Chapter 21
by @maidambu41
*BAƘIN HAURE....🐾🐾*
{Greed for Money is the roots of all evils🫀}
Arewabooks:maidambu41
Wattpad:Mai_Dambu
Mallakar:Mai_Dambu
*021*
Ni dai ba zancen ga abinda ya faru ba, sai da gari yayi haske sannan muka fahimci dayawanmu, sun b'ata a sahara. Shafa baby nayi na ganta a bayana har lokacin, ajiyar zuciya na sauke tare da fara niman hanyar fita, a hankali nake tafiya ina niman Ummi ashe guguwar tayi gaba da ita can, mune yan baya da abin ya fi ritsawa da mu, don haka a hankali muka yi ta bayyana daya bayan daya, muka isa inda suke jiran mu, kafin wani lokaci mun sake haduwa sai dai ba dukkanmu aka kuma haduwa ba, wasu sun bace wasu kuma sai gawarwakinsu. Da sassarfa uwar mugu ta amshi Baby. "Da fatan babu abinda ya same ta?" Girgza kai nayi ina son tambayarta Addah. "Duk suna lafiya, karfin tsayawarmu anan kece, domin Yallabai yace ba zai bar nan ba, sai an samo mishi ke da Baby." Ta cigaba da duba yarinyar har wurin shi, amsarta yayi ya hure mata fuska saboda yan kuran da suke fuskarta.
Haka muka cigaba da tafiya har sai da muka ji babu dad'i, domin wasu sun tafi, bamu tsaya ba sai da rana ta faɗi, a wani ƙaramin gari, tun kafin mu shiga garin na fahimci mutanen garin suna maraba da zuwanshi, garin dauke yake da kabilu biyu, hausa da fulani, domin ga alamu sune suka kafa garin. Sannan kowa ka gani yana da abin yi, ma'ana Babu wanda zaka gani yana zaune haka. Gaishe shi ake yana amsawa har muka bar cikin kauyen muka kara nausa daji, anan ne na fa kara yarda Allah daya gari Banban. Dajin da muka nufa gona ce ni nace lambu, babu irin shukar da babu a cikinshi, sannan akwai cigaban zamani. Lokacin da muka isa wucewa damu aka yi wasu gidajen da suke zagaye da wani gida can, gaba da gidanshi. Yanayin gidan kamar irin dakunan kwanan dalibai ne, gado da katifa har da bargo. Kwanciya muka yi barci yayi gaba damu.
***
Niamey.
Suna kwance wuri guda, hannunsu sarkafe da juna. Kana ganinsu kasan lovers ne na gayawa yan gari. "My heart meke damunka?" "Hmmm! Kudi naje hajiya ta bani ta hanani, raina a b'aci na zo nan." Shafa kanshi Sajjid yayi yana faɗin. "Kamar nawa?" Mikewa yayi yana faɗin. "A'a ka barshi zan tafi na sayar da motata." "Kana dani kace zaka sayar da motarka, baka yarda ina sonka ba ne? Kasan yadda iyayenmu suke gaba da juna amma kake tsammanin zan iya rayuwa babu kai? Ko wancan mutumin gidanku ba zan tab'a yafe mishi ba."
"Idan na yafewa kowa, Majid ba zan yafe mishi ba, sai na saka shi biyan abinda ya aikata." Sai da Sajjid ya gama hasala Amaan Mamman Ba'are, sannan ya dauki kudi masu yawan gaske, ya bashi ya kai hannu fuskarshi. "Kayi hakuri nasan Aryan da Majid yan uwanka ne, amma ina matuƙar jin haushinsu, ina ta kokarin koyawa kaina dauke kai akansu amma na kasa. Ka gafarce ni." Sajjid ya faɗa kamar zaiyi kuka, a rikice Amaan ya rungume shi. "Zan taya ka lallubar hanyar da zamu ga bayansu."
"Allah!"
"Da gaske zan iya kome matukar zaka yi farinciki." Murmushi Sajjid yayi yana faɗin. "Ban yarda ba, don na baka kudi kake fadar haka." Mai da mishi kudin yayi yana faɗin. "Bana bukatar kuɗinka, lokaci zai nuna maka ina sonka ne don Allah ko kudinka."
Murmushi Sajjid yayi yana juya idanu ya ce mishi. "Dauka ka tafi nasan kana sona ne don Allah, wasa nake maka." Ya fada yana cusa mishi kudin tare da mishi chakulkuli. Dariya suka saka bakiɗayansu. Sai da suka yi wanka sannan Sajjid ya raka Amaan har wurin Motarshi ya bar gidan, kiran Mahaifiyarshi yayi yana faɗin. "Jakin yaron nan ya faɗa fa!" Ajiyar zuciya Tani tayi ta ce mishi. "Ban yarda zai iya mana wani aiki ba, ka dawo haka ina son ganinka."
"An gama!" Ya fada yana shafa ciwon da yake goshinsa. "Kada ka dauki lokaci." "Tow." Ajiye wayar yayi yana hararar shi, tabbas idan ya samu hali sai Hajiya Tani ta biya abinda ta aikata, ba ita ta haife shi ba ko ita ta halicce shi sai ya mata abinda ba zata manta da shi ba, kuma yanzu ma zai cigaba da mata biyayya. Tun yana Yaro take azabtar da rayuwarshi har girmanshi bai huta ba, yanzu ma don yana da abu me muhimmanci ne ya barta take raye. Yasan duk wannan fadi tashin da yake ba don kanshi yake ba, iya ita kanta yake mata, sannan shu'umar mace ce ta gaske da ba zata iya daukar rainin hankali ba, yasan ita ce ta haife shi, amma baya tunanin zata iya d'aga mishi kafa, idan ya mata kuskure shi yasa a duk lokacin da yayi kuskure da girman shi sai ta illata shi.
Shi kuma a nashi tunanin yayi girman da dole ta daina dukarshi, domin yau da gobe ya wuce wasa, sannan ba zai cigaba da zuba mata idanu tana dukar shi ba.
--
Washe gari.
Hajiya ta hada kan Iyalanta zuwa Marad'i, har da Amaan yana Motarshi a baya, Hajiya da su Aryan suna mota daya, sai hira ake kamar yadda suka saba ana zolayar juna, Aryan ke tuka motar, shi yana zaune a gefen Aryan din, idanunshi rufe. *Ka taimaka min kada na mutu!* Bude idanunshi yayi yana kallon gefen hanya, tare da juyowa yana kallon su Hajiya da suke dariyar Widad, ta dage sai magana take tana mita. "Ya dai Hammayo?" "Babu kome." Tabbas yaji muryarta, amma kuma yasan don ya damu kanshi jiya da niman Umaimah bai samu number ta ba, asalima jiya har da mafarkin abinda ya faru, yana son ganin likitan da yake mishi therapy, lumshe idanun yayi cikin wata irin gajiya, domin baki daya yana jin wani sabon yanayi na kara kusanto shi, kara jingina yayi da motar, ya shafa fuskar wayar shi da aka sauya mata screen. A hankali ya gwada kiran Ammar. Ai kuwa yana shiga ya ƙara bude manyan idanunshi masu kyau da sheki. "Ammar ka nimo min number da zan samu Umaima."
"Ok Sir ya kake ya hutun naka."
"Alhamdulillahi! Sir sai muka ji labarin ba zaka dawo ba. Sir"
"Zamu yi magana an jima;" ya fada yana kashe wayar. "Wai da gaske ba zaka koma Nijeriya ba?" Inji Aryan, "I ba zan koma ba " ya faɗa yana kauda kanshi,karar da wayarshi tayi ya sa shi duba screen din wayar. Shiga kan message din yayi ya tura mishi. "Thanks!" Sannan ya danna number, can sai gashi ta shiga. "Ya yarinyar nan take?" "Eyeeeee!" Bakiɗaya suka zuba mishi idanun suna jiran abin da zai fada, "ok please ki bincika ina son sanin yadda take." "Amma ya kamata kayi min sallama sannan ka gaishe ni!" "Kin ga bani da." "Yes nasan baka da lokacin gaisuwa. Nima na bincika last month an ce an samu crisis a garinsu." Cikin wani tsuke fuska ya ce mata. "I don't care Koda ace garin babu kowa, ki nima min information akanta. Domin ina son sanin yadda take ne." "But niman abu kake sai nake jin babu dad'i kamar kana saka ni lallai sai na maka abinda." "Ok taimaka min" ya faɗa a gajiye da kuma son maganar ya ƙare. "Shi kenan zan bincika in sha Allah."
A hankali ya sauke wayar daga kunnenshi yana me fatan Allah yasa ba mutuwa tayi ta sanadin abinda ya farun nan ba, domin bai san me zai ce ba. Zufa ne ya shiga karyo mishi Aryan da Hajiya kuwa sun tsare shi da idanun suna son ƙarin bayani. Juyawa yayi ya ga yadda suka saki baki. "Wacece ita?" "Aaaah ba fa wani abu ba ne, kawai na mata treatment ne a gidana." Daga haka ya ja bakin shi shiru , duk yadda suka so yayi magana gum yayi da bakinshi. Zurfin ciki irin na Abdul Majid ai ya b'aci, ita kan Hajiya tayi mamakin yadda aka yi ya bukaci jin labarin wata. Tasan duk inda yake rayuwa bata taɓa jin labarin mace a tare da shi ba, duk da taso hada shi aure da Yar Kanwarta wato Zaytoonah, amma al'amarin yaƙi yiwuwa asalima tunda tayi mishi maganar aure bai kara yarda ya bada fuska ba, har suka isa marad'i bai ce uffan ba, itama bata kuma yarda tayi magana ba, sai da suka isa Gidan Alhaji Abubakar Abzin, dake ya tashi daga tsohuwar unguwar da suka san shi. Aryan kadai yasan unguwar da suka koma.
Sun same shi a gida, Hajiya na bayan Aryan ita da matar Aryan da Yaranshi, Majid yana mota yana waya. Suka shiga cikin gidan, yana kallon Amaan Mamman Ba'are ya fito tare da Matarshi, da Yaranshi sai lokacin ya bude motar shima ya fito suka kalli juna. "Hammayo ina wuni!!" "Lafiya!" Ya faɗa, don ya lura matar Amaan bata da nutsuwa da tarbiyya, yaran ma gasu nan kamar su kamar uwarsu, an musu shigar diban albarka. Dauke kai Amaan yayi, hala yana jiran Majid ya gaishe shi. "Daada ina kwana!" Inji Amir. Daukar Yaron Majid yayi, yana ce mishi. "Lafiya lau Amir Ba'are." "Daada kafi Abbanmu kyau, kuma ka fishi kirki." Murmushi yayi yana kallon Amaan din. "Baya daukarka ne?" Girgiza kai yayi yana faɗin "Daada kana dariya shi kuma baya dariya." Murmushi ne ya kwace mishi yana kara rike Yaron, da sallama suka shiga babban falon gidan. "Daada nima ka ɗauke ni." Inji little Abdul. Ajiye Amir yayi ya dauke shi yana dariya. "Abdul Majid kannenka sun maka wayo kaga sun tara zuri'a saura kai." Murmushi Iya tayi tana kallon Abdul Majid, ta nuna shi da sandarta tana faɗin. "In sha Allah, Matarshi da uku-uku zata cika mishi iyali."
Murmushi ne ya subucewa Hajiya, ta ce mishi. "Allahummah Amin, Iyah Allah ya yarda." Ta fada tana kallon Majid da yasa fuskar shanu. Wasa da hannun Abdul yake. "Captain Allah ya kawo mana kai kenan " murmushi yayi yana me sunkuyar da kanshi, "Eh Abba!" Kura mishi idanu Alhaji Abubakar Abzin yayi kafin ya ce. "Allah ya jikan Mamman da rahama! Ya yafe mishi kurakuransa."
"Allahummah Amin" suka fada baki daya,. Abincin da aka kawo musu, suka ci bayan an basu wuri. Bayan sun gama Hajiya suka shiga cikin gidan yan mazan suka nufi masallaci, basu dawo ba sai da aka yi la'asar sannan suka shigo, anan aka kara gaisawa sannan aka bude shafin hira. Kafin, suna hirar karamin D'an Alhaji Abubakar Abzin ya shigo. Mahdi Abubakar Abzin, sosa kai yayi yana faɗin. "Abba kayi hakuri don Allah." "Taya zan cigaba da barinka a matsayin lauyana? Dole na nemo wani da zai cika min alƙawari." "Ka kara hakuri dai Abba! Nifa ba zance ka biya ni ba, duk Lauyan da zaka dauka sai ka biya shi kudi me yawa." Daure fuska Alhaji yaji ya ce mishi. "idan har bukata zata biya ai shikenan babu matsala sai inbiya, amma meye amfanin badi ba rai? Meye amfanin ka tunda bana biyanka jeka ka ajiye min aikina." "Alhaji ni zan nima maka wani lauyan." "Bana so ai Ni ba makaho ba ne."
"Allah ya huci zuciyarka." Ya zauna yana dauko wasu jakakkuna ya ajiye, waya Alhaji Abubakar Abzin ya dauka yayi magana. Kafin ya ajiye. "Lauyan Mamman yana zuwa." Kallon shi Hajiya tayi sannan ta ce mishi. "Abba ban gane ba!" Kallon Majid yayi kafin ya ce mata. "Majid zan bawa hakkinshi sanadin rayuwa da mutuwa, sannan ga shi nan ya bukaci na yi mishi wani aiki." Sunkuyar da kai Majid yayi, yana murmushin farinciki, yau Allah ya kwace shi daga tarkon Hajiya.
Can Lauyan yazo, "Malam Sulaiman!" Murmushi yayi yana faɗin. "Na'am Soja marmari daga nesa." Kallon Aryan yayi ya Banka mishi harara. Murmushi yayi ya ce. "Ba zaka gane yadda rayuwa da mutuwa take ba, shi yasa kake min kallon munafiki." Gyaran murya Alhaji yayi sannan ya bude taron da Addu'a, kafin ya ciro wasu takardu ya mikawa Mahdi. Shi kuma ya mikawa Lauyar Mamman Ba'are, shi kuma ya mikawa Majid, ya amsa yana kallon Alhaji Abubakar Abzin, "takardun ka ne, tun lokacin da aka haifeka Mamman ya bude maka kamfani anan da katsina." Sunkuyar da kai yayi yana kallon kasa, "Alhaji Mamman Ba'are bai kyauta ba, amma kuma ya rayu da boye kaunarka domin kada a kassaraka. Ke kanki ni nace ya nisanta ki da iyalinshi domin nasan cewa zaki zame mishi alkhairi." Mikewa Aryan yayi ya ce."ku dakata!" Ya nufi Amaan, kamar wani dan sanda haka ya shiga caje shi ya fitar da kome daga waya har agogon hannunshi, da zobe hatta botir din kirjinshi, a hankali wani abu ya fado. "Hmm!" Hajiya tace tana kallon Amaan cike da takaici, haka Aryan ya fitar kome. "Ko zaki bani sarkar wuyarki?" Hajiya ta mikawa Matar Amaan hannu. "Tow" ganin yadda suka tsareta da idanun. Haka ta mika musu harda agogo da dan kunnenta. Aka fita da shi waje, "Amaan baka da kunya. Baka da kunya baka da kunya ba zan maka baki ba amma ina rokon Allah ya shirye ka." Ko tari bai yi ba, "Abba ka cigaba." Gyara zama yayi yana kallon Amaan cike da takaici. "wancan takardun naka ne, wannan kyauta ce bayan an haifeka ya samu alkhairi mai yawan gaske, haka yasa ya cire wanan ya ce na baka naka ne, Hajiya Abdul Majid ya nemi na baki wannan takardur kiyi hakuri ki fahince shi." Amsa tayi ta ga takardar sallama ce daga aiki. Kallonshi tayi tana faɗin. "Ban san me yasa ka yanke haka ba, amma nasan kana da hujja me karfi."
"Aryan zai rike matsayinki na Chairwoman zai zama Chairman na kamfanin Ba'are, Anisah zata rike matsayin CEO!" Kallon Abdul Majid suka yi, sunkuyar da kai yayi yasan sarai irin kallon da Aryan yake mishi. "Amaan zai rike board director. Sa'adatu kin girma da zaki hakura da wannan gwagwarmayar, Abdul Majid ya bukaci haka domin ki huta."
"Abba shi fa?" Kallonta yayi yana son fadar mata abin da Abdul Majid din ya yanke amma yana shakkar yadda zata dauka. Mahdi ya ce mata. "Zai tafi karatu ne jami'ar sojoji da yake kasar Afrika ta Kudu." Ji tayi harshen ta ya mata nauyi da tayi magana, tana son tayi magana amma ta kasa tilas tayi shiru tana kallon Majid, "kin san me yasa bai bawa Jamilah wani matsayi ba? Saboda ga takardar asibitin shi zata rike matsayin shugaban asibitin. Amaan Mamman Ba'are zai rike matsayinshi ne baki daya."
Ajiyar zuciya Hajiya take saukewa a kai akai, cikin Murmushi Lauya yace. "idan Hajiya ta ce zata bawa Aryan matsayinta sai an sakata gaba da magana amma da mai gayya me aiki ya daura wanda yake so zai yi wuya a samu matsala." "Wallahi haka ne!" Suka fada bakinsu a haɗe. "Abba Alhaji ya gama abin da ranshi yake so, nima ina niman izinin nayi wanda raina yake so!" Murmushi Alhaji Abubakar Abzin yayi yana faɗin. "Kiyi yadda kike so!" "Aure nake son yayi, kuma na zab'a mishi yarinyar da zai Aura.............
#Mai_Dambu