DA'IMAN ABADAN

91-100

by @jameelarhsadiq6388

*🌺DA'IMAN ABADAN🌺*

_Hot love and fate story_


Na

_YAR'MUTAN KANKIA_


_MANAZARTA WRITERS_


*BOOK ONE*



*PAGE 91-100*


***


*NO EDITING❌*


_Ba damuwarka bace hawana online please malan I beg ka fita daga harkata_


kurama sakon nata ido yayi yana kallo.ya kuma maimaita karanta sakon nata yafi sau ba adadi,maimakon yaji haushin sakon nata sai yaji ya tsinci kanshi a cikin farinciki ya nemi fushi ya rasa.kalma Malan ka fita daga harkata shine yafi bashi dariya ma,wai ya fita daga harkarta bayan kuma yanzun ya fara shiga harkar tata tunda dai ko tana so ko bata so shine dai zai zama mijin nata,yana cikin sake kallon sakon nata Moha ya shigo yana cewa.."ka tashi mu shiga cikin gida kasan su Mom sun dawo." Kallon Moha yayi kamar ba zai magana ba sai kuma yace.."Ina sane so nike sai su Dad sun shigo sannan dan akwai maganar da nike son nayi dasu."


"Wace magana kenan."?


Cewar Moha yana ajiye wayar hannunshi dan daman gama wayarshi kenan Zubaida ya shigo room din,dan tabe baki yayi yana ajiye wayar tashi yace.."maganar wanann yarinyar mana." Murmushi Moha yayi yana cewa.."Broth wace yarinyar kuma." Harararshi yayi yana cewa.."ban sani ba please Moha wace yarinyar zan maka magana idan ba wanann marar kunyar yarinyar ba Zulaihat?dole nayi maganinta sai na koya mata hankali."


Fuuuu ya tashi ya shige toilet sai daure fuska yake,shi Moha murmushi yayi yana dage kafadunshi ya cigaba da wayarshi da Zubaida cikin so da kaunar juna,Koda Najib ya fito daga wanka direct gaban mirror ya nufa ya fara shiryawa kamar mace dan lotion din da yake using dasu wata macen ma bata dasu dan sun kusa kai biyar banda cream kuma ko wane sai ya shafa da yake bai tara suma kasunbace kawai da gemu ya gyarasu ya shafa masu mai da yake using dasu.wardrobe yaje ya fiddo wani white yadi mai kyau da tamsi ya saka yasaka hula white da takalmi hadda agogonshi apple ce white mai kyau ya saka ya fashe jikanshi da turaruka masu kyau da tsada ya dauki wayoyinshi ya kalli Moha yace.


"Zaka iya tasowa mu tafi."


Murmushi yayi yana cewa.."Babe byee zamu shiga cikin gida love you muaahhhh." Murmushi Zubaida tayi tana ajiye wayar tana kallon Zulaihat tace.."Sis fatan kinyi ma Dr Najeeb ya gajiyar hanya ko."?tsaki tayi tana girgiza kai tace.."Banyi ba kuma ba zanyi ba,Kinga Sis pls ki daina yi man maganarshi dan bansan ji sam."


"Amman Sis a gaskiya baki kyauta ba kaso mai sonka fa." Tsaki tayi tana cewa.."ce maki yayi yana sona?yaushe yayi dake sona yake?tom bari kiji na lura kema ya sanyenki kamar yanda ya sanye Umma da kalaman banza da wofi irin nashi.Najeeb ba sona yake ba kamar yanda nima bansonshi kawai zai aureni ne saboda wata muguwar manufa tashi nima kuma na shirya bi dashi da yanda yazo haka zan ansheshi."


Dafata Zubaida tayi tana cewa.."wallahi Sis Dr Najeeb yana sonki yana balain sonki so sosai ma tun kafin ya furta maki nasan da haka,kin manta number da ke maki text a da HA shin kin taba zaunawa kiyi tunanin waye HA kuwa Sis."?


"Bazanyi ba.ya kamata ki sani Sis banda lokacin tsayawa tunanin waye wani HA.ina hama da karatu ban damu da nasan waye shi ba dan ba matsala ta bace."murmushi Zubaida tayi tana cewa.."wai Sis yaushe kika zama haka?kamar ba ke ba." Turo baki kawai tayi bata sake cewa komai ba sai goge hawaye da ta kamayi dan zuciyarta zafi take mata sosai idan aka anbaci Najeeb a gabanta.(nidai nace Zulaihat ayi dai a sannu fah ahtoh lol🥂)



★★★


Ko wane part sun shiga sun gaida iyayen nasu sannan suka wuce part din Hajja dan sunsan a can ne zasu tadda su Dad a wajen Hajja dan acen suke firar dare.duk ranar duniya da sallama dauke a bakinsu suka shiga zaka samu waje a kasan carpet suka zauna suka mika gaisuwa a wajen su Abbu sannan suka kalli Hajja Najeeb ya fara gaisheta ,tsaki Hajja tayi tana cewa."Dan Ubanka ba zan ansa ba,ka gama yi man tsakin dazun shine yanzun dan kaga su Hamisu shine zaka wani gaisheni kamar na kirki?daman zama.jiranka nike wallahi yau sai naci ubanka Hamisu gashi nan zaune a gabana." Fashewa tayi da kuka tana face mijina ta nuna Dady ta cigaba da cewa.."Kai Hamisu kayi ma danka magana idan kuma ba haka ni zan tashi na bar maku gidanku na koma asalina daman Ina zaman zamana a wudil kuka daukoni kuka maidoni nan.dan kawai yaranku su ringa yi man rashin kunya da tabbata bayan ni na haifeku da ban haifeku ba ai ba zaku haifesu ba."


Matsawa kusa da Hajja Alhaji Hamisu da Alhaji Kabir sukayi a tare suka dafata suna cewa.."Hajja dan Allah kiyi hakuri." Dan shuru sukayi sannan Alhaji Hamisu ya cigaba da cewa."Hajja in shaa Allah daga yau hakan ba zai sake faruwa ba,kuma bake zaki bar gida ba dan wannan gidan kece ma mai iko dashi dan duk abuda muka mallaka a duniya naki ne dan Allah Hajja kiyi hakuri ki daina kukan nan."


Sauke ajiyar zuciya tayi tana cewa."A'a Hamisu ni nagaji da wannan wulakanci daga wannan sai wannan. nidai gidanku kawai zan bar maku dan haka gobe sanmako zanyi sai wudil." Girgiza kai Alhaji Kabir yayi yana cewa.."Dan girman Allah Hajja kiyi hakuri hakan ba zai sake faruwa ba."share hawayenta tayi tana cewa." Sai dai kam cikinmu ku zabi daya ni ko yaranku." Murmushi Dad yayi yana share mata hawayenta yace.."ke muka zaba Hajja yanzun ya kike so ayi."?


"Aure nike so ayi masu su bamu waje suje can su karata su da matansu mu mun huta da wannan fadin rai."


"To Hajja yanda kika ce haka za'ayi ai,amman anya suna da matan a kasa ma kuwa."?tsaki Hajja tayi tana tashi tsaya ta kama kuhu tana cewa."ai wallahi ko basu da yanmata sai anyi ma wannan gwardawan aure. sun bar mana gida zanje wudil da kaina na sama masu mata."


Cikin kwantar da murya Abbu yace."to Hajja zauna ayi maganar fahimata. tunda ga yaran nan aji ta bakinsu idan basu da wanda zasu aure sai aje wudil din a sama masu matan." Zama tayi tana hura hanci tana cewa.."wannan kuma can matsalarku ce dan ni na gama magana ta aure dai ba fashi." Girgiza kai kawai Dad yayi dan idan da sabo to sun saba da rigimar Hajja,gyaran murya yayi yana kallon su Najeeb yace.


"Har sau nawa zamu gaya maku ku daina yi ma mahaifiyarmu rashin kunya?to bari kuji shine farko da na karshen akan yin haka ku. sani itace silar zuwanmu wannan duniyar nan shashashu kun bani kunya Kun bani mamaki da girmanku kuna abu kamar masu cin kasa."


"Daga haka kudai ji abinda tace aure za'ayi maku idan kuna da matan da kuka sasanta to,idan kuma babu zataje wudil ta sama maku cikin yan uwa."


Kasa Moha yayi da kanshi yana cewa.."ayi hakuri in shaa Allah hakan ba zata sake faruwa ba." Dan shuru yayi yana Sosa kanshi dan kunya yaji tana neman rufeshi sai motsi yake da baki magana yake son yi ya kasa, Shima Najeeb hakuri ya bada bai sake cewa komai na sai.kallon Mamakin da yake ma Hajja wai shi take kokarin yi ma auren dole da ace baida mata kenan tabbas da ta kasheshi ta kuma.gama dashi dan shi ya lura ba zai iya iyawa da rigimar Hajja ba.


Dad ne ya katse shirun yana cewa.."alamu sun nuna cewa baku da matan da kuke so to Hajja yaushe kike son zuwa wudil din dan sama masu matan."? A tare suka dago suna cewa.."Aa Dad Muna da wanda muke so fah." dariya Abbu yayi yana cewa.."kunji shikiyen yara wato daman kuna da yanmata shine kuke wani nainoke kai ai da sai Hajja ta sama maku yan wudil muga ta karshe."


Murmushi kawai sukayi nan suka tautana akan maganar Hajja har kuka ta kara rushewa dashi. dan dadi batayi tunanin borin nata zai zama nasara ba,dan ba yau ta fara yin haka ba hakan maganar auren nasu sai dai tayi ta gama a lailasheta akan nan da sati biyu zasu fiddo sai kaji shuru. amman gashi yau magana ta zama gaske.burinta ya kusa cika na ganin auren manyan jikokin nata guda biyu wanda tafi so a cikin jikokinta bama kamar Najeeb da yaci sunan babban danta wanda Allah yayi ma rasuwa tun yana karaminshi kuma sak halinshi Najeeb ya kwaso na rashin son yawan magana.basu bar part din Hajja ba sai sha daya na dare sannan suka koma.shidai Najeeb wanka kawai yayi ya kwanta dan yayi alkwarin ba zai sake kiranta waya ba balle yayi mata magana ta whatsapp tunda haka ta zaba.


Washe gari Najeeb da kanshi ya kira Umma yai mata bayanin yanda sukayi dasu Dad dinsu sai da ya gama sannan Umma ta numfasa tace.


"Naji maganarka Najeeb amman banyi tunanin maganar auren zata taso da wuri haka ba,ga kuma karatunsu kaga yanzun zasu shiga aji ukku ya za'ayi da karatun nasu."? murmushi yayi yana cewa ."hakane Umma wallahi muma haka maganar tazo mana kwatsam,kuma maganar karatu ba damuwa bace Umma munyi maki alkwarin barinsu suyi karatu har zuwa matakin da suke da ra'ayin tsayawa bamu da wannan matsalar daga mu har iyayenmu kuwa."


Ajiyar zuciya Umma ta sauke tana cewa.."Alhmadullilah idan har hakane ai ba matsala daman karatun shine abun ji kuma ai komai lokaci ne lokacin ne nasu yazo shiyasa.Allah yasa albarka in shaa Allah zanje nayi ma Mahaifin Zubaida magana komai kenan kunji.sannan kuma itama Mamana zamuyi waya da kawu Shima komai kenan duk zakuyi Allah yayi maku albarka."


Da Amin ya ansa yayi mata godiya ya kashe wayar daman yayi wanka ya shirya.tashi kawai yayi ya wuce wajen Hajja yau ba da fada ta tarbaishi ba dan a cikin farinciki take kallo daya zakayi mata ka gane ,da kanta ta bashi abinci yaci sai nan nan take dashi shi abun dariya yaso bashi kamar ba Hajja ba,sai da ya huta sannan ya gaya mata yanda sukayi da Umma nan ma barke mashi tayi da kuka tana gode ma Allah. tun yana bata hakuri har ya gaji ya tashi ya bar mata part din ya wuce na Mom dan gaida mahaifiyar tashi da yake jinta har can kasan zuciyarshi,Koda ya shiga shuraima ce zaune a dinning tana shan tea,gaidashi tayi ya ansa yana tambayar ta Mom tace ta shiga kitchen yanzun.samu waje yayi ya zauna yana kallon wildlife abunda ya tadda suna kallo kena. kuma yasan aikin Shuraima ne dan bata da aikin da ya wuce kallon wild har mamaki take bashi.


Bayan ta fito daga kitchen saukowa yayi ya gaisheta ta ansa cikin so da kauna ta tambayeshi lafiyarshi ya ansa mata da lafiyalau. nan tayi mashi maganar auren da ake shirin zuwa nema masu fatan alkhari tayi masu da yake Hajia Murjanatu daman ba ruwanta dan ita macece mai saukin kai da kauda kai tana da kawaici.da nuna komai ba komai bane , komai Hajja zatayi mata bata daga Kai ta kalleta sai dai kawai ta bata hakuri.dan bata son hitina da tashin hankali sam,kuma hayaniya da yawan magana basu cika damunta ba shiyasa Hajja ke yawan cema Najeeb Mai halin irin na uwarshi dan duka halinta Najeeb ya kwasoshi na rashin magana da ma komai sai kuma yayan Dad da ake gaya mashi mai sunanshi Shima yana da shigen halin nasu.


Daga nan part din Hajia Zainab ya wuce wato mahaifiyar Moha suna kiranta da Ammi. nan ma ya dade sosai dan sai da yayi bacci ma sannan ya fito ya koma part dinsu dan yin wanka yayi Shirin sallah.


*Bayan kwana biyu*


Angama komai dan harta neman aure anje anyi kuma an basu har rana duk a tsada ta biki. randa Zulaihat taji an tsada masu ranar aure ba karamin hauka tayi ba a cikin room dinsu tayi kuka har sai da ta fara ciwon kai sannan ta hakura tayi shuru amman hawaye basu daina yin zarya a saman fuskarta ba.sai dai da sun zubo ta share tana gaya ma Allah dan wani irin zafi take jin akan maganar auren nasu.


Hajja tace ba zasu koma kano ba dan basu komawa kano da zama ba baki daya.sai dai asan yanda za'ayi,amman bata yarda ba dole su dawo Abuja da dama dan matansu anan Abuja za'a kawosu a gidajensu.


Sosai akeyin daru da ita dan an kusa sati ana hama da ita akan tayi hakuri.ta murje Ido tace itace Sam bata yarda ba idan sun je kano a halin yanzun to zance zasuje idan kuma anyi aure to zasuje gaida surukarsu,ba yanda suka iya suka nemo transfer suka dawo University of Abuja duk da ba haka Dad yaso ba,yaso su ajiye aikin su dawo campany.amman sunce Aa suna son neman na kansu suma,daga nan kuma suka shiga nema ma su Zulaihat green card suma su dawo nan Abuja su kammala nasu karatun.cikin ikon Allah sun samu da yake suna da C.G.P.A Mai kyau basu yi wani wahala ba komai ya zama normal haddata level ba'a rage masu ba.duk da Umma batajin dadin nisan da zasuyi mata ba, amman taji dadi sosai hakan na nuna mata yaranta sun samu mazaje na gari Wanda take masu fatan samu a Koda yaushe.


Yau tunda suka tashi suke shiri ba kama hannun yaro dan har kunshi da kitso duk sunyi ita Zulaihat abun mamaki yake bata ta rasa wani irin asiri Najib yayi ma su Umma haka. har suke wannan rawar jikin a kanshi,bata da zabi kuma bata da yanda zatayi dole ta saki jikinta wajen bada hadin Kai wajen gyaran gida da duk girkin da Zubaida ta kirkira za'ayi masu,Hakan da tayi sai ya kara ma Umma current sosai akan ta yarda ta anshi auren Najib kamar yanda take bukata hakan yayi mata dadi sosai dan har fuskarta ta nuna haka.


Itama taji dadi da taga Umma cikin walwala tasan walwalar bata wuce na ansar auren Najib da tayi sai dai ita kadai tasan abunda ke cikin zuciyarta gamai da auren,dan ba zatayi auren wahala ba.ba zata aureshi ya maida baiwarshi yar'aiki ba.ba shirya hakan ba sam.zata aureshi dan Umma tana so kuma zata aureshi ta koya mashi hankali ta sauke mashi wannan miskilancin da ke dawainiya dashi.shi ba kowa ba sai shigen girman Kai da miskilancin tsiya kamar ba lecturing yake ba,dan karamin tsaki taja ta cigaba da yanke cabbage da su cucumber da carrot da take da yake spaghetti salad zasuyi masu dan Zubaida tace Dr Moha yana sonshi sosai.shiyasa ta zage tana yankar kananu yanda zasuyi attractive din mutum dan kyaun su.


Bayan ta gama hada ingredients din da zatayi spaghetti salad dasu irin su waken gwangwani da cabbage optional ko salad (amman anfi anfani da salad kan cabbage idan kuma kina bukata zaki iya using dasu duka biyu,zan lissafo maku ingredients din sai kuma muyi procedure din dan yana kara lafiya ga jikin Adam sosai yana Kara kuzarin jiki sosai).


Ingredients


Cabbage/salad

Carrot

Cucumber

Kwai

Waken gwangwani

Bama

Salad cream

Spaghetti (mai kananun murji)

Sweet corn

Yellow pepper and green


Procedure


Zaki daura ruwanki saman gas ko murhu a tukunya idan ruwanki ya tafasa sai ki dauko taliyarki ki zuba a cikin ruwan ki motsata sosai dan karda ta dunkulle waje daya,ki bata 5min sai ki taceta a gwagwa ruwan ya tsane sosai.daman already kin gama yanka su carrot dinki shape din da kikeso sai dai ba'a yankesu manya kananun yanka yafi kyau da daukar Ido,sai ki dauko Bamarki da Salad cream kiyi mixing dinsu waje daya dai dai yanda zai isa kayan salad dinki,daman already ki dafa kwain ki yanda yayi maki sai ki yanke shi shima sai ki dauko babbar container dinki wanda zata isasheki ki zuba duk ingredients dinki a ciki.


Taliyar spaghetti zaki dauko ki fara sakawa a cikin rubber da zakiyi using da ita(amman spaghetti din sai kin kara rage mata tsawo sosai ta zama dai batayi tsawo da yawa ba kuma batayi gajera ba sosai) daga nan sai ki zuba yankanken kwain ki sai ki zuba sai kisa cabbage dinki sai carrot dasu yellow pepper sai kuma sweet corn dinki ki zuba ta ki saka wanken gwangwani sai mixing dinki na cream din ki zuba sai ki motse ki tabbatar da sun hade jikinsu waje daya sai ki rufe kin gama.(Zaki iya cin shi hakanan ko kuma kice bread dashi har da shinkafa ma).


Bayan sun gama hada spaghetti salad dinsu suka koma suka hada masu papaya milkshake suka ajiye gefe( yana da kyau ki rinta yawaita cin pawpaw(Gwanda) dan tana gyara jiki sosai da sosai 💯) .


Bayan sun gama kuma suka yi masu minipancake sannan suka wuce room dinsu dan yin wanka su fara shiryawa dan Dr Moha yace ma Zubaida flight din 1pm zasu biyo,koda suka shigo room dinsu fadawa tayi saman gado tana jera tsaki gami da cewa.."Ina dalili wallahi duk na gaji kama gama.walaha ba sannu bare na gode wallahi dan harda Dr Moha a wanann tafiyar da ba abinda zai saka ni sa hannu ayi dani. daman ance wani nacin arzikin wani."


Dariya Zubaida tayi tana cewa.."habawa Sis ai tuni na gano ki ta ciki na ciki. dan haka na daina wasting time dina akan neman favour wai ki daina ko kiyi dan na harbo jirginki Amaryar Najeeb."


Pillow ta wurga mata tana cewa.."nidai yarinya ta fita idona na kulle tun muna mu biyu." Daga kafadunta Zubaida tayi mean I don't care tace."Daman ai tabarmar kunya da hauka ake nadeta,wallahi kin ban mamaki wai jiya kece har 1am kina aikin kallon picture din Dr Najeeb idan bakyasonshi mai ya kai ki ta kallon dan mutane ki murmushi har da hunging fa anya kuwa Sis."


Ai tashi tayi tayo kan Zubaida tana kai mata bugu toilet ta fada tana dariya dan tasan ta gama da Zulaihat da ta nuna mata ta ganta tana kallon pictures din Dr cikin dare. duk da ba wannan ne na farko ba tasha kamata kawai shuru take ,gajiya tayi da pretending dinta ta fito fili ta gaya mata.(lol gasky kam Zubaida kin harbo jirginmu da gaske kuwa🙄).


Rasa ina zata saka kanta tayi dan kunya,amman da ta duba taga ai jiya ne kawai ta gani sai ta dan ji sanyi a ranta ta maje ta cigaba danna wayarta tana jiran fitowar Zubaida itama ta shiga dan ta watsa dan wani irin zafi ake kamar ta kurma ihu haka take ji.


Koda Zubaida ta fito bata bi ta kanta ba ta shige toilet duk da ta lura da irin da kallon da Zubaida take mata harda dariyar ma,amman ta dauke kanta ta nuna bata gani ba dan bata da bakin magana a nan kam.


Koda ta fito wanka taddawa tayi Zubaida na zaman tsara kwaliyar sai kace wata sabuwar amarya tsaki tayi tana girgiza kai tace.."ai gwara Umma tayi maki auren nan dai Sis tun kafin ki fara mana subbatu cikin dare."


"Warrr." Cewar Zubaida tana kyalkyalewa da dariya tana cewa.."ai gwara ni da nike komai nawa a baiyana da masu yi ta karkashin kasa warrrr." Harararta kawai tayi ta zauna ta shafa mai ta saka kayan ta murza daurin kyallabi mai kyau da daukar hankali daga nan bata sake shafa ma face dinta komai ba sai lipgloss da ta shafa ya kara ma brown lips din ra kyali kamar a lashe.


Suna gama shiryawa suka koma parlor suka kara gyarashi suka kunna bonner dan flight dinsu yayi leading suna hanyar zuwa gida suna gamawa suka koma room din Umma suka cigaba da labari kallonsu Umma tayi tana murmushi tace.


"Masha Allah yaran Umma kunyi kyau Masha Allah,sai dai matsalar daya ce."kallon juna sukayi suna kallon Umma kusan a tare suka ce.."maiye matsalar."? Murmushi tayi tana cewa.."baku shafama idanuwanku kwali ba." Sunbura baki sukayi suna cewa.." ai Umma bamu using dashi sosai shiyasa." Dariya suka ba Umma har sai da ta dara ta sake kallonsu tace.."Ashe har yanzun baku ida cika manyan mata ba."


"Amman Umma maiyasa kika ce haka."?


"Saboda baku shafa kwali baku san kwali shine sirrin kyau ba."?


Dariya Zubaida tayi tana cewa.."haba Umma yanzun kwalin shi zai zama sirrin kyau tom ina kuma aka bar jan baki."?


"Zubaida jan baki daban haka kwali ma daban ko wane da rawar da yake takawa a wajen fiddo kyaun mace,amman shi kwali daban yake ina nufin daban kololuwa ma dan haka bari na shafa maku sai ku kalli mirror duk zaku bani labari."


Shafa masu kwalin Umma tayi ta kara gyara masu fuskar tasu aikuwa sunga banbanci sosai da suka saka kwalin.dan ya kara fiddo masu da haskensu har da kwarjini sai da ya kara masu suna cikin mamakin yanda kwalin ya maidasu sai ga Moha ya kira Zubaida gasu a kofar gida kashe wayar tayi ta gaya ma Umma sannan ta kira shi tace su shigo da sallama suka shigo har cikin parlorn suka samu waje suka zauna.


Lumshe idonshi yayi ya bude yana mai kara bude kofofin hancinshi yana shakar kamshin parlorn mai saka natsuwa da kwanciyar hankali...yana son kamshi sosai dan shi ko asiri za'ayi mashi aka bi ta hanyar kamshi tom ba zaiyi wahalar kamashi ba,sun kusan five minutes da zama sannan suka fito a tare suka shigo parlorn cikin sallamarsu mai cike da natsuwa a tare suka ansa sallamar tasu sai dai shi Najeeb ba'aji muryarshi ba sai dai lips dinshi sun motsa sabanin Moha da sukaji muryarshi. take ta kara tsuke fuska dan ba tason wanann wulakancin nashi ace ansa sallama ta gagari musulmi abun da akwai ban mamaki sosai.


Samun waje sukayi suka zauna suka gaishesu nan ma bai ko motsa ba yana a yanda suka tadda shi idanunshi a lumshe sai dai ita Zubaida tana lure dashi ya ansa sabani ita Zulaihat da ta ida kaiwa wuya ji take kamar taje ta kama faska mashi maruka masu masifar bala'in zafi da zasu saka shi ya dawo a cikin hankalinshi,dan fakaitar idon su Zubaida tayi da suke ta yi ma juna wani kallon soyayya ta wurga mashi harara ta murguda baki sarai ya gani dan tunda suka shigo hankalinshi da idonunshi duk suna akanta ba tare da ita ta lura da hakan ba,dan sai tayi tunanin lumshe idonshi suke sai dai a'a kare mata kallo yake tas.tayi mashi kyau sosai ji yake kamar ya maidata ciki ko ya huta da yanda sonta yake azabtar dashi ba dare ba rana,yakan tambayi kanshi shin wani irin so yake mata har haka,yana jinta a can cikin kasan zuciyarshi komai tayi kyau yake mashi baya gajiya da kallon beauty face dinta.


Dan karamin tsaki tayi marar sound tana tashi ta fice waje sai turo baki take, ganin ta fita itama Zubaida ta tashi ta bi bayanta murmushi kawai yayi yana ce ma Moha.."kullun sonta kara karuwa yake a zuciya ta." Murmushi kawai Moha yayi. dan shi shedane akan son da Najeeb yake ma Zulaihat,yana mamakin yanda yake danneshi yake control dinshi idan har yana gabanta yana mamakin yanda yake nuna mata bai damu da ita ba ,bayan kuma kullun baida magana sai tata, idan anaso aga yayi doguwar magana to ayi maganarta ya rasa mai ke damunsu su duka biyu ga son juna a cikin kwayar idonsu amman miskilancin ya hana su baiyana ma juna shi.


Abinci suka shigo masu dashi sannan suka zuba masu suka basu waje dan sakewa suci kyau.aikuwa hakan yayi ma Najeeb dadi dan kusan duk abunda suka girka favourite dish dinshi ne har abun mamaki ya bashi kamar sun sani kuwa zagewa yayi yaci ya koshi dan kuwa papaya milkshake sai da yasha kusan two cup dan daman baya gajiya da shan shi ko kadan. kuma baya bakunta duk inda yaje ya ganshi dan yanason shi sosai.


Bayan sun gama suka shigo suka kwashe warmers din suka bar masu spaghetti salad dan shi haka nan ana iya cin shi ba tare da an nemi mahadi ba haka ma papaya sune kawai suka bar masu.


Fitowa Umma tayi suka gaisa sosai ta tambayesu ya mutun gida ta dan zauna suka dan yi fira ta koma ciki ta turo masu su Zulaihat tunda suka shigo Moha yayi ma Zubaida wajen kusa dashi suka juya masu baya suka cigaba da soyayyarsu,su kuwa manya manya maganin manyan kwari ko kallon inda dan'uwanshi uake basu yi ba sai danna waya da Najeeb yake ita kuma Madam Zulaihat ta kame ta kuma tsuke fuska tamau ta maida hankalinta gaba daya a wajen tv tana kallo. shi kuma yana danna wayarshi yana kara korawa da papaya dinshi haka suka kusa shafe three hour ba wanda yayi ma wani magana ,Koda suka tashi dan tafiya suyi sallah bata ce mashi komai ba. kuma bata tashi ta rakashi ba kamar yanda Zubaida tayi ma Moha,tana zaune har Zubaida ta dawo kallonta Zubaida tayi tana cewa.


"Wallahi Sis abunda kike sam bakya kyautawa sai kace bama ke ba.idan kina yin wani abun.kamar wanda bata taba shan inuwar silin ba.haba dan Allah be wise mana." Kama baki tayi tana kallon Zubaida da ta kulle Ido tana neman zabga mata rashin kunya ,tsaki tayi tana tashi ta bar mata parloun ta koma room din su danyi sallah dan taga take taken Zubaida so take ta ja mata balli a wajen Umma shiyasa take wannan maganar a parlor har tana kokarin daga murna.


Koda ta shiga room dinsu toilet ta shiga tayo alwallah ta kaffabara Sallah.tana cikin sallah Zubaida ta shigo itama allwallar tayo tayi sallah suna gamawa sukayi addua sannan Zubaida ta cigaba da cewa.."ko kadan banji dadin abunda kikayi ka Dr Najeeb ba wallahi ai ya wuce wannan wulakancin a wajenki wallahi."


Dafe kai tayi tana cewa. "inalillahi haba Ina dalili sai kace dole sai anyi maganar,mai kuma nayi da zaki damaini da magana daya sai kace dole."


Itama Zubaida cikin fada ta taso tana cewa.."dakata haka dan Allah Zulaihat enough,ban damu da komai zaki ce ba. kuma ban damu da komai zakiyi ba abunda na sani daya ne ko ki so ko karda Allah yasa kiso sai na gaya maki gaskiya wallahi dan ba tsoronki nike ba."


Lura da Zubaida ta dau zafi har ma ta fita daukar zafin sai ta sauko tana cewa.."ai daman bance kina tsorona ba Sis amman Dan Allah mai nayi har haka? haba Sis."


Tsaki Zubaida tayi tana cewa.."fadin kalmar mai nayi tana cusguna man zuciya Sis ki fito fili kawai ki anshi laifinki ba sai mun tsaya yin doguwar magana ba,amman kema kinsan baki kyauta ba kin kuma kunya tani wallahi."


Kama hannunta Zulaihat tayi suka zauna bakin gado ta fara cewa.."naji Sis amman Shima harda laifinshi.Sis kinga fa yanda yake man ya nuna man ni ba kowa bace yana nuna bani da wani matsayi a wajenshi ,barshi ma ina da matsayi kamar yanda kike fada amman haka ake zance Sis?nida shi wa ya kamata ya janyo zance ni ko shi?naga dai.har gaida wanann bawan Allah nayi ko ya ansa sai ma ya nuna baisan da halitata a wajen ba.shin Sis ni zan baida kaina na kama takularshi da surutu dan kawai Ina son muyi aure ko dan karda yaji ba dadi,am tired gaskya Sis am serious am very tired."


Dafata Zubaida tayi tana share mata hawayenta tace.."hakane sis kema kina da naki uzurin kiyi hakuri ki kuma cigaba da hakuri haka yake halinshi kenan kuma wallahi yana sonki Darling na gaiyaman kallar son da yake maki.ko wataran naji da kunne idan muna waya bai sani ba ya shigo sai kawai ya fara maganarki ki fahimceshi first shine ya dace kiyi ba biye mashi ba kina abunda kikaga yana ba.


"Shikenan Sis zanyi yanda kika ce in shaa Allah."


"Allah yasa much luv Sis." Daga haka suka cigaba da hidimarsu suka sake gyara fuskarsu suka koma wajen su Moha bayan sun dawo daga sallah ,bayan sun zauna tace.


"Sannu da dawowa." Sai da ya mula yasha iska sannan yace.."yauwa sannu." Bata sake ce mashi komai sai da suka hada ido da Zubaida ta daure ta sakar mashi murmushi tana cewa..Uhm yauwa." Can can kuma yace.."biki yana ta matsowa wani irin event kike bukatar yi."? Dago kanta tayi tana kallonshi sai kuma ta girgiza kai kawai ta maida kallonta wajen tv.gyara zamanshi yayi yana cewa.."fine tunda baki bukatar komai dan zuba man salad din nan." Zuba mashi tayi ya fara ci suna dan magana jefi jefi haka suka wuni cikin daure ma juna sai 8pm.suka wuce accomodation dinsu akan gobe zasu wuce 10am dan Najeeb yana da lecture din da zaiyi ma yan mester 2-4,har bakin mota suka rakasu sannan suka wuto gida.



*AMATULLAH DATA SERVICES*


*MTN*

500MB-140

1GB-270

2GB-540

3GB-810

4GB-1080

5GB-1350

6GB-1620

7GB-1890

8GB-2160

9GB-2430

10GB-2700


*AIRTEL*

500MB-180

1GB-350

2GB-700

3GB-1050

4GB-1400

5GB-1750

6GB-2100

7GB-2450

8GB-2800

9GB-3150

10GB-3500


*GLO*

500MB-180

1GB-350

2GB-700

3GB-1050

4GB-1400

5GB-1750

6GB-2100

7GB-2450

8GB-2800

9GB-3150

10GB-3500


9MOBILE

500MB-150

1GB-300

2GB-600

3GB-900

4GB-1200

5GB-1500

6GB-1800

7GB-2100

8GB-2400

9GB-2700

10GB-3000


VIA✓8160508316

Jamila Bello Abubakar

Opay bank

VIA✓0777512438

Jamila Abubakar Bello

Access bank


*** for call or whatsapp


*👭GARKUWAR MATA👭*

*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*

*GA*

*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*

Rage tumbi💯

Nono💯

Sanyi💯

Karin kiba💯

girmar hips💯

Ni'ima💯

Sabulai💯

Humra💯

Turarukan wuta💯

Matsi💯

Miski💯

Dilka💯

Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki

GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari

DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI

*****

*****