NI DA YAYA ARMAN

11-12

by @autarmama

*NI DA YAYA ARMAN* 🍏

Hot love story♥️🔐


```MALLAKAR```

*Hajara L Sadeq*


📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚


بسم الله الر حمن الر حين


*BOOK ONE*📔

🅿️...............11&12



....." Malam wa ya baka izinin d'aukar yarinyar Chan a mota?cikin gaskiyarshi saurayin ya ce "Kayi hakuri na ganta ne a hanya ta rasa abun hawa shine na rage mata hanya kuma sonta nake ba son yaudara ba so na Aure Dan tunda na ganta Naji ta tafi da imani na " Wani irin wawan kallo ARMAN ya gallamai ji yake kamar ya shakeshi ta maza kawai yayi ya ce "Matar Aure ce Dan haka karka k'ara bibiyarta ko kaji a ranka kana sonta Wata alaka ta k'ara shiga tsakaninku zan kulleka hope ka gane ya na gama fad'ar haka ya juya ya shige ciki shiko saurayin sosai yayi mamakin jin cewar Matar Aure ce har yana murna yayi Babban kamu cike da jin haushi ya juya.








Aira ko ta na shiga Bangaren inna ta yi sai rarraba idanu take kamar wata marar Gaskiya Daga Amma sai inna a palourn Amma nayiwa Inna Karin karatu tsaye tayi jikin Bango ta kasa ko motsawa ta na haka ARMAN ya shigo daga ganinshi.kasan ranshi yayi mugun b'aci kanta yayi gadan gadan kafin ta juya ya chafkota Cikin zafin nama ya murde mata kunne k'ara ta saki Dan taji zafi sosai Karanta ta jawo da hankalinsu Amma cike da masifa ya ce " Uban waye wancen d'in Wanda ya saukeki a mota "Cikin kuka Aira ta ce " Yaya nima bansanshiba Dan Allah kayi hakuri Bazan sakeba ka sakarmun kunne da zafi"








"ke harkinyi girman da zakishiga motar wani k'ato ko ?ina alkawarinmu dake daman idan bana nan irin abunda kike ko?k'ara fashewa tayi da kuka ta ce "a a yaya wlh yau dinma tsautsayine" Sakin murdewar yayi tare da wurgata ta durkushe ta fasa kuka mai tab'a zuciya har cikin ranshi yake jin kukan nata ganin irin kukan da take ya sanyashi sanyaya zuciyarshi dan ba abunda ya tsana sama da kukan Aira Shima durkusawar yayi cikin kwantar da murya ya ruko hannunta ya ce "Sorry " Bama ta saurareshi ba saici gaba da kukanta da tayi murza hannayenta ya fara ya ce "Sorry my cutie bazan sakeba kema karki sake kinji kinsan banason ganinki da kowani d'a namiji shiyasa na kasa control d'in zcyta please karki sake in baso kike zuciyata ta tarwatse ba " Rungumeshi tayi cikin kuka ta ce "Bazan sake ba yaya kayi hakuri " Shafa bayanta yafara nan ya fara Lallashinta kamar ba shine ya gama zafutartaba.






Inna ko da Amma suna nan suna kallon Ikon Allah "Murmushin jin dad'i inna ta yi ta ce " Allah nagode maka Tabbas mafarkina ya kusa zama Gaskiya Allah cikamun burina na ganin Auren Hajara da Muhajid Tabbas nasan ta silar hakan ne kad'ai za a iya samun sulhu tsakanin iyayensu.








Da misalin k'arfe 10 na dare Aira sanye take cikin kayan bacci Nan ta d'auko wayarta ta ta boye cikin locker ta fiddota ta bud'e data nan tayi ta ganin message d'in mutane na shigowa frnds d'inta na mata congrats Number yaya Arman da tayi save da "My yaya ta shiga taga rabonshi da online one.week kenan Hakanan kawai tayi mai slm Dan daman ya fad'a mata shi chat bai dameshiba gwarama Twitter yana shiga yaga labarai.






Amma ce ta shigo d'akin Aira bata lura ba maza tayi zata boye wayar da sosai ta tsorata Ta ce " Amma Me kikazo yi"Cikin in ina take maganar murmushi kawai amma tayi ta zauna ta ce "hmm Aira kenan ni bantaba tunanin akwai abunda zaki iya b'oye munba Kinsan tun muna yara bama boyewa junanmu komai kuma muna rik'ewa junanmu sirrikanmu to me yasa kwanannan kike neman chanzamun kinsan dai ko mutum muka kashe bamaiji" Ajiyar zuciya Aira ta sauke tasan hakane tun suna yara basa b'oyewa junansu komai a hankali ta ce "Sorry sis "ya wuce amma ta ce sannan ta Amsa wayar hannun Aira ta ce " Wow Sis 13 ce fa "Dariya Aira tayi ta ce " Kina mamaki ne "Sannan taje ta rufo kofar Dan kar Wanda ya shigo " Amma ta ce wa ya baki 13 Aira "yaya Arman ta bata amsa kai tsare dare da dawowa ta zauna" Arman "Amma ta fada sannan ta ce "Kai amma Allah yiwa Yaya Arman albarka Gaskiya Yaya ARMAN ba k'aramun sonki yake ba Aira" wara idanu Aira tayi ta ce "So fa kikace sis" So kuwa sis Arman ya jima da fara sonki fahimta ce kawai bakiyiba amma Arman ba k'aramun so yake maki ba ko ince kuke yiwa junanku.








"kamo hannunta Aira ta yi ta ce " sis kina nufin yaya Arman sona yake"kwarai kuwa Ke wace irice Aira da baki gane so ,baki ganin kishinki b'arob'aro a idanunshi Abunda ya faru dazu ma Kad'ai ya isa ya k'ara tabbatar maki da irin son da Arman yake maki Bayan nan ma alamomin soyayyarki da yake gwada maki a fili suke ba a boye ba Aira ko k'aramun yaro zai iya fahimtar soyayyar dake tsakaninku ni a zato na kinjima da ganewa kiyi tunani ki gani".








Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da lulawa duniyar tunani tun daga rayuwarsu ta baya har zuwa yanzu ,me yasa a cikin gidan ita kadai yake sakewa,me yasa ita kadai yake farantawa,ita kadai ya damu da ita,ita kadai yake kishinta ita kadai da dama Tabbas sai yanzu ta gane Yaya Arman sonta yake sosai gabanta ya fad'i kallon Amma tayi tace "To sis ni kuma ina sonshi? Ta k'arasa fad'a cikin sigar shagwaba Dariya Amma tayi sosai ta ce .








" ke sis wlh baki rabo da abun Dariya ni zaki tambaya ai zuciyarki zaki tambaya"Turo baki tayi ta ce "To fad'amun menene alamomin so?Alamomin so suna da yawa Aira Amma zanfada maki Kad'an daga cikinsu saiki duba kiga idan kina daga cikinsu " Shak'uwa tayi yawa tana daga cikin Alamun so,damuwa da halin da dayan ku yake ciki "Damuwa da rashinshi a kusa dake koda kuwa na y'an dak'ik'a ne,kishi,shine babbar alamar Zurmiya a cikin soyayya,kyautatawa,ko da yaushe idan kika kalleshi kiji farinciki ya mamaye zuciyarki koda kuwa a waya Ne,jin bazaki iya rabuwa dashi ba duk rintsi duk wuya " ga sunan da yawa Aira kiyi tunani.






Shiru tayi tare da Zurmiyawa duniyar tunani Tabbas inko hakane so ta jima da afkawa kogin soyayyar yaya Arman soyayyarma ba ta wasaba cike da damuwa ta ce "Tabbas sis najima da Fara son yaya Arman koma Ince da soyayyarshi na ginu tun bansan kaina ba nakejin Duka abubuwan nan da kika lissafo game dashi ina tsananin sonshi son ma bana wasa ba a da haukana na d'auka duk wannan din shakuwa ce saida kika lissafo nagane Abunda ake nufi da so da Chan shirmen banza na kawai nake sannan ta kamo hannun ta tace.










" Sis ya zanyi help me please ina sonshi sosai ya zanyi kin tabbata shima yana sona"Cike da tausayin y'ar uwar tata ta ce "Karki damu sis son da yake maki ya linka son da kike mashi Wanda na gani a idanuna kedai kawai ki bari har zuwa lokacin da zai furta miki" Hakika indai kika samu Yaya Arman sis kingama samun wani jin dad'i a duniya Dan nasan zaiyi wuya a samu Wanda zai kula dake ya nuna maki tsantsar k'auna da soyayya Bayan yaya Arman Dan Arman mutum ne da kowace mace ta sameshi ta more ,Abu d'aya kawai nake Tsoro kuma nake jiye muku Iyayenmu na tabbata Abba Da Daddy bazasu tab'a yarda Kuyi Aure ba inba wani ikon na ubangiji ba shine Babban abunda yake tsoratani"Hawaye sosai Aira take ta ce "Ina sonshi sis Bazan yarda a rabamu dashi ba Abba bazai iya rabamu ba Inajin da sonshi aka halicceni a yanzu bana jin tsoro ko shakkun komai da zan tunkara indai akan a rabamu da yaya Arman ne na gwammace Ranar na mutu".










ta fad'a tana fashewa da kuka " Sosai Amma ta tausayawa y'ar uwar tata Rungumeta tayi ta ce "Insha Allahu sis babu mai rabaku sai mutuwa nan tayi ta Lallashinta ranar daki daya suka kwana Wanda Aira baccci kauracewa idanunta yayi sakat tunanin Arman ya hanata bacci da kalaman y'ar uwarta Tabbas tasan indai hakane so to baiyi mata kamun wasa ba yayi mata kamun da ita kanta bazata iya control d'in zuciyarta ba sai Bayan asuba bacci ya d'auketa hakan yasa washegari tayi ranar bacci sai 12 ta tashi.






©©©©©©©©©©©©©




B'angaren Arman Shima hakan ta kasance Dan Sosai yakejin son Aira a ranshi Wanda shi kanshi bazai iya kwatanta shi da komai ba Sosai yakejin Haushi idan ya tuno ganinta da yayi da wani a tsaye tunani yake akan ya fito ya furtawa Aira abunda ke ranshi koko ?zata amince dani ko akasin haka? Ta na sona kamar yanda nake sonta ko har yanzu Kallon yaya takemun?Daren ranar bacci kauracewa Idanunshi yayi Yasan son Da yakewa Aira daga Allah ne Dan koda bai shiga zuciyar zukatan masoya ba yaji yanda sukejiba ya tabbata son da yake yiwa Airanshi babu wani mahaluk'in masoyin da zai iya yiwa masoyiyarshi kalarshi ba.






Washegari jiki ba kwari ya tashi koda mumy ta tambayeshi lafiyanshi qlau kawai yace mata nan take fad'a mashi Daddynshi jirginsu ya taso tun d'azu sun kusa isowa sai sannan ya d'anji sanyi sanyi a ranshi Dan sosai yakeson ganin Daddy Mummy tace yaje ya shirya nan da 30 minutes zai k'arasa.






Arman da kanshi shida Mummy suka taryo Daddy daga Airport Hannun Daddy rik'e da na Arman Dan ko Wanda bai saniba yasan irin tsananin son da Daddy ke yiwa Arman kasancewarshi shi d'aya tilon d'anshi a duniya.






Bayan Daddy ya huta yaci abinci Mummy sai Nan nan take da mijin nata Kallon Arman yayi ya ce "Son ya London d'in Fatan ka dawo lafiya" Lfyqlau Daddy "Masha Allah yaushe kuma zaka koma wajen Aikin naka" ran Monday sukace Daddy nama zata zasu d'an bani Hutu tunda kaga su suka turani London d'in nadawo na zata sunbani ko hutun 2weeks ne amma jiya sun kirani suke ceman Monday suke Son na koma"Dafa kanshi Dady yayi ya ce "Toh nan kusa kenan Kaga yau muna Friday to Allah ya kaimu Monday din Ai nasan d'ana jarumine Shiyasa basason suyi missing d'in aikishi ".








Murmushi Arman yayi Dan sosai yakejin dad'in yanda Daddy kullum ke kod'ashi shi d'anshi jarumine jajirtaccene tun yana yaro haka yake cemashi shi jarumine Ranar Yini sukayi suna Hira da Daddy Dan ko gidan Inna bai lek'a ba Yau cikin hirar ne yake cewa "Daddy Inna na ta nemanka" murmushi yayi ya ce "Insha Allahu gobe idan na huta zanje na gaisheta.








Washegari Daddy da Arman su kaje ya gaishe da Inna shida Security d'inshi Wanda koda yaushe suna biye dashi Arman bai samu ganin Aira ba dan Inna tace mai suna makaranta kasancewar da safe sukaje daga Chan suka wuce asibitoci Dan duba marassa lafiya sannan yayi musu alheri sosai wannan na Daga cikin abunda yasa mutanen jahar suke tsananin sonshi da son mulkinshi danshi mutum ne mai kirki da kuma tausayi ga Gaskiya da rukon amana.






Ran Sunday da dare Arman ya je gidan Inna Dan bankwana da Airanshi koda ya fad'a mata zai koma wajen Aiki kuka ta sanya mashi ita batason yake nesa da ita dak'yal ya lallab'ata yace zasu dinga Video call kullum kuma suna waya duk saiyaji bayason ma Tafiyar Dan dai ya zama dole Amma shi Zama da Airan shi ya fiye da mashi komai.






Tunda Arman ya tafi kullum cikin waya suke da video call kamar ma suna tare Aira suncigaba da Jarabawarsu ta neco ita da Amma sosai suka maida hankalinsu ga karatunsu har yanzu babu Wanda yasan da wayar Aira a cikin gidan Bayan Amma koda yaushe son Arman Kara ninkuwa yake a cikin Zuciyarta.








Ranar da Arman ya cika sati Biyu da tafiya Ranar Su Aira suka gama neco d'insu sai farinciki suke suda class mate d'insu ana tashan hotuna a wayar Aira nan Duk wasu suka amshi numbobinta ranar ji suke kamar karsu rabu daga karshe suka sha kuka musamman Aira ita da frnds d'inta Khady bestynta sosai suka shaku koda yaushe a school tare suke yawo nan sukayiwa juna Alk'awarin ziyartar juna akai akai Sai wajejen 6 suka gama hotuna da bankwana suka fito Bakin gate domin tafiya gida Suna fitowa Wata wulfefiyar Mota Fara me masifar kyau Aira ta gani parke .








Ganin mai fitowar ne ya sanyata wara idanu sosai yayi cikin sky blue din shadda ta tasha Aiki hular kanshi hadaddiya wadda a k'alla zata kai 100k Rungume yake da hannayenshi da suke sanye da Wrist din zinare kara wara idanu tayi Dan tabbatarwa da shi d'inne koko Gizau ne shiko kafeta yayi da idanu murmushi kawai yake sakar mata sosai tayi mashi kyau cikin unifoam dinta Light blue Hijab da Dark blue din wando y'ar k'aramar hijab dinta tare da rafar rigarta da ta sauko har gwuiya anyi mata hular hijab d'in da yadin wandon jelar rigarma haka ji yake Kamar ya je ya rungumota Aira ganin da gaske shi d'inne de gabanta ai batasan lokacin da ta saki Hannun Khady ba ta ruga a guje tayi wajenshi tare da Rungumeshi tama mance ta tsiraran mutanen class d'insu dake wajen Cike da murna da farincikin ganinshi ta ce My yaya........✍🏿




*Share fisabilillah*



*_Miss Hajo ce*_🤙🏿