Chapter 2
by @mamanteddy
ποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈ
*DIJAMAH 'YAR FULANI*
ποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈποΈ
Plz hajiya inkinsan baxakimun Comment ba,tohhh don allah karki karantamun novel...
Masu Comment Allah yabar kaunaπ
______________________
Alh.maccido kuwa jin wannan tambayan da 'yar jaridan tayimae,nan take yasa shi ka'duwa,inda lokaci guda ta tado masa da tsohon famin dake cikin zuciyan sa...
Kasa bata amsa yayi,don dama bae shirya basu amsan kowani tambaya ba,balle kuma wannan tambayan nata...wanda kullum da tunanin iyalin nashi yake kwana da shi yake tashi.
'Daga mata hannu yayi,alaman baya da lokacin bata amsan ta,inda nan take jami'an tsoron da ke bayan shi,wasu a gaban shi,sukayi saurin rufamai ta hanyar dakatar da 'yan jaridun...nan take kuwa 'yan jaridun suka hau...hayanin yansu ta hanyar cewa" don allah ranka ya da'de minti 'daya mukeso muyi magana da kai...
Wannan 'yar jaridan ne takuma cewa " don allah yalla6ai ka bani amsan tambayata...haka dai kowa yake jefo nashi maganan.inda ministern yakasa ce masu komai...wanda nan take excout din shi suka bu'de mai motan da xai shiga.aiko da shigan shi jami'an tsaro da sojoji da 'yan sanda sukayo bayan shi...sauran mutane kuma suka cigaba da mae kirari ta hanyar cewa" Allah yakara kwana...maccidon mu,maccidon Alkhairy....
Haka suka dinga ihu,dae irin ta matasa,don kafun yabar wurin saida yayi masu Alkhairyn da yasa ba,kuma da suke mai kirari a kan sunan...
Niko sai da nakuma maimaita sunan,ina jin jinawa,kunsan suna linxami....hmm maccidon Alkhairy... Duk wanda ko akasan shi da abu...lallai yayi Alkhairy n ne har yagaji....tohhh Allah yabamu Alkhairy....
'Bangaren ummahn dijah kuwa da shiganta bukka,ta cidda dijah,kwance akan tabarman kaba...inda tuni ta jingine sandan ta,ta fulani a gyafe...
Xama ummah tayi ha'di dacewa" miyatti allah dijahma...yau kinga mun dawo ruga,ruwan sama bae bugemu ba.
'Dagowa dijahma tayi daga kwancen da take,nan ta kara matsawa kusa da umman nata,sannan tace"ehhh ummah,yau allah ya taimakemu...
"Ummah ne tace" dijamah bari na dama maki fura da nono kisha,don nasan kina jin yunwa yanxu ko!!!
"Dijahma ne tayi saurin cewa" ehhh ummah, kaman kinsan yunwa ko nakeji...
Dariya ummah tayi inda nan tace"taya baxan san abun da dijamah na takeso ba!!!
"Dariya dijamah tayi,inda nan takuma cewa" ummah nonon da aka dafah yaune....
Ehhh dijah na...bari na dama maki yanzu...
Batare da dijamah takuma cewa"komai ba,ta cigaba da kalllon ummah,wanda take aikin dama mata furan.
Bayan ummah tagama dama mata ne,tamika mata ha'di da cewa" toh gashi dijaman umman ta.maxa kisahnye.
"Tohh umma miyatti...
Kafin ummah ta bata amsa nan takuma cewa" ummah yaushe ne xaki dafamun marori...!!!
Wato tana nufin shinkafah...
"Murmushi ummah shattu tayi" inda cikin sanyin muryanta irin na fulani tace"gobe xan dafa maki marori,kinsan gobe da fita lumo...don haka acan sai na siyo maki...inmun dawo ruga mu dafah ko!!!
Umma ta 'karke maganan cikin kafe dijamah da ido.
Nan cike da farin ciki da 'doki dijamah tace"umma da gaske gobe da lumo???
"Murmushi umma tayi" ha'di da cewa" ehhh gobe da yawo ko!!!
Nan dijahma takuma dariya ha'di da cewa"lahhh umma ae baxani yawo ba,xan tsaya na saida maki da nono...kinga masamu sha'de da yawa koh!!!
Dariya ummah tayi ha'di da cewa"ehhhmmm dijamah kenan,kicemun dai kina farin ciki xaku ha'du da binttu acan...
Bawae xamu samu shade ba(wato ku'di)
Nan dijamah ta hau dariya,ganin ummah ta gano dalilin farin cikin da takeyi....
Haka ta amshi furar ha'di dafara sha,tana kuma xuba mawa umma surutu.
__________________________
Washegari da subahi ummah ta shirya dijamah,don su fito lumo da wuri...
Inda dijamah ansha dige dige na fulani...fuskan nan yasha jan jambaki da ba'kim kwallli...
Haka suka kama hanyar lumo dake cikin garin Adamawa....
Ummah na gaba,yayin da yadikko da dijamah ke tafe suna xuban da suka saba,don yadikko biye mawa dijamah take intana surutun ta,don umma wata xuvin har dariya ma yadikkon ke bata,intana biyemawa dijamah n.
A haka suka isah,kasuwa.inda da isan su wannan kasuwa,kowa ya hau dijamah... Dijamah
..!!!
Don gaba 'daya mutanen kasuwan ba wanda baisan dijamah ba.
Yayin da kowa ke kaunarta musamman yanda take surutun ta dakowa,koda bata sanka ba...infact dijamah irin wa'inan yaran ne masu shiga ran mutane...kowa nasu ne..
Tun da ta isah ta bar wurin umman nata.inda tuni sun game da bintutu...wanda nan take suka nitse cikin firansu da suka saba.da tsokanan mutane fa'da.
A haka kafin 'karfe uku,tuni kwaryoyin nonon da suka fito dashi ya 'kare...don haka ummah ta fara niman dijahma don su 'dau hanyan komawa rugansu.
Dijamah....!!! Dijamah....
Nan ummah tahau kiran sunan dijamah, wanda dijamah dajiyo kiran umman nata, yasa tayi saurin amsawa,ha'di da nufota...don tasan rugansu xasu koma yanxu.
Kaman daga sama umma taji wata murya ta kira sunan ta da" Hajiya Aisha...
Cikin sauri umma tajuyo ha'di da kare ma mekiran sunan nata kallo...
Tabbas baxata manta da uwani ba,a rayuwanta...
Cikin sauri uwani ta nufota...ha'di da share kwallan idonta..
A hankali umma tace" uwani kece,ashe kinan na.
"Uwani ce cikin tausayama ummah tace" ehh nice,dama kina nan hajiya ta!!!kinsan halin da ko.....
Saurin 'daga mata hannu umma tayi" sakamakon xuwan dijamah...
Shiru uwani tayi,inda nan ta maida kallonta ga dijamah,wanda ke raba ido kaman mae laifi...
Kama tagani sosai da mahaifin dijamahn.
Inda cikin murya can kasa tace"wannan yarinyan kine...itace khadijan dana sani!!!
Goge hawaye umma tayi,inda cike da dauriya tayi murmushi wanda tafi kuka ciwo....
Nan tace"ehhh itace dijamah...
Nan take uwani ta rungume dijamah, cike da farin ciki,inda a xuciyanta take kisima abubuwa da dama.
Horn da moton bayan su,ya hauyima uwani ne,yasata cikin sauri tasaki dijamah, ha'di da cema ummah"hajiya...a wani ruga kuke anan?
Umma ne ta tsaya kameΒ² don sam bata son,wani yasan inda take,ita da 'diyar ta ta...
Kaman daga sama taji dijamah na cewa" A RUGAR HAR'DO muke.....
Gaban umma ne ya fa'di,inda lokaci 'daya tahau tunanin abun da xatayi akan lamarin.
Nan uwani tayi saurin cewa"insha'allah my deejah xan kawo maku xiyara,nida Abban ki....
Cike da matsanan cin farin ciki dijamah tace"lahhh dama nima da baba!!!...irin na bintoto...?
Tausayim dijamah ne yakama uwani,inda nan take ta 'daga mata kai alaman ehhh,sannan tacigaba da cewa"kwanan
nan xakiga Abbanki...
Don da xaran yado kasan nan xaiji wannan kyakykyawan albishir,wanda ni kaina nasan bani kadai xan samu Alkhairy daga gareshi ba,har mada sauran mutane...wanda basu mason da xancen yana da iyali ba.....
_______________________
To be continued....βπ»