TRIPLETS (YAN UKU) BOOK 1 CMPLT

13-14-15

by @queenofsurprise1

*💞 TRIPLET'S💞





*💞The beginning💞*



*Episode 13-14-15*




*KANO*


Da murna da farinciki su Irfan suka shigo office ɗin daddy, jin shigowar su yasa daddy saurin goge hawayen face nashi ya miƙe ya shiga toilet ɗin cikin bedroom ɗin, sauri sauri ya wanke face nashi ya ɗan gyara jikin sa ya fito, zaune ya same su saman kujerar da yake zama, Irfan na zaune saman kujerar, Imran na zaune saman visitor chair,


suna ganin daddy ya fito suka kara faɗaɗa murmushin su Imran na faɗin "Bappa bamu zo da wuri bako?" Kakalo murmushi dole daddy yayi wadda ake cewa tafi kuka ciwo, yana kokarin yin magana Irfan sarkin basira ya rigashi da cewa "Bappa me ya sameka meke damun ka?" Cikin sauri daddy yace "babu komai Just I'm feeling headache ne" cikin sauri Imran yace "Bappa muje hospital mana to" girgiza kai daddy yayi ya nufi hanyar fita yana faɗin "No muje gida kawai naji sauki" kallon Irfan Imran yayi, yayin da shima Irfan ɗin shi yake kallo, shiru sukayi sai da daddy ya fice san Imran yace "Irfan me ka fahimtar game da Bappa dan ni ina ganin kamar a koi wani damuwa bappa bai taɓa yimin haka ba ka duba fa ka gani yau office nashi muka zo amma ya fice ya barmu a ciki, ni da wani lokaci ma idan nazo garin nan wallahi saboda son da yake min ajiye aiki yake a ranar ya ɗau hutu dan muyi hira koda kuwa bai da lafiya baya taɓa kyaleni na zauna shiru amma yau har ya fita ya barmu a office na shi kai a koi matsala" jinjina kai Irfan yayi kafin yace "kayi gaskiya Imran duk da ban san halin bappa sosai ba amma tabbas yana cikin wata damuwar yanzu dai tashi muje, ma karasa maganar a gida" miƙewa Imran yayi ba tare da ya sake magana ba, shima Irfan ya miƙe suka gera suka fice waje, yau daddy ko system na shi bai ɗauka ba haka suka wuce gida.


AKIL


Tsaye yake a tsakiyar palon daddyn Jelly, sanye yake da wando jeans baki da riga fari tas ta ɗaura cardigan mai hula a saman kayan nasa, ya sako hulan a kan sa, tsaye yake yana fuskantar makekiyar Tv plasma dake manne a bango ya bawa bene baya, ya duƙar da kai kasa ya zura hannu a aljihun sa da alama wani abun yake jira.


Da sallama Akila Aafia da Umaisha suka sauƙo daga sama suka shigo palon, wucewa Akila tayi taje ta rungume sa ta baya cikin shagwaɓa take faɗin "I missed you yaya Akil" juyowa yayi ya rungumeta yana faɗin "Missed you too heartbeat" yayi maganar dai dai lokacin da idon sa ya sauƙa kan Umaisha da Aafia dake tsaye kusa da centre table, nan taƙe ya ɗaure fuska tare da sakin Akila cikin tsawa yace "Waya baki izinin fita? Ina kuma kuka je nazo gidan nan ɗazun baku nan?" Ba Umaisha kawai ba har Akila sai da ta tsorata da yadda yayi maganar, nan take Umaisha jikin ta ya fara ɓari dan tana da tsoro sosai kirjin ta ya fara dukan uku uku


tsawa ya kuma daka mata "Ke bada ke nake bane?" Murya na rawa tace "Kayi hakuri mun bi su yaya Imran ganin gari ne shine yanzu suka dawo damu suka wuce office ɗin daddy" "Zo nan!!" Ya faɗa yana kare mata kallo, cikin tsoro ta kariso gaban sa zata tsugunna ya dakatar da ita ta hanyar nuna mata baya buƙata da hannun sa,


hannu yasa ya riƙo kunnan ta ya murɗe da ɗan karfi, cike da bada umarni ya fara magana "Daga yau sai yau idan kika kuskura kika sake fita ba tare da ni na baki izinin ba Allah ba zan yi kaffara ba daga ranar zaki dawo ɗaki na da zama kuma karki yi tunanin idan kin dawo ɗaki na ɗin daɗi zaki ji, no rufeki zan rinƙa yi ko palo ba zaki leƙa ba kin ji na gaya miki" hawaye Umaisha ta fara yi saboda murɗe mata kunne da yayi yana mata zafi sosai,


ganin tana hawaye ne yasa ya saki kunnen nata tare da ciro handkerchief daga aljihun sa ya goge mata hawayen yana faɗin "Idan kika sake bari hawayen ki suka zuba ranki zai ɓaci ban son ganin su in ma na farinciki ko na bakin ciki dukka bana son gani" shiru tayi ta sunkuyar kanta kasa ita kunyar sa ma take ji


tsawa ya daga mata "Ke ɗago ido ki kalle ni ban son munafurci sai kuyi ta wani sunkuyar da kai idan mutun na muku magana a waje amma da zarar anyi aure duk sai ku riƙiɗe ku zama tantiran yan iska masu lasisi sai ka rasa ina sunkuyar da kai lokacin da ba'a yi auren ba yake, sai ku watsar da komai ku ɗauko rayuwar dabanci da hauka to ni bana son munafurci komai na a fili nake dan haka na san komai game da halin mata karki fara min munafurcin kun nan tun yanzu, ki nunamin true color ki kawai a wuce wajen!!" ikon Allah ita dai Aafia zubawa Akil ido kawai tayi babu ko kyabtawa ita kuwa Akila in da sabo ta saba da halin sa,


cike da jin kunya Umaisha ta ɗago kai tana ɗan kallon sa kasa kasa "Ke nace ban son munafurci ko, ki kalli cikin ido na kawai tun yanzu yafi min a kan kiyi ta ɓoye fuska sai munyi aure kizo kina tsayamin a kai kina min wallahi tallahi kina kallo na cikin ido, shi abokina ma da yayi rashin Sa'a har ce masa ake idan ya isa yace tak al halin lokacin da yake neman auren ta tsabar kunya da biyayya irin nata itace Amyra a islamiyar su, amma daga yin auren su ta dawo rikakkiyar yar daban cikin gida to ni ban yarda da wan nan iskanci idan mace ta min abu dukan mutuwa zan mata" Allah Sarki Umaisha bai war Allah ko kala bata ce masa ba tayi shiru tana jin surfan da yake


"Zan wuce Kaduna yanzu ina son ki faɗa min me kike da buƙata" cikin sauri ta girgiza kai tana faɗin "Bana buƙatar komai" tayi maganar cikin sanyin murya, guntun tsaki yaja tare da sanya hannu ya ɗauko ledar da ya ajiye sama hannun sofa tun shigowar sa, ya miƙa mata yana faɗin "Na miki setting na komai na wayar karki kuskura naga number wani a wayar nan naki idan ba na family ki ba, san nan zan kara ja miki kunne a kan maganar fita ko nan da kofar gida ban yarda ki taka ba, bayan haka ban yarda ki rinƙa yawan magana ba kina hira da mutane ban yarda da wan nan ba banso" ya kai karshen maganar tare da ciro wrafer sabbin ɗari biyar biyar daga aljihun wandon sa wadda a kalla zasu kai 50k ya miƙa mata yana faɗin "Ki sai kati idan na cikin wayar ta kare san nan zan sa azo a ɗauke ki aje a buɗe miki Account dan nasan baki da shi" girgiza kai tayi cikin sanyin Murya tace "A'a yaya Akil ka bar kuɗin ka nagode wayar ta isa" a fusace ya ɗaga hannu zai wanka mata mari Akila tayi saurin riƙe hannun sa tana faɗin "Ansa kuɗin Umaisha ki tafi ɗaki idan kinje ki tashi Jelly daga barcin ya isa haka yamma yayi sosai" jiki na kerma Umaisha ta ansa kuɗin da gudu ta haura sama Aafia tabi bayan ta.


Kallon face ɗin Akila yayi cike da so da kauna yace "Heartbeat me yasa kika riƙeni?" Murmushi ta saki tana faɗin "Yaya Akil bakaga yarinya bace? Kamar ni fa take shi is 15 years fa, yanzu zaka iya dukana?" Girgiza mata kai yayi alamar a'a kafin yasa hannu yana shafar kan ta a hankali yace "Heartbeat ai ba wanda ya isa ya taɓa ki a kasar nan ya kwana lafiya babu shi wallahi" faɗawa tayi saman kirjin sa tana dariya tana faɗin "that's why I love you my lovely brother" duƙo da kan sa yayi ya manna mata kiss a goshi ta tare da raba jikin su ya nufi hanyar fita yana faɗin "Sai kun dawo ni na wuce Kd ki kula min da kan ki san nan ki faɗa wa yarinyar nan karta kuskura na sake bata abu taki ansa, zan iya karyata a kan hakan kin san bana son hakan" kafin Akila tayi wata magana ma ya fice daga palo, bin sa kawai tayi da ido tana mamakin irin halin sa.


Akil yana kutsa motar sa waje gate ɗin, su kuma su daddy suna kutso motar su cikin gida, ko kallon in da su daddy suke bai yi ba yaja motar sa ya bar layin gaba ɗaya ya miƙi hanyar airport.


Daddy kuwa yana kashe motar sa a parking space ya fito ya nufi cikin gida, kai tsaye bedroom nashi ya wuce ya rufo kofar ya sanya key,


Ko da su Irfan suka shigo palon, babu kowa shiru palon ganin haka sai suka kara sanin ba lafiya ba dan haka sai suka wuce masaukin su dan suje suyi wanka anjima suzo su tambayi daddy ko zai faɗa musu meke damun sa.



💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*ABUJA*


Shiryawa sukayi Rimsha cikin Abaya doguwar riga blue color, kayan sun ansa jikin ta, kyanta ya kara bayyana, da kyar mum ta iya ɗaure mata dark black curly hair tan nan saboda tsantsin gashin, tayi light make up a face nata, kamar ka sace ta ka gudu saboda kyau da tayi, ga dara daran fararen sleeping eyes nata nan sun sha kwalli sai kyan su ya kara bayyana sai ɗaukan hankali suke, su gwaggo dukkan su sai da suka yi magana a kan kyan idon Rimsha, idon nata a koi ɗaukan hankali da kyau sosai, idan ka kalleta in the first place zaka yi tunanin barci take ji koda kuwa daga barci ta taso sabo idon nata kamar zata lumshe su haka suke, gasu dara dara fafare tas kamar auduga kwayar idon nata kuma dark brown ne mai ɗaukan hankali gwanin ban sha'awa, sai faman lumshe su take tana buɗe wa, mum na fama da ɗaure mata kai.


Ita kuma Jehan sanye take da wandon jeans Ash color da top fari tas, ta tara gashin kanta tayi parking har baya, Mum na ce mata ta sanya hijabi sai faman turo baki take tace "mummy I told you I don't like hijab" shiru mum tayi bata sake magana ba dan tasan daddy ba zai ɗauke ta haka nan ba hijabi su fita ba


Tsab suka kammala shirin su ita dai Rimsha ta sanya mayafin rigar ta a kan ta, sun yi kyau over musamman Rimsha dake da wata iriyar jiki wadda ko wani kaya ta sanya sai ya zauna a jikin ta kamar dan ita a ka yi shi sai ya lafe yabi shape ɗin coca colar ta ya lafe kamar dan ita a kayi su, koda kuwa kayan Jehan tasa sai yabi shape ɗin coca colar ta ya zauna dai dai kamar nata ne while Jehan kuma tafita ƙiba kaɗan


Zaune a palo suka isko daddy yana jiran su, da sauri Rimsha ta tafi ta rungume sa tare da manna masa kiss a kumatu tana faɗin "Sorry dad for keeping you waiting" manna mata kiss shima tayi a goshi yana faɗin "No don't worry about that, have you done?" Gyaɗa masa kai tayi alamar eh sun gama, ɗago kai yayi ya kalli Jehan dake tsaye tana latse latsen wayar ta, "Where is your hijab Jehan?" Daddy ya tambaya yana kokarin miƙewa, turo baki tayi kamar biro cikin shagwaɓa tace "Allah daddy i don't like the hijab at all" kallon Rimsha yayi kafin yace "Kawo min Hijabin ta" da sauri Rimsha ta wuce ta nufi sama,


Jim kaɗan ta dawo hannun ta ɗauke da Malaysian hijab mai kyau fari tas yasha kwalliya da stone masu kyalli, ansa daddy yayi da kan sa ya sanya mata hijabin san nan ya riƙo hannun su suka fice mum na ta musu addu'ar dawowa lafiya da Allah ya tsare hanya


Sai faman kwaɓe fuska Jehan take haka suka wuce parking space, da sauri ɗan sandan dake tuƙa daddy yazo ya buɗe musu kofar motar suka shiga gidan baya, daddy ya zauna a tsakiyar su,


Ba tare da ɓata lokaci ba ɗan sandan ya shiga mazaunin driver yayiwa motar key suka bar gidan.


Direct *Jabi Lake Mall* suka nufa a parking space ɗan sandan yayi parking ya fito ya buɗe masu motor, suka fito suka nufi cikin Mall ɗin suka shiga suka wuce Boutique (wajen sayar da kayan sawa)


Rimsha ta gwada wan nan ta cire wan nan, ta gwada kaya yafi a ƙirga duk wanda tasa se tayi complain a kan bai mata ba.


Se daga baya tayi final choice akan wata wedding dress (kayan Amare) doguwar riga ce fara kal me high neck ga ƙasan ta ya buɗe sosai yana jan ƙasa daga saman kuma fitted da dogon hannu ne Amman net ne hannun, rigar ta zaɓa tare da ɗauko high heel black color sai crown sima black color, Sai ɗankwali wanda zata daura shi ma black.


Wani ma'aika ci ne ya nufa Rimsha da irin abun da Amare ke sawa wanda ake rubuta Bride To Be, cikin natsuwa ya fara magana "Me zan rubuta maki anan" yayi maganar cikin harshen turanci yana nuna mata abun, da murmushi ɗauke a face nata tace abata inda zata rubuta.


shi dai daddy ya zuba mata ido duk matsin ta akan idonsa, Jehan kuma kamar ba ta a wajen tayi shiru hankalin ta na a kan wayar ta tana latsawa,


Miƙa mata Memo aka yi da pen, ta ansa tayi rubutu ta miƙa masa, 5mins ya dawo da abun black anyi rubuta da farin zare an rubuta ta gaban * Happy graduation First lady Rimsha* ta baya kuma aka rubuta *Finally done with primary school*. Amsa tayi ta nufi daddy tace "look daddy how does it look?" Tayi maganar tana miƙa masa,


zaunar da ita yayi a saman cinyar sa sannan ya amsa abun cike da so da kauna yace "It looks beautiful" murmushi tayi tana kwantawa a ƙirjin sa karaf dara daran sleeping eyes nata suka sauka akan Jehan dake zaune tana latsa waya kaman ba ita a gurin "Jehan aren't you buying the clothe" Rimsha ta faɗi cikin kulawa tayi maganar tare miƙewa daga cinyar daddy ta nufi Jehan ɗin ta zauna a gefen ta, tana kallon face nata


Miƙa wa shima daddy yayi ya nufo su yana faɗin "My Jehan what's wrong bazaki sayi kayan bane?" Ya faɗi cike da kulawa yana ƙaraso wa wajen nasu, tsaki tayi tace "Daddy kayan da nake son saya I can't find the picture on my phone" tayi maganar cikin sanyin murya, buɗar bakin daddy sai cewa yayi "kinga kayan da Rimsha ta ɗauka?" Girgiza masa kai tayi alamar a'a tana faɗin "No daddy am busy looking for the picture, my mind wasn't there" jinjina kai daddy yayi kafin yace "okay take a look at that outfit there" yayi maganar yana nuna mata irin rigar Rimsha dake rataye a matsayin sample, zumbur Jehan ta miƙe tana murmushi wanda ya kara fito da kyan ta, "Yeah daddy it's, it looks more beautiful in reality" ta kai karshen maganar tare da wucewa ta nufi wajen rigar, sosai ta kurawa rigar ido tana kare masa kallo kafin ta juyo tace "Daddy what about the rest of the stuff?" Tayi maganar tana zuba masa dara daran Idon ta "zasu yi maki irin kayan da Rimsha ta zaba ai" Cewar daddy ya kai karshen maganar tare da juyowa ya kalli ɗaya daga cikin ma'aikatan yace "Get her what to write what she wants for you to write for her" ya ƙai karshen maganar yana nuna mata gefen sa akan tazo ta zauna, ba musu ta dawo ta zauna kusa da shi, ma'aikacin ya kawo mata, ita ma tayi nata rubutun tagama ta miƙa masa


Miƙa wa daddy yayi tare da riƙo hannun su yana faɗin "muje mu karasa shopping ɗin kafin suyi packaging ɗin, it's getting late now" miƙewa sukayi suka nufi kofar fita, juyo wa daddy yayi yace "package everything in less than 30 minutes we'll be back in a while" Ya kai ƙarshen maganar tare da fice wa ɗan sandan sa ya rufa masu baya, tun kafin su fice ma'aikatan suka amsa da "Alright Sir" Jiki na rawa suka fara haɗa masu kayan suka yi packaging suka saka a leda suka yi bill ɗin.


A bangaren su Rimsha kuwa direct cikin mall suka nufa suka sassayi kayan da zasu kai na party, ko mai kayan ciye ciye na students, abubuwa sosai suka saya kama daga Capri-son, Happy hour, Munchit, Cocopops sweets kala kala komai seda suka saya daga ƙarshe suka sayi leader ɗin party park, Jehan ta ɗauki na Barbie Rimsha ta ɗauki ta Sofia, the first suna fitowa dara daran idon Rimsha ya sauka akan Ice cream cikin zumuɗi tace "Daddy i want this Ice cream" tayi maganar tana nuna masa Ice cream ɗin "No my Siha sanyi yayi yawa" marairaice masa face tayi kamar zata yi kuka, cikin sauri yace "A'a My Rimsha me abun kuka kuma ɗauki dole ma ai na sai miki kefa Jehan zaki sha?" Turo baki Jehan tayi tana faɗin "Ni Smoothie nake so" jinjina kai daddy yayi Rimsha ta ɗauki ice cream ɗin daddy ya biya suka fice daga wajen


suka koma Boutique aka yi masu Bill na kayan da suka ɗauka, daddy ya bada ATM nashi, suka ansa suka sanya a POS na su san nan suka miƙo masa POS ɗin dan ya saka pin nashi, a tare Jehan da Rimsha kowa ya miƙa hannu suna rige rigen wai su zasu saka kowa yaƙi bari ɗaya yasa, mamaki ne ya kama daddy, a mall da zai biya kuɗin ice cream shi ya sanya pin da hannun sa basu damu ba sai a nan ne zasu ce su zasu sa.


Da dai daddy ya ga basu da niyar bari ɗaya yasa pin ɗin sai ya ansa ya sanya pin ɗin ya raba gardama.


Ɗan sandan su na tsaye yana riƙe da kayan da suka sayo a mall ɗin, zai ɗauki kayan Boutique ɗin ɗaya daga cikin ma'aikatan yayi saurin ɗauka yace "Its my duty lemme take it to the car" haka akayi ya kai masu kaya har mota daddy ya ciro rapper na 500 ya bashi godiya ya rinƙa zubawa har suka bar wajen ya juya ya koma bakin aikin sa.


Ko da suka koma gida su mum na palour suna jiran su. Daddy da Rimsha ne kawai suka yi sallama, Jehan kuwa cinyar Gwaggo ta haye ta fin cike Hijab ɗin kanta tana faɗin "My Goggo am tired am hungry" shafa kanta Gwaggo tayi tace "sorry let's go and have dinner daman ku muke jira" ta ƙai karshen maganar tana kama hannun ta suka nufi dining. Ita kuwa Rimsha gun Mum ta nufa ta zauna a gefen ta ta kwantar da kanta a kafadar ta "let's go and have dinner" mum ta faɗi tare da kama hannun Rimsha takai ta kan dining gun su Gwaggo ta dawo wajen daddy ta masa Sannu da zuwa tace suje su ci abinci tun da yayi wanka kafin su fita in yaci abinci se yayi wankan kwanciya. Jinjina kai yayi san nan suka wace dining ɗin suka fara cin abinci.



After some hours.


RIMSHA & JEHAN


Zaune suke a Palon sama Kowa Cikin kayan bacci.

Sun baza tulin kayan da suka sayo suna aikin sassakawa a leda, se kusan 11 pm Suka kammala sannan kowa ya nufi makwacin sa kamar yadda suka saba sai murna da farinciki suke.



*PRIZE-GIVING* DAY


A yau ne ranar ƙarshe da zasu makaranta zasu yi hutu sunyi shirin su kaman amare komai irin daya Gwaggo ta daura masu ɗankwali kaman gwaggoro suna sanye da danƙara danƙaran gold kaman larabawa, sun fito sun yi kyau over. Daddy na sanye Cikin danƙareriyar getzener ɗinkin babbar riga Fara kal anyi mata Aiki na Manyan Mutane da Blue ɗin zare ya saka Hula ita ma blue takalmi ma blue se kamshi yake zubawa kaman sabon ango.


Bayan sun yi breakfast se wurin 9:30am suka bar gida kasan cewar 10:00am ne partyn Rimsha ta matsa su tafi shiyasa suka tafi da wuri.


Tun daga bakin gate ɗin an tsara komai anyi adon da ballons kalar uniform ɗin makarantar, a cikin Hall ɗin makarantar za'a yi partyn kowa yayi shiga ta alfarma.


Daddy a motor sa ya tsaya yace da ɗan sandan ya rakasu ajujuwan su ya kai masu kayan su, haka akayi tun daga nesa da ajin su ƴan ajin su Rimsha suka rinƙa mata kirari "Our first lady is now our Princess" aji ta shige suka fara gaisuwar rungume rungume juna da students yadda suka saba, Aunty ta fito ta amsa kayan da ɗan sandan ya biyo Rimsha dasu.


Jehan kam tuni ta wuce zuwa class ɗin su tace ma ɗan sandan ya fara kaima Rimsha se ya kawo mata na ta kayan, bayan Aunty ta amsa kayan Rimsha sai ɗan sanda ya nufi ajin su Jehan ya kai mata nata kayan, san nan ya dawo parking space wajen daddy ya tsaya a gefen motor.


10pm


Dukkanin ɗalibai da malamai duk sun hallara a Babban Hall ɗin makarantar wasu parents ma duk sun shigo Jehan da Rimsha se zuba ido suke suga shigowar daddyn su bama su kaɗai ba kowa jira yake yaga shigowar Nawazuddeen amma shiru bai shigoba.


Sai 10:30am ya shigo yana tafiya ta ƙasaita irin na manyan mutane kana ganin shi ko baka san wanene ba zaka san ba ƙaramin mutum bane. Malamai ne cike harda me makarantar duk suka miƙe don girmama shi, ɗalibai ganin Malaman su sun miƙe yasa suma suka miƙe sauran parents ma haka, shi mai makarantar ne ya zo ya taro daddy ya miƙa masa hannu sukai musabaha. San nan ya masa jagoranci zuwa inda aka tanada domin shi, kafin ya zauna ya buƙaci a bashi mike zeyi magana, jiki na rawa MC ya bashi aka kashe kiɗan dake tashi saman sama, Cikin natsuwa da wannan zazzakar voice nashi yayi Sallama dinbin al'umma dake wajen suka amsa masa sannan ya buɗe musu taro da addu'a da turancin, daga ƙarshe ya musu godiya ga karrama shin da suka yi sannan ya buƙaci kowa ya zauna kamin shi ma ya zauna. Duk abinda ke faruwa akan Idon mummy da Gwaggo ne da sauran dubban al'umma waɗan da suka kalla live a TV ciki harda abokan takarar daddy.


Mai makarantar ne ya amsa mike ɗin cikin girmamawa yace "ku tafa masa" gaba ɗaya Hall ɗin ya dauki tafi raf, raf, raf, na kusan tsawon minti biyu,


san nan mai makarantar ya yi Godiya ya gabatar da speech akan makarantar ya gabatar da Malaman makaranta gaba ɗaya sannan daga bisani ya nemi daddy da ya bama students gifts nasu da award nasu. Amsa masa daddy ya yi.


makarantar ya fara kiran students ɗaya bayan ɗaya suna zuwa amsar gift nasu da award nasu, da aka zo kan Rimsha Ita kaɗai Awards Guda huɗu taci Best in Islamic Studies, best in English, Best in Mathematics, se best in home economics. Sannan aka bata wani medal na The person with the Highest points. Daddy sabida murna seda ya mata hawaye a cikin bainar Jama'a, ta ƙara so gabansa ta share masa hawaye tace "Daddy In Sha Allah we'll keep making you proud" murmushi yayi yana kokarin tsaida hawayen sa, Jehan ta ƙara so wajen cikin harshen turanci tace "Daddy please stop crying" ta faɗi kaman zata yi kuka murmushi shi ne ya kubce masa ya haɗe su gaba ɗaya ya rungume yace "Am proud of you my daughters Allah ya yi wa rayuwar ku Albarka" gaba ɗaya Hall ɗin suka amsa da Amin Amin, shi bema san yayi maganar da ƙarfi ba har suka ji.

Miƙewa yayi ya ciro check a aljihunsa wanda already ya rubuta tun a gida ya miƙama me makarantar yace "gashinan Sadaƙatul Jariya school fees ne na Mutane 500 complet har su gama makarantar nan, ku sanar da marasa ƙarfi da suke son ƴaƴan su suyi karatu basu da halin biya musu gashinan na biya" "Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu Akbar" Hall ɗin ya dau Kabbara, Mutuwar tsaya da ta zaune manya manyan masu kuɗi da sukazo taron domin ƴaƴan su suka yi, sun sha ruwan mamaki irin kyautan da daddy yake, baya jin kyashi ko kaɗan, shi kuwa daddy bai jira cewar kowa ba yace su Rimsha su ɗauki stuffs ɗin su su wuce gida, haka kuwa a kayi suka ɗauka suka nufi mota sai sauri daddy yake dan bai son jama'a su tsaida shi suce zasu yi hoto.


Yana zuwa parking space ɗan sandan sa ya buɗe kusu mota suka shiga, da sauri ɗan sandan yaja motar suka bar school ɗin.



Share fisabilillah 👏


To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai


💞Star Lady💞


*💞 TRIPLET'S💞




***



*💞The beginning💞*



*Episode 14*




*KADUNA*


*Unguwar sarki*



Hajiya Umaiya na sume a tsaye, shi kuma Abba yana sume a kwance har sai da Lami ta dawo daga kasuwa, ta isko su a sume, ihu ta fasa tayi kan Hajiya tana kiran sunan ta, tana taɓa Hajiya, Hajiya ta zube kasa wanwar, kara tsorata Lami tayi ta nufi fridge ta ɗauko ruwa jikin ta sai kerma yake ta buɗe ruwan, tsabar kiɗimewa da tayi bata san lokacin da ta juyewa Hajiya ruwan gaba ɗaya a kan taba, Ihu Hajiya ta fasa mai razaba kwakwalwa tare da miƙewa zaune tana zazzare ido kamar an tare ɓera a tarko, waige waige ta fara yi kamar mai neman wani abun, can idon ta ya sauka kan Abba dake sume cikin tsoro tace "Ke Lami me yasami Alhaji? Yaushe ya dawo?" Kara zaro ido waje Lami tayi murya na rawa tace "Nima a nan na dawo na same ku kuna sume" kara waro ido waje Hajiya tayi, tayi shiru tana kokarin tunano me ya faru, amma ta kasa tuna komai, jiki ba kwari ta yunkura tana son miƙewa, sai ji tayi gaba ɗaya jikin ta ya mata nauyi sosai, dafe kan ta dake sara mata kamar zai fashe tayi da kyar ta iya miƙewa tana faɗin "Kawo min ruwa" da sauri Lami ta miƙe ta ɗauko wani ruwa a fridge ta dawo ta miƙewa Hajiya, ansan ruwan Hajiya tayi tare da duƙawa kusa da Abba ta tarfo ruwan a hannun ta ta shafa masa a face nashi, dogon numfashi yaja tare da saukewa a hankali, ya waro idon sa waje ya fara bin saman da kallo kafin ya sauko da idon sa kan face ɗin Hajiya, a hankali ya miƙe zaune yana kallon Hajiya "Alhaji yaushe ka dawo?" Hajiya ta tambaya tana zaro ido, shiru yayi yana bin ta da kallo, "Alhaji kayi magana mana"


da kyar ya iya motsa bakin sa yace "Hajiya yaushe na dawo? Ba ina Abuja ba?" tashin sense shiru Hajiya tayi tana kokarin tunano yaushe Alhaji ya dawo, amma ina ta kasa tuna komai, shima Alhaji shiru yayi yana kokarin tunano yaushe ya dawo bayan shi dai yasan yana Abuja wajen meeting to ya akayi ya dawo gida


Almost 30mins sunyi shiru suna tunani daga karshe suka hakura da kokarin tunano me ya faru da su, haka suka miƙe suka wuce sama ran su cike da tunani fal.


Hayewa saman gadon Abba Hajiya tayi ta kwanta ta dafe kan ta dake tsananin sara mata kamar zai fashe, shi kuma Abba yaja kafar sa a hankali da kyar da kyar ya shiga toilet dan yin wanka,


a ta kaice dai su Hajiya sun manta komai da ya faru sun manta da abun da ya faru da Hajiya Zainab.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*WASHINGTON DC*



*LOT 33*


*06:00am*


Sanye yake da short mai ɗan girma zuwa gwiwar sa sky blue kyakkyawar cinyoyin nan nasa a waje ga kyawawan gashi dark brown kwance a cinyar nasa daga sama har zuwa idon sahu na kafar sa, jikin sa na sanye da farar riga mara nauyi mai karamin hannu, kyau iya kyau Tiger na da shi kyakkyawan Bature ne sosai sai iskanci kala kala, ba kalan da bai iya ba rashin kutunci ne cike fal a kan sa,


A hankali yake takawa har ya haura sama gaba ɗaya, ya tura kofa ya shiga wani waje mai kama da ɗaki, sai dai gaba ɗaya wajen da glass a kayi shi, kasan wajen kuma kyakkyawar grass carpet ne a wajen launin kore, waje ne mai girman plot 1, an kawata wajen sosai ga luntsuma luntsumar kujerun hutawa san nan ga injunan motsa jiki kala kala a wajen, da gani kasan wajen training na su ne, ga in juna da mashuna kala kala masu kyau da tsadar gaske, wajen dai ba'a chewa komai sai dai masha Allah.


A hankali Michael ya kariso cikin wajen, kusa da wani mashin na motsa hannun ya tsaya, yayin da wani matashi ke kwance a wajen yana ɗaga wasu kana kana nan karafuna.


Kallon tsab Michael yayi wa matashin kafin yace "Good morning photo copy" Ajiye karafunan hannun sa guy ɗin yayi tare da miƙe wa zaune, subhanallah tsarki ya tabbata ga Ubangiji dayayi wayan nan halittu, guy nan kamannin sa ɗaya sak da Michael ba abun da ya raba su sai kwayar ido da gashin kai, Michael gashin kan sa dark brown ne, shi kuma guy nan gashin kan sa ya rina ta ya sanya mata color ta dawo light brown mai kama da golden, sai kuma kwayar ido Michael kwayar idon sa light brown ne shi kuma guy ɗin nan nashi idon light ash ne masu kyau, ban da ido da gashi komai nasu ɗaya ne.


Kallon tsab guy ɗin yayi wa Michael kafin yace "how are you doing this morning?" "I'm going well" ya faɗa tare da wucewa ya nufi wajen motsa kafa, har ya kai wajen sai kuma ya juyo yana faɗin "James yaushe Romeo zai dawo?" Komawa James yayi ya kwanta ya ci-gaba da ɗaga karfen da yake yana faɗin "I don't know maybe this week" shiru Michael yayi ba tare da ya sake magana ba, shima James shiru yayi ba tare da ya sake magana ba suka ci gaba da motsa jikin da suke.



07:00am dankareriyar gold watch dake ɗaure a hannun su tayi kara lokacin guda alamar awa ɗaya ta karu a kan lokaci, kallon juna suka yi, kusan a tare suka ajiye karafunan hannun su, kowa ya sanya hannu yana kokarin kashe karar watch ɗin, dankareriyar gold watch ne mai bala'i kyau da tsada iri ɗaya ba abun da ya raba watch ɗin, ko ina zasu je watch ɗin na hannun su basa rabuwa da shi sai dai in zasu yi barci ko zasu yi wanka shi ne suke cirewa,


Tsai da karar watch ɗin sukayi a tare, dai dai lokacin jibga jibgan Bodyguard na su guda huɗu suka shigo wajen hannun su ɗauke da plate masu ɗauke da cup na ruwan lemon wadda masu motsa jiki ya kamata su sha idan sun kammala motsa jikin nasu,


Rabuwa bodyguard ɗin suka yi, biyu suka nufi wajen Michael biyu kuma suka nufi James, cikin girmamawa suka miƙa musu plate ɗin, ba musu kowan nen su yasa hannu ya ɗauki cup ɗin suka kafa a ɗan karamin bakin su.


Cikin ƙan ƙanin lokaci suka shanye lemon ɗin tas, tare da mai da cups ɗin saman plate dake hannun bodyguard ɗin, daman ka idar motsa jikin kenan shan 1 cup na lemon idan an kammala.


Bayan bodyguard ɗin sun fice ne Michel ya kalli James yace "Photo copy zan je na shirya na wuce school yanzu" ba tare da James ya kalle sa ba yace "Ba za dai ka dai na ce min photo copy ba ko?" Miƙewa Michael yayi yana faɗin "To ai kai photo copy ne da gaske dama aikin sojan kawai kai ma ka shiga da ya fima yawon ban zan da kake ɗin nan kullun gaka wajen partyn abokai, ka gama school kana zaune" shiru James yayi ba tare da ya sake magana ba, sai mamaki yake wai Michael ne yake ce masa mai yawon banza to ba gwara shi ba ya samu ya kammala school ɗin, aiki ne dai kawai bai fara ba kuma baya ra'ayi yin koma ne hutu kawai yake sonyi a gida shi kuma fa, wuce wa Michael yayi ya fice daga wajen ya nufi bedroom na shi.


A hankali shi ma James ɗin ya miƙe ya wuce nashi bedroom ɗin dan yaje yayi wanka.


After some hours.


James ya fito sanye da wandon jeans baki da t-shirt navy blue masu bala'i kyau da tsada sai kamshi yake zubawa, kai tsaye parking space ya nufa, yaje ya shiga motar sa kirar *Bugatti centodieci* ya tayar


ko da yazo fita parking space ɗin sai da wan nan na'uran ta faɗi sunan motar da number ta da kuma sunan wanda ya ke cikin motar, san nan gate ɗin parking space ɗin ta buɗe, James ya danna hanchin motar waje.


Yana fita ya saki kiɗa mai tashin kai yana kaɗa kan sa yana tuƙi cikin kwanciyar hankali.


Kai tsaye *medina Hotel* ya wuce, horn ɗaya yayi a bakin gate ɗin masu gadi wajen suka buɗe masa, ya kutsa hancin motar sa a ciki ya nufi parking space, yana kashe motar ba tare da ɓata lokaci ba ya fito tare da sanya fake face a face na shi dan kar kowa ya gane sa san nan ya shige cikin katafaren hotel ɗin.


Manya manyan Alhazawan kasar ne a wajen sunyi cincirindo shi kaɗai a ke jira daya iso gaba ɗaya sun zauna saman luntsuma luntsumar sofan dake cikin ɗakin hotel ɗin, cikin taku irin na jaruman maza ya kariso wajen, ya kara ɗaure fuakar nan tasa tamau, zama yayi gefen wani jibgegen Bature wadda da ka gansa kaga wadda Naira ta zauna ma sosai, ba tare da ɓata lokaci ba suka fara tattaunawa.


Almost 40 mins suna tattaunawa nawa kafin daga bisani wan nan jibgegen Baturen ya jawo trolley dake gefen sa ya buɗe zip ɗin ya fito da wasu pistol gun ya fara rabawa mutanen dake wajen, ko wan nan su yana amsa yayi godiya amma da a kazo kan James sai yaki ansa, kallon sa Baturen yayi tun kafin yayi magana James yayi saurin cewa "Ba zai yiwu na shiga gidan mu da gun nan ba, idan nace zan shiga da ita tofa sai an kama ni dan gidan mu na da tsaro sosai" jinjina kai Baturen yayi kafin ya mai da gun ɗin cikin a kwanakin ya ajiye yana tunanin wai ma James ɗan waye ne dan bai san asalin wanene James ba kawai harkalla ta haɗa su,


Cike da tunani fal ransa ya fito musu da wani abu kamar daskararren jini ne a ka yayyan ka, ko wan nan su ya amsa da fara'a amma ban da James shi fuska a ɗaure ya amsa, kallon su Baturen yayi san nan ya basu umarnin a kan su cinye abun, ba musu suka sanya a bakin su suka cinye, shiru ogan nasu yayi na yan mintoci kafin yace zasu iya tafiya sai a zama na gaba kuma, da sauri James ya miƙe kamar mara gaskiya ya bar wajen ya nufi motar sa ya shiga ya bar hotel ɗin da gudun gaske.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*ABUJA*


Zaune Rimsha take saman sofa mai zaman mutun 2 a palon kasa tayi shiru ta kura idon ta a kan makekiyar Tv dake kunne ana labarai a kan wan nan Baturen,

da sallama daddy da mum suka shigo Palon sai murmushi suke kai da ganin su kasan suna cikin farin ciki da annashuwa.


My siha a na kallon labarai a kan TGA ne?" Cewar daddy yayi maganar tare da zama kusa da ita, a hankali ta kwanto jikin sa tare da ɗago dara daran sleeping eyes nata cikin shagwaɓa tace "Daddy yau ba TGA nake kallo ba na asalin nake kallo GAR shi ne asalin General of the army R ɗin kuma ban san ma'anar ta ba" shafa kan ta yayi yana murmushi, zama mum tayi gefen ta tana faɗin "Ni Rimsha wlh bana gane wa mutanen nan naki yau kiga wan nan gobe wan nan to shi kuma GAR ɗin waye shi?" Miƙewa tayi zaune daga jikin daddy cikin sauri tace "Mum GAR shine asalin jarumi na ai shima TGA ɗin yana burgeni amma ba kamar GAR ba" jinjina kai mum tayi tace "Ni kam Rimsha ba abun da na gane game da wan nan bayanin naki kyale ni kawai muje a kina san kallon TGA" komawa Rimsha tayi ta kwanta jikin daddy tana faɗin "Nima mum ba wani gane wa nake ba suna rikita min kwakwalwa sai yau na lura da mai light blue eyes ɗin nan da mai light ash eyes ɗin ashe ba mutun ɗaya bane na gano gakan ne ta sunan su, mu kullun bamu duba suna kawai idan mun ga hoton shi kenan ban taɓa tunanin GAR su biyu bane sai yau sun caza min kai, mai light ash ɗin idon nan shi ne TGA mai light blue idon kuma shi ne GAR wato General of the army kenan kuma shi ne jarumi na, ban taɓa luraba sai yau, suna kama over idon su ne kawai ya ban ban ta su" shi dai daddy shiru yayi yana jin ta amma ba wai dan ya fahimci kan zancen nata ba, dan shi ba wani zama yake yana kallon labaran Usa Army's ɗin nan ba, ita dai mum amsa mata kawai tayi amma ba wai dan ta gane kan zancen nata ba, shiru gaba ɗayan su suka yi suka zubawa Tv ido suna taya Rimsha kallo, while ita kuma Jehan tana ɗaki tana zubawa Gwaggo shagwaɓa da iya shege.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*KADUNA*


Abba da Hajiya Umaiya sun manta komai da ya faru da su da rana a cikin gidan, sosai abokan Abba ke kiran sa a waya suna tambayar sa Alhaji Mustapha sai dai yace musu tun da ya dawo basu haɗu ba domin kuwa tabbas babu abun da Abba da Hajiya suka iya tunawa, shi Abba ma ya kasa tuna lokacin ma daya kamo hanyar Kaduna shi iya sanin sa yana Abuja bai san ya akayi ya dawo ba.


Kamar kullun bayan sun gama cin abincin dare suka wuce bedroom na Abba dan su kwata, da kyar Hajiya ta iya samu tayi wanka saboda kasala da take ji jikin ta duk zafi yake mata kamar wadda a kawa mugun duka, a ɓangaren Abba shima hakan ne gaba ɗaya jikin sa ciwo yake masa, haka dai suka lallaɓa suka yi wanka tare da shirin barci suka kwanta.


Cikin dare sai juyi suke dukkan su sun kasa barci, dafe ciki Hajiya tayi kamar zata yi kuka tace "Abban Imran yinwa nake ji sosai kamar zan mutu" da mamaki ya miƙe ya kunna lamp na gefe da gefen gadon, abun ya ɗaure masa kai cikin kasalalliyar murya yace "Hajiya yinwa kuma?" Gyaɗa masa kai tayi alamar eh, yasha ruwan mamaki sosai dan basu taɓa jin yinwan dare haka ba


A hankali ya koma ya kwanta yana faɗin "Muna da sauran takeaway a palo ai kije kici ni zan sha Yoghurt dan nima yinwa nake ji kuma banson cin abinci da tsohon daren nan, idan kin gama cin abincin naki ki tahomin da L&Z Yoghurt mai sanyi guda ɗaya" to kawai Hajiya tace tare da sauƙo wa daga gadon ta nufi Palo.


Ko da ta shigo palo wutar palon a kashe, kai tsaye ta wuce wajen switch ta kunna wutar palon nan take haske ya gauraye ko ina a cikin Palon,


Waro ido waje tayi kamar idon ta zai fito waje ya faɗi kasa, nan idon ta ya mata arba da tashin hankali da kwakwalwa ba zai ɗauka ba, jibga jibgan mutane su uku ne zaune saman sofa jikin su duk jini idon nan nasu launin jini ga fuskokin su bakake kirin abun tsoro, wata yar kyakyawan matashiyar yarinya ce zaune a tsakiyar palon ta na fukantar kofar palon ta bawa Hajiya baya, ta dukar da kai kasa kamar tana cin wani abun,


cike da ruɗu da tashin hankali murya na rawa Hajiya tace "A..Ab..Abla" cikin sauri yarinyar ta ɗago tare da wayan nan dodan nin dake zaune saman sofa, tabbas Abla ce ke zaune tana cin namar mutane ɗanye idon Hajiya ya gane mata, kai kallon ta hajiya tayi kan abun da Abla ke ci,


razanannen ihu Hajiya ta fasa ganin namar jikin mutun Abla ke ci, sai lokacin Hajiya ta iya tuna abun da ya faru ɗazun, dan kuwa naman Jikin Zainab Abla ke ci, Hajiya na kokarin guduwa ta koma sama idon ta ya sauka kan wasu dodan nin dake zaune saman kujerun table suna cin ɗanyen nama ga face nasu abun tsoro idon nan nasu kamar zai fito waje, ga launin idon jawur kamar jini suna da katon hanci Kamar kofa ga girman baki kamar masai ga idon na su ma manya manya masu firgitar da ɗan adam, ihu Hajiya ta kuma fasawa kamar makoshin ta zai fashe amma ina gaba ɗaya gidan ba wan da ya kawo mata ɗauki, a guje ta juya kamar zata mutu ta koma bedroom nasu.


Tana shiga tayi arba da wani tashin hankali, dan kuwa wayan nan dodan nin ta gani suna tsere da Abba sun hana shi fita, shima sai ihu yake amma ba'a iya jiyo sautin ihun nashi, ga dai bakin sa na ihu amma ba wanda ke jin komai, tsabar tsorata Hajiya yanke jiki tayi a wajen ta sume.


Shi kuma Alhaji ya daɗe yana tsere da wayan nan sheɗanun dodan nin gashi sai zane sa suke da wasu zabga zabgan bulalu a bayan sa, duk ta in da ya gudu sai yaji sun zabga masa wan nan bulala mai baki biyu dake hannun su a tsakiyar bayan sa, sai ihu yake amma ba mai iya ji.


Gaba ɗaya gidan sai rugugi yake kamar tashin sautin gangan sheɗanu amma ba mai iya jiyo rugugin sai Abba shi kaɗan dan Hajiya kam ta jima da sumewa


Tun Abba na iya gudun cetan ransa har ya kasa ya zube a kasa a bakin toilet ya sume a wajen, yana suma komai ya tsaya chak dodannin suka ɓace, amma kafin su ɓace sai da suka zanawa Hajiya wani karfe a bayan ta suka fasa mata baya, sai jini ke malala, san nan suka ɓace.


Tashin sense ba'a sa maka rana wai meke faruwa gidan Abba ne? Muje zuwa yanzu wasan zai fara.


Abba da Hajiya dai a wan nan daran a haka suka kwana, abun mamaki kuma ko da suka tashi da safe sun manta komai sun kasa tuna komai sai mamakin ciwukan da sukaji a jikin su suke, sai tambayar junan su suke wan nan ciwon fa, dukkan su ba mai bawa ɗan uwan sa amsa dan basu da amsan sun manta komai basu iya tuna komai.


Da kyar Abba ya iya miƙewa ya ɗauki wayar sa ya kira doctor sa dan yazo ya duba su.


Baa ɗauki lokacin sosai ba sai ga dr yazo, koda dr ya duba su sai yace shi bai ga komai ba, mamaki ne ya kara bayyana a face nasu Abba da kan sa ya sanya hannu dai dai sai tin in da dodannin nan suka zanawa Hajiya karfen nan yake ta jini, yasa hannu a wajen yana nunawa Dr, amma dr yace shi bai ga komai a wajen ba, clean yake kallon wajen, sun shiga ruɗani sosai daga su har dr, domin kuwa shi dai Abba shi da Hajiya ga ciwo na nan suna gani a jikin su amma a ce musu ba ciwo, ga jinin su nan sai zuba yake dr yace musu bai ga komai ba, shi Abba ma a face nashi ciwon yafi yawa duk dodannin nan sun zazzane masa face nashi da wan nan zabga zabgan bulalu nasu sai jini fuskar keyi amma shi dr baya ganin komai very smooth yake ganin face ɗin Abba, tashin hankali ba'a sa maka date


Abba da ya ga dr ya dage a kan shi bai ga komai ba sai ya fara tunanin to ko dai dr ya samu taɓin hankali ne, dan haka sai ya sallame sa, ya ɗauki waya ya kira driver sa a kan yazo ya kai su hospital, nan driver ke sanar masa ai yana Abuja a hotel ɗin da suka sauƙa tun jiya yake jiran sa bai gan shi ba ya kira layin sa bata shiga, zaro ido waje Abba yayi tare da dafe kan sa yana kokarin ko zai tuna wani abu da ya faru, yaushe ya dawo Kaduna meke faruwa da shi ne, sai jerawa kan sa tambayoyin da bashi da amsan su yake, hakan yasa ya gane ba dr ke da matsala ba shi ne ke da matsala


ita dai Hajiya ta kasa magana tana kwance shiru sai hawaye da take saboda azaban zafin da bayan ta ke mata in da dodannin nan suka yanke ta, gashi kuma dr yace bai ga komai ba alhalin ga ciwo nan karara kwance a bayan ta yana mata raɗaɗin azaba san nan ga jinin ta sai zuba yake amma dr yace bai gani ba kuma har ma da jinin dake zuba dukka bai gani ba wan nan wani irin masifa ne? Haka ita ma ta rinƙa jerowa kan ta tambayoyin da bata da amsar su, tana yi tana hawaye.


Wunin ranar dai haka suka wuni cikin tashin hankali da damuwa, Abba ya kira likitoci daban daban amma duk wanda yazo sai yace bai ga komai ba, tun abun na basu mamaki har suka dai na mamaki suka rungumi kaddara suka lallaɓa suka taimakawa junan su wajen yiwa kan su dressing na wajen, sunayi suna hawaye dukkan su.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*After some day's*


su Akila kowa ya koma gida sun gama yiwa daddyn jelly hutu, kafin su koma ba yadda su Imran basu yi da daddy ba a kan ya faɗa musu damuwar da amma yaki sai yace musu ba komai, da suka matsa masa da tambaya sai ya ɓata rai ya ɗaure fuska cikin umarni yace karsu sake tambayar sa, haka suka hakura ba dan su rinƙa so ba.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*KADUNA*


Irfan yasha ruwan mamaki ganin yadda aka gyara masu gidan su ga kuɗin da Abbi ya samu, san nan ga karatun master's degree nashi da zai je yayi a uk wow abun ya masa daɗi over har azumi godiya ga Allah sai da yayi, su Aafia kuma an samu babban waya ga babban makaranta nan rashin mutunci ya karu dozin dozin, ita kam Umaisha wayan ta biyu ga wan da Akil ya saya mata san nan ga wadda a ka kawo mata, murna awajen su ba'a magana


cikin kurna Aafia ta kira Kawar ta Rufaidat da suka gama secondary tare, ta sanar da ita abubuwan da suka samu na alkhari, sosai a fili Rufaidat ta nu mata farincikin ta san nan ta dora mata da cewa tana taya ta murnan samun babban makaranta, suma Allah yasa su samu mai dafa masu, da murna Aafia tace In Sha Allah zata faɗa wa Abbin ta zai taimaka musu, sai godiya Rufaidat ke yi sukayi sallama


dukkan kawayen ta da sukayi secondary sai da ta kira ta sanar musu da abun alkharin da ya same su, sosai suka rinƙa taya ta murna, ita kam Umaisha daman bata da kawaye. Wan nan kenan



*WASHINGTON DC*


zaune Michael yake a *Harvard community garden* ga lucky Copper Winston a gefen sa,

kan sa na kan wayar sa yana latsawa, su John suka iso wajen suka same sa, zama suka yi gefen sa Test na faɗin "I'm feeling hungry bro's" ya faɗa yana kallon Michael dake faman latsa waya, John ne yace "Okey kuje super restaurant mana kuyo oder sai a kawo muku nan" satar kallon Michael Dest yayi hakan yasa John ya gane me suke nufi, basu da kuɗi kenan, kallon Michael ɗin John yayi kafin yasa hannun a aljihun sa ya fito da kuɗi yana kokarin basu kenan wasu turawa su biyu suka iso wajen,


ganin yan matan yasa su John juyowa a sukwane suna kallon Michael da kwata kwata hankalin sa baya kan su, cikin sauri Dest yace da yan matan "Kuzo muje" yayi maganar a tsorace dan bai san hukuncin da Michael zai masa ba idan ya ga yan matan a wajen, tsawa ɗayar yarinyar ta daka masa tana faɗin "babu in da zanje har sai ka bani kuɗin zubar da cikin nan" tashin sense jin muryan mace yasa Michael ɗagowa da sauri yana kallon su, ihu Dest ya fasa yana ja da baya, ba Dest kawai ba har John sai da ya ja baya, nan take idon Michael ta canja launi zuwa ja cikin tsawa yace da yarinyar "leave this place before I open my eyes!!" Kallon sama da kasa tayi wa Michael kafin tace cikin faɗa "Kai ba da kai nake ba tukun nan kuma idan kaga na bar nan to na samu abun da nake so ne" girgiza kai kawai John yayi yana yiwa yarinyar addu'ar Allah ya ceceta, shi kuwa Michael a fusace yace da Copper "give her a good punishment" zaro ido waje Dest da Test suka yi, shi kuwa John godiya ma yayi ga Allah dan Michael bai bata horo sosai ba, yayi mamaki sosai, dan kamar yadda su Michael su ka tsani Mum ɗin su haka suka tsani duk wata mace a duniya shi yasa duk masu aikin gidan su sojoji ne kuma maza, mace bata zuwa ko in da inuwar su take dan suna ganin dukka mata irin ɗaya suke da mum ɗin su, hakan yasa duk wata macen da tayi gigin zuwa in da suke to kuwa ta shiga uku, sun tsani mata over kuma duk mum tasu ce silar komai.


Dirowa kasa Copper yayi tare da girgiza jikin sa, yana miƙa, durkusawa kasa Dest yayi ya riƙe kafafun Michael yana faɗin "Please Michael forgive my wife bata san kai wanene bane shiyasa kaga ba'a School nan take ba, bata san ka ba da bazata zo kusa da kai ba please she's pregnant kuma ina bala'i son cikin nata sosai" shiru Michael yayi kamar bai san da mutun a wajen ba, shi kuwa Copper tun da ya riga ya ansa umarni sai ya daka haushi mai razanar da kwakwalwa wadda yasa matan fasa ihu suka watsa a guje, kamar jira Copper yake yabi bayan su, yana gudu yana girgiza jikin sa, kuka sosai Dest ya fara ya ci-gaba da rokan Michael a kan ya dakatar da Copper kar cikin jikin matar sa ya zube, shi kuwa John da gudu yabi bayan su Copper duk da yasan ba zai iya dakatar da Copper ɗin ba, dan ba wanda ya isa ya dakatar da shi sai Michael ɗin da ya haɗa su da shi,


shima Test duƙawa yayi suka haɗu suna rokan Michael dake zaune yana latsa wayar sa hankalin sa kwance.



Share fisabilillah 👏


To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai


💞Star Lady💞


*💞 TRIPLET'S💞




***



*💞The beginning💞*



*Episode 14*




*KADUNA*


*Unguwar sarki*



Hajiya Umaiya na sume a tsaye, shi kuma Abba yana sume a kwance har sai da Lami ta dawo daga kasuwa, ta isko su a sume, ihu ta fasa tayi kan Hajiya tana kiran sunan ta, tana taɓa Hajiya, Hajiya ta zube kasa wanwar, kara tsorata Lami tayi ta nufi fridge ta ɗauko ruwa jikin ta sai kerma yake ta buɗe ruwan, tsabar kiɗimewa da tayi bata san lokacin da ta juyewa Hajiya ruwan gaba ɗaya a kan taba, Ihu Hajiya ta fasa mai razaba kwakwalwa tare da miƙewa zaune tana zazzare ido kamar an tare ɓera a tarko, waige waige ta fara yi kamar mai neman wani abun, can idon ta ya sauka kan Abba dake sume cikin tsoro tace "Ke Lami me yasami Alhaji? Yaushe ya dawo?" Kara zaro ido waje Lami tayi murya na rawa tace "Nima a nan na dawo na same ku kuna sume" kara waro ido waje Hajiya tayi, tayi shiru tana kokarin tunano me ya faru, amma ta kasa tuna komai, jiki ba kwari ta yunkura tana son miƙewa, sai ji tayi gaba ɗaya jikin ta ya mata nauyi sosai, dafe kan ta dake sara mata kamar zai fashe tayi da kyar ta iya miƙewa tana faɗin "Kawo min ruwa" da sauri Lami ta miƙe ta ɗauko wani ruwa a fridge ta dawo ta miƙewa Hajiya, ansan ruwan Hajiya tayi tare da duƙawa kusa da Abba ta tarfo ruwan a hannun ta ta shafa masa a face nashi, dogon numfashi yaja tare da saukewa a hankali, ya waro idon sa waje ya fara bin saman da kallo kafin ya sauko da idon sa kan face ɗin Hajiya, a hankali ya miƙe zaune yana kallon Hajiya "Alhaji yaushe ka dawo?" Hajiya ta tambaya tana zaro ido, shiru yayi yana bin ta da kallo, "Alhaji kayi magana mana"


da kyar ya iya motsa bakin sa yace "Hajiya yaushe na dawo? Ba ina Abuja ba?" tashin sense shiru Hajiya tayi tana kokarin tunano yaushe Alhaji ya dawo, amma ina ta kasa tuna komai, shima Alhaji shiru yayi yana kokarin tunano yaushe ya dawo bayan shi dai yasan yana Abuja wajen meeting to ya akayi ya dawo gida


Almost 30mins sunyi shiru suna tunani daga karshe suka hakura da kokarin tunano me ya faru da su, haka suka miƙe suka wuce sama ran su cike da tunani fal.


Hayewa saman gadon Abba Hajiya tayi ta kwanta ta dafe kan ta dake tsananin sara mata kamar zai fashe, shi kuma Abba yaja kafar sa a hankali da kyar da kyar ya shiga toilet dan yin wanka,


a ta kaice dai su Hajiya sun manta komai da ya faru sun manta da abun da ya faru da Hajiya Zainab.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*WASHINGTON DC*



*LOT 33*


*06:00am*


Sanye yake da short mai ɗan girma zuwa gwiwar sa sky blue kyakkyawar cinyoyin nan nasa a waje ga kyawawan gashi dark brown kwance a cinyar nasa daga sama har zuwa idon sahu na kafar sa, jikin sa na sanye da farar riga mara nauyi mai karamin hannu, kyau iya kyau Tiger na da shi kyakkyawan Bature ne sosai sai iskanci kala kala, ba kalan da bai iya ba rashin kutunci ne cike fal a kan sa,


A hankali yake takawa har ya haura sama gaba ɗaya, ya tura kofa ya shiga wani waje mai kama da ɗaki, sai dai gaba ɗaya wajen da glass a kayi shi, kasan wajen kuma kyakkyawar grass carpet ne a wajen launin kore, waje ne mai girman plot 1, an kawata wajen sosai ga luntsuma luntsumar kujerun hutawa san nan ga injunan motsa jiki kala kala a wajen, da gani kasan wajen training na su ne, ga in juna da mashuna kala kala masu kyau da tsadar gaske, wajen dai ba'a chewa komai sai dai masha Allah.


A hankali Michael ya kariso cikin wajen, kusa da wani mashin na motsa hannun ya tsaya, yayin da wani matashi ke kwance a wajen yana ɗaga wasu kana kana nan karafuna.


Kallon tsab Michael yayi wa matashin kafin yace "Good morning photo copy" Ajiye karafunan hannun sa guy ɗin yayi tare da miƙe wa zaune, subhanallah tsarki ya tabbata ga Ubangiji dayayi wayan nan halittu, guy nan kamannin sa ɗaya sak da Michael ba abun da ya raba su sai kwayar ido da gashin kai, Michael gashin kan sa dark brown ne, shi kuma guy nan gashin kan sa ya rina ta ya sanya mata color ta dawo light brown mai kama da golden, sai kuma kwayar ido Michael kwayar idon sa light brown ne shi kuma guy ɗin nan nashi idon light ash ne masu kyau, ban da ido da gashi komai nasu ɗaya ne.


Kallon tsab guy ɗin yayi wa Michael kafin yace "how are you doing this morning?" "I'm going well" ya faɗa tare da wucewa ya nufi wajen motsa kafa, har ya kai wajen sai kuma ya juyo yana faɗin "James yaushe Romeo zai dawo?" Komawa James yayi ya kwanta ya ci-gaba da ɗaga karfen da yake yana faɗin "I don't know maybe this week" shiru Michael yayi ba tare da ya sake magana ba, shima James shiru yayi ba tare da ya sake magana ba suka ci gaba da motsa jikin da suke.



07:00am dankareriyar gold watch dake ɗaure a hannun su tayi kara lokacin guda alamar awa ɗaya ta karu a kan lokaci, kallon juna suka yi, kusan a tare suka ajiye karafunan hannun su, kowa ya sanya hannu yana kokarin kashe karar watch ɗin, dankareriyar gold watch ne mai bala'i kyau da tsada iri ɗaya ba abun da ya raba watch ɗin, ko ina zasu je watch ɗin na hannun su basa rabuwa da shi sai dai in zasu yi barci ko zasu yi wanka shi ne suke cirewa,


Tsai da karar watch ɗin sukayi a tare, dai dai lokacin jibga jibgan Bodyguard na su guda huɗu suka shigo wajen hannun su ɗauke da plate masu ɗauke da cup na ruwan lemon wadda masu motsa jiki ya kamata su sha idan sun kammala motsa jikin nasu,


Rabuwa bodyguard ɗin suka yi, biyu suka nufi wajen Michael biyu kuma suka nufi James, cikin girmamawa suka miƙa musu plate ɗin, ba musu kowan nen su yasa hannu ya ɗauki cup ɗin suka kafa a ɗan karamin bakin su.


Cikin ƙan ƙanin lokaci suka shanye lemon ɗin tas, tare da mai da cups ɗin saman plate dake hannun bodyguard ɗin, daman ka idar motsa jikin kenan shan 1 cup na lemon idan an kammala.


Bayan bodyguard ɗin sun fice ne Michel ya kalli James yace "Photo copy zan je na shirya na wuce school yanzu" ba tare da James ya kalle sa ba yace "Ba za dai ka dai na ce min photo copy ba ko?" Miƙewa Michael yayi yana faɗin "To ai kai photo copy ne da gaske dama aikin sojan kawai kai ma ka shiga da ya fima yawon ban zan da kake ɗin nan kullun gaka wajen partyn abokai, ka gama school kana zaune" shiru James yayi ba tare da ya sake magana ba, sai mamaki yake wai Michael ne yake ce masa mai yawon banza to ba gwara shi ba ya samu ya kammala school ɗin, aiki ne dai kawai bai fara ba kuma baya ra'ayi yin koma ne hutu kawai yake sonyi a gida shi kuma fa, wuce wa Michael yayi ya fice daga wajen ya nufi bedroom na shi.


A hankali shi ma James ɗin ya miƙe ya wuce nashi bedroom ɗin dan yaje yayi wanka.


After some hours.


James ya fito sanye da wandon jeans baki da t-shirt navy blue masu bala'i kyau da tsada sai kamshi yake zubawa, kai tsaye parking space ya nufa, yaje ya shiga motar sa kirar *Bugatti centodieci* ya tayar


ko da yazo fita parking space ɗin sai da wan nan na'uran ta faɗi sunan motar da number ta da kuma sunan wanda ya ke cikin motar, san nan gate ɗin parking space ɗin ta buɗe, James ya danna hanchin motar waje.


Yana fita ya saki kiɗa mai tashin kai yana kaɗa kan sa yana tuƙi cikin kwanciyar hankali.


Kai tsaye *medina Hotel* ya wuce, horn ɗaya yayi a bakin gate ɗin masu gadi wajen suka buɗe masa, ya kutsa hancin motar sa a ciki ya nufi parking space, yana kashe motar ba tare da ɓata lokaci ba ya fito tare da sanya fake face a face na shi dan kar kowa ya gane sa san nan ya shige cikin katafaren hotel ɗin.


Manya manyan Alhazawan kasar ne a wajen sunyi cincirindo shi kaɗai a ke jira daya iso gaba ɗaya sun zauna saman luntsuma luntsumar sofan dake cikin ɗakin hotel ɗin, cikin taku irin na jaruman maza ya kariso wajen, ya kara ɗaure fuakar nan tasa tamau, zama yayi gefen wani jibgegen Bature wadda da ka gansa kaga wadda Naira ta zauna ma sosai, ba tare da ɓata lokaci ba suka fara tattaunawa.


Almost 40 mins suna tattaunawa nawa kafin daga bisani wan nan jibgegen Baturen ya jawo trolley dake gefen sa ya buɗe zip ɗin ya fito da wasu pistol gun ya fara rabawa mutanen dake wajen, ko wan nan su yana amsa yayi godiya amma da a kazo kan James sai yaki ansa, kallon sa Baturen yayi tun kafin yayi magana James yayi saurin cewa "Ba zai yiwu na shiga gidan mu da gun nan ba, idan nace zan shiga da ita tofa sai an kama ni dan gidan mu na da tsaro sosai" jinjina kai Baturen yayi kafin ya mai da gun ɗin cikin a kwanakin ya ajiye yana tunanin wai ma James ɗan waye ne dan bai san asalin wanene James ba kawai harkalla ta haɗa su,


Cike da tunani fal ransa ya fito musu da wani abu kamar daskararren jini ne a ka yayyan ka, ko wan nan su ya amsa da fara'a amma ban da James shi fuska a ɗaure ya amsa, kallon su Baturen yayi san nan ya basu umarnin a kan su cinye abun, ba musu suka sanya a bakin su suka cinye, shiru ogan nasu yayi na yan mintoci kafin yace zasu iya tafiya sai a zama na gaba kuma, da sauri James ya miƙe kamar mara gaskiya ya bar wajen ya nufi motar sa ya shiga ya bar hotel ɗin da gudun gaske.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*ABUJA*


Zaune Rimsha take saman sofa mai zaman mutun 2 a palon kasa tayi shiru ta kura idon ta a kan makekiyar Tv dake kunne ana labarai a kan wan nan Baturen,

da sallama daddy da mum suka shigo Palon sai murmushi suke kai da ganin su kasan suna cikin farin ciki da annashuwa.


My siha a na kallon labarai a kan TGA ne?" Cewar daddy yayi maganar tare da zama kusa da ita, a hankali ta kwanto jikin sa tare da ɗago dara daran sleeping eyes nata cikin shagwaɓa tace "Daddy yau ba TGA nake kallo ba na asalin nake kallo GAR shi ne asalin General of the army R ɗin kuma ban san ma'anar ta ba" shafa kan ta yayi yana murmushi, zama mum tayi gefen ta tana faɗin "Ni Rimsha wlh bana gane wa mutanen nan naki yau kiga wan nan gobe wan nan to shi kuma GAR ɗin waye shi?" Miƙewa tayi zaune daga jikin daddy cikin sauri tace "Mum GAR shine asalin jarumi na ai shima TGA ɗin yana burgeni amma ba kamar GAR ba" jinjina kai mum tayi tace "Ni kam Rimsha ba abun da na gane game da wan nan bayanin naki kyale ni kawai muje a kina san kallon TGA" komawa Rimsha tayi ta kwanta jikin daddy tana faɗin "Nima mum ba wani gane wa nake ba suna rikita min kwakwalwa sai yau na lura da mai light blue eyes ɗin nan da mai light ash eyes ɗin ashe ba mutun ɗaya bane na gano gakan ne ta sunan su, mu kullun bamu duba suna kawai idan mun ga hoton shi kenan ban taɓa tunanin GAR su biyu bane sai yau sun caza min kai, mai light ash ɗin idon nan shi ne TGA mai light blue idon kuma shi ne GAR wato General of the army kenan kuma shi ne jarumi na, ban taɓa luraba sai yau, suna kama over idon su ne kawai ya ban ban ta su" shi dai daddy shiru yayi yana jin ta amma ba wai dan ya fahimci kan zancen nata ba, dan shi ba wani zama yake yana kallon labaran Usa Army's ɗin nan ba, ita dai mum amsa mata kawai tayi amma ba wai dan ta gane kan zancen nata ba, shiru gaba ɗayan su suka yi suka zubawa Tv ido suna taya Rimsha kallo, while ita kuma Jehan tana ɗaki tana zubawa Gwaggo shagwaɓa da iya shege.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*KADUNA*


Abba da Hajiya Umaiya sun manta komai da ya faru da su da rana a cikin gidan, sosai abokan Abba ke kiran sa a waya suna tambayar sa Alhaji Mustapha sai dai yace musu tun da ya dawo basu haɗu ba domin kuwa tabbas babu abun da Abba da Hajiya suka iya tunawa, shi Abba ma ya kasa tuna lokacin ma daya kamo hanyar Kaduna shi iya sanin sa yana Abuja bai san ya akayi ya dawo ba.


Kamar kullun bayan sun gama cin abincin dare suka wuce bedroom na Abba dan su kwata, da kyar Hajiya ta iya samu tayi wanka saboda kasala da take ji jikin ta duk zafi yake mata kamar wadda a kawa mugun duka, a ɓangaren Abba shima hakan ne gaba ɗaya jikin sa ciwo yake masa, haka dai suka lallaɓa suka yi wanka tare da shirin barci suka kwanta.


Cikin dare sai juyi suke dukkan su sun kasa barci, dafe ciki Hajiya tayi kamar zata yi kuka tace "Abban Imran yinwa nake ji sosai kamar zan mutu" da mamaki ya miƙe ya kunna lamp na gefe da gefen gadon, abun ya ɗaure masa kai cikin kasalalliyar murya yace "Hajiya yinwa kuma?" Gyaɗa masa kai tayi alamar eh, yasha ruwan mamaki sosai dan basu taɓa jin yinwan dare haka ba


A hankali ya koma ya kwanta yana faɗin "Muna da sauran takeaway a palo ai kije kici ni zan sha Yoghurt dan nima yinwa nake ji kuma banson cin abinci da tsohon daren nan, idan kin gama cin abincin naki ki tahomin da L&Z Yoghurt mai sanyi guda ɗaya" to kawai Hajiya tace tare da sauƙo wa daga gadon ta nufi Palo.


Ko da ta shigo palo wutar palon a kashe, kai tsaye ta wuce wajen switch ta kunna wutar palon nan take haske ya gauraye ko ina a cikin Palon,


Waro ido waje tayi kamar idon ta zai fito waje ya faɗi kasa, nan idon ta ya mata arba da tashin hankali da kwakwalwa ba zai ɗauka ba, jibga jibgan mutane su uku ne zaune saman sofa jikin su duk jini idon nan nasu launin jini ga fuskokin su bakake kirin abun tsoro, wata yar kyakyawan matashiyar yarinya ce zaune a tsakiyar palon ta na fukantar kofar palon ta bawa Hajiya baya, ta dukar da kai kasa kamar tana cin wani abun,


cike da ruɗu da tashin hankali murya na rawa Hajiya tace "A..Ab..Abla" cikin sauri yarinyar ta ɗago tare da wayan nan dodan nin dake zaune saman sofa, tabbas Abla ce ke zaune tana cin namar mutane ɗanye idon Hajiya ya gane mata, kai kallon ta hajiya tayi kan abun da Abla ke ci,


razanannen ihu Hajiya ta fasa ganin namar jikin mutun Abla ke ci, sai lokacin Hajiya ta iya tuna abun da ya faru ɗazun, dan kuwa naman Jikin Zainab Abla ke ci, Hajiya na kokarin guduwa ta koma sama idon ta ya sauka kan wasu dodan nin dake zaune saman kujerun table suna cin ɗanyen nama ga face nasu abun tsoro idon nan nasu kamar zai fito waje, ga launin idon jawur kamar jini suna da katon hanci Kamar kofa ga girman baki kamar masai ga idon na su ma manya manya masu firgitar da ɗan adam, ihu Hajiya ta kuma fasawa kamar makoshin ta zai fashe amma ina gaba ɗaya gidan ba wan da ya kawo mata ɗauki, a guje ta juya kamar zata mutu ta koma bedroom nasu.


Tana shiga tayi arba da wani tashin hankali, dan kuwa wayan nan dodan nin ta gani suna tsere da Abba sun hana shi fita, shima sai ihu yake amma ba'a iya jiyo sautin ihun nashi, ga dai bakin sa na ihu amma ba wanda ke jin komai, tsabar tsorata Hajiya yanke jiki tayi a wajen ta sume.


Shi kuma Alhaji ya daɗe yana tsere da wayan nan sheɗanun dodan nin gashi sai zane sa suke da wasu zabga zabgan bulalu a bayan sa, duk ta in da ya gudu sai yaji sun zabga masa wan nan bulala mai baki biyu dake hannun su a tsakiyar bayan sa, sai ihu yake amma ba mai iya ji.


Gaba ɗaya gidan sai rugugi yake kamar tashin sautin gangan sheɗanu amma ba mai iya jiyo rugugin sai Abba shi kaɗan dan Hajiya kam ta jima da sumewa


Tun Abba na iya gudun cetan ransa har ya kasa ya zube a kasa a bakin toilet ya sume a wajen, yana suma komai ya tsaya chak dodannin suka ɓace, amma kafin su ɓace sai da suka zanawa Hajiya wani karfe a bayan ta suka fasa mata baya, sai jini ke malala, san nan suka ɓace.


Tashin sense ba'a sa maka rana wai meke faruwa gidan Abba ne? Muje zuwa yanzu wasan zai fara.


Abba da Hajiya dai a wan nan daran a haka suka kwana, abun mamaki kuma ko da suka tashi da safe sun manta komai sun kasa tuna komai sai mamakin ciwukan da sukaji a jikin su suke, sai tambayar junan su suke wan nan ciwon fa, dukkan su ba mai bawa ɗan uwan sa amsa dan basu da amsan sun manta komai basu iya tuna komai.


Da kyar Abba ya iya miƙewa ya ɗauki wayar sa ya kira doctor sa dan yazo ya duba su.


Baa ɗauki lokacin sosai ba sai ga dr yazo, koda dr ya duba su sai yace shi bai ga komai ba, mamaki ne ya kara bayyana a face nasu Abba da kan sa ya sanya hannu dai dai sai tin in da dodannin nan suka zanawa Hajiya karfen nan yake ta jini, yasa hannu a wajen yana nunawa Dr, amma dr yace shi bai ga komai a wajen ba, clean yake kallon wajen, sun shiga ruɗani sosai daga su har dr, domin kuwa shi dai Abba shi da Hajiya ga ciwo na nan suna gani a jikin su amma a ce musu ba ciwo, ga jinin su nan sai zuba yake dr yace musu bai ga komai ba, shi Abba ma a face nashi ciwon yafi yawa duk dodannin nan sun zazzane masa face nashi da wan nan zabga zabgan bulalu nasu sai jini fuskar keyi amma shi dr baya ganin komai very smooth yake ganin face ɗin Abba, tashin hankali ba'a sa maka date


Abba da ya ga dr ya dage a kan shi bai ga komai ba sai ya fara tunanin to ko dai dr ya samu taɓin hankali ne, dan haka sai ya sallame sa, ya ɗauki waya ya kira driver sa a kan yazo ya kai su hospital, nan driver ke sanar masa ai yana Abuja a hotel ɗin da suka sauƙa tun jiya yake jiran sa bai gan shi ba ya kira layin sa bata shiga, zaro ido waje Abba yayi tare da dafe kan sa yana kokarin ko zai tuna wani abu da ya faru, yaushe ya dawo Kaduna meke faruwa da shi ne, sai jerawa kan sa tambayoyin da bashi da amsan su yake, hakan yasa ya gane ba dr ke da matsala ba shi ne ke da matsala


ita dai Hajiya ta kasa magana tana kwance shiru sai hawaye da take saboda azaban zafin da bayan ta ke mata in da dodannin nan suka yanke ta, gashi kuma dr yace bai ga komai ba alhalin ga ciwo nan karara kwance a bayan ta yana mata raɗaɗin azaba san nan ga jinin ta sai zuba yake amma dr yace bai gani ba kuma har ma da jinin dake zuba dukka bai gani ba wan nan wani irin masifa ne? Haka ita ma ta rinƙa jerowa kan ta tambayoyin da bata da amsar su, tana yi tana hawaye.


Wunin ranar dai haka suka wuni cikin tashin hankali da damuwa, Abba ya kira likitoci daban daban amma duk wanda yazo sai yace bai ga komai ba, tun abun na basu mamaki har suka dai na mamaki suka rungumi kaddara suka lallaɓa suka taimakawa junan su wajen yiwa kan su dressing na wajen, sunayi suna hawaye dukkan su.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*After some day's*


su Akila kowa ya koma gida sun gama yiwa daddyn jelly hutu, kafin su koma ba yadda su Imran basu yi da daddy ba a kan ya faɗa musu damuwar da amma yaki sai yace musu ba komai, da suka matsa masa da tambaya sai ya ɓata rai ya ɗaure fuska cikin umarni yace karsu sake tambayar sa, haka suka hakura ba dan su rinƙa so ba.


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞


*KADUNA*


Irfan yasha ruwan mamaki ganin yadda aka gyara masu gidan su ga kuɗin da Abbi ya samu, san nan ga karatun master's degree nashi da zai je yayi a uk wow abun ya masa daɗi over har azumi godiya ga Allah sai da yayi, su Aafia kuma an samu babban waya ga babban makaranta nan rashin mutunci ya karu dozin dozin, ita kam Umaisha wayan ta biyu ga wan da Akil ya saya mata san nan ga wadda a ka kawo mata, murna awajen su ba'a magana


cikin kurna Aafia ta kira Kawar ta Rufaidat da suka gama secondary tare, ta sanar da ita abubuwan da suka samu na alkhari, sosai a fili Rufaidat ta nu mata farincikin ta san nan ta dora mata da cewa tana taya ta murnan samun babban makaranta, suma Allah yasa su samu mai dafa masu, da murna Aafia tace In Sha Allah zata faɗa wa Abbin ta zai taimaka musu, sai godiya Rufaidat ke yi sukayi sallama


dukkan kawayen ta da sukayi secondary sai da ta kira ta sanar musu da abun alkharin da ya same su, sosai suka rinƙa taya ta murna, ita kam Umaisha daman bata da kawaye. Wan nan kenan



*WASHINGTON DC*


zaune Michael yake a *Harvard community garden* ga lucky Copper Winston a gefen sa,

kan sa na kan wayar sa yana latsawa, su John suka iso wajen suka same sa, zama suka yi gefen sa Test na faɗin "I'm feeling hungry bro's" ya faɗa yana kallon Michael dake faman latsa waya, John ne yace "Okey kuje super restaurant mana kuyo oder sai a kawo muku nan" satar kallon Michael Dest yayi hakan yasa John ya gane me suke nufi, basu da kuɗi kenan, kallon Michael ɗin John yayi kafin yasa hannun a aljihun sa ya fito da kuɗi yana kokarin basu kenan wasu turawa su biyu suka iso wajen,


ganin yan matan yasa su John juyowa a sukwane suna kallon Michael da kwata kwata hankalin sa baya kan su, cikin sauri Dest yace da yan matan "Kuzo muje" yayi maganar a tsorace dan bai san hukuncin da Michael zai masa ba idan ya ga yan matan a wajen, tsawa ɗayar yarinyar ta daka masa tana faɗin "babu in da zanje har sai ka bani kuɗin zubar da cikin nan" tashin sense jin muryan mace yasa Michael ɗagowa da sauri yana kallon su, ihu Dest ya fasa yana ja da baya, ba Dest kawai ba har John sai da ya ja baya, nan take idon Michael ta canja launi zuwa ja cikin tsawa yace da yarinyar "leave this place before I open my eyes!!" Kallon sama da kasa tayi wa Michael kafin tace cikin faɗa "Kai ba da kai nake ba tukun nan kuma idan kaga na bar nan to na samu abun da nake so ne" girgiza kai kawai John yayi yana yiwa yarinyar addu'ar Allah ya ceceta, shi kuwa Michael a fusace yace da Copper "give her a good punishment" zaro ido waje Dest da Test suka yi, shi kuwa John godiya ma yayi ga Allah dan Michael bai bata horo sosai ba, yayi mamaki sosai, dan kamar yadda su Michael su ka tsani Mum ɗin su haka suka tsani duk wata mace a duniya shi yasa duk masu aikin gidan su sojoji ne kuma maza, mace bata zuwa ko in da inuwar su take dan suna ganin dukka mata irin ɗaya suke da mum ɗin su, hakan yasa duk wata macen da tayi gigin zuwa in da suke to kuwa ta shiga uku, sun tsani mata over kuma duk mum tasu ce silar komai.


Dirowa kasa Copper yayi tare da girgiza jikin sa, yana miƙa, durkusawa kasa Dest yayi ya riƙe kafafun Michael yana faɗin "Please Michael forgive my wife bata san kai wanene bane shiyasa kaga ba'a School nan take ba, bata san ka ba da bazata zo kusa da kai ba please she's pregnant kuma ina bala'i son cikin nata sosai" shiru Michael yayi kamar bai san da mutun a wajen ba, shi kuwa Copper tun da ya riga ya ansa umarni sai ya daka haushi mai razanar da kwakwalwa wadda yasa matan fasa ihu suka watsa a guje, kamar jira Copper yake yabi bayan su, yana gudu yana girgiza jikin sa, kuka sosai Dest ya fara ya ci-gaba da rokan Michael a kan ya dakatar da Copper kar cikin jikin matar sa ya zube, shi kuwa John da gudu yabi bayan su Copper duk da yasan ba zai iya dakatar da Copper ɗin ba, dan ba wanda ya isa ya dakatar da shi sai Michael ɗin da ya haɗa su da shi,


shima Test duƙawa yayi suka haɗu suna rokan Michael dake zaune yana latsa wayar sa hankalin sa kwance.



Share fisabilillah 👏


To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai


💞Star Lady💞