


Ba haka Dr Najib yaso ba ,yaso yaga Zulaihat koda sau daya ne ji yayi kamar ya kirata waya ta fito sai kuma yana jin nauyin Umma ba yanda ya iya haka ya hakura suka shiga motar. ji yayi bai iya koda driving nan ya mikama Moha key yana komawa wajen mai zaman banza ,ansar key din yayi ya tada motar suka tafi dan rage karar radio yayi yana cewa.."A gaskiya Zulaihat ta bani tausayi baiwar Allah.dan Allah Najib ka sauke girman kan nan naka ka kula da yarinyar nan. karda kace zaka nuna mata gadara azo ayi ba da kai ba naga hausawa na cewa durkusawa wada ba gadarcewa bace."


"Hakane ai kasan yanda nike sonta ba zan taba bari wani abu ya cutar da ita ba,amman na lura kanta rawa yake zan bita a yanda tazo man ne idan da hankali tazo welcome sai muyi soyayyarmu idan kuma da hauka tazo nan ma normal sai na nuna mata na fita iya hauka." Dariya Moha yayi yana cewa.."idan kuma tace bata sonka fah.?" Waigowa yayi yana kallonshi sai kawai yayi murmushi baice komai ba,shima Moha murmushin yayi bai sake cewa komai ba.


★★★


Kallon Zubaida tayi tana tabe baki tace.."dan ma baki ga yanda yake ma Umma biyaiya ba sai ki rantse kice bashi bane Dr Najib marar mutunci da tausayi ba, ita kuma Umma sai wani nuna jindadi take dan kawai bata san baida hali ba shiyasa ni wallahi bansan ko ganinshi gashi ya wani yi mana zaune a gida sai kace gidansu."ita dai Zubaida dariya tayi tana cewa.."Sis wallahi ki rage wannan abun ba abu bane mai kyau and ya kama ta dai ki rage wannan tsanar da kike mashi ina guje maki karda ta juye ta koma so fa." Dafe kirji tayi tana turo baki gami da matso yan kananun kwalla tace.."amman wallahi Sis kin gama dani kin cuceni haba Sis mai nayi maki mai zafi haka? Da zaki hadani da Dr Najib ko masoya na rasa ai wallahi ba zan iya soyayya dashi ba balle aure koda shine autan maza kuwa."


Yanda take maganar har cikin zuciyarta take fitowa wata irin tsana take ma Najib yanda bai sonta itama bataji zata iya son shi ba,dariya ta kama yi tana cewa.. "Kedai ki bar cika baki wallahi ni soyayyarku dariya ma take bani Allah ko." Tashi tayi tana kaima Zubaida bugu tana cewa.."wallahi Sis ki fito idona na kulle.ban san haka ban san wulakanci ni ba kawarki bace na lura kin rainani a gidan,amman tunda ni bakijin magana ta bari naje na fadawa Umma sai ta shiga tsakanina dake.."


Rikota Zubaida tayi tana yin kallar tausayi tace.."na tuba ba zan k'ara ba Aunty ki yafeman. karki hadani da Umma daman tana cikin wannan fushin kuma ki k'ara daura man wani ba zan sake ba amaryar Dr." Pillow ta wurga mata tana tashi ta bar mata dakin ,parlon Umma ta shiga tayi kwaciyarta bisa three seater tana karatu dan ta lura idan ta biyema Zubaida sai ta bange a banza bata karanta komai ba gashi Monday zasu fara exams.


Tunda abun ya faru su Zulaihat basu sake shiga school ba suna gida suna karantunsu basu aikin komai dan Umma ta dauke masu tace suyi karatun ita zataji da aikin gidan,da sunso yi mata gardama amman ta nuna ita haka take bukata kuma take so sai suka saka mata ido kawai suka cigaba da karatunsu idan suka samu sarari su dan kama mata koda girki ne.


Yau zasu fara exams tun asuba basu tsaya siririta ba da wuri sukayi komai suka fita kuma cikin ikon Allah suna fita suka samu mai naped tsaye a kofar gidansu koda suka tambayeshi tafiya zaiyi? yace masu eh,suka shiga suka gaya mashi inda zai kai su koda ya kaisu. da zuka bashi kudi yace a'a an bashi kudin tuni daukarsu ce kawai nashi sunyi mamaki sauri suke shiyasa basu tsaya tambayarshi waye ya sakashi wannan aikin ba suka shiga exmas hall zuciyarsu fal da mamaki.


★★★


Alkhamis yasha wuya a hannun yan sanda dan mugun bugu sukayi mashi,gashi makaranta ta hana a bada bellin dinshi ba yanda iyayenshi basuyi ba da sunzo wajen Dean affairs sai yace masu sai dai sunje wajen Dr Najib shine kawai zaice ayi belling dinshi ayi .dan shi yayi ma rashin kunya a matsayinshi na malami ,haka iyayen Alkhamis suka kama zarya basu wajen Najib basu police Najib ya kulle ido yaki cewa komai koda sunzo sai dai yace su tafi gida za'a sakeshi haka ya kama yi masu.


Yau Alkhamis satinshi biyu a wajen police duk sun chanza mashi kamanni sun koya mashi tarbiya koda Dr Najib yazo sai ya kama yi mashi kuka yana cewa ya tuba yasa a sakeshi ba zai sake ba,sab'anin da.da yake auna mashi zagi yana cewa idan har ya fito sai yayi ma Zulaihat abunda har su mutu ba zasu manta dashi ba.haka yake cewa a duk lokacin da Dr yazo police din.


Murmushi Dr Najib yayi da aka fiddo mashi Alkhamis ya durkusa a gabanshi sai kuka yake yana mashi magiya akan ya tuba ba zai sake ba. ya bar shi haka ya hukuntu ,kallonshi Dr Najib yayi yana ce ma D.P.O.."Oga ni har yanzun ban yarda da tuban yaron nan ba,dan haka kawai a mai dashi a cigaba da koya mashi hankali kawai gaskiya."


Rike mashi kafafu Alkhamis yayi yana kuka yana cewa.."dan Allah ka rufaman asiri ka duba Allah ka dubi girman Allah kayi hakuri wallahi ba zan sake ba har abada ni inda take ma wallahi ba zan sake kallo ba. unguwarsu ma ba zan sake zuwa ba." Cire hannunshi Dr Najib yayi d'aga jikinshi yana kallon D.P.O yace.."har yanzun dai ina kan bakana ban yarda dashi ba tunda dai kaima shedane akan furuncin da ya dunga yi akan dilabata,karda a sakeshi yaje yayi mata wani abun kamar yanda yake fadi."


Gyaran murya D.P.O yayi yana kallon Alkhamis yace.."Kwarai kuwa da bakinka kace zakayi mata abunda har a mutu ba za'a manta ba,Kaga kenan furuncinka sun kunshi abubuwa da yawa irin su fyade da bugun mutuwa kai harda ma kissan kai duk suna ciki tunda jam'i kayi."


"Wallahi Aa ku rufaman asiri daman fadi kawai nike amman ba har zuciya ba dan Allah Yallabai ka gafarceni wallahi nayi maka alkwarin unguwarsu ma na daina zuwa." Girgiza kai D.P.O yayi yana cewa.."wannan maganar ai bata kyalewa bace Alkhamis kayi furuci ai,dan haka cell zamu maidaka case dinka za'a kai shi a kotun sulhu gaka ga iyayenka ga iyayen yarinyar da kuma wasu d'aga cikin dalliban makaranta har da yan unguwarku da yan unguwarsu da kuma mu da alkhali anyi komai a rubuce shedu susa hannu sannan zaka bar wajen nan."


Ba kukan da Alkhamis baiyi ba amman a banza haka aka sake mai dashi D.P.O yasa aka rubuta takardu aka aika duk inda ya fada,washe gari kuma duk sun hallata bayan kowa ya zauna alkhali ya shigo aka karanto case aka kuma fadi furuncin da yayi akan yarinyar take alkhali yayi rubuta a takarda ya d'ago yaba maba takarda ya fara karantawa kamar haka..


_Ni Alkhamis Amadu nace zanyi ma Zulaihat Aminu abunda har ta mutu ba zata mantaba,dan haka na yarda duk abunda ya samu Zulaihat Aminu nine kuma na yarda da hukuncin da hukuma zata zarta a kaina mutane ku shedda._


Alkhamis cewa yayi ya yarda ya saka hannu aka ba kowa ya saka hannu akayi printing din takardar aka ba kowa tashi sannan akayi belling din Alkhamis har kasa ya duga yana ma Najib godiya dan shi kadai yasan wahalar da yasha a wajen yan sanda.


★★★


Tunda suka fara exams kullun da sun fito suke tadda mai naped a kofar gida shigewarsu suke dan idan sunce basu shiga to watarana kuwa zasu iya yin missing din exams dan unguwarsu akwai wahalar samun abun hawa..kuma sun tambayi mai naped wa ya turoshi sai yace wasu ne shi bai san sunansu ba,sun dai bashi kudi sunce ya ringa kaisu school daga ranar basu sake tambayarshi ba suka cigaba da hidimarsu.


Course din Dr Najib shine last peper dinsu a 200 level kuma cikin ikon Allah sun samu intervel har na kwana ukku,dukufa sukayi kan karatun dan ko dan aikin da suke fitowa suna taya Umma dainawa sukayi da Umma tace duk karatun ne ya hanasu motsi har haka? Ce mata sukayi eh ai course din Dr Najib ne course din yana da wahala gashi kuma malamin da ya dauki course din shima ba sauki gareshi ba.dan har yafi course din zafi ma,sosai Umma ta kama yi masu dariya wai yafi course din zafi kenan zafi biyu ya hade masu a waje daya.


Ana gobe zasuyi course din kusan kwana sukayi zaune sai wajen 3:30 suka kwanta shima Dr Moha ne ya kira Zubaida yace idan karatu suke su ajiyeshi hakanan su kwanta karda suje filin exams din kuma su manta abunda suka kwana suna karantawa.


Godiya tayi mashi da shawarar da ya basu ta kashe wayar tana kallon Zulaihat da keta karatu tana gengadi tace su kwanta inji Dr Moha aikuwa ko gardama ba tayi ba ta kwanta daman ta gaji ga ciwon kai,koda suka tashi da asuba suna sallah suka cigaba da karatunsu sai wajen Tara suka fito tsakar gida danyi wanka. suna fitowa suka shirya abinci suka ci bayan sun gama suka cigaba da karatunsu da yake sai 12 suke da exmas din.goma nayi suka kira mai naped dinsu yace ai yana kofar gidansu tuni har zasu tashi Umma ta fito tana cewa.."idan kun fito ku biya wajen gyaran kai da kunshi ayi maku dan gobe zakuyi bak'i." Da to suka ansa bayan sun anshi kudin da ta basu suka wuce zuwa 11 suna cikin makaranta samun waje sukayi suna cigaba da karatunsu har 12 ta kusa suka je venue suka zauna.


Alhamdulillahi dadin karatu kenan,yanda wasu ke kukan tayi zafi wasu kuma murmushi suke suna cewa tayi dadi sosai wasu kuma tsaka-tsakiya batayi zafi ba batayi dadi ba sosai, koda suka dauki bags dinsu suka kama hanya dan samun abun hawa su wuce wajen gyara Dr Najib ya parking gabansu kallonsu yayi yana cewa.


"kullun ai sai nace ku shigo kuke shigowa ko.?"

Zubaida ce ta bude ta shiga tana cewa.."sorry sir." Itama Zulaihat shiga tayi amman batace komai ba tada motar yayi yana cewa.."ya Exmas din." Nan ma Zubaida ta bashi ansa da Alhamdulillah amman mutuniyar bace komai ba sai ma maida hankalinta waje da tayi tana kallon mutane shima watsi yayi da ita ya cigaba da driving dinshi Zubaida ce ta gaya masu inda zasu har bakin wajen ya kaisu yana ba Zubaida kudi su kara amman taki ansa sai da yayi mata Jan ido ta ansa yace idan sun gama suka rasa abun hawa ta kira Moha sai azo a daukesu da to ta ansa tayi godiya suka shiga....Da kallo ya bisu yana murmushi wai shi Zulaihat take ma haka zaiyi maganinta ne soon ta dai shigo hannunshi.


*Ayyya Dr Najeeb kafa fiye complain fah🤔,ba Kai ka koya mata irin halin ba lol😂*


Koda suka shiga ciki tarba suka samu ta mutuncin kamar dai ko da yaushe sun tadda ana ma wasu amare gyaran jiki sai suka samu waje suka zaune,Zubaida ce ta lissafa kudin da ya basu d'agowa tayi tana kallon Zulaihat tace.."Sis 15k ce ya bada." Tsaki tayi tana cewa.."matsalarku ce daga ke har shi,daman duk ke kika ja mana fad'a a wajen Umma maiyasa kika ansar masa kudi."?kwabe fuska Zubaida tayi tana turo baki gaba tace.. "Haba Sis kinfa san halin Dr Najib ba sai angaya maki ba,so kike naita yi mashi gardama har yayi man fad'a ko."? Harararta tayi tana cewa.." Sai mai idan yayi maki fad'a?nace dai ai ba kasheki zaiyi ba ko?sai ki ajiye kudin gefe in mun koma gida kiba Umma ta kira shi waya yazo ya anshi tsiyarshi ni wallahi ko kudin bani son gani ma."


Saka kudin tayi a jikka tana cewa.."yanda kikace ai haka za'ayi Sis."tabe baki tayi tana kallon Zubaida tace.."niko Sis nace wasu kalar bak'i zamu har haka da Umma tace ayi kunshi da kitso?nifa abun ya daure man kai tun dazun." Gyara zamanta Zubaida tayi tana cewa.."nima wallahi Sis abun akwai ban mamaki tunda bata tab'a yi mana haka ba.ko suwaye wannan bak'in? Dagani suna da fahinmanci a wajen Umma gaskiya. "


"Gaskiya kam har na kosa ayi mana ko mun koma mu k'ara gyara gidan mu samu wani abu mu girka masu." Cewar Zulaihat haka suka kama tautauna abunda ya dace su girka ma bak'in Umma...ba tare da bata lokaci ba aka fara yi masu gyaran kai sai kuma gyaran farce aka tsintsara masu kunshinsu mai kyau da tsari dan har yafi wanda ya goge kyau da tsaruwa ,yau ba wani gyaran jiki akayi masu ba dan duka yaushe akayi masu wata daya kenan,fuska dai wata a cikin ma'aikatan wajen ta matsa sai da aka gyara fuskar sai daukar ido take koda suka fito suka fahincin zasu samu matsalar abun hawa sai suka kira mai naped din da yake kaisu school suka gaya mashi inda suke yazo ya dauke su.


Koda suka kirashi sai da ya kira Dr Najib ya gaya mashi izinin daukosu ya bashi sannan ya kashe wayar yana kallon Moha yace.."Angama masu amman Zulaihat ta hana Zubaida kira sai dai suka kira mai naped." Dariya Dr Moha yayi yana girgiza kai yace.."Zulaihat rigimar duniya Najib zaka sha fama da rigimar Zulaihat gaskiya." Murmushi kawai yayi yana tura hannunshi cikin gyarairar sumar kanshi yace.. "Rabu da ita duk zan iya mata,kawai dai ta shigo hannu." Dariya Moha yayi yana cewa..da kamar yaushe zamuje zancen."? Agogonshi ya kalla yace.."after ish'i ai yayi ko."? D'aga kai yayi yana game dinshi dan Moha ba daga baya ba wajen game.


★★★


Koda suka koma gida sai da suka shiga room din Umma suka nuna mata kumshin da gyaran gashin da akayi masu tasa albarka tace sai su shiga kitchen su dafama bak'in abinci sai da suka yi sallah sannan suka nufi kitchen...koda suka shiga sai da sukayi shawarar abunda zasu girka masu da yake suna da garin masa na kamfanin *MASALINA* daukoshi kawai sukayi suka yi hadin masar sannan suka fara nadin samosa da spring roll sosai suka hada masu kayan lakumashe da na motsa baki suka hada masu juices da milkshake, sallar mangariba sukayi sannan suka fito suka fara gyara tsakar gida Zulaihat tayu shara yi tas .Zubaida tayi mopping suka gyara parlon tas suka kunna tureren wuta bayan sun kunne tsintsiyar kamshi sun kuma fashe ko ina da room freshener.


Room din su suka koma suka fara shirin wanka Zubaida ta fara shiga sannan Zulaihat kafin ta fito Umma ta shigo ta kawo masu wani laces ash mai ratsin black sai wani turare mai saukin kudi amman yanada dadin kamshi ta ajiye masu tace suyi kwaliya mai kyau da kallo suka bi Umma fuskarsu ciki tab da mamakin Umma suyi kwaliya? Wannan wasu irin bak'ine haka masu kayan mamaki tunda suka dawo Umma take shirya ma zuwansu kallon juna sukayi kanan suka d'aga kayan sabbi ne kuma style din yayi masu kyau sosai zura doguwar rigar sukayi suka zauna sai da suka yi sallar ish'i sannan suka fara shiryawa poder suka shafa dan har da jan baki suka shafa kuma yayi masu kyau sosai ya kara fiddo masu da haskensu da kuma kwarjininsu.


Cikin natsuwa suka k'arasa shiryawa suka wuce room din Umma da kallo ta bisu fuskarta shimfide da murmushi tace.."masha Allah yan biyu kyautar Allah kunyi kyau sosai Allah yayi ma rayuwarku albarka." A tare sukayi dariya sai Zulaihat ta cinno baki gaba tana cewa.."Ayya Umma ki daina had'ani da ita kinsan fa na girmaita." Dariya Umma tayi tana cewa."Mamana uwar yanson girma duk da kin girmaita ai baki fita girman jiki ba sai dai tsawo ko.?" Dire kafafu ta fara tana cewa.."nidai nidai Umma naji duk da haka dai." Dukansu dariya suka saka Umma na cewa.."shikenan na daina Mamana uwata ta kaina." Dariya tayi tana rufe fuskarta Zubaida ce tace.."wai ni Umma wasu irin bak'ine zakiyi haka har yanzun basu zo ba ko dai kwana zasuyi."?girgiza kai Umma tayi tana cewa.."ko d'aya ba kwana zasuyi ba yanzun haka suna kan hanya ina jin sun kusa k'arasowa ma."


"Amman Umma yan nan cikin garin kano ne kenan."? Cewar Zulaihat nan ma d'aga mata kai Umma tayi tana cewa.." Kwarai kuwa yan asalin nan kano ne amman iyayensu suna zaune a abuja aiki ya kaisu su kuma suna zaune anan kano suma aiki ya kawo su." Har ta bude baki zatayi magana wayar Umma ta fara ringing dole tayi shuru tana had'iye maganarta.


Daukar wayar Umma tayi tana murmushi tana kallonsu sannan tace.."ok shikenan bari azo a shigo daku." Murmushi tayi bayan ta saurari abunda akace daga d'ayan bangaren ta ajiye wayar tana kallon Zubaida tace.."maza tashi kije ki shigo dasu suna kofar gida." Cikin jindadi Zubaida ta tashi ta daukar hijab dinta ta saka sannan ta nufi kofar gida cikin doki tana son ganin su waye wannan bak'in masu daraja a wajen Umma.


Ita kuwa Zulaihat taso ace ita Umma ta aika dan shigowa dasu dan taga su waye itama dai kam,amman ai zasu shigo zata gansu tasan dai ko su waye to suna da mahinmanci a wajen Ummarsu kam..koda Zubaida ta fita bata lura da motar su Dr ba da yake sun kashe motar kuma basu kunna fitilar motar ba gefe da gefenta ta waiga bataga kowa ba har zata juya suka danna mata horn sai anan ta maida hankalinta a wajen...Sam bata ganesu ba da yake kullun cikin chanza mota suke kamar wasu gwannati har bakin motar taje tana dan yin nocking a hankali gami da sallama lumshe Dr Moha yayi yana jin sonta na fisgarshi kumshinta yayi mashi kyau sosai ,zuge glass din yayi yana cewa.."sannunki dai yan mata." Wani ja da baya tayi tana kallonsu sai kuma tayi murmushi tana cewa.."Laaa Sir wai da kune bak'in da Umma zatayi."? Murmushi yayi yana bude motar ya fito yace.."Kwarai kuwa mune gashi har mun iso kodai mu koma ba'a murna da ganinmu.?"Cikin wasa yayi mata tambayar girgiza kai tayi tana cewa.." Wai rufamana asiri ku shigo sannunku da zuwa."


Murmushi sukayi sannan sukayi gaba tana baya har suka shiga,har cikin parlo ta saukesu tana sake yi masu sannu da zuwa sannan ta shiga cikin bedroom din Umma zaune ta tadda Zulaihat sai labari suke da Umma samun waje tayi ta zauna tana cewa.."Umma ashe su Dr ne bak'in naki.?" Murmushi Umma tayi tace.."ba zama zakiyi tambaya ba tunda idonki ya gane maki ke Mamana tashi kuje ku kai masu abun motsa baki."


Kalllon Zubaida tayi ta kalli Umma tace.."Umma wasu su Dr din.!?"yanda tayi tambayar cike da al'ajabi da mamaki girgiza kai Umma tayi tana cewa.. "Zaku tashi kuje kun bar mutane zaune ko ni naje da kai na.?" Tashi sukayi suna nufar parlon da sallama suka fito ji tayi zuciyarta tana tsalle kamar zata fado kasa tsabar takaici mai hakan ke nufi? Wani zuminci suke sun kullawa mai karfi haka?dakyal ta ida isowa cikin parlon tana mai kallon Dr Moha tace.." Sir sannuku da zuwa barkanku da dare."


Murmushi Dr Moha yayi yana cewa.." Yauwa Zulaihat barkanmu dai ya gida ya kuma dare."murmushi itama ta sakar mashi tana cewa.."lafiya lau Alhamdulillah."gaba tayi tana fita daga parlon ta wuce kitchen tadda Zubaida tayi tana jera abunda suka girka a babban tire jingina tayi jikin bango tana cewa.


"Sis nifa duk kaina ya daure ban gane komai ba ina cikin duhu sosai daman sune zasuzo Umma ta sakamu kitso,kunshi,har da sabbin kaya.?"Itama Zubaida furzar da numfashi tayi tana cewa.." Sis nima nan a cikin duhun nike nayi nayi na gano ma'anar wannan hidimar na kasa kinga dauki muje mu kai masu karda Umma tayi fad'a kuma."


Gyade kai tayi tana daukar tire din abincin ita kuma Zubaida ta dauko su jug da cup da duk abunda suka tanada suka kai masu,suna ajiyewa Zulaihat ta tashi ta shigewarta room din Umma tana cinno baki gaba,kallonta Umma tayi tana cewa.


"Mamana ba dai kanwarki ba kika baro da aikin zuba masu abincin." Tabe fuska tayi tana cewa."Umma ai nasa munyi mai wuyar tunda mun girka kuma mun kai masu ko.?" Dakuwa Umma tayi mata tana cewa.."gidanku Mamana naci gidanku yau ga rashin tunani da wayau ace har kanwarki ta fiki iya karrama bako?zaki tashi kije kiyi abunda ya dace ko sai na sab'a maki.?"


Tashi tayi tana cewa..."yi hakuri Umma ba zan sake ba." Tsaki Umma tayi tana cewa.."da dai ya fiye maki." Fitowa tayi fuska a turnuk'e babu fara'a sai tura baki take gaba haka ta iso ta tsuguna tana wurgama Zubaida harara tace."mai kike zuba masu.?"Murmushi Zubaida tayi tana cewa.."brown rice din ko Sis." Tabe baki tayi tana daukar plate ta zuba ta saka salad da duk abunda ake zubawa ta tura a gaban Dr Najib tana tsiyaya carrot juice din ta mik'a mashi.


Tunda ta dawo yake kallonta duk wani movement nata akan idonshi take yinshi shi dariya take ba shi sai wani ifizi take dan anzo gidansu..a cikin zuciyarshi yayi tsaki yana cewa.."yarinya kenan duk kiyi ki gama na kusa yin maganin wannan sabuwar rashin kunyar da kike tak'ama da ita." Murmushi kawai yayi idan ya tuna saura tik'i kadan ta shigo hannunshi duk da yana sonta amman hakan ba zai hana ya koya mata hankali ba ,dan ya lura wata sabuwar balaga take rudarta.


Kafeta da ido yayi yana aika mata da wani kallo wanda yasa take ta shiga taitayinta tana sauke kanta k'asa wani sabon tsoronshi ya shigeta take har sai da fuskarta da kwayar idonta suka nuna haka..saboda wasu kwallah suka taro sukayi kwance a saman kwayar idon nata dakyal ta samu ta hanasu zubowa,kin ansa yayi ya kuma ki daina kallonta k'asa tayi da kanta a hankali tace.."Sir ga juice. " dan karamin tsaki yaja wanda sai da ya maido da hankalin Moha wajenshi da yake aunama cikin shi daddar brown rice din da ta gaji da dadi da kuma tsokokin naman kazar turawa,had'a ido sukayi da shi yana girgiza mashi kai itama Zubaida sai da ta sake shiga taitayinta dan tsam ta tashi zata bar wajen Moha ya dakatar da ita yana cewa.." Yi zamanki ki karasa aikin lada." Murmushi tayi tana koma wa ta zauna.


A hankali ta sake cewa cikin muryar kuka.."Sir." D'agowa yayi again yana cewa.." Ai nasa shima ai wullo man zakiyi." K'asa tayi da kanta tana cewa.."Sorry Sir." Nan ma baice komai ba sai ya dauki juice din ya dan kurba yayi mashi dadi kam sosai da sosai sai da yasha kusan half sannan ya dauki plate din ya fara ci ba laifi yaci da yawa kam.kuma duk abunda suka girka sai da suka ci dai dai misali...bayan sun gama Umma ta fito kamar jira Umma na fitowa suka tashi suka bar masu parlon sai da suka gaisa sosai suka kara magana da Umma sannan ta tashi taje ta kira su tace su koma zasuyi magana mai mahinmanci da su Dr har Umma ta juya ta dawo tana ce ma Zulaihat.. "Mamana dan Allah idan kinje ki samu bulala ki zanesu karshen fushi da kumbura fuska kenan."


Cikin b'acin rai Umma tayi maganar tana fitowa ta bar masu dakin da kallo suka bita Zubaida ce tace.."Sis gaskiya koni banji dadin abunda kikayi ma Dr ba ,haba ai ko ba komai kin daga mashi tunda gidanku yazo ko.?" Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa."bakiji yanda nike ji bane shiyasa ko kadan ban san ganin fuskarshi kuma wata magana ce zamuyi dasu kuma bayan gaisuwar da mukayi.?"


"Duk da baki son ganin fuskarshi ki saki fuskarki ko dan Dr Moha da Umma mana da kuma ni kaina and maganar da zamuyi nima ban sani ba idan munje munji koma maiye ne ko.?"


Daga mata kai tayi tana yin gaba itama tana bin bayan ta da sallama suka shiga parlon.wannan karan fuskarta a sake take ba kamar dazun ba sake gaidasu sukayi a karo na biyu sai sukayi shurun dan basu san mai zasu ce masu ba,bama kamar Dr Najib da komai nashi ya kwance mashi baisan mai zaice ba dan wannan shine karo na farko a rayuwarshi da ya fara zuwa wajen mace,bai san mai zaice ba bai san ya akeyi ba kallon Moha yayi yana langwabe kai murmushi Moha yayi dan yasan waye Najib bai taba soyayya ba sai akan Zulaihat in fact common charting baiyi da mace dan duk basu gabanshi gwara shi yana dan taba soyayya a online ba laifi dan gyaran murya yayi ya fara cewa.


*AMATULLAH DATA SERVICES*


*MTN*

500MB-140

1GB-270

2GB-540

3GB-810

4GB-1080

5GB-1350

6GB-1620

7GB-1890

8GB-2160

9GB-2430

10GB-2700


*AIRTEL*

500MB-180

1GB-350

2GB-700

3GB-1050

4GB-1400

5GB-1750

6GB-2100

7GB-2450

8GB-2800

9GB-3150

10GB-3500


*GLO*

500MB-180

1GB-350

2GB-700

3GB-1050

4GB-1400

5GB-1750

6GB-2100

7GB-2450

8GB-2800

9GB-3150

10GB-3500


9MOBILE

500MB-150

1GB-300

2GB-600

3GB-900

4GB-1200

5GB-1500

6GB-1800

7GB-2100

8GB-2400

9GB-2700

10GB-3000


VIA✓8160508316

Jamila Bello Abubakar

Opay bank

VIA✓0777512438

Jamila Abubakar Bello

Access bank


*** for call or whatsapp


*👭GARKUWAR MATA👭*

*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*

*GA*

*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*

Rage tumbi💯

Nono💯

Sanyi💯

Karin kiba💯

girmar hips💯

Ni'ima💯

Sabulai💯

Humra💯

Turarukan wuta💯

Matsi💯

Miski💯

Dilka💯

Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki

GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari

DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI

*****

*****