002
by @jeeddah3256
*KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)
NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU
#Love Story
#Gwagwarmaya
#Team Tagwaye novels
002.
Banda tsananin bugawa babu abunda zuciyarta keyi hoton cakawa yaya Abba wuƙa da ta yi ya kasa barin gilma mata cikin idanuwanta har, lokacin kuma ta kasa yiwa Hafeez bayani da ya gaji da tuki ya gangara gefen titi ya yi parking motar tare da kasheta duka. A hasale ya juyo yana faɗin."ki yi min bayani Sadiya kinbar zuciyata acikin duhu da tashin hankali da tunani ki faɗamin ina mijinki da kika fito cikin wannan dare?""na kashe sa Hafeez!" kalmomin da suka fito da kyar daga bakinta kallonta yake with so much shock acikin fuskarsa tamkar da wani yare ta yi masa magana "Na kashesa Hafeez da gaske bazan iya rayuwar aure da yaya Abba ba. Zan iya mutuwa idan muna zaune a gida daya dashi ba zai iya jure hakan ba. Wallahi zuciyata ba zata iya jurewa ba, ban taɓa yi masa soyayyar aure ba, baya ga ta yan uwantaka wanda nake hangosa a matsayin yayana wanda muke uba ɗaya dashi na rasa Meyasa Daddy yayi tunanin haɗamu aure dashi. Lokaci ɗaya Daddy ya rusa dangantakar dake tsakanina da yaya Abba."ta ƙarasa maganar cikin shesshekar kuka dan ko kaɗan bata hango shock din dake kwance cikin fuskar Hafeez sale ba. Hafeez ya haɗiye wasu busassu miyau a hankalinsa ya yi mugun tashi
"Sadiya kin fara shaye-shaye ne daman?"Hafeez ya faɗa cikin rawar murya, girgiza masa kai kurum ta shiga yi ga baki ɗaya abirkice take. Tasan labarin mutuwar Yaya AB ya riga ya zagaye duk wanda yake da alaƙa dashi "kisan kai ki ka yi akan wani banza tunani naki."Hafeez ya faɗa sounding so very harsh duk da ya fahimci ko kaɗan bata cikin natsuwarta lokacin jin yake kamar ya kwaɗawa Sadiya mari kifa kansa ya yi jikin sitiyarin mota yana ambaton Allah a ransa yama rasa kalar tunanin da ya kamata yayi a wannan lokacin
Sun fi minti goma a haka babu mai magana a cikinsu sai shesshekar kukan Sadiya dake tashi a motar mai ciked a danasanin abinda ta aikata tare da hango makomar rayuwarta, ta tabbatar itama kasheta za ayi tada motar Hafeez yayi batare da ya sake yiwa Sadiya magana ba, ya harbata kan titi bai tsaya da ita ko'ina ba sai cikin harabar Bon hotel ya kashe mota Sadiya ta ɗago rinannun idanuwnta tana ƙarewa harabar wurin kallo, duk da bata cikin natsuwarta ta gane hotel ne Hafeez ya kawota wani irin mummunan faɗuwa gabanta ya yi.
Tunda take a rayuwarta ƙafarta bata taɓa tako cikin hotel ba tun tana budurwa, ballantana yanzu da aure akanta ace ta shigo hotel da tsohon saurayinta ganin bata motsa daga inda take ba sai bin Hafeez ɗin take da kallo cike da gajiya a muryarsa yake faɗin."muje mu kama ɗaki Sadiya mu samu mafita kinga yanzu dare yayi ban san inda zan ajeki ba bayaga nan,
Jiki sabule ta balle marfin motar tabi bayansa har zuwa cikin reception ɗin
Ya kama masu ɗakin da zasu sauka su tattauna dan yasan babu maganar su kwanta suyi bacci daga ita har shi.
Tana tsaye tana kallonsa har ya dawo da key a hannunsa ya kalleta yana faɗin suje babu musu tabi bayansa cikin wani irin sanyi jiki da kansa ya buɗe ɗakin ya shiga sa'anan tabi bayansa ciki da parlor ne ta nemi kujera mai cin mutum ɗaya ta sulale ta zauna tana jin tsoro da tashin hankali na cika zuciyarta lokaci ɗaya.
Dafe kansa Hafeez yayi da duka hannunsa biyu ya rasa ma wane kalar tunani zaiyi tabbas mata duka ragaggen tunani ne dasu idan banda hauka taya zatayi kisan kai bancin tasan itama kasheta za ayi.
"Sadiya ya zama dole gobe kije ki gurfana agaban iyayenki ki nemi gafarar su bamu da tabbas akan AB ɗin ya mutu ko yana raye.
A wani irin razane take faɗin."Na koma kace Daddy ya yankani Nima?"meyasa baka fahimta saboda son da nake yi maka na kasa karɓar yaya Abba a matsayin mijina, na kasa karɓar ƙaddarar zama gidansa, idan har soyayyar da kake min da gaske ne bai kamata kace na koma gidanmu cikin wannan yanayin ba Hafeez."baki buɗe Hafeez ke kallonta to me kike so nayi?"so kike na gudu dake muje wani wurin muyi aure ko yaya?"ke idan zaki iya barin iyayenki ni bazan iya barin nawa iyayen ba. kallonsa kawai sadiya keyi a wannan lokacin tana mamakin kalaman dake fitowa daga bakin Hafeez din.
"ke kin san dole idan aka wayi gari akaji mutuwar AB acikin garin Kano dole a shiga nemanki so ki ke ki jamin masifa Sadiya ina zaman zamana."na faɗa maki gobe da safe zan kai ki gaban iyayenki ko ki hau adaidaita sahu ki tafi da kanki kar ma aganmu a tare a ɗauka da haɗin bakina kika kashesa. Ki tashi ki shiga ciki ki barmin parlorn, kallon Hafeez take tamkar bashi ba duk yabi ya sauya shin ina soyayyar da yake ikirarin yana yimata?
"Sadiya ki daina yimin irin wannan kallon. miƙewa Sadiya tayi ta nufi cikin bedroom ɗin gefen bed ta zauna ta dafe kanta tana tunanin makomar rayuwarta mai cike da na sani tasan 'yan gidansu yanzu sun tsaneta duka kannenta da iyayenta, duk akan Abba Bashir."tun farko ban amince da wannan auren ba Daddy meyesa kazo ka lalata komai sadiiya ta ƙarasa maganar tana danna kanta ciki pillow ta saki wani irin kuka mai girgiza zuciya da ruhi.
Daga Daddy har Hajiya mariya wacce yaranta suke kira mami tsaye suke a bakin emagency suna ganin yadda likitoci ke kai da kawo, batareda an masu bayanin wane hali Abban yake ciki ba saboda tashin hankali suna wurin a tsaye har qarfe huɗu na a asuba, sauro kuwa duk ya gama canye naman jikinsu dan basu mabi ta kansa ba tashin hankali bai sa sunji cizon da yake masu ba. Hawaye na zuba a idanu Mami tana addu'ar Allah ya tashi kafaɗun Abba, idan suka rasa Abba batasan wane hali zasu shiga ba. wani babban likita ne ya fito daga ɗakin da Abba ,yake ciki da sauri Alh Bashir ya nufesa cikin sauri da rawar murya yake faɗin."likita ya jikin nasa?"girgiza kai matashin likitan yayi yace su samesa a office ga baki ɗaya har Abdulkarim da yake tare dasu suka bi likitan kowa jikinsa a mugun sanyayye, bayani likita yayi masu wanda da kyar da taimakon Allah Abba,ya tsira da rayuwarsa sai dai yaji mugun rauni acikinsa sun masa allurar bacci daga Daddy har Mami wata irin ajiyar zuciya suka shiga saukewa a boye shima Abdulkarim sai lokacin ya samu ya dawo cikin natsuwarsa banda tsinewa Sadiya babu abunda yake a aransa
Abdulkarim ya kalli Daddy yana faɗin."suje gida kafin washe gari zai zauna da Abba ɗin, suna mota Mami taga kiran siyama ya shigo a wayarta
daman ta fito da ita ne koda wani zai kira acikinsu, lokacin karfe biyar da rabi na asuba mami ta dauka cike da ƙarfin hali tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta."Mami ina kika je keda Daddy?"meya faru?"Siyama duk ta ruɗe.
"gamu nan kan hanya siyama da haka mami ta katse wayar har suka kai gida daga Mami har Daddy kowa da abunda ke cin zuciyarsa gashi har lokacin likita bai basu damar ganin yaron nasu ba, zaune suka tarar da Siyama a parlorn da kayan bacci riga da wando masu kauri ajikinta tana ganin iyayen nata ta nufosu tana tambayarsu lafiya.?"mami ce tayi ƙarfin halin faɗin.yayansu ne babu lafiya Amman da sauki siyama ta dafe kirji zuciyarta na bugawa take faɗin."meya samu yayanmu Mami?"nan take Siyama ta ruɗe
"Na faɗa maki da sauki. Dama Daddy ko tsayawa baiyi ba ya nufi bangarensa kai tsaye yana tunanin hukuncin da zai yankewa Sadiya wannan lokacin, ba dai shi zata wulaƙanta ta tozarta ba."ina Aydah?"kema mami kin san tana can buɗe da baki tana baccin musamman yanzu da ba sallah zatayi ba.
"To kije kiyi shirye-shirye sallah da kin gama ki tasheta kuzo mu haɗu kitchen mu haɗa breakfast na kaiwa yayanku."da haka mami itama ta nufi bangarenta suna gama sallah daga Mami har ya'yan nata kai tsaye kitchen suka nufa suka fara shirye shiryen dora breakfast da yar aikinsu a gefe. Aydah sai turo baki take ganin an katse mata baccinta daman yan biki tun Jiya kowa ya kama gabansa daman babu wanda ya faɗawa Aydah Ab na hospital har suka gama break fast kowa ya nufi ɗakinsa dan yin wanka tun kafin su wuce Mami ta kalli Aydah dan tasan tana iya komawa bacci dan tasan halinta da shegen son bacci "karki koma baccin asara wanka za kiyi ki fito muje asibiti.
Sai lokacin Aydah ta dawo gaban Mami duk a tsorace take "Mami waye babu lafiya?"
Ta faɗa tana ƙoƙarin fashewa Mami da kuka, Mami ta sakar mata da harara tana faɗin."kefa dadina dake sakarya ce.
"To Mami waye babu lafiya?"
Aydah ta faɗa hawaye sun cika idanuwanta lokaci ɗaya dama ita ce mai rauni acikinsu kuma ita ce autar Mami.
"Yayanku ne.
Kuka Aydah ta fashe dashi lokaci ɗaya duk tabi ta rikicewa Mami tana faɗin "meya same sa Mami?
Duk Aydah ta rude ta fita hayyacinta daman duk cikin kannen Ab yafi shaƙuwa da ita tasu kuma tafi zuwa ɗaya idan kana son kaga bacin ran Ab a gidan to ka taɓa masa Aydah, komai Aydah ta samu yayansu shima komai ya samu na Aydah ne, haka Siyama da Sadiya ke jin haushinsa Mami tayi tai masa faɗa tace ya daina nuna bambanci a tsakani kannensa haka zai cewa mami ya daina gobe kuma ya ci-gaba.
Aydah na wanka tana kuka duk tabi ta firgice tana ta tunanin wane irin ciwo ne zai kwantar da yayansu daren Jiya daren angwancinsa cikinsu daga Mami har Daddy babu wanda ya faɗa masu asalin meya samu Abba ɗin.
Siyama ta daɗe da shiryawa tana zaune tana jiran fitowar Mami takun stairs taji ta dauka Mami ce sai taga Aydah ce ta fito sanye da hijab har kasa kallonta kawai siyama keyi har ta ƙaraso tana tambayar mami bata fito ba ?"Siyama ta tallabe cheeks ɗinta cike da matsananciyar damuwa dauke a fuskarta take faɗin."Nima ita nake jira.
Juyawa Aydah tayi ta koma sama dan duba Mami idan ta shirya ga baki ɗaya ta ƙagu ta ganta asibiti wurin yayansu da Mami taci karo saura kaɗan su bugu Mami taja da baya a tsawace ta ce "wai meyasa bakida natsuwa ne ko kaɗan kina tafiya sharaf -sharaf bakya duba gabanki,
Ko yaushe baki tafiya a natse.
Mami ta faɗa tamkar zata rufe Aydah da duka.
Baki Aydah ta turo tana bai wa Mami haƙuri ta juya ta koma parlorn, Mami ta ja tsaki tabi bayanta daman Daddy yana fitowa masallaci asibitin ya koma ,Mami ce take tuƙasu a mota har zuwa asibitin daidai su Mami suna fita lokacin kuma Hafeez ya ƙaraso da sadiya a ƙofar gidansu.
#Love Story 2023/2024
#Jiddah Aliyu
#Asmy b Aliyu
#Team tagwaye novels
#Kurman Allo.