81-90
*🌺DA'IMAN ABADAN🌺*
_Hot love and fate story_
Na
_YAR'MUTAN KANKIA_
_MANAZARTA WRITERS_
*BOOK ONE*
*PAGE 81-90*
***
"Zulaihatu. " maida kallonshi wajen Zubaida yayi yace."Zubaida." Yanda ya kira sunayen nasu babu wasa a ciki yasa suka natsu suna ansawa a tare,murmushi yayi yana gyara zamanshi yanda zai ga reaction din kowa ce a cikin su idan ya fadi abunda ke cikin zuciyarshi...cigaba da cewa yayi.."ina son ku natsu ka bani aron hankalinku dan magana zani mai mahinmanci a garemu daga mu har ku." Numfashin bakin shi ya furzar yana daukar ruwa ya dan surb'a kadan ya ajiye ya cigaba da cewa."bama kamar ke Zulaihat inason ki natsu ki saurareni da kyau akan duk abunda zan gaya maki fatan kin gane.?"d'aga mashi kai tayi tana wasa da yatsun hannunta,ba abunda gabanta yake sai faduwa danma tana inallilahi wannan wace irin magana ce haka? Wanda take da mahinmanci irin haka? Kamar saukar aradu haka taji dirar maganar Dr Moha a cikin dodon kunnanta yana cewa.
"Daman munzo ne mu gaya maku muna sonku,ma'ana muna son aurenku muyi rayuwa ta *DA'IMAN ABADAN* ,Najib yana son ki Zulaihat ni kuma Allah ya daura man son Zubaida sonku muke ba da wasa ba,kuma ba zuwa makayi ba mu tsaya muta b'ata ma juna lokaci shiyasa kafin muzo anan sai da Umma tasan komai ta kuma yarje mamu tace ta bamu ku sai dai muzo mu gaya maku dan mu sasanta mu fahimcin juna."
Dafe kanta tayi da hannayenta duka biyun tana jin dumm waje bangaren kan, dan wani irin juya mata parlon yake komai ya rikice mata bata ganin shi da kyau sai dai double komai ya koma mata upsize down.bata fahimtar komai bata gane mai sukeyi, dakyal ta fisgo kuka tana cewa.."Impossible." Sai ta tashi ta fice daga parlon gaba d'aya tana koma wa room dinsu bisa gado ta fad'a tana mai ida rushewa da kuka tana cewa..."har abada in shaa Allah ba zamu taba had'a inuwa d'aya da kai ba,ban sonka na tsaneka nasan kaima ba sona kake ba so kake ka aureni ka ida kasheni da bak'in halinka."
Ko motsawa baiyi ba duk abunda ta gama da impossible din da tace ta bar masu parlon duk bai nuna yasan tanayi ba. ko da kuwa fuskarshi ta nuna bai bari ba,duk da har can k'asan zuciyarshi yaji zafin abunda yarinyar tayi mashi,mai take nufi?impossible! Impossible!mean ba zata aureshi ba kenan? Haka take nufi Najib zuciyarshi ta bashi ansa ,tabbas da sake dan sanda yaga gawar soja.
Cikin sanyi jiki da nuna rashin jindadin abunda tayi Moha ya kalli Zubaida,itama k'asa tayi da kanta tana jin kamar ta nitse wajen dan kunya abu biyu ya taro ya hau kanta ga wannan magana ta Dr Moha da yayi ta kamar saukar aradu babu zato babu tsanmani ga kuma nuna rashin amicewa da Zulaihat tayi a take tun kan aje ko ina. rasa bakin magana tayi sai sunna kai da take yi kamar wanda ta saci hatsin ma'auna,tashi Dr Moha yayi yana kallonta yace.
"Mundai gaya maku abunda ke rainmu a kan ku ina fata a anshemu hannu biyu ayi maraba damu." Murmushi kawai tayi tana wasa da yatsunta dan ta kasa cewa komai shima murmushi yayi yana cewa.."alright I understand zamu baku time dan kuyi shawara and gobe zamu tafi abuja danyi hutun season."
"Allah ya kiyaye ya kaiku lafiya." Har cikin rainshi Dr Moha yaji dadin addu'arta ,shima Dr Najib kallonta yayi yana cewa.."Amin Zubaida and idan kin shiga room ki cema Zulaihat ta kula da kanta ban yarda ta kula kowa ba sannan bance taje ko ina ba har sai da izinin Umma." Cikin mamaki take kallonshi da saurarenshi shida ba'a ce ana sonshi ba har ya fara kwafa doka,gaskiya karfin halinshi yana bata mamaki kam sosai.da to ta bishi sai da ta rakasu a bakin motar su bayan sun yi ma Umma sallama suna tada motar tana koma wa gida tana shiga ta nufi room dinsu bata ciki sai kawai ta zarce room din Umma tasan can ta koma.
Tana shiga ta samu waje ta zauna gefen Zulaihat da take kuka tana cewa.."Umma dan Allah ki rufaman asiri ki sake man wani zab'in ,dan Allah Umma ki duba Allah ki dubi girman Allah karda ki daura man aure da Dr Najib wallahi kashe ni zai yi ba sona yake ba mugune." Kuka take sosai tana durkushe gaban Umma tana magiya cikin takaicinci da kayan hushinta Umma ta kalleta tace."kin tai bata idan ya aure ki kasheki zaiyi.?"Da sauri ta d'aga kanta tana cewa.."eh Allah Umma dan nasan waye Najib ba imani ne da shi ba,sannan kowa yasan a faculty ba mutunci gareshi ba idan karya nayi mashi ga Sis nan ki tambayeta."
Girgiza kai Umma tayi tana cewa.."ba tambayar da zanyi ma Zubaida dan naga ansar da nike bukata a fuskarta."dan gyara zama Umma tayi tana cewa."Mamana." D'agowa tayi fuskarta cike tab da kwallah sai jera ajiyar zuciya take Umma bata damu da rashin ansawarta ba ta cigaba da cewa.."kinsan dai ina son ki ko?kinsan har abada ba zan taba zab'a maki abunda zai cutar dake ba ko?kinsan akan ki ba abunda ba zan iya sadaukarwar ba ko?in har ke zaki kasance cikin farinciki ba tare da kinyi kukan maraici ba." Dan shuru Umma tayi tana jawota jikinta ta kwantar da ita bisa cinyarta ta cigaba da cewa.
"Alkwari Na daukarma Yaya Aminu akan ki Mamana nayi alkwarin baki kulawa da ilimi mai inganci sannan kuma zai aurar da ake ga mutun nagartaice mai ilimin addini da na zamani wanda ya san mutuncinki yake kuma kaunarki da kishinki wanda zai saki farinciki na har *ABADAN* ya rayuwa dake da dadi ba dadi yaji ba zai iya yin nisa dake ba koda na second goma ne,ya kasance kullun kina zaune a zuciyarshi ba dare ba rana wanda zaji mutuwa ce kawai zata rabaku dan itama dan dole ce."
Hawaye Umma ta share dan duk randa ta tuna da dan uwanta mai sonta da kaunarta sai ta zubda kwalla,ta cigaba da cewa.." Duk wannan kulawar da jindadin da na lissafo ba wani namiji da zai yi maki koda rabinta ne sai Najibullahi, Najibullahi yaron kirki ne yana da kunya da tarbiya ga ilimi ga kuma kishi,yana son ki sosai kuma yana kishinki akanki ba abunda ba zai aikata ko kin manta akan sonki yayi dambe a gaban students din shi,kishin abunda Alkhamis yayi maki yasa ya tsaya tsayin daka sai da ya kwashi kashinshi a hannu.yayi wannan duk dan yana sonki da bai son ki da bai yi ba."
Cikin muryar kuka tace.."Amman Umma kullun cikin yaman fad'a yake baya man kirki ko kadan dan Allah Umma ki taimaka."girgiza kai Umma tayi tana cewa.."Naji Mamana amman abunda nike so dake ki bashi lokaci idan har bai kwanta maki a rai ba sai asan yanda za'ayi." Murmushi tayi tana kara lefewa jikin Umma tana share hawaye da bayan hannunta, ita san ba lokaci ba komai zata bashi ba zata taba sonshi ba har abada ,ba zasu taba zama inuwa d'aya ba dan jininsu ma bai hadu ba sam,Murmushi ta sake saki dan tasan yanda Umma take sonta ba zata taba yi mata auren dole ba...itama Zubaida Umma tambayeta ya tana son Dr Moha ko itama bata sonshi,sunkuyar da kanta k'asa tayi tana cewa.."A'a Umma ina sonshi." Murmushi Umma tayi tana cewa.."Alhamdulillah Allah ya albarkaci rayuwarku." Amin suka ansa sai da suka kara yin fira a wajen Umma sannan suka wuce room dinsu.
★★★
Koda suka koma gida basu wani tsaya neman abinci ba ruwa suka watsa da yake garin ana zafi sosai sannan suka dawo parlo dan fara marking din exams,Moha fahimta yayi idan har baiyi ma Najib maganar Zulaihat ba to miskillancinshi ba zai barshi shi yayi ba.duk da yana jin zafi a zuciyarshi, yasan waye Najib wajen yar'banzar zuciya wanda ya rasa a ina yayi gadonta dan gyaran murya yayi yana cewa.."Najib ya kamata fa ka sake tako,dan ga dukan alamu Madam fah zata bamu matsala sosai." Murmushin gefen baki yayi yana duba exams dinta yace.."ni nagama da wannan babin ai,matsalar daya ce ace bata san matsayinta a wajena ba. tunda ta sani ai shikenan ta yarda ayi ta dadin rai ko akashin haka duk ya rage damuwarta ba tawa ba."
Tsaki Moha yayi yana cewa.."wallahi kaji matsalarka sai ana gaya maka gaskiya ka kak'i fahimta nace maka karka biye ma dokin zuciya azo ayi ba da kai ba,amman na rasa maiyasa kake haka ita yanzun taitali da lailashi take bukata a wajenka har ta soka."
Cikin tsawa yace.."ba zan lailasheta ba idan har sai na lailasheta zata aureni sai dai ta mutu,kuma wallahi nine nan mijinta bata isa ta auri wani d'a namiji ba ina raye a doran k'asa karyarta tasha banban da ta soni da karta soni nidai abu daya na sani shine sai ta *AURENI DOLE* kuma muyi rayuwa ta aure har *DA'IMAN ABADAN*."
Dafa shi Moha yayi yana saukowa daga dokin fushin da ya hau yasan waye Najib dole ya dunga sausauta harshe wajen yi mashi magana karda maganar shi ta kara tunzurashi yasan kuma magana d'aya yake a rayuwarshi kaifi d'aya ne,cewa yayi.
"Amman Najib sai naga kamar hakan bai dace ba,aure soyayya yana da dadi ana gina rayuwa Cikin so da kaunar juna ana gina gidan da bai rushewa ayi rayuwa ta *DA'IMAN* a cikin gidan har *ABADAN* kuwa shin ba za ka so kayi irin rayuwar ba a gidanka kai da Zulaihat."? Dafe kanshi yayi yana furzar da iska mai zafi a bakinshi yace.." Moha ba zaka fahimceni ba kaima,yarinyar ce ta cika zafin kai da yawa baka ga abunda tayi ba dazun?Impossible tace fah Moha, shiyasa nima nike nuna mata na fita iya hauka ita nata haukan karami ne Moha idan banyi mata ta mahaukaci ba to ina ji ina gani zata zama mallakar wani ba ni ba.Moha understand me please Zulaihat ba kamar Zubaida bace mai saukin kai ,Zulaihat tana da zafin kai da shirme wanda kuka ya zama abokin firarta yanzun haka kukan take tana can tana yinshi gangar jiki da zuciya sun jiman haka,dan haka inason ka fahimceni ba zan zuba ido ba ina kallon ta jaman asara."(koba asara ba Najeeb🙄,Anya kuwa Najeeb ya dauko hanyar billewa?uhmmm mudai namu ado👁️ warrr😂)
Shuru Moha yayi yana nazarin maganarshi ,shi dai bai fahimci komai ba sai kawai ya bishi da ya fahimta Allah yasa su dace da Amin ya ansa ya koma ya cigaba da marking scrip dinshi dan baya son yaje dasu gida nan yake son ya gama yana bukatar hutu yana bukatar space yaji da matsalar da ake damun zuciyarshi akan son yarinyar da ya lura baya gabanta bata sonshi a hankali ya furta..."zaki soni ne watarana ki kaunaceni ki taitalani ki riritani kamar kwai sannan kuma kiyi kishina kamar zaki mutu soon I'll promised to you." duk da Moha yaji abunda yace sai ya nuna baiji ba hankalinshi ma baya wajen yana ga marking din da yake shima.
★★★
Sai da ta gama kukanta sannan taje toilet ta wanke fuskarta ta fito ta kwanta..data ta bude ta shiga whatsapp tayi kallon status sannan ta maida ma wanda ta gadama reply ta kyale wanda batayi niya ba,sako ya shigo na wata number tsaki tayi tana yin delate ko tsayawa karantawa batayi ba ,cigaba da hidimarta tayi da wata course mate dinsu Rukayya tayi mata magana nan ta tsaya suna gaisawa sake shigowa message din yayi tsaki tayi tana shiga cikin sakon ta fara karantawa.
_Maza kashe datar nan ki kwanta tun kafin ranki ya b'aci_
Dogan tsaki tayi tana cewa.."aikuwa da nayi niyar sauka amman yanzun na fasa sai naga yanda zakayi ubana." Groups ta shiga ta kama karanta messages har da su saurarar voice,hakan kuwa ya rage mata nauyin da take ji a zuciyarta dan wasu voice din idan ta saurara dariya yake ba wani kuma takaici sai dariya take abunta dan yanda akeyin drama a group dinsu na schools idan taji anan sai ta koma a group dinsu na secondary nan ma taji dramar da ake kwasa tasha dariyarta...sake turo mata wani sakon yayi ta share sai da messages din yayi kusan 20min sannan ta shiga ta karantawa.
_karki yarda na sake yi maki magana akan ki kashe datar nan ranki sai ya b'aci sosai dan har gida zan zo maki shashasha._
tsaki ta kuma ja tana tura mashi emoji irin wannan *🤷🏻♀️* ma'ana so what,ta cigaba da hidimarta sake mata magana yayi yana cewa.
_wannan shine magana ta karshe da zan maki dan Allah karda ki kashe datar._ tana karantawa sai ta kashe datar tana goge number duka ta koma tayi kwanciyarta tana sakin tsaki sai masifa take ita d'aya kamar sabon kaimu.
Tsaki yayi yana wurgar da wayar yace.."ai da baki sauka ba,da sai na nuna maki ke k'aramar marar kunya ce stupid." Cigaba da marking din shi yayi yana sak'awa da k'ancewa yanda zai gyara ma yarinyar zama,tabbas raini yana kokarin shigowa amman zaiyi maganinta sai ya saita mata brain dinta da kuma hankalinta gami da natsuwa.
Taitara kayan yayi ya ture yana yin addua ya kwanta dan komai ya fice mashi a rai rintse idonshi yayi yana cewa.."zanyi maganinki sai nayi maganin rashin kunyar taki."
*BAYAN SATI BIYU*
"Sannu da hutawa Umma." Dagowa Umma tayi tana kallonsu sai kuma ta girgiza kai tana kallon Zulaihat shafa addua tayi tana cewa.."Mamana." Dago da kanta tayi tana Kallon Umma dan murmushi tayi tana wasa da zoben hannunta tace.
"Naam Umma." Matso da ita jikinta Umma tayi sosai tana kwantar da kanta bisa cinyarta cikin muryar lailashi ta fara cewa.."duk akan maganar Najib ne kika rame haka kika shiga damuwa."? Da sauri ta dago kanta daga bisa Umma tana girgiza kai kasa magana tayi ga kuma kunyar Umma da ta baibayeta ta rasa dalilin da yasa ta kasa yarda da auren Najib duk da tasan har abada Umma ba zata taba yi mata zabin tumin dare ba,murmushi Umma tayi tana cewa.
"Karda ki boye man komai Mamana.idan har kin san baki son Najeeb ba zan maki dole ba kam.duk da dai inason ki aureshi saboda natsuwarshi da kuma hankalinshi da tarbiyarshi dan Najeeb yaron kirki ne ba abun gudu bane kuma raina na bani zan rike man ke amana ba zai barki kiyi kukan maraici ba.koda kuwa bayan rai nane shiyasa nayi maki sha'awar aurenshi ba dan komai ba." Murmushi tayi tana share hawayenta ta kama hannun Umma tana cewa.."Umma tuni na yarda da batun auren Dr tun randa kikayi man maganar na yarda fatana Allah ya bamu zaman lafiya ya kauda fitina." Sosai kalaman Zulaihat sukayi ma Umma dadi dan har sai da fuskar Umma ta nuna hakan tana cewa.."Allah yayi maku albarka baki dayanku yasa farinciki mai daurewa a rayuwarku yaran Albarka." Da Amin suka ansa su dukansu Umma maida kallonta wajen Zubaida tayi tana cewa.."ke kuma ya batun Muhammadu banji kince komai ba ko baki sonshi.?" murmushi tayi tana sunnan da kanta kasa wai ita kunya dan kasa magana tayi sai dai ruwan murmushi da Umma take zaggawa,itama Umma Murmushin tayi tana mai cigaba da saka masu albarka daga nan suka shiga firarsu ta yau da gobe.
★★★
Tafiya tayi riba cikin ikon Allah su Dr Najeeb sun sauka birnin taraiyya Abuja daga airport Khaleed kaninsu yazo daukarsu cikin murnar da dokin ganinsu suka tarbi juna,sannan suka kama hanyar zuwa estate dinsu lifecamp da yake nan suke zaune koda suka iso wani irin fareren gida na gani da fada dan tsayawa a fadi tsaren gidan sai a kwana ba'a gama ba.(gidan novel kenan lol🤪) Dan babban gidane mai dauke da shashe har guda hudu kuma duka ginin irin daya ne sai BQ da ke gefe wanda gateman dinsu yake zaune da iyalanshi.
Daga gefen gidan kuma wani dan garden ne wanda yaji kayan lambu sosai a cikin irin su kankana da su cabbage carrot da green beans pineapple da apple dadai sauransu duk akwai a cikin,daga wani bangaren kuma pool ne babba wanda ya Kara ma gidan kyau sosai ga su dawisu an baza a gidan sai shawagi suke banda su biri da su Zaki and tiger da aka sa a cikin keji ana basu kulawa ta musaman.
Koda suka fito cikin motar direct part din tsakiya suka dosa su dukansu da sallama a bakinsu suka shiga...wata farar dattuwace zaune a cikin parlorn tasha white glasses da suka kara fito mata da kyaunta duk da tsufa ya kamata amman da yake Jindadi da kwanciyar hankali sun boye tsufan nata dan ba zakace tsofuwar ta kai shekara 70 ba a duniya dan jikinta tsam yake idan ka kalleta sai kace bata wuce shekara 50 ba zuwa ta 60.
Zaune take tana kallon. yar aikinta na zaune gefenta tana mika mata apple tana ci wata kuma tana gefe tana goge mata lailen da aka sa mata,da yake Hajja ba daga ba baya ba wajen kunshi dan bata barin hannunta fari fas ba kunshi kulle cikin kunshe hannun take da ya goge tana sa a maida mata wani,wannan al'adarta ce haka ta daura matan yaran nata a kai har da jikokinta basu rabuwa da kunshi kuma bata son asa ko wani irin laile idan ba na hausa ba,sai dai yanmatan su takan barsu su saka black idan za'ayi masu na zane amman mudun jan laile za'ayi da to lalen hausa ne za'ayi using dashi. tun suna mita har sun daina sunzo sun saba dan kuwa ba yanda zasuyi da ita.daman ko zasuyi complain din bama suyi a gabanta sai dai bayan idonta dan mudun akace za'ayi a gabanta to ranar sai sunyi da nasani dan Hajja ba daga baya ba wajen fada.
Koda suka shigo Moha ne ya matsa wajen Hajja yana kwantar da kanshi bisa cinyarta yace.."missing you tsohuwa mai ran karfe,nayi missing din masifarki."Ture kanshi tayi daga bisa cinyarta tana cewa.."Uwarkace Missing kaji ko Moha?ban hanaka yi man wannan yaren yahudancin naku ba?bari Ubanka Kabiru ya dawo sai naci ubanshi a gabanka kazo godaidai dakai kana hayeman kafa dan kaga tafi taka lafiya."
"Ai kinji ke matsalarki wallahi ba mutun ya dawo gida ba yazo ya kuma hadu da wanann masifar taki ke aikinki kenan ga kuma zagi mai ya shigo da Abbu ciki daga cewa nayi kewarki shikenan sai ki hau zagina ba ko sannu da zuwa haka zan aureki kina zagina na fasa na barma Najib daman shine daidai ke."
Kama baki Hajja tayi tana tafa hannu tana rushewa da kuka tana cewa.."shikenan duniya tazo karshe to dan Ubanka ba dani kake ba da uwarka Zainab kake kaji ko,da uwarka kake ba dani ba yo daman ni mai zanyi dakai jiki duk ya mutu nasan koni nan na fika karfi kuma bari ubanka yazo zaizo ya samaini dole yau sai ya nuna maka matsayina a gidan dan Ubanka."
Kuka take bilhakki da gaske harda fashe majina tana cewa yau sai Kabiru yazo ko Hamisu yayi mata tsakani da Moha shi kuma ya sata a gaba sai dariya yake mata yana Kara tun zurata dan idan da sabo ya saba da wannan halin nata.tsaki mai tsawo Dr Najeeb yaja yana tashi ya bar masu part din baki daya saboda wannan halin nata shiyasa bai cika shigowa wajenta ba. ita sam bata san arziki ba ta cika ballo matsala daga wanann sai wanann aikinta kenan shi kuma Moha da yake irinta ne ya kama biye mata yana janta.
Sakake Hajja tayi tana bin kofa da kallo kamar ba ita bace mai kuka ba,ta kusa minti biyu tana kallon kofa kafin tayi kwafah tana cewa..."kaima Uwarka Murjanatu kayi ma tsaki dan Ubanka Hamisu mai mugun halin tsiya. ba gwara kowan kowa ba da kowan dawa ba,zaka dawo ka samainine mutumin banza mutumin wofi ace kullum mutun fuskarshi babu annuri babu fara'a." Kwafah ta sake yi tana kallon Moha tace.."Moha mijina tashi kaje kaci abinci kaji na ma yafe maka yaron kirki karda ka yarda ka biyo halin wancan ja'irin mai mugun halin tsiya mai hali irin na uwarshi anya kuwa wannan yaron ba masanjanshi akayi Hamisu ba a wajen haihuwarshi."? Yanda tayi tambayar with so serious ya ba Moha dariya sai da yayi mai isarshi sannan yace.."nima ina tunanin haka gaskiya Hajja,amman ni na fasa matar dake na barma Najib shine dai dai ke ai."
"Yo tsoranshi nike ne aka ce maka.ni nasan maganinshi bari dai iyayen naku su dawo aure za'ayi maku can kuje ku karata duk iskancin mutun yaje mace ta laddatar dashi,kuma ba zaku sake komawa kano da sunan aiki ba idan zaku tsaya kuyi aiki a wajen iyayenku ku tsaya idan kuma ba zaku tsaya ba can damuwarku dan nagaji da wannan yawon naku kan iska baku kano baku Abuja ku ga Yan Boko duk sai nayi maganinku daga ku har su Hamisu dan na lura sune suke daure maku har kuke wanann yawon kamar wasu engineer."
Shidai Moha baice mata komai ba dan ya lura yau yan rigimar ne a kanta dan haka sai ya kama bakinshi yayi shuru yaje ya zuba white rice with peppersoup ya zauna yaci ya koshi sannan ya tashi ya wuce part dinsu koda ya shiga bai shiga room din Najeeb ba nashi ya shiga ya watsa ruwan ya kwanta dan ya huta kafin su Mom su dawo daga wajen aiki.
Shiko Najeeb bayan ya fito daga part din Hajja sai tsaki yake dan shi baisan halin tsohuwar shiyasa kullun cikin fada suke ,ita ta cika fada da zagi shi kuma sam baisan zagi dan bai hada iyayenshi da kowa ba amman ita idan ta tashi sai ta kira sunan Uban mutun sai ta zaga dan kawai ita ta haifi mutun sai kuma ta kama zaginshi shi. bayason haka,sake wani tsakin yayi yana fadawa toilet wanka yayi ya fito ya shirya cikin tree queter ya fito.kitchen din part dinsu ya shiga ya dafa indomie ya hada tea ya dawo cikin bedroom dan yunwa yake ji kuma su Ammi basu nan suna office balle yaje wajensu yaci abinci ya kuma je wajen tsohuwarcan ta cika mutane da hayaniya ko dan sannu da zuwan nan babu ma.
Koda ya kama cin abincin maida plate din kitchen yayi ya wanke da kanshi dan Najeeb ba daga baya ba wajen tsaffa.daman part dinsu babu masu aiki da ankawo masu sai da yayi yanda yayi yasa suka daina zuwa dan yace basuso su iya yi da kansu sai da rain Mom ya baci akan hakan dan bata ga dalilin da zaice zasuyi aiki da kansu ba.bayan ga yan aiki cike da gida duk yanda ta nuna mashi rashin amincewarta akan bukatarshi sai ya kai maganar sama dan Hajja ya gayamawa kuma ta mora mashi baya.shiyasa ko wane part akwai masu aiki kusan biyar zuwa sama amman banda nasu dan kowa shi yake gyara bedroom dinshi parlorn kuma roster ce idan wannan yayi yau gobe wannan zaiyi daman su uku ne kawai maza a gidan.yana bukatar hutawa shiyasa bai kira Zulaihat ba sai dai ya kira Umma ya sanar mata da sun sauka lafiya sannan ya maida wayarshi silent ya kwanta kafin anjima ya shiga part din su Mom ya gaidosu idan sun dawo daga wajen aiki.
★★★
Koda suka shigo room dinsu shiga toilet tayi dan yin wanka,sai da tayi kukanta mai isarta sannan ta fara wanka sosai take jin zuciyarta tana mata zafi idan ta tuna wai Dr Najeeb shine zai zama mijinta nan da wani lokaci idan yazo.taya zata zaune da wanda baisonta?taya zata iya zama da wanda tafi tsana a duniyar nan?shine fa mutumin da yake sakata kuka kullun shine mutumin da yake son yaga bayanta ta kowace hanya,tasan ba dan komai yace zai aureta ba sai dan ya musguna mata ya wulakanta ta shine cikar burinshi anan duniya ganinta a kasa,share hawayenta tayi tana girgiza kanta tace.."Ina ba zan yarda ba zan nuna mashi wannan ba Zulaihat da ya sani da ba ce mai raunin zuciya,zan nuna maka da da yanzun ba daya ba Najeeb zan aureka amman ka sani sai kayi nadamar aurena da kanka zaka sakeni dan zan nuna maka ni ba kwanwar lasa bace dan ada ka takani yanda kaso amman banda yanzun zan lasa maka takobi mamaki." (Gaskiya ne Zulaihat har kin fara bani tsoro fah 🤣)
Share hawayenta tayi tana ida wanke jikinta ta fito ta shirya cikin halfgawn pink mai masifar kyau ta kuma Kara mata kyau abunka da farar fata,wayarta ta dauka ta kunna data ta shiga whatsapp dan gaisawa da course mate dinta...tana cikin chatting sai ga notice din Najeeb ya shigo tsaki tayi tana kauda kanta daga message din nashi ta cigaba da chatting dinta sake shigowa wani yayi nan ma again tsaki tayi shiga cikin message din nashi dan ganin da mai yazo. Karantawa tayi tana sakin wani dogon tsaki ta rubuta dan short note ta tura mashi tana turo baki gaba kamar yana gabanta...sai da tayi 5min da turo mashi sannan ya shiga dan ganin ansar da ta bashi fara karantawa yayi kamar haka.
*AMATULLAH DATA SERVICES*
*MTN*
500MB-140
1GB-270
2GB-540
3GB-810
4GB-1080
5GB-1350
6GB-1620
7GB-1890
8GB-2160
9GB-2430
10GB-2700
*AIRTEL*
500MB-180
1GB-350
2GB-700
3GB-1050
4GB-1400
5GB-1750
6GB-2100
7GB-2450
8GB-2800
9GB-3150
10GB-3500
*GLO*
500MB-180
1GB-350
2GB-700
3GB-1050
4GB-1400
5GB-1750
6GB-2100
7GB-2450
8GB-2800
9GB-3150
10GB-3500
9MOBILE
500MB-150
1GB-300
2GB-600
3GB-900
4GB-1200
5GB-1500
6GB-1800
7GB-2100
8GB-2400
9GB-2700
10GB-3000
VIA✓8160508316
Jamila Bello Abubakar
Opay bank
VIA✓0777512438
Jamila Abubakar Bello
Access bank
*** for call or whatsapp
*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*****
*****