Page 8
by @maidambu41
*NAAZNEEN❤🔥 <Eight>*
EXQUISITELY BEAUTIFUL
#Mai_Dambu
'Top-Notch
Season 3
بسم الله الرحمن الرحيم
Bikin a unguwar Maitama ake yi, kusan ma za a ce, makotansu Saifullahi-Khalid ne, wanda yake kwance har lokacin bai koma aiki ba. A hankali Auta ya turo kofar dakin Saifullahi-Khalid din da ya zurawa tv idanu.
"Ya Saif!"
Juyawa yayi ya kalle shi, sannan ya mai da kan Tv gabanshi. "Dama Ummi ce tace na gaya maka, ko zaka zo ka amso mata sako ne?"
Ware idanu yayi, kamar zasu fado kasa, dama gashi manya manya, wanda suka kawata zankad'ed'iyar fuskarshi. "Sakon me?"
"Nima haka ta ce min!"
"Ok!" Ya ce tare da miƙewa ya nufi dakinshi, daura jallabiya yayi a saman kayan jikinshi. Wayarshi ce tayi haske, dauka yayi ya ga Masallacin da yake musu karatun sati-sati ne suke kiran shi. A hankali ya kashe kiran ya kira su, "Assalamu alaikam, Barka dai Imam!" Aka faɗa a can,"Amin wa'alaikamun Salam,Yawwa barka dai!" Ya bada amsa.
"Mun jika shiru ne, shi ne muka ce bari mu kira ka."
"Allah sarki, babu komai in sha Allah ina nan zuwa."
"Ubangiji ya kawo lafiya, ya kuma baka lafiya."
"Amin Ya Allah."
Daga haka ya kashe wayar, duk wani abin da ya shafi Ibadarshi, an raunana su. Allah ya taimaka ne ma yake kokarin yin wani abu, dan ba karamin abu aka mishi ba. Yana gamawa ya fita, tare da nufar part din Ummi. Bayan ya shiga ya same ta zaune tana rarrashin Auta, Basmah tana jinsu.
"Ummi da kin bar ni na kwad'a mishi marin ne ma!"
"Babana don Allah ka kai shi, ya amso cake ɗinshi." Kallon Auta yayi sannan ya mika hannunsa yana riko na auta, ranshi baya son ya fita, amma kuma baya jin zai ce a'a a fitar.
A hankali suka bar gidan, zuwa waje yana jan motar yana kallon hanyar. "A ina...?" Bai karasa tambayar ba idanunshi ya sauka a kan Gimbi da take tsaye da wasu yan mata, tana dariya. Sanye Da Kayan biki. Kanshi ne ya dauki wani irin bala'in kara, dakyar ya cire idanunshi akan ta, ya cigaba da tafiyar. Wani irin azazzalar da zuciyarshi take masa yasa shi dole ya koma gefen titin unguwar yayi parking. Zufa ke karyo mishi kamar an tsoma shi cikin mangyada aka ciro shi.
Kifa kanshi yayi da sitiyerin motar, "Ya Saif!" D'ago kai yayi ya kalli Hashim. "Baka da lafiya ko?" Girgiza kai yayi, sannan ya ce masa. "Ina zuwa!" Ba musu ya cire sit belt din, ya fita daga cikin motar ya nufi inda ya ga yan matan nan, suna tsaye. Koda ya je wurin babu Gimbi babu alamarta.
Haka ya gama nimanta bai ganta ba, sannan ya juya wurin motarsu, suka bar wurin. Dakyar ya kai auta ya amso cake din, suna dawowa ya hangota tana sauka daga mota, da sauri yayi parking. Ya fito tsabar sauri ma, wata mota kamar zata kwashe shi. Haka ya tsallaka yana me shan gabanta yana haki.
"Baiwar Allah!" A dan razane tayi baya, tana nuna shi, sannan ta nuna kanta. "Ni?"
"Ke! Please muje ga mota ta can!" Juyawa tayi ya ga motar, kafin ta girgiza kai tana kokarin barin wurin. "Please ina son magana dake, idan babu hali bani number wayarki."
Wani banzan kallo ta mishi sama da kasa, sannan ta ce mishi. "Ni matar aure ce!"
Wani bala'in dauke wuta yayi, "please ki saka mijinki ya sake ki, wallahi ina kaunarki."
"Malam bani hanya!"
"Please ki saurare ni!"
"Ok bani number ka, idan na samu lokaci zan kira ka." Hadiye yawu yayi ya karanto mata numbershi, rab'a gefenshi tayi bata ce mishi cikanka ba. Kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha, farinciki da walwalar shi lokaci guda suka dawo, ya koma cikin motar ya zauna, yana sauke ajiyar zuciya. Sannan suka bar kofar gidan, yadda bai yiwa auta magana ba, shima Hashim bai bi ta kanshi ba, koda suka isa gida kowa ya wuce nashi hanyar ne, tunda ya iso gida ya saka wayar ya gaba yana gani, kafin ya rasa me ke yake mishi dad'i. Sai da ta kai yaƙi daukar kiran kowa gani yake zata kira shi.
Gimbi.
Tsabar farinciki, kamar tayi ta ihu ita ɗaya sai murna take, take ta kira Siyamah da Linah ta fesa musu, ai dama sun gaya mata, ita ce dai bata yarda ba. Amma sun san aikin ba Allah, karya kace bai maka ba. Don haka suka bata shawara ta wana shi kafin ta yarda su sake haduwa. Haka kuwa akayi, duk da bata so ba. Haka taki kiranshi.
Tashin hankalin da Saifullahi-Khalid ya shiga kamar ya zauce, domin yadda yaga rana haka yake ganin dare, gashi duk tambayar da za a mishi bai tab'a cewa ga abin da yake damun shi, a bangaren Gimbi itama tana jin babu dad'i, sannan tana yawan nazarin matuƙar ta bar abuja basu hadu ba, tayi sake reshe kama ganye kenan fa, da ita da asara duk ɗaya ne.
Ajiyar zuciya ta sauke tana jin ba zata iya barin garin abuja basu hadu ba don haka ta gyara kwanciyarta. Tare da lumshe idanunta, gobe za a gama bikin daga nan kowa zai kama gabanshi, "Baki yi barci ba ne?" Inji Amina Nuhu Giyad'e.
Sai da ta tabe baki,wanda haka ya zame mata jiki, ta ce mata. "Eh wallahi." "Gobe za a gama bikin, gaskiya ba zan iya komawa Bauchi a gobe ba, sai jibi zan dan zaga cikin gari nayi wani kamu." Kallon Amina Nuhu Giyad'e tayi tana imagine yadda take wani iyayi zaka rantse da Allah irin kyawawan ne, amma take wani salo. "Tow ko na bi yarima a sha kid'a ne?"
"Me zai hana?" Suka kwashe da dariya, har wurin asuba, basu tashi sallah ba sai da gari ya waye suka tashi, dake Gimbi bata damu da sallah ba, cewa tayi tana off. Cigaba da barci tayi sai da Amina ta tashe ta, tayi wanka suka fita.
Suna fita daga gidan bikin ta hango Saifullahi-Khalid tsaye, domin tun safe ya bar gidansu yazo ya tsaya a kofar gidan. Tana ganin shi ta tsallako titin. Juyawa tayi tana kallon Amina Nuhu Giyad'e, da ta shiga rud'ani.
"Nayi ta jiranki tun jiya."
"Oh sorry, na mance da kai ne!" Kallonta yayi kafin ya sauke numfashi ya ce mata. "ina ta jiran ko zaki kira, amma kice kin manta da ni."
Cikin tsiwa ta ce mishi.
"Hala ka ajiye ni, gadinka ne ko? Kaga don na tuna ka ne yasa nazo wurinka sai an jima."
"Please ki tsaya, ko suna na, zaki tambaya ai?" Yayi maganar cikin sigar rarrashi.
"Ok meye sunanka?"
"Saifullahi-Khalid, ko kai kowannensu zaki iya kira zan amsa, ya sunan Gimbiyartawa."
Wani fari tayi da idanu, sannan ta ce mishi.
"Ai ka canki sunan, da kanka."
"Hmm! Gimbiya?" Ya kuma tambayata,
Gyada kai tayi tana lumshe idanunta.
"Gimbi kizo muje, kafin ya tafi ya bar mu." Inji Amina Nuhu Giyad'e.
Gabatar da ita Gimbi tayi, tana gaya mishi.
"Gimbi?" Ya tambaye ta, gyada kai tayi tana faɗin. "Gimbiya Baby Yusuf Bogoro!"
"Oh! Dukkan mun yan Bauchi kenan!"
Gyada kai Amina Nuhu Giyad'e tai, tana girmama a ina Gimbi ta samo Balarabe haka. "Kawarmu gashi bamu gama magana ba zaki dauke min ita, Ya kenan?"
"Tow ai sai na tafi na barku tare."
Gyada kai yayi yana faɗin. "Kin kyauta!"
Tafiya tayi ta barsu a wurin, a ranta tana jin wani irin mamaki. Shima daukar Gimbi yayi suka fita, idan da ace can baya ne, Gimbi bata isa tsayawa a gefenshi ba, amma dake al'amarin ba daya ba ne, yanzu kan sai yadda tayi da shi, haka suka fita tun safe, sai la'asar suka dawo,dake unguwar kowa harkan gabanshi yake..
Sosai suka samu kusanci da juna, wanda ta kai kamar ba zasu rabu ba, bayan an gama budar kai, aka sallame su. Sai lokacin hankalinta ya dawo jikinta, dakyar suka samu inda zasu kwana, amma a daren Saifullahi-Khalid sai da ya fito ya same ta, suka tafi yawo.
Saifullahi-Khalid mutumin kirki ne, bai san wannan irin rayuwar ba, ba don kome ba sai don gidansu da familynshi.
Tun lokacin da Gimbi ta samu Saif a hannaunta, ta kara haukata shi, a kasa da sati Uku aka shiga nima mishi aurenta, a lokacin Yayunshi mata da yan uwan Babanshi maza da mata sunki auren, amma ina ya kafe, wacce ta kawo karshen rikicin Hajja Marih ita ta tsaya aka yi auren babu yadda suka iya, amma daga yanayin Familyn Maman Gimbi suka tabbatar babu mutanen kwarai, kuma basu da kome da zasu iya bikinsu na mutanen katagum.
A bangaren Babanta kuwa, cewa yayi ya mata miji, abin da ya haifar musu tashin hankali da Maman Gimbi da Babanta akayi ta kai ruwa. Wanda daga karshe honorable da kanshi ya zo yace ya fasa auren Gimbi, don dole haka ta saka Saifullahi-Khalid a gaba da jifa, wanda yaƙe jin kamar ana zuke jinin jikinshi. Yadda ya d'aga hankalin lallai a nima mishi aurenta. Hajja Marih ta fara shan jinin jikinta. Bata cika shiga sha'aninsu ba, amma a wannan tak'in da kanta ta tafi har Abuja, kallonshi kawai tayi na wani lokaci kafin ta ce mishi.
"Malam Alhaji, yaushe kika zama haka? Akan me zaka zama haka? Anya kana addu'a kuwa? Baka addu'a nasan da kana addu'a da ba zaka rikice akan mace haka ba, don haka kuwa daga gobe juma'a zamu fara da ikon Allah, duk me nimanka da sharri zai koma kanshi. Munyi imani da Allah da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, albarkacin alqur'ani sai mun ga bayan masu niman ganin bayanka."
Shi dai bai ce mata kome, dattijuwar nan bata yi kasa a gwiwa ba, ana maganar aurenshi a gefe guda. Ana saukar Alqur'ani.
A cikin sati daya, al'amarin auren gimbi ya fara tangal - tangal. Domin har an saka rana an gama kome maganar aure kamar an shuka dusa, babu shiri ta wuce kaltungo. Kura mata idanu ba Allah yayi, ganin yadda take kuka wiwi.
"Maganar auren ya fara lalacewa, a taimaka min ayi wani abu."
Kallon madubin kogon yayi, ya nuna da isgar hannunshi ya ce.
"Wannan shi ne ko?"
"Eh!"
Tashi yayi ya dauko wasu tantabaru bakaken wuluk ya ce mata. "Wadannan sune bakakkrn tantabarun soyayya, idan har suka mutu soyayyarki zai mutu, a zuciyarshi. Idan suka rayu har da yayyafa, babu me raba ki da Saif sai mutuwa."
Haka yayi ta tsafe su har sai da ya jika su da tsafi, sannan ya bata tare da cewa. "Ki tabbatar da kin saka a cikin gidanku, kina zuwa gida ki kira shi, ki watsa musu wannan ruwan bayan kin kira shi. Aure kuwa na gaya miki, ranar juma'a za a daura aurenki da shi."
Haka ta ajiye mishi abin da ta kawo mishi, sannan ta bar ramin, tana tabbatar da babu Allah.
Da wannan ta baro garin, tana shigowa gidan tayi abinda ya ce mata, ai kuwa a daren sai ga kiran Saif. Babu kakkautawa itama tayi biris shi, kada kuce baya kula da addu'a ne a'a jarabawar shi ce Gimbi.
Washi gari kuwa kamar mahaukaci haka ya zama a cikin gidan, don dole suka tawo Bauchi nima mishi auren ranar Laraba, suka kwana Alhamis.
Ranar juma'a aka shaida aurensu, duk da a ɓangaren iyayenshi basu so aurenta, amma babu yadda suka iya, tunda shi yaji ya gani yana sonta. Sai da aka yi auren hankalinsa ya dawo jikinshi. A hankali kome ya juye tare da kazamta, domin dai Ummin ta hana shi tafiya da ita, don haka suka saka idanu akanta, sannan yan uwanshi kiri-kiri suka tsaneta. Musamman da suka lura da cewa dan uwansu sai yadda tayi da shi.
Bata da ikon shiga cikinsu, sai kyara da tsangwama, a gefe guda tana da kawayenta da suke mata kaiwa da komowa. Wannan yasa baki daya bata yi wasa wurin rike wuyarshi ba.
Yanzu shekararsu bakwai kenan, sannan ya ɗauke ta zuwa lagos, akan Gimbi Saifullahi-Khalid ya rabu da kowa abin tausayi har uwar da ta haife shi.
Kowani gefe kuwa kokuwar ya dawo da shi tsaginsa yake, a wannan lokacin Aunty Mariya ta shirya mishi zancen aure ne, domin yana yawan kiranta, ita ɗaya ce bata rabu da shi ba, akan Gimbi sai da ya zane Basmah saboda sun yi faɗa da Gimbi.
Itama kuma Gimbi fadar da suka yi tayi alƙawarin ajiye Basmah a wuri guda, mijin da zata aura yayi hatsari wanda shirin Gimbi ne, sannan ta bakantata a idanun masu niman aurenta. ....